You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

waya muna zuwa ya bada umurnin itata koma dakin mahaifiyar ta ni kuma mama ta rikeni da yayana tun wanan lokacin ban kara jin wani magana a kan zancen ba.
Yanzu ina son matana ta koma dakin ta don ina son mu tafi tare saboda cikin jikinta da ke girma ba zanso barin ta nan ta haihu bana nan ba.
Hjy bata bari yakai zancen ba ta bude baki tace karana ke nan kakai wurin iyayyen ka ko ?
Hjy kiyi shiru nan ai yanzu ba karan ki ya kawo ba inhar kina da laifi zancen Alh dai muke son jin manufarshi nayin wanan hukuncin daya yanke ?
Kawu ya dago kai yana sallama kafin ya fara fadin lalai nayi hakan ne kan a zauna lafiya don banyi wanan abin da wani manufa a raina ba sai don karin zumuncin dake tsakani na da yan uwana koda bayan bana raye ne.
Sai kuma wanan yaron da ya dauko muna yar ahalulkitabi a matsayin mata yazo min da ita na duba gaban sa hakan ba zai haifar mashi da alfanu ba a rayuwan shi nan gaba
Liman yace haka Allah yace ayi Alh hakkun kayi gaskiya sai kawu yace ashe ni ban sani ba ita hjy yin hakan har wanan lokacin bai mata dadi ba.
Kai balarabe da mustapha ga baba nan zaune da ranshi tsohon yana jingine da sandan shi baiyi magana ba har lokaci kai kawai ya kada masu.
Ba zabi da baki na basu ba takarda na watsa da sunayen yarana mata da nake da niyar basu a lokacin diyan ya uwana.
Koba haka akayi shi a falin nan ba ya sake tambayan su suka amsa da hakane.
Yace daga baya jimmai ta tuma ta kafe bata yarda da auren shi umar ba da yarinyar nan tun kafin in basu takarda saida na kafa sharadin idan jummai tayi korafi akan auren nan a bakin auren ta.
Subbahanallahi liman ya furta kawu yace kwarai anan falon na fade shi gaban kowa jin haka jimmai ta yarda da hakan ta amince.
Saidai ashe bansan da manufa ta amincewa hakan ba azuciyanta na dauka daga ta fahinci abinda na hango nayi wanan hadin daga baya.
Saidai ashe ita a wurin ta ta dauki wanan abin gaba tsakanin ta da maimuna gata nan.
Yakai bayan yaron nan ya wuce da mayarshi ashe ta kafa mai sharadin banza kan idan yaje ya sako muna yar mutane da akai min alfarma aka dubi mutuncina akabamu.
Ita mai diya mace da aka cuta tana karama sosai a lokacin aka ba danta batayi koraglfin haka ba sai jummai ne zata kasa hakkuri ta rugumi kaddara har yakai yaran nan sun haifi diya uku acan batare da sanin mu ba anan .
Kullun na kira saidai suce suna lafiya yana zuwa kasan nan ya koma ba tare da ita ba duk bai fada muna sun samu karuwa a tsakanin su ba .
Ashe duk gudun mahaifiyar shi taji wanan yakw boye muna hakan koda suka dawo hakkurin hakan kawai ya bamu a lokacin nayi fada sosai dashi daga baya na fahinci abinda yake nufi da hakan.
Sun dawo gida fitinan mahaifiyar shi kan yarinyar nan sai karuwa yakeyi bata bar masa mata ta zauna lafiya ba haka kuma bata bar kishiyan ta sun zauna gidan nan lafiya ba.
Har takai ta kwashi yan uwan ta zuwa gidan yaran nan tayi tataki kan ta shirya zata aurowa danta mata da take bukatan shi da ita a duniyan nan.
Ba wani ya fada mun ba ya ciro wayan shi yana laluben yace kai balarabe shedane tare tsohuwar mu ta kiramu ta nuna muna video nan da yarinyar nan murja ta dauko na cin mutuncin da sukaje sukayi a gidan wai sunzo duban dakin da zasu saka yarsu.
Wanan dalilin yasa na kira yaran nace kowa ya dauki dan shi a zauna lafiya duk da na fada mata kafar yarinyar a gidan umar gashi fitan ta gidan nan nawa har abada ke nan.
Naga alaman ta amince da hakan kuma a zuciyar ta tunda zaman yarinyar nan gidan nan ba wani sauyi da suka samu kullun fitinane da uwar yar nan.
Har yau ban taba kiran su da sunan maimuna takawo min karan jimmai ba gata zaune amma ita a kullun cikin korafi take anmata dai an mata a gidan nan.
Kawun hjy ya nisa a lokacin yace jummai amma baki biyo halin mu ba wallahi tir da Allah waddai da wanan halin naki.
Keda kanki zaki hana rayuwan danki zaman lafiya don wani kudirin ki na baza can da kika sa azuciyar ki gareki wai farau kishiya jummai ?
Kawu da kubar wanan zancen don yarinyar nan ba zata koma gidan umar ba har abada shine abinda na yanke akan maganan nan mamu tace.
Kowa na falon ya kallo ta don jin abinda ta fada tace kwarai kawu hakkurina ya kare a kan hjy tunda kan auren nan yakai har hjy ta kira min da mahaifiyata da yar yawon duniya.
Subbahanallahi hjy da girman kike wanan furcin ga yar uwan ki ya kasance hakan gaskiya ne ai ba fade yakamata ki mataba illa shiryuwan Allah gareta.
Kawu balarabe yace a ina wanan zancen ya fito haka mara dadin ji kuma ?
Liman ne ya katse su da fadin salamu alaikum suka amsa masa yace da farko wanan al,amarin baiyi dadin ji ba ace babban gida irin na Alh mutumin da duk unguwan nan yaro da babba ake ganin mutuncin sa yau ace a halin sa ne ke wanan irin rikicin kamar gidan da babu adini a cikin sa.
Alh kaima kana da naka laifin a wani bangare a ina ka taba jin iyayyen sun samu ikon kwatar yarsu a hannun mijin ta ?
Wanan sai idan shi mai auren ya bude bakinsa yace bayayin auren ya fasa wanan ba sauran abin yi sai a raba auren.
Yanzu duk mu bar wanan zancen tunda ga ma,auratan a zaune gaban mu ya juya ya kalli yaya yace Umar Faruq kazo tafiya da matar kane a yanzu ?
Cikin ladabi yaya yace abinda nake so ke nan idan hakan zai samu a yanzu.
Amma idan zai tafi da ita sai an bani dama ya karbi nawa bukatan auren yar wurin sabuwa da nake son yayi.
Da sauri kawunta yace bukatan auren diyar sabuwa jummai kina da hankali kuwa a rayuwan ki son kan ki har yakaiki ki halaka kan ki da kan ki yaro suna zaman lafiya da matar shi zaki dauko zancen yar sabuwa da basu da tarbiya ki jefa a cikin ahali ki ?
Kawun nata yai mata tas a wurin yayan ta yana taya shi dole taja bakin ta tayi shiru don babu hanyar yin magana a wurin gareta kuma.
Yace ka dauki matarka ka tafi wanan magana ya kare a wurin nan yanzu don haka idan ka shirya daukan matar ka ka dauketa ku tafi.
Mamu tace ta bishi kuma a haka kawu ku tuna fa ba daku zata zauna ba dasu ne hjy kuma ba fasa abin nan zatayi ba ga yarinyar nan tana fadin haka ta fashe da kuka.
Jikin kowa a falon sanyi yayi a lokacin ganin mamu na kuka nima na fashe da kukan lokaci guda falin yayi tsit ana sauraren sautin kukan namu.
Kawun hjy yace kuyi hakkuri ansan an cuta maku ana makan cutarwa din don wanan bata da alaman fasa halinta tunda ta kulla da sabuwa.
Yanzu ai ga yarinyar nan a zaune itace ke zaman aure ba wani ba yana da kyau muji ra,ayin ta idan zata bi mijin ta su tafi a yanzu din.
Da sauri yaya ya dago kai kalli kawun hjy da idanuwan shi da suka kada sukai ja a cikin natsuwa yana fadin malam kada kuyi haka yanzu a lokacin nan da suke jin zafi da ciwo a zuciyar su don furcin mahaifiyar dataji kuma.
Kawun hjy yace umar ka kwantar da hankalin ka ba zabi bane hakan hakkintane itama za a bata don muji ra,ayinta a kanka yanzu.
Ya juyo gareni yace Fatima kiyi hakkuri ki daina kukan nan kiyayya a filin Allah da tozarci haka baida dadi ko kadan .
Fatima kindai ji hukuncin da muka yanke a gaban ki yanzu shin zaki bi mijin kine ku tafi koko wani shawara kika yanke a zuciyar ki ?
Kaina a duke ban dago ba sai hawaye nake yi ina tunane a zuciyana ra,ayin uwata da take kokarin kwato min yancina a gurin hjy zanbi koko tausayin mijina da yayana da suka koma kamar marayu zan bi yanzu.
Jin malam ya kara kiran sunana yana fadin Fatima ke muke saurare muji ra,ayin ki yasa na dago kai a hankali na kalli inda malam din yake a daidai wurin kuma yaya Umar din shima yake zaune a kasa.
Karab idanuwa na suka sarke a nasa ni yake kallo da jajayen idon sa da suka kade ko kiftasu bayayi a lokacin bashi kadai ba duk wanda ke falon a lokacin ido ya zuba min don jin me zan fada.

ZAINAB IDRIS MAKAWA
17/11/2021, 07:16 - 🤐🤐🤐: Na sake dukar da kaina a kasa ina dan sheshekan kuka kowa a wurin ya zuba min ido suna saurarena a lokacin.
Azuciyana sai faman tunane nake ba zan yarda in bi yaya a wanan lokacin ba don kwatar wa uwata martsnbata a gurin hjy dake ganin don abin hannun danta mamu ta zuga kawo ya cusa ni gareshi a nata tunanen ke nan ita.
Kowa yasa tsakanina da mahaifiyata akwai shakuwa da yawa wanda har mutane ke ganin bata kawaici a kaina irin da akewa dan fari don shakuwane sosai da aminci a tsakani na da mahaifiya ta.
Don shi kanshi yaya idan muna waya wani lokaci da mamu ya kance min shike nan kun koma aminai dake da mahaifiyar ki don na lura a cikin ki babu wanda take so kamar ki.
Nakan ce mai kasan banda Amma mamu bata da wani wanda suka shaku a baya yanzu ko Amma girma ya kamata dole wani shawaran dani zatayi shi.
Sannan ina tuna da namiji ba dan goyo bane in watsawa uwata kasa a ido yanzu a gaban jama,a yazo uwarshi ta tursasa shi yai auren da take so da wani ido zan kalli mahaifiya ta daga baya.
Kai Allah waddan naka ya lalace kan yar nan duk kabi ka susuce kanka a banza kamar itace autar mata a duniya.
Na rasa mai kagani a wurin yarinyar nan ka juye a lokaci haka babawo har suna daukan kansu su wata tsiyace yanzu muryan hjy ce kewa yaya fada a wurin lokacin.
Wanan ai da gani sun gama da kaine don bayin kai sake bane wanan abin don anga wurin cin banza an mayar da kai shanuwar tatsa.
Kawun hjy yace jummai wanan wani irin kalamai ga danki kike furta wanan magana nan haka a gaban kowa babu dadin ji.
Kawu bari na fada mai gaskiya don Allah idan ba an gama dashi ba zai zaunar damu a nan haka kan wanan diyar makaskanta har ana son a fada min magana akanta.
Don kawai suna kurin sun rabani dashi zaiyi kokarin ya kunyatani a gaban jama, a haka yasa ai min dariya nan gaba kan bijire min da yayi.
Tana aje maganan ta lokacin zuciyana ya gama tafasa da kalaman ta mai daci a garemu tana ganin don abinnhannun shi yasa nake zaune tare dashi ke nan ko me ?
Nace malam ba zan bishi ba gara kawai mu rabu kowa ya huta da wanan fitinan ba don kuma shi yaya yai min komai a zamun yasa na yanke wanan hukuncin ba don kawai hjy tasan koda dan ta ko babu zan iya rayuwa a duniya .
Amma ko yanzu mahaifiyata tace in bishi a shirye nake da in bishi don ni bai taba kasawa dani ba a zaman mu tare ko yanzu ba nayi mashi haka don gazawan shi bane sai dai kawai don kwanciyan hankalin mu gaba daya har shi.
Aikin bamza ke nan inji hjy don kin san ba wani kadari zakiyi ba koda kin koma din gare shi.
In banda abin dan yau har me yaron nan ya gani ga wanan kodadan yarinyar haka da zaka nace mata kamar autan mata.
Kaiyya jummai dadin me kikaji ga hankan yau dan kin raba auren yaran nan da hannun ki saboda mugun halin ki na baza.
Da kina da hankali da tunane dan zaman wurin nan da mukayi yanzu ya isheki darasi a rayuwan ki amma babu komai gaki ga dan naki sun bar maki shi kan mugun nufin ki na banza sai ki aura mai wace kikeso ya zauna da ita mu gani.
A a kawu meye laifina a ciki zancen nan yanzu sun gama dashi ne tunda sun samu abunda suke so gare shi yanzu baida sauran amfani a gare su.
Gaba daya wurin ya hargitse a lokaci guda masu ganin laifin mamu na fadi na hjy kuma sun fi yawa.
Na dago ido na saci kallon yaya Umar dake zaune ya kura min ido makwal din wuyan shi yana zuwa yana dawowa saboda bacin rai bai iya furta komai ba a lokacin.
Wani iri naji a raina na rashin amincewan da banyi in bishi hakan yana nufin na watsawa yaya kasa a idone a bainan yan uwan mu yanzu .
Banda abinda da zanyi don kimar uwata da martabanta a gurin hjy dake ganin abin hannun danta muke so nake zaune dashi da sauri na dukar da kaina kasa ina sauraren kalami kowa a lokacin.
Muryan mamu ne ya katse ma kowa maganan shi a wurin da tace Umar ya dago kai ya kalleta ba tare da ya iya amsa mata a fili ba.
Yau kake son tafiya da matar ka ko sai ta shirya zuwa gobe ko jibi ku tafi kowa yayi shiru yana sauraren su a falon.
Yaya yace idan ta shirya yau din sai mu tafi ba wani matsala bane tace to gata nan na danka maka ita amana a hannun ka.
Kayi hakkuri da komai da ya faru ita din mace ce yar uwata tasan irin kuncin da nake fuskanta ga auren ku yasa ta zabi in bada zabi a kan ku yanzu.
Insha Allahu nayi maki alkawarin rike ta amana kamar yadda na rike maki ita a baya maman twices.
Take falon gaba daya aka dauki kabbara lokaci guda sai lokacin kawu sani yai magana tunda aka zauna kowa na magana baice uffan ba a gurin.
Alhamdullahi anzo gurin da nake son akai kawu ya furta kowa ya mayar da kallon shi gare shi yace da farko dai niba umar Fatima a matsayina na kawun ta kuma mijin uwarta.
Wanda hakan yana daga cikin rashin zaman lafiyan auren nan ga baki daya sai gashi yanzu a karo na biyu uwarta ta kara mika maka nauyi da amanar yarta da hannun ta kuma ka dauka.
Aikin banza inji hjy tace tana jan tsuki kawu yai murmushi kafin yace ba bako a wurin nan da baisan halin ki ba jimmai don haka na baki zabi daga yau ko ki bar yaran nan su zauna a cikin salama ko rayuka su baci a gidan nan.
Gashi nan a gaban ki idan baki zaki masa ya lalace a kan auren yar uwanshi da baki so sai ki masa a gaban kowa muji.
Shidai daya nuna ma duniya matarshi tafini gare shi zai fada ya yafeni a matsayin uwa a gare shi yau.
Yaya ya dago kai a hankali cikin halin shi na natsuwa yace mama ban ki kiba don Fatima kina nan a matsayin uwa a gareni kamar yadda Allah ya halat min fitowa ta tsatson ki.
Amma mama wanan halin mu kike barwa abin fada a gari ace duk kan mu gaba daya babu mai jin dadi a gurin ki daga mu har iyalin mu mama ?
Yau yaya kike son wanan bawan Allah yayi da rayuwan shi ne a lokacin da muke tunanen samun natsuwa da inganta a tare dashi lokacun ne kuma ke mahaifiyar mu kike kokarin tarwatsa mashi rayuwan shi dana iyalin shi.
Ina mama kin sha fada muna don mu kike hakkuri da daddy da zaman gidan nan a yanzu don mama kike kokarin sai wata tabar nata iyalin ta tafi.
Shin mama idan anyiwa Salma wanan hukuncin ko Nafisa zaki ji dadin abin nan ace sarakansu suna muzanta maki diya a gaban ki suna aibanta su haka.
Nan rikicin Nafisa daya taso munji bawai bamuji ba mama Fatima ita ta kwato maki inci ga wullakancin da dan iskan yaro nan yazo har gida yai maki da iyayyen shi Fatima ita ta hana a dauki kayan a gidan nan tare da basu amsan maganan banzan da suka zo dashi.
Mama may kike so damune wai a rayuwan mu mu bamu ji dadin ki ba hakama iyalin mu basuji dadin ki na kasancewa sarakuwa a garesu ba kaf din su babu wace kike so da zuciya daya a cikin su.
Shin gatan da daddy yai muna a yau muke jin dadin shi hakan laifine ke a gurin ki mama.
Mama na rokeki ki bamu salama da iyalan mu mu zauna lafiya don Allah yarinyar nan fatima iya biyayya tana maki yau har yakai ta fara baki amsa ga maganar ki.
Mama ina kara rokon ki kiba bawan Allah nan salama duk a cikin mu yafimu karfi ya fimu kulawa dake yadda ya dace babu a binda Fatima ta isa tasa shi kota hana shi aka abinda yake maki da sauran yan uwan shi don Allah wanan abin ya wuce hakana ki barsu su zauna lafiya na rokeki mama habbib ya kare fadi da hada hannayen shi gurin daya lokaci guda.
Wani irin kuka hjy tasa tana fadin Habbib ni zakaiwa rashin kunya tunda kaine isashe marakunya wanda ya isa.
Mama ni ban maki rashin kunya ba gaskiya na fada don ni ba zan dauki hakan ba shima dai hakkuri yake yasa kika samu nasaran kokarin rabashi da matar shi.
Zatai magana liman ya tareta da fadin watau hjy shi musulunci yazo da sauki ga wanda ya fahince shi.
Diya da kike gani amana ne a garemu iyayye haka ma diyan suma rashin biyayya ga iyayye wani babban gibine garesu a wurin Allah.
Abindana fahinta a nan shine yaran ki kaf dama abokan zaman ki duk hakkuri suke da ke kenan.
Shin hjy baki tunanen mutuwa yana iya riskan bawan shi a kowani lokaci a cikin ko wani irin hali.
Hjy me kika tanadarwa zuwan wanan lokacin yanzu ace mutanen da Allah ya halatta zaman ki dasu duk korafin su dayane a kanki babu dadin ji haka ?.
Malam liman baka san komai ba a nan kiran ka akayi kazo kayi sulhu a gidan nan don haka kayi abinda ya kawo ka kawuce.
Assha magana ya kare jummai Allah ya shiryeki ku tashi mu tafi banga fanin zaman mu wurin nan ba kawu ku barta dantane idan taga dama yau ki tsine masa dan ki daine.
Bana wani ba zaki iya duk abinda kikaga dama gareshi saidai ki sani kamar yadda malam Liman ya fada su diya amana a wurin mu.
Mu dai mun sheda danki yayi maki biyayya yadda ake so don ga shedun haka ya samu habbib yace kwarai kawu.
Don ni shedane duk wata yana bata sama da dari biyar na bukatan ta wanda ni din nan in nayi wuta da kyat zata iya samun dubu hamsin zuwa kasa dashi a wuruna.
Lokacin hjy tace ina wuta ta saka habbib don tonon asirun da yai mata a bainar jama,a tana kokarin tsine mai yana fasin babu abinda zai same ni da yardan Allah mama don nafadi gaskiya Allah shi yace mu fadeta komai dacin ta ai.
Ina ga yanzu ya dace a bar wanan zancen tunda akai ga manufa shi umar zai dauki matarshi su tafi shike nan magana ta kare a nan.
Ke kuma hjy Allah ya huci zuciyar ki inji malam liman ya katse maganan yana tashi zaune.
Kuka Amma ta saka tana fadin Jummai ubangiji ya saka min a kanki ba zan taba yafe maki lalata min zuria da kikayi ba.
Ya umar yace kai haba Amma abin da da uwa yaji haushin maganan Amma kuma zuwa ga mahaifiyar shi.
Dole in fadi haka umar wanan bata da mutunci ko kadan bata san Annabi ya faku ba a zuciyar ta.
Umar tashi kuje kawu balarabe yace yana umurtan umar din sai yaya umar din ya juya wurin hjy yana fadin kiyi hakkuri mama da abinda ya faru ki yafe muna.
Yana fadin hakana ya mike yana kallona yana fadin tashi muje kaina na dukar kasa idona yana fitar da hawaye.
Ya duka inda sultana take barci a jikina ya dauke ta tashi kibi mijin ki Mamu tace min a hankali haka yasa na dago ido ina kallon ta ina hawaye tace jeki ubangiji Allah ya albarkaci auren ku da Albarka aka amsa da amin muka fice daga shiyan Amma.
Kuka nake wiwi a kofa muka samu hjy maryam zaune saman dan dakalin shigowa wurin Amma ta zauna.
Ki bar kuka Fatima haka yafi maki zaman gida kai kuma sai ka kara hakkuri da mahaifiyar ku kundai saba da halin hjy.
Mun gode yace mata muka wuce ta bimu da kallo ita tasan abinda take tunane a zucuyanta lokacin.
Part din mamu na nufa yace ina zakije kuma abu zan dauka na bashi amsa yace ki barshi ko menene har gobe zan dawo in daukar maki dare yayi yanzu banson tukin dare garin nan.
Wayata zan dauko na bashi amsa a cikin kuka barshi nace maki haka yasa dole na bar wayan muka fice daga gidan.
Tun kan mu isa wurin motar yasa remote ya bude motar bude min gaba yayi na zauna ya dora min sultana a jikina ya zagaya ya shiga motar.
Har lokacin kuka nakeyi ban bari ba cikin natsuwa naji muryan shi yana fadin ina son ki Fatima kin sani ba zan iya rabuwa dake yadda mama take nufin inyi ba.
Ban zabe ki na bar mama don in bata mata rai ba na zabi zama da kene don hakan shine alheri a garemu baki daya har maman da bata gane ba a yanzu.
Don na gane zafi da ciwon rashin ki a tare da mu yanzu don nagane rasa ki a tare dani wani matsala zai haifar muna nan gaba dani da yarana.
Ban taba zato ko tsanmanin zaki zabi mahaifiyar ki ki barni ba koda yake kinyi hakan a cikin hikima da basira irin naki kike gani hakan kuma da kikayi baisa naji wani abu game da

Please Login or Register in order to submit comment