You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

har da cewa Alhassan ya na kiran ummi da biri, kuma ta faWa suna dariya"""

"Jiki a sanyaye ya ce ""Biri kuma? Cin mutuncin ya kai haka? Wallahi mariya ummi ba mummuna ba ce ba, tana dai da"

"duhu ne, kuma ™wayar idonta ce da ba irin tamu ba, amma ba mummuna ba ce ba"""

"Mariya ta numfasa ta ce ""Ni ba wannan ba, duk wanda ya ci zarafin ummi, na san bani na halicceta ba, amma abun"

"da yake damuna, a zamanin nan yarinya ta kai mutuncinta Wakin aure, ya ta ™are ina ga idan ummi ta samu miji, gaya"

masa zamu yi ga abun da ya same ta? Idan muna gaya masa waye shaida babu tabbacin a lokacin dukkaninmu da

"muka sani muna raye. Idan kuma muka rufa, zai yi mata kallon mutuniyar banza, ummi ta san abun da ya faru da ita mummunan abu ne."

"Ina tausayawa yarinyar nan abubuwan da suka baibaye rayuwarta, ina tausayawa ™alubalen da zata fuskanta wata™ila bana nan a lokacin balle na tayata kwasar raWaWin, amma ina tausayawa ummi, idan ba ta samu miji mai tawakalli ba, za ta fuskanci wula™anci, wa zai so mini ummi tsakani da Allah, ya karSi ™addarar da ta same ta? Wallahi baban ummi ba zan yafe wa yaron nan ba, ya cuce ni ya cutar da rayuwar ummi, ko idan ta ™ara girma zata manta oho, haryanzu bata yadda na bar ta a Waki ita Waya, an cuce ni"" tayi maganar kuka mai ™arfi yana ™wace mata."

"Balarabe yayi ajiyar zuciya, yana jin Waci a zuciyarsa ya ce ""Wallahi mariya ni kaina abun nan yana ci mini zuciya, ba yadda na iya, mahaifiyata ta riga ta yi mini kandagarki, ™etare maganar ta na iya shafar mu baki Waya, amma in sha"

"Allah, ina sanya ran Allah ba zai wula™anta ummi ba, dan Allah kiyi ha™uri mariya, wallahi idan kina kukan nan, sai na ji kamar na bijirewa umarnin iya, na Wau matakin abun da aka yi wa ummi""."

"Ta share hawayen ta, ta ce ""Kar ka yi haka, aikin gama ya riga ya gama, ko ka Wau mataki, wannan wani miki ne a"

"zukatanmu da ba zai taSa warkewa ba""."

"Yayi shiru ya zubawa mariya ido, shi kansa ya san mariya ba ™aramin ha™uri take yi ba, zama da shi. Tsakaninta da shi"

"babu wata matsala, amma azabar wahalar da take a gidan, duk ta rame ta yi duhu, soyayar kirki ba sa samun sakewa su nunawa juna, saboda azabar iya."

"Ihun Ummi suka ji, hakan ya sanya su yin rige-rigen fita tsakar gida da gudu."

"Ummi suka tarar da Alhassan Wan wurin saminu, ya tattara gashin ummi, ya murWe shi a hannunsa, jijiyoyin kanta"

"sun mimmi™e, duk ta gigice."

"A guje mariya ta ™arasa, ta hankaWe shi, ta ™wace ummi da ke kuka."

"""Alhassan me ummi tayi maka ka murWe mata gashi haka?"""

"Cikin fitsara yaron ya ce ""Šan magenmu take mana wasa da shi"""

"A fusace mariya ta ce ""Kuma saboda zalunci ka rasa me zaka yi mata, sai izaya da gashinta?"""

"""To waye ya ce ta taSa mana magenmu, ana ta nemansa?"""

"Cikin zafin rai, mariya ta Wauke Alhassan da mari."

Sai da balarabe ya waro ido.

"""Tura ta fara kaiwa bango, wane irin zalunci ne haka? Ummi fa ´a ce ba baiwa ba, wallahi duk wanda ya kuma dokar"

"mini ´a sai na ci ubansa. Dama a ciki nake da kai, na samu labarin kana ce mata matashiyar buranya, uwarka ce mai kama da buranya ba ita ba"""

"""Wayyo Allahana iya, a taimake ni ta kashe mini ido"" Alhassan ya wage baki yana kwarmato"""

"Bakomai ya hana balarabe taSuka komai ba, face sanin idan iya ta fito ba ™aramar tijara zata yi ba, kuma ™arshe su zata Worawa laifin""."

"Buje a hannu iya ta fito daga banWaki tana faWin ""Menene haka? Kashe yaron zaki yi me yayi miki?"""

Alhassan ya kwashe ™arya da gaskiya ya gaya mata.

"Ta kuwa hau sababi ""Balarabe kana tsaye take neman yin kisan kai, shikenan an taSa ´ar gwal sai tayi yin™urin cire"

"masa ido. Duk Wawainiyar da ubansa yake yi a gidan nan? Wace irin Wawainiya ce ba yayi da ku, wasu lokutan ba har ciyar da kai yake ba da iyalin naka, da baka ganin kowa da mutunci sai su, saboda zuciyarka ta riga ta mutu, baka da amfani ka kashe zuciyarka ka auri mai ™ashin tsiya, baka da komai sai sokonci da son mace, wadda maganarta ta fi tawa, tun da tana baka abun da bana baka, to kayi ™o™ari ta kashe masa Wa, wallahi duk matakin da ya Wauka a kanku, babu ruwana ko da kuwa wurin hukuma zai kai ku"""

"Cikin takaici mariya ta ce ""Wato iya saboda baban Alhassan yana da kuWi shi ne Wa, da idan aka Waukar masa mataki"

"ba zaki hana ba, ummi ce da aka ketawa haddi ba ´a ba? Iya Allah fa"" cikin hanzari balarabe ya girgiza mata kai. Cikin"

Wacin zuciya ta koma Wakinta.

"""Ai da ka bar ta ta cigaba da gaya mini magana, ta tabbatar mini da bata da tarbiyya, kai ban da ina tsoron Allah da"

"wallahi tuni na saka ka saketa, ko Allah ya sa ™ofar arzkin ka ta buWe, idan ya so ka auro falla-fallan mata, mu samu ta haifa mana masu kyau, kadara irin arziki"""

"Bai cewa iya komai ba, ya shiga Waki, ya tarar mariya ta rungume ummi, tana aikin kuka. Zai yi magana ta Waga masa"

"hannu, ta yi masa alamar ya rabu da ita, haka ya ™yaleta ya fice."

"Har ya tafi kasuwa tunani yake yi? Ko haya zai nema ya tashi ya bar gidan, ya san ba iya ce kaWai ke da hakki a kan sa"

"ba, iyalansa ma na da hakki a kan sa, kuma suna bu™atar walwala, amma iya ta takura su da yawa, kuma ya san ba zai iya biyan haya ba, kuma duniya zata zage shi, ya kasa zama da matarsa ya fifita iyalansa a kanta, haka yayi ta tunani, ba tare da samun mafita ba."

"Mariya ma wuni tayi tunani da zancen zuci, ita kanta ta san bata isa ta tafi gida ba, ta ce tayi yaji saboda takurar"

"uwar miji ba, ba babanta ba yayyenta maza kawai sun ishe ta, babu mai goya mata baya, dan ko hirar take musu, idan ta je ganin gida, sai ace uwa ce a wurinta idan da kara da tarbiyya."

"Gidansu irin iyayen nan ne masu kashe ´a´ansu su raya na wani a gidan aure, saboda dattaku dan gidansu gidan malamai ne."

"Kuma ko kusa ba zata iya gaya musu cewar an yi wa ummi fyaWe ba, saboda ita kanta da take ta hayagagar rashin bi wa ummi hakkinta, tana yi ne saboda abun yana damunta, mussaman nuna wa da ake yi ´ar kamar ba ta da amfani, saboda babanta ba shi da kuWi."

"""In sha Allah ummi sai ahalin nan sun kwanta a kafaWarki, Allah ya nesanta ki da talauci, ya baki ikon cin jarrabawar"

"nan da ni da ke baki Waya. Allah shi ya san dalilin da ya sanya yayi ki a haka, kuma ya jarrabeki Allah ya baki mai kula da ke, ko bana raye"" haka ta wuni cikin kuka da damuwa."

"***"""

"Rayuwa ta cigaba da tafiya, umma ta cika shekaru shida a duniya, sai dai bata sauya zani ba, domin kuwa gorin yau daban na gobe daban, haka iya ke yi, a kan cewa balarabe ba ya iya tsinana komai, a gidan komai shi ne koma baya."

"Haka zalika balarabe, ya fara tunanin mi™ewa ya nemi kuWi, ko dan samawa iyalin sa farinciki da kwanciyar hankali,"

"mussaman ´ar ™aramar yarinyar nan, da aka mayar da ita tamkar wata halitta daban."

"Yau suna kwance da daddare tare da mariya ya ce ""Maman Ummi kin san wani abu?"""

"Ta ce ""A'a"""

"""Ina ga ´an kuWaWena da nake tarawa, zan je birni in ga abun da zan iya yi, ko Allah ya sa na samo arziki"""

"Mariya ta kalle shi ta ce ""Baban ummi baka yadda da yadda Allah ya ajiye mu ba? Na san babu daWi abun da iya take yi maka, amma dai ka yi ha™uri da barin garin nan, ka tafi yawon neman kuWi, raba bawa da arziki sai mutuwa, dan"

"Allah kayi ha™uri"""

"Ya gyara kwanciyarsa ya ce ""Maman ummi, tun da abun nan ya faru da ummi, ji nake tamkar ina kan wuta, gidan"

"galibi duk maza ne tana cikin haWari, sannan ki duba ki ga yadda ake yi mata a gidan nan, Wazu fa suna tafe da yarinyar nan da take Waukarta ta tafi da ita islamiyya, yara suna tsokanarta ba™ar tukunya mai ™yalli, ba ki ji zuciyata ba, wallahi yanzu haka bani da burin da ya wuce tashi na bar gidan nan."

"Da nayi tunanin ko kano zan je wurin yaya hashimu idan da wata hanya da zai Wora ni a kan kasuwanci, to kuma bana son na je na Wora masa Wawainiya, kuma kin ga shi Wan boko ne, iya ta ce sai na bi su Rabiu kudu neman kuWi, bana son yin nesa da ku, amma na fuskanci idan na cigaba da zama a haka, wahala zamu cigaba da sha""."

"Mariya ta nisa ta ce ""To, ni dai dan ta ni, wallahi baban ummi zan cigaba da ha™uri, komai lokaci ne, amma duk abun"

"da ya shafi umarnin iya, babu ruwana a ciki, Allah ya taimaka ya bayar da sa'a, ummi kam za ta yi gwagwarmaya wadda sai dai mu bata gudunmawa ba zamu iya tare mata ba."

"""In sha Allah komai zai zo da sau™i, kuma zai wuce umminmu zata rayu cikin farinciki"""

"""Allah ya sa"""

"Ya amsa mata da ""Amin"""

"Abu kamar wasa, Iya ta din ga yi wa balarabe kwarmato, a kan lallai ta yi magana da Rabi'u ma™wabcin su, lallai ya"

"nemo kuWi, ya bi shi lagos, ya Wora shi a kan hanyar neman arziki."

"Bashir ba shi da kuWin da aka ce ya tanada, dan kuwa rabi'u cewa yayi ya tanadi dubu Wari, harkar fawa yake a lagos,"

ya je ya koya masa.

"Ya ce wa iya ba shi da halin kuWin nan ta ce ""Ai dama ba zaka yi su ba, Allazi babu wanda ya karSo jakadancin talauci zuwa duniya, ka je ka tambayi ilyasu, ko sagir, ga saminu, ko Yahaya, tun da su masu zuciyar nema ne, kuma ba a"

"rasa nono a riga, su baka aro."

"Bashir baya son dalilin da zai sanya ya keta billensa ya nemi alfarmar ´an uwansa, saboda yadda ba sa yi da shi."

"Amma bisa ga umarnin iya, ya tambayi sagir aron kuWi, amma ya kada baki ya ce ""In ara maka kuWi, ka biyani da me?"

"Gaskiya ba zan iya ba, kuWin nan masu wahalar samuwa, na baka in yi sadakar dole da ba niyya, kayi ha™uri kawai"". Ya ji ciwon abun da yayi masa, amma ya dake ya gayawa maman ummi."

"Ita kanta mariya abun yayi mata ciwo, abun da iya take musu ya sanya ta tsane ta, duk da ita ta haifi mijinta, tattara"

"samirun ta, har da zobenta da aka saya mata lokacin aure ta sayar, sai ganinta yayi da kuWi, dan ita kanta wula™ancin da ake yi masa yana bata haushi."

Ya din ga yi mata faWa a kan sayar da kayanta da tayi.

"Ta ce ""Idan har tafiyarka zai sanya iya farinciki, a daina wula™anta mu, ka tafi kawai Allah ya tsare"""

"Ya ri™e hannunta ya ce ""Na gode mariya, Ubangiji Allah ya saka miki da alkahirin sa, ya ™ara miki ha™uri, kada Allah"

"ya sa na ci amanarki, ko a yanzu ko a gaba, Ubangiji Allah ya kula mini da ku"" haka ya din ga zuba mata addu'a kamar ta yaye masa gaba Waya matsalolin sa."

"Saura kwana Waya ya tafi, da ya shiga ya fita, sai yayi musu addu'a, ya sanya musu albarka da ita ummi."

"Da daddare mariya ta shirya masa kayansa a wata jaka, tana ta yi masa addu'a. Ya zura mata ido yana kallon ta."

"""Wai wannan kallon fa?"""

"""Da za ace in nuna matar aljanna a duniya, zan nuna maman ummi"""

"Tayi murmushi ta ce ""Zaka fara ko?"""

"""Allah ba wasa nake ba amaryata"" ta kwashe da dariya ta ce ""Ko ba amarya ba, da wannan ´ar tamu nake amaryar,"

"in zo in fara tara kayan Wakin auren ummi, wai wa ya ganni maman amarya ranar auren ummi ba zama""."

"Yayi dariya ya ce ""Kema Win yaushe aka yi naki auren ki ke hango auren ummina, in sha Allah sai ta yi karatu mai"

"zurfi, Allah ya sa kan na tafi Win nan akwai rabo a cikin nan, ummi ta samu Wan uwa"""

"""Amin ya Allah, ni kaina ina son jariri wallahi"""

"""To Allah ya bamu mai amfani, ya bani kuWi na halal na wadata ku, mu rayu cikin farinciki"""

"""Amin, amma yanzun ma Alhamdilillah, ai kuWi ba su ne farinciki ba"" sosai suka din ga hira, tana ce masa ban da"

"kallon matan yarabawa idan ya tafi lagos, ya din ga yi mata dariya."

"Har ta yi barci, amma shi ya kasa bacci, ya tashi daga kan gadon, ya koma shimfiWar ummi, da ta yi nisa a baccinta"

sosai.

"Ya kunna fitila yana kallonta, sam bai ga munin ´ar sa ba da mutane suke faWa suna zuzutawa."

"Ya din ga shafa gashin ummi, yana kallonta."

"Mariya ta yi juyi ta hango shi, ta ce ""Baban ummi, ko saka maka ita zan yi a jakar ka ku tafi, wannan ™auna haka?"""

"Yayi murmushi ya ce ""Ko yara nawa zan haifa ummi ta daban ce a zuciyata, ina ™aunar yarinyar nan"""

"Mariya ta ce ""To kar dai ummi ta mamaye ko ina a zuciyar, a rage mini wuri"""

Yayi murmushi yana cigaba da kallonta.

"Juyi ummi ta yi taga hasken fitila, Wan razana ta yi, saboda haryanzu ba ta manta yadda aka yi mata fyaWe ba, dan"

"daren da aka yi mata fyaWe ta tuna, da ™arfe ta ce ""Baba"""

"Ya ce ""Na'am ummina"""

"""Kai ne"" tayi maganar tana shafa fuskarsa."

"""Eh Ummina"""

"Ta ce ""To"" ta cigaba da lumshe ido zata koma bacci."

"""Ina ™aunar ki ummina, Allah ga ´a ta da mata ta, Allah ka kula mini da su, ´ar kyakywar Wiya ta"" yayi maganar yana"

jan kumatunta. Ummi ta Wora hannunta a kan nasa tana murmushi ta cigaba da bacci.

"Washegari da zai tafi har soro suka raka shi, ji yake tamkar kar ya tafi, amma yana fatan idan har tafiyar ta sa zata"

zama silar walwalar iyalin sa gara ya tafi.

"Sai da iya ta fara maganganunta na rashin mutunci, a gaban mutane tana neman yi musu tijara, sannan suka rabu ya"

tafi.

"Kwanaki uku da tafiyar baban ummi, kewa duk ta ishi ummi da mariya, sai dai tafiyar ta sa bata sanya sun samu"

"sassaucin jaraba da masifar iya ba da gore-gore, gashi a lokacin waya bata yawaita ba, dan haka ba wanda ya san halin da wani yake ciki."

"Bai fi sati biyu ba da tafiyar sa, abun da ya bar musu duk ya ™are, gashi abu kamar wasa, muraran yara ke cigaba da"

"cin zalin ummi, ga farmaki da Idris yake cigaba da kai mata, loka-lokaci da wasu daga samarin gidan, dan ma yanzu ta yi wayo sosai da sosai, da ta gansu sai gudu."

"Cin zali a wurin ´an samarin yaran nan maza, tamkar sun samu sa'ar su, saboda tana mace, abu kaWan sai a kai mata"

"duka, ko ayi mata wata izayar ko a gida ko a makaranta, saboda ana ganin ummin tamkar sokuwa, kuma babu mai tare mata, da mariya tayi magana iya tayi kanta da tijara."

"Šan abun da ya rage a hannunta, ta fara fanken sayarwa, saboda ta samu abun juyawa, amma sai da iya ta cinye"

"jarin da cin bashi, tare da tula mata ayyukan da zasu hanata sana'ar."

"Abubuwa fa suka fara yi wa mariya da ummi yawa, duka ko ta ko ina, wani ta iya karewa, wani ta kasa sai dai tayi"

kuka ta gaya wa Allah.

"Tana tsakar gida tana wanke-wanke, ta samu da ™yar ta ji™awa ummi garrin kwaki, bayan ta dawo daga makaranta"

"tana sha, ta ji hayaniya ta yi yawa a waje. Bata damu ba ta cigaba da aikinta."

"Da gudu Alhassan ya shigo ya ce ""Babar ummi Albishirinki?"""

"Ta kalleshi ta ce ""Albishirina kuma? Menene?"""

"""Wai baban ummi ´an fashi suka kashe a hanya, zasu taho gida daga ikko!!!"""

Ayshercool

08081012143

*CUTARWA!*

Watpad ayshercool7724

Arewabooks ayshercool7724

YouTube https://www.youtube.com/@CoolhausaNovels What's app 08081012143

BRIGHT PENS

(FREE BATCH)

P4

"Wani irin jifa mariya tayi da kwanon hannunta, ta mi™e a gigice jikinta na wata irin tsuma, zuciyarta na bugawa da"

saurin gaske amma ta kasa magana.

"Mi™ewa ummi ta yi ita ma, tana bin su da kallo."

"Iya ta fito a gigice ta ™undumawa Alhassan ashariya ya ce ""Uban wa ye ya gaya maka haka? In ji wani Wan iskan""."

"Ilyas da saminu ne suka shigo, fuskokin su babu walwala."

"""Ku gyara wurin da za a shigo da balarabe, Allah ya yi masa rasuwa, tun safe muka tafi Waukko gawarsa"""

"A gigice iya ta ce ""˜arya ne ban yarda ba, ya za ayi ace ya mutu? Balaraben ne ya rasu? Waye ya kashe shi, ya aka yi"

"aka kashe shi?"""

"Sagir yayi sallama tare da idris, ya ce ""A ina za a kwantar da shi idan an shigo ne? Ana jira fa"""

"Mariya ji take abun kamar mafarki, addu'a take Ubangiji Allah ya sanya mafarki ne, Allah ya sa ba mijinta ne ya mutu"

"ba, Allah ya sa ba baban umminta ne ya mutu ba""."

"Magaji ya shigo da tabarma, ya shimfiWa, aka yi sallama tare da ´an sanda, da rabi'u da suka tafi tare, aka shigo da"

"gawar bashir, tana ta Wigar da jini."

"Nan da nan gida ya cika da jama'a, Iya sai ihu take tana kururuwa tana kuka, kai da gani ka san jahilci ya samu gidin"

"zama a wurin iya, saboda yadda take ihun ta shiga uku ta lalace."

"Jiki na rawa mariya ta saka hannu ta buWe mayafin da aka rufe gawar bashir, fuskar nan fayau kamar yana bacci, kamar wanda yayi wanka ya fito haka gawar take, ga ™irjinsa in da aka harbe shi, jini yana ta zuba."

"""Innalillahi wa Innalillahi raji'un"" shi ne abun da mariya ke ta nanatawa, tare da fatan Allah ya saukar mata da"

nutsuwa da dangana.

"Ummi ta shafa fuskar sa tana faWin ""Baba ka tashi, baba ka tashi daga bacci mama tana kuka"" cikin haWe rai sagir ya"

yi wa ummi tsawa ya ce ta tashi.

"Sa'adatu ta ce ""Haba baban auwwalu, ka tausaya musu mana""."

"Mutane suka cika gidan dan™am, saboda mutane sun san bashir sosai, mutum ne na mutane mai matu™ar ha™uri da girmama mutane."

"Sai ajiyar zuciya kawai mariya take yi, tana rungume da ummi, aka shiga da shi Wakin Iya, aka yi masa sutura, sannan"

aka ce su je su yi sallama da shi.

"Har a lokacin mariya ta gaza zubar da hawaye, sai wata irin ™una da zuciyarta ke yi mata, abu kamar wasa bashir"

"shikenan an yi an gama, rayuwar ta ™are."

"Duk da yarinta ta ummi, amma ta san idan an mutu ba a dawowa, tayi kuka idonta duk ya kumbura, ta dinga taSa"

"shi tana ""Baba ka tashi, ka ce zaka sai mini ´ar tsana in yi addu'a ka samu kuWi, kullum ina yi maka addu'a"""

"Mariya kam zubawa gawar ido kawai tayi, tana kallon ikon Allah, wai bashir ya mutu."

"Sa'adatu ta ce ""Mariya ki ri™e yarinyar nan, za a shigo a Wauki gawar"""

"Mariya kamar sokuwa, dan kamar ma ba ta iya gane me ake cewa."

"Aka zo aka Wauki gawar bashir, ana ta iface-iface, ummi ta ri™e ™afar Saminu wan mahaifinta, da suka Waga gawar, tana wani irin kuka, amma babu tausayi ko imani, ya angije ta ™asa suka yi waje."

"Allah sarki, ba ta karaya ba ta sake bin su, tana faWin ""Ku dawo da baban, zai tashi fa, bacci yake yi"""

"Surayya, wadda take ´ar autar su bashir, ta ri™o hannun ummi tana kuka, ta rungume ta, tana ta rarrashinta."

"Gida ya cika da jama'a ana gaisuwa, mariya kuwa ta samu gindin bishiyar da ke tsakar gidan ta rakuSe, tayi shiru ba"

"ta cewa komai, ita kaWai ta san azabar da zuciyarta take yi mata."

"Bata san hawa ba, ba ta san sauka ba, ta ji muryar iya na bala'i a cikin mutane ""Dama ya za ayi mutuwar ta dame ta,"

"ai dama ba dan Allah take zaune da shi ba, kalleta a ™e™ashe ko kuka ba ta yi ba, alhalin ita ta takura lallai ya tafi neman abun duniya, ya zo ya wahalta mata, wallahi ban yafe miki ba"""

"Daram! Gaban mariya ya faWi, jin abun da iya ta faWa na ™arshe."

"Mutane suka shiga salallami, surayya ta ce ""Haba iya, haba iya, baki san kukan zuci yafi kowanne ™una ba, gara ke"

"kin yi kukan, ita kaWai ta san me take ji a zuciyarta, da can ba ta ce ya tafi neman kuWi ba, sai yanzu, dama Allah ya yi ajalinsa a can za same shi""."

"Ai nan ta mayar da faWan kan surayya, wanda hakan ya tilasta mata yin shiru, wasu suka goyi bayan iya saboda"

"makira ce, wasu kuma suka goyi bayan mariya, kowa ya san kusan halinta Waya da mijinta, ba sawa ba fitarwa, akwai ha™uri da juriya, mussman a zamanta da iya."

"Yadda ta ga rana haka taga dare, abu goma da ashirin, ga raWaWin mutuwar mijinta, ga sharrin da iya ta ™ulla mata,"

"wai ita ce silar mutuwar sa, ita ta hura masa wuta ya tafi neman kuWi."

"Ta rasa me ta tsarewa iya, take yi mata wannan azababbiyar ™iyayyar, saboda kawai tana auren Wan ta, abun da ba"

"haka take yi wa sauran sirikanta ba, kuma dukkansu babu wanda yake yi mata biyayyar da take yi mata, kawai ta camfata cewar ita ce mai farar ™afar da ta toshe masa hanyar arzikin sa, ya kasa gaba ya kasa baya, gashi ya Wauki son duniya ya Worawa mariya, yana matu™ar son ta da ™aunarta."

"Ko fuskanta Iya tayi sun yi mu'amalar aure, ta ga sun yi wanka, to wunin ranar, haka zata wuni cikin Sacin rai da tashin hankali, a wurin iya ta din ga ™ir™irar mata laifi kenan tana ci mata mutunci, ta rasa wannan masifar, ga uwa"

"uba ummi sunan kishiyar ta ne da ita, wanda hakan ya sa ta ™ara tsanar ummi, ga ´a´anta sun ri™e ta uwa, abun da ta dama suke sha, amma tana masifar kishi da uwar su."

"Washegari da azahar, dangin mariya suka dira a jigawa, suka zo gaisuwa, haka zalika Yahaya, yayan bashir da yake"

"birni, shi ma ya zo ta'aziyya, ya ji mutuwar bashir ba kaWan ba, abun ya girgiza shi, dan kaf cikin ´an uwansa, ko wanda suke ciki Waya, basa shirin da suke yi da bashir, saboda biyayyar sa, yana matu™ar girmama shi."

"Yana son ummi, kasancewar sunan mahaifiyarsu ne shi ma da ita, marigayiyya uwar gidan malam hashimu."

"Ya tarar ana ta fama da ummi, ba ta ci abinci ba, sa'adatu da ba wani shiri suke yi da mariya ba, amma mutuwar"

"bashir, da abubuwan da iya ke ta yi, ya sanya wani irin tausayin su ya kamata."

"Yahaya ya ga yadda ake fama da ummi, tana kwance a jikin mariya, ba wanda ya iya cin abinci a cikinsu."

"Duk da tana tsoron maza sosai da sosai, kuma shi baya yawan zuwa gidan, amma ta gane shi, dan yana kama da"

"babanta sosai, kuma yana bata tsaraba idan ya zo."

"Ya ™arasa ya Wauketa, ya saka hannunsa a nata, ya ce ""Mamana, ki din ga yi wa babanki addu'a, kuma ki din ga cin abinci, kuka ba zai yi magani ba"""

"""Baba ba zai dawo ba ko, ya mutu wai?"" Tayi maganar hawaye na zubo mata, kamar an kunna famfo."

"""Ba zai dawo ba ummi, amma zai ji daWi idan kina yi masa addu'a"""

"Cikin kuka ta ce ""Na fi son ya dawo"" ya din ga share mata hawaye, cike da tausayawa."

"Sai dai yayi mamakin yadda iya ke ta hantarar mariya, tana cikin alhinin mutuwar mijinta, ga ´an uwanta a gida,"

amma iya na ta masifa da nanata ta kashe mata Wa.

"Ya dubi Iya ya ce ""Haba iya, haba iya da wanne za ta ji? Ya za ayi ta yi sanadiyyar mutuwar mijinta, mijin da suka yi"

"auren soyayya, shekara bakwai tare, ko sulhu ba a taSa yi musu ba, ki ce ita ta kashe shi, ga ´an uwanta a gida ai babu daWi"""

"""Yahaya, ni fa nake zaune da yarinyar nan, ni na san abubuwan da take aikatawa, azabar son zuciyarta ya sanya ta"

"hura masa wuta ya tafi neman kuWi, gashi nan ya mutu a banza, yaron nan ha™urin zama yake yi da ita"""

"Yahaya ya ce ""A'a iya, idan na zo fa muna hira da bashir, a bar kaza cikin gashinta kawai banda tone-tone, amma"

"batun ace mariya

Please Login or Register in order to submit comment