You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

Allah ya baku zaman"

"lafiya ya baki juriya"" suka gama salallaminsu suka tafi."

"Ta dawo tsakar gida, ta haWa takalmanta ta zauna, ta zubawa hanyar ™ofar gida ido, in da Allah ya taimaketa, ba™in da suka zo, sun saka yara su je gida, sun Waukko bokiti, an cika mata shi da ruwa, da haka ta samu na alwala."

"Da la'asar aka turo ™anin idris ya kawo wa ummi, abinci ta karSa ta ce masa dan Allah ya tayata zama kar ya tafi,"

tsoro take ji.

"Cikin ikon Allah bai tafin ba, ya tayata zama, har suka ci abinci tare, sai magariba ya tafi ya bar ta ita Waya ™wal kamar"

mayya.

"Hashim ya rasa in da zai sanya ransa, damuwa ta din ga sassa™ar zuciyarsa, gashi tun da aka Waura aure, bai saka"

"idiris a idonsa ba, yana son zuwa gidan ummi, amma yana tsoron yaje ya tarar da abun da ba shikenan ba, da zai"

Waga masa hankali.

"Baban su Idris ya samu Iya yake tambayarta, ya za ayi da dangin mahaifiyar Ummi, yakamata a sanar musu."

"Iya ta ce ""Rabu da su, gayyar tsiya ko an gaya musu uwar mai za su tsinana, talakawan banza, ba su ajiye komai ba"

"sai buzu da tawwada sai allo, ai a haka aka tsaface mini Wa, aka shanye shi ba ya moruwa sai abun da take so, yanzu idan suka sani tsaf za su yi wata ™ulla-™ullar, a bari sai komai ya lafa, an kwana biyu sai a aika musu da goro da alewa ace na aurar da jikata, shikenan"""

"Saminu ya ce ""Amma Iya za su ga kamar ba a kyauta musu ba fa"""

"""Ita abubuwan da tayi mini kyautawar ta yi? Can su ™arata yarinya ce dai na aurar da ita"""

"Saminu ya jinjina kai, amma dai ya san abun da aka yi ba a kyauta ba, ko ba komai suna da hakki a kan ummi, tun da"

´ar su ce ta haifeta.

"Ummi haka ta sake kwana a gidan nan, ita kaWai babu idris babu alamarsa, haka ta sake yin kwanan tsoro da tashin"

hankali.

"Sai dai wayewar garin Allah, babu wanda ya tuna da ita balle ya aiko mata da abinci."

"Babar idiris ta fara ™orafin, tun da aka kai ummi, Idiris bai zo ya ko gaishe su ba, har maganar ta je kunnen iya, ita ma"

"tayi maganar a ranta, amma kasancewar sai a ranar ba™i suka gama watsewa, abun ya dawo kanta."

"Rai a Sace ta aika Alhassan, ta ce ya je gidan ummi, ya ce Idris ya zo tana nemansa."

"A hanyar ™ofar fita, ya tarar da ita a zaune, tana kallon masu wucewa."

"""Ke ummi, kina amarya kina zama a hanyar ™ofar gida kina le™e?"""

"Duk da ba shiri suke yi ba, ummi ta ce ""Tsoro nake ji, nikaWai ce a gidan"""

"Ya ce ""TaS, ina yaya idiris, Iya ta ce yaje tana nemansa"""

"Ummi ta ce ""To ai bai taSa zuwa gidan nan ba, ni tun da aka kawo ni ban ganshi ba"""

"Ya waro ido ya ce ""Ke da gaske!? Ke kaWai ki ke kwana a gidan nan?"""

Ta Waga masa kai alamar eh.

"Ya ce ""Sannu da ™o™ari, kuma ki ka zauna? Kodayeke idan ma ki ka ™i zama kin san sauran, bari na je na gaya wa"

"Iyan"""

"Hankalin iya ba ™aramin tashi yayi ba, da jin cewar wai tun da aka kai ummi bai taSa kwana a gida ba."

"Ta Wau mayafi ta tafi gidan ummi, a nan tsakar gida suka tarar da ita a zaune."

"""Ke ummi, ashe tun da aka kawo ki, Idiris bai kwana a gidan nan ba?"""

Ummi ta Waga mata kai alamar eh.

"""Kuma dan ubanki ki ka ja baki ki ka yi shiru baki faWa ba? Har sai da na aiko, ke da na nemeki na rasa haka na yi"

"miki, ba yawon nemanki na tafi ba? Wato baki damu da shi ba ko?"" Ummi dai ta yi shiru ba ta ce komai ba."

"Iya ta yi ta mata masifa, sannan ta fita, daga gidan, ta saka aka tafi kasuwa aka kirawo babansa, da sagir aka ce"

"musu, ba a ga idiris ba."

"Iya ba ta damu da tsawon kwanakin nan, ya ummi take ba, ta ci abinci ko ba ta ci ba, bata bi ta kan hakan ba."

"Aka din ga yawon nemansa, wurin abokansa da sauransu, da ™yar aka gano shi, can wurin wani abokinsa ya koma, a"

can yake kwana.

"Iya ta same shi ta din ga zaginsa, ta in da ta shiga ba ta nan take fita ba, mahaifinsu ma kamar zai kai masa duka,"

saboda takaici da Sacin rai.

"Hashim kallon su Iya yake yi, yana tausaya musu ranar da hakkin ummi zai kama su baki Wayan su, babban abun da yake ™ara bashi mamaki, irin yadda ba wanda yake iya yi wa musu a kan duk wani son zuciyarta."

"Ummi ba ta san me yake faruwa ba, sai ma tunanin Allah ya sa Idris yana lafiya, tun da an ce tun ranar Waurin aure"

ba a sake ganinsa ba.

"Da ™yar tayi sallar la'asar, saboda yunwar da take ji, cikinta sai ™ugi yake yi, har wani jiri take ji idan ta tashi, ban da"

"ruwa ba abun da ta sha, tana son fita nemawa kanta mafita, amma an ce idan ta fita ba da izinin Idris ba, Allah zai"

"™onata, gashi kuma tana son komawa makaranta, amma ba ta ganshi ba balle ta tambaye shi."

"Sallamar yaro ta ji, tayi sauri ta fito daga Wakin, wani yaro ta gani da kwano, ya ce mata ""Gashi in ji mamanmu"""

"saboda ™uruciya da yarinta, ummi ba ta tambayi daga ina ba, ta karSa ta ce ta gode."

"Dafaffen rogo ne, da ™uli-™uli, ko wanke hannu ba ta yi ba, ta hau rogon nan da ci, saboda yunwar da take ji."

"Ta gode wa Allah bayan ta kammala, duk da ba ™oshi tayi ba, saboda Wan kaWan ne aka zubo shi a kwano."

"Ta fito da kwanon tsakar gida, ta saka ruwa tana girgijewa, dan ba ta da ko omo."

"Kamar wanda aka cillo, ta ga idiris ya shigo, babu ko sallama, hannunsa ri™e da jakar kayansa, wata irin nannauyar"

"ajiyar zuciya ta yi, saboda faWuwar gaba da tsorata."

"Babansa da yake bayan sa yayi sallama, ummi ta amsa ta tsuguna ™asa ta ce ""Baba ina wuni?"""

"""Lafiya ™alau, ya gidan?"""

"Kai a ™asa ta amsa masa da ""Lafiya lau""."

"""Gashi nan, duk ranar da bai kwana a gidan nan ba, da safe ki je gida ki sanar da ni, zaka ga yadda zan yi da kai,"

"mutumin banza wanda bai san abun da yake yi masa ciwo ba, an lallaSa abun nan a rufawa juna asiri, ka daina"

"Waukko mana magana, amma kana ™o™arin tona mana asiri"" mahaifinsa yayi masa kaca-kaca, sannan ya tafi."

"Ummi ji ta yi kamar tabi bayan sa, dan ta wani fannin zamanta ita kaWai babu Idris shi ne rufin asirin ta."

"Ta ajiye kwanon da take Waurayewa, ta nemi wuri can a tsakar gida ta zauna, tana ta addu'a a zuciyarta."

"Idris kuwa ya cika yayi fam! Kamar ya fashe saboda tsabar ba™in ciki da takaici, fuskar ummi kawai idan ya kalla, ji"

"yake kamar ya sha™eta ta mutu, me zai yi da wata ummi, mummuna kamar ba bil'adama ba, aba kamar bayan garwa."

"Tsaki yayi ya fito zai sake fita, aikuwa ta sake razana, kai tsaye inda take ya nufa, ta fara ™o™arin mi™ewa tsaye, ya"

sanya ™afarsa ya tankaWata ta faWi ™asa.

"""Shine ki ke je ki ka gaya musu bana kwana a gidan nan ko? Idan na kwana a gidan uwar me zan yi miki?"""

"Da sauri ta girgiza kai ta ce ""A..aA'a iya ce ya aiko nemanka, wallahi ba faWa na yi ba"" tayi maganar cikin rawar"

murya.

"""Rufe mini baki"" yayi maganar yana dukanta a ka da hannunsa."

"Ta saka hannu bibbiyu ta dafe kanta, saboda jin zafin dukan da tayi, dan ma Allah ya taimaketa, tudun gashinta bai"

bari ta ji zafin sosai ba.

"""Idan ki ka kuskura ko da wasa, ki kai ™arata, sai na yanka ki, kuma azabar da zan gana miki, sai kin gudu da ™afarki,"

"ke baki san yadda na tsaneki ba ko? Zaki gani yanzu ai, banza mai kama da dabbobi"""

"Kame jikinta take sake yi, saboda gudun kar ya kuma dukanta, aikuwa sai da ya sake takata da ™afarsa, sannan ya"

fita.

"Sai da ta tabattar ya fita, sannan ta iya Wagowa a hankali, ta bi hanyar da ya fita da kallo."

"Ta kalli jikinta, da ya Sata mata da ™asar takalminsa, tun da tazo gidan sau Waya tayi wanka, shi ma ba soso babu sabulu. Kayan jikinta tun wanda ta zo da su ranar da aka kawota, Iya ta ce za a aiko mata da kaya, amma shiru."

"A hankali ta saka hannu ta karkaWe ™asar, tana takaicin yadda ya ™as™antar da ita ta hanyar takata da takalminsa mai"

datti da taSo.

"Tayi shiru tana ta sa™e-sa™e a zuciyarta, ta haWe gwiwoyinta, ta kifa kanta, ta nemi hawayen ma ta rasa, sai zafi da"

™unar zuciya.

"Yaya Hashim bai zo ya ganta ba, maman na'ima ba ta zo ba, tayi ta lissafin mutanen da take sanya ran su zo su ganta,"

amma basu zo ba.

***

"A Sangaren mariya kuwa, tuburan depression ya zame mata hauka, ga ta dai a nutse, sai dai babu cikekken hankali, wasu lokutan sai hankalin ya dawo, ta yi ta harkokinta, amma da abun ya juyo, sai daina cin abinci, ta daina magana."

"Duk wanda ya shigo da ™aramin Wa gidan, sai ta ce sai an bata umminta, ko ta Wauki fulo tana yi masa wasa, ta ce"

ummi ce.

"Idan ´an yara mata suka shigo gidan, suma sai tayi ta kiransu da sunan ummi. Ta ce ""Yaya Wanlami, kalli yadda ummina tayi wayo ta girma""."

"Ya amsa mata da ""Tubarkallah, ki yi ta yi mata addu'a, Allah ya ™ara rayata"""

"Ta Wan yi shiru sannan ta ce ""Ba ummi ba ce, ummina ba™a ce mai kyau, bari in tashi in zuba ruwa in yi mata wanka,"

"na goyata garin nan da sanyi"""

"Yayi saurin tashi, ganin da gaske tana ™o™arin kama ´ar mutane ta yi mata wanka, ya ce ""Ki yi ha™uri in anjima sai ki"

"yi mata wankan""."

"""To ai bana son babanta ya dawo ya tarar da mu, ba mu yi wanka mun yi kwalliya ba, kaga yana son turare da lallen"

"da nake yi masa, baban ummina har kayan kasuwa yake sayo mana"" haka tayi ta gwamutsa masa zantuka."

"Yayi shiru yana kallonta, ba zai manta zuwan ™arshe da yayi gidan Iya ba, da yaje da maganar neman alfarmar"

"Waukar ummi, ko na ´an kwanaki ne, dan hankalin mariya ya kwanta, ta fara samun matsala a ™wa™walwa, amma ta kada baki ta ce Allah ya ™ara, hauka yanzu ta fara da yardar Allah sai ta din ga bi bola-bola hakkin ran Wan ta ne."

Tun daga nan yayi alwashin ummi ko ´ar gwal ce ba zai kuma zuwa da niyyar a bashi ba.

"Mama ta fito ta taya shi lallaSa mariya, suka mayar da ita Waki, sai surutai take, tana basu labarin baban ummi da"

"kuma ummi, sai dai ko da wasa ba ta zancen Iya, ko sauran mutanen gidan sai ummi da babanta."

"Ummi ta sakankance idiris ba zai kwana a gidan ba, dan haka har ta hau kan tsurar katifar ta kwanta, sai dai ta kasa"

"rufe idonta tayi bacci, saboda tana jin tsoro, ga gari hadari na ta haWuwa, sai addu'a take Allah ya sa kar ayi ruwan sama."

"Sai da hadarin ya haWo gaba Waya tare da iska, kawai ta ga hasken tochlight a tsakar gida, inuwar Idris ta hango, ya"

"tunkaro Wakin. Ta runtse idanunta, tana fatan Allah yasa ba shi bane ba, sai dai ta ji ya mayar da ™ofa ya rufe, hakan ya tsananta bugun zuciyarta."

"Ba ta san me yake yi ba, saboda ta rufe idonta, ™afafuwanta ya taka ya ce ""Ke dalla tashi"" yayi maganar a matu™ar"

"kausashe cikin rawar jiki ta motsa, ta tashi zaune, me zata gani Idris a tsaye a kanta tsirara kamar mahaukaci."

"Ihu ta saki, ta runtse idanunta ta dafe kanta da hannayen ta."

"""Dalla malama rufe mini baki, ki tashi na ce, uban meye baki sani ba? Munafukar banza da ta wofi, ma™aryaciya an cuceni an haWani da saura, har da zuwa ki gaya musu bana kwana a gida, ai na san kin san komai kin saba""."

"Kyarma ta fara yi, ta™i motsawa, aka kece da wani irin ruwan sama mai ™arfin gaske, ba ka jin komai, sai sautin"

zubarsa da ™arfin gaske a kan kwano.

"Ganin za ta Sata masa lokaci, ya sanya ya jefar da fitilar hannunsa yayi kanta, kamar zararre."

Ayshercool

08081012143

*CUTARWA!*

*MIKIYA WRITER'S ASSOCIATION*

BRIGHT PENS

(FREE BATCH)

P12

"Kamar mai shirin tarayya da dabba, haka yayi kan ummi, ya fara yage suturar jikinta, yana ja tana ja, tana ihu tana"

bashi ha™uri.

"""Ba zaki rufe mini baki ba?"" Yayi maganar cikin fusata."

"Warin bakinsa ya daki hancin ummi, kai ka ce an buWe masai."

"Sai dai ba ta gama sha™e warin bakinsa ba, warin gashin kanta ya daki hancinsa, gashi ne fal Allah ya bata shi, sai dai"

"kasancewar babu gyara babu tsafta, ya sanya yake wani irin tsami mara daWin sha™a."

"Sai da ya ware gashin ya sauka bayanta, warin ya ™aru har wani gafi gashi gashin yake yi, saboda tururin warin dauWa"

da ™azanta.

"˜yale gashin yayi, ya cigaba da ™o™arin rabata da suturar jikinta, sai dai nan ma jikin ummi, warin dauWa yake yi, da"

"tsamin gumi, saboda rashin wanka da kula."

"Har Wauke numfashin sa yake yi, ita kanta ummin warin hammatar idiris Win ya hanata sukuni, yafi ™arfinta nesa ba kusa ba, amma ba ta gaza ba wurin ™o™arin kare kanta."

"Duk da a duhu ne bai hana shi, kifa wa ummi mari ba da dukkan ™arfinsa, Allah ya sa hannunta ya samu ba fuskar"

"ba, amma sai da ta gigice."

"Marin da yayi mata ya sanya ta saka kataSus, har ya cimma in da yake burin zuwa, sai dai wari da ™arni mai haWe da"

"zarni ya bugi hancinsa sai da yayi baya, take ya ji cikinsa ya yamutsa masa, kamar zai yi amai, nan da nan zuciyarsa ta fara tashi."

"Duk yadda ya so Wauke numfashin sa ya kasa, wani irin ba™in ciki da takaici ya ninku a zuciyarsa, ya laluba ya Waukko"

"fitilarsa ya hasketa, ta kare jikinta sai kuka take yi."

"Ya tashi ya rufeta da duka, abun da ta fi tsana, ya din ga takata da ™afarsa, sannan ya janyota ya hankaWata waje ana"

"wannan ruwan saman, ba tare da imani ko tausayi ba. Kuka take iya ™arfinta, tana danna ™ofar Wakin, amma ya saka sakata ta ciki."

"Tsakar gidan ya sha™e da ruwa, saboda rashin magudanan ruwa a unguwar."

"Jikinta duk ya yage mata sutura, kuma a haka tsirara ya hankaWota waje cikin ruwan sama."

"Ga wani irin tsoro take ji, balle ta tafi Waya Wakin, haka ruwa ya din ga dukanta tana kuka. Tun tana saka ran ruwan"

"zai Wauke, har ta zubawa sarautar Allah ido, ™afafuwanta suka gaji saboda tsayuwa, ruwan saman nan ya ™arasa zuba a kanta."

"Ta din ga buga ™ofar Wakin a hankali ta na cewa ""Dan Allah yaya idiris ka buWe mini na Wauki kayana, sanyi nake ji dan Allah"" tayi bugun har ta gaji, jikinta ya din ga wata irin karkarwa saboda sanyi."

"Ruwan, bai gama Waukewa ba, ta fara takawa a hankali ta na ™an™ame jikinta saboda ™yan™yamin ruwan da ya kwaso dagwalon unguwar ya shigo ya taru a gidan."

"Šaya Wakin ta nufa, sai dai kasancewar ba taga babu ™ofa, a buWe yake, shima ta tarar ya malale da ruwa, babu in da za ta zauna, ta samu wuri Waya ta raSe tana cigaba da kuka."

"Har garin Allah ya waye ummi na tsaye, babu wurin da zata raSa ta zauna, saboda an yi ruwa ba Wan kaWan ba."

"Gari ya fara haske tana sanya ran ya buWe ™ofa ta suturta jikinta, amma bai buWe ba, ta din ga fargabar kar a zo gidan"

a tarar da ita jikinta babu sutura.

"Sai da gari yayi haske tar, sannan ya zare sakata ya fito ya shiga banWaki, tana hangen sa ta taga, ganin ya shiga"

"banWaki, ya sanya ta fita ta shiga Wakin, ta kwashi kayanta da duk ya yayyaga, ta saka, jikinta sai wata irin tsuma yake yi, saboda sanyi, ga ciwo da jikinta yake yi mata da ™afafuwan ta."

"A gurguje ta yi alwala, ta koma Wakin yin sallar asuba, duk a Warare take cikin tsoro take yin ta."

"Aikuwa a raka'a ta biyu ya dawo Wakin, bai damu da salla take yi ba, ya hankaWeta, saboda wata irin tsanarta da yake ji a cikin zuciyarsa."

"Ta mi™e ta cigaba da sallar, ya tsaya a kanta yana kallon ta yana huci, da ta idar da sallar, ta mi™e zata bar masa"

"Wakin, amma ya janyota ta baya, ya sake hankaWata ™asa."

"Wata irin ashar da yayi mata sai da ta kalleshi a firgice, ya din ga Wura mata ashar yana cin mutuncin ta da na"

"iyayenta, har da mahaifinta da ba ya raye a duniyar, har da kiranta da ´ar iska lalatacciya."

"Ummi ta yi shiru ta sunkuyar da kanta ™asa, ta nemi hawayen ma gaba Waya ta rasa."

"Har zai fita ya dawo, ya din ga dukanta hannu da ™afa, cike da tsana da jin haushin ta."

"Ya gama rashin mutuncinsa ya fita, ta tashi a hankali, ta koma gefe tayi zuru da ido."

"Sai a lokacin kuma ta samu damar yin kuka, jikinta sai ciwo yake yi, ga yunwa tana ji, gashi haryanzu sanyi take ji, ta"

"kwanta a wurin, ta hau bacci."

"Sallamar da Iya take kwaWawa a tsakar gida ne, ya sanya ummi farkawa, ta fito da sauri, ta ga Iya tare da yaya, mahaifiyar su Idris."

"Murmushi ummi ta yi ta ce ""Iya sannu da zuwa, yaya ina kwana"""

"""Ai kya bari mu shigo mu zauna ko"""

"Ta basu hanya suka shiga Wakin, suka zauna, yaya tayi ™uri tana kallon ummi, Iya ta ce ""Ke lafiya na ga kayanki a"

"yayyage?"""

"""Ba komai"""

"""Kamar yaya ba komai, kamar wadda ta yi dambe"" hawaye ne ke shirin taruwa a idon ummi."

"""Kuma dan ™azanta tun da aka kawo ki baki canza kaya ba, yau wurin kwana biyar""."

"Ummi ta buWe baki za ta yi magana, ta kasa hawaye suka riga maganar fita."

"Yaya ta ce ""Menene na kuka kuma ummi?"""

"Iya ta ce ""Sangarta mana, idan zaki yi wa kanki ™iyamullaili ki zauna ki daina wannan kukan shikenan, idan ba zaki"

"daina ba, sai ki yi ta yi, ga kaya nan na Webo miki a kayan auren da aka kaiwa waccan, abun bai yiwu ba, sauran an sayar an bashi kuWin yayi muku cefane, sadakin ki kuma, na bayar a sayo akuya a bayar da kiwo""."

"""Dan Allah iya ki mayar da ni gida, bana son zaman nan"""

"""Ki kiyayeni ummi, tun kan na Sata miki rai, bana son shashanci, ki tashi ki yi wanka ki canza wannan kayan"""

"Tashi ummi ta yi tana kuka, ta fita tsakar gida, suma fitowar suka yi, wai har tafiya za su yi."

"Ummi ta tsaya tana kallonsu, suka fice, wai wata unguwar zasu je, to da me za ta yi wankan, ko ruwa ba ta da shi? Ta"

"koma Waki ta zazzage lesar vivar da Iya ta kawo mata, atamfa ce kala uku, sai sabulun wanka uku, man shafawa Waya da soson wanka."

"Sai kuma 'yar tsala, a ™ulle a leda, ummi ta ture kayan ta kwanta, wani irin zazzafan zazzaSi ya rufeta, saboda dukan"

ruwan sama.

"Sai da ummi ta kwana biyu tana zazzaSin nan, babu abun da ya shafi Idris, da ya dawo zai koreta daga Wakin, bayan"

"ya gama ci mata mutunci da zaginta, wasu lokutan sai yayi mata dukan tsiya ma, duka na cin mutunci, haka take kwana a Waya Wakin da babu ko ™ofa a ciki, idan aka yi ruwan sama, haka zai sameta a Wakin nan."

"˜arshe ma ya watso mata kayanta da ga Wakin da katifa take, ya ce ta koma Waya Wakin."

"Da ya tuna ™arin da ya ji tana yi, da kuma yadda suka din ga lalubeta tana yarinya, sai ya ji ya ™ara tsanarta, da ganin an bashi saura."

"Dama abinci ba a magana, ba bata yake yi ba, wasu lokutan ne idan yaran gidan su za su zo, babar Idiris Win kan zuba"

mata abinci a kwano a kawo mata.

"Tana kwance a Waki tana numfarfashi, zazzaSi da ciwon kai sun ™i sauka, fitsari ya dameta, ta tashi da ™yar, ta je ta"

"yi, tana shirin komawa Wakin, ta ji an ce ""Ummi"""

"Tana waiwayawa taga Na'ima, ai sai ta nemi ciwon ta rasa, cikin wani irin zafin nama, ta rungume Na'ima ta fashe da"

kuka.

"Ita ma Na'iman kuka take yi, ta Wago ummi ta kalleta ta ce ""Ummi ba ki da lafiya ne? Na ji jikinki zafi?"" Ta jinjinawa"

na'ima kai.

"""Innalillahi wa Innalillahi raji'un, yanzu ummi a rasa wanda za a aura miki sai wannan Wan iskan, dukan ki yake yi kenan? Kalli shaidar yatsu a fuskarki"" Ummi dai ta yi shiru, daga baya ta ce ""Mu shiga Waki"""

Saroro na'ima ta bi Wakin da kallo.

"""Ummi kar ki ce ba su yi miki kayan Waki ba?"""

"""Suna can Wakin, koro ni yayi nan shi ne yake kwana a Wakin"""

"Na'ima ta zauna tayi kuka mai isarta sannan ta kalli ummi ta ce ""Wai ke ba ki san in da mamanki take ba? Anya ma"

"kuwa sun san halin da ake ciki?"""

"""Yaya Na'ima nifa tun da aka tafi da mama ban sake ganinta ba, dan Allah idan kin san in da take ki kaini, na gaji,"

"wallahi yaya Idris dukana yake yi, duk jikina ciwo yake zai kasheni"""

"Ta rungume ummi, ta din ga rarrashin ta, ta ce ""Kiyi ha™uri ummi, ban ma san an yi miki aure ba, mama ce ta aika"

"™anin mijina ya gaya mini, Allah yana sane da ke ummi, bari na je gida na kawo miki abubuwan da na kawo miki, sai na kawo miki tabarma da labule, a kafa a Wakin, tabarmar ki din ga kwana a kai"""

"Ummi ta yi ta mata godiya, ta bata abinci, ta aika ™annenta suka sayo mata magani, aka kafa labule, ta shimfiWa"

"tabarma, sai Wakin ya Wan yi kyan gani."

"""Yaya na'ima, dan Allah idan Allah ya yassare miki, ki saya mini wando, nawa ya ™arasa lalacewa, ba zai saku ba"""

"""Ummi meyasa ba zaki din ga zuwa wurin mama kina gaya mata ba? Ya za ayi ki rayu da wando guda Waya, abun da a"

"™alla a rana ana so ki canza biyu"""

"Ummi ta yi shiru, tana wasa da yatsun hannunta, yanzu ma dan ta ™ure ne ta nemi alfarmar na'ima, dan idris ya"

"™arasa shi, wandon har da in da ta kama take ™ullewa."

"Ta ji daWin zuwan na'ima, ta bata abubuwa da yawa, har da kuWi, sai bayan la'asar ta tafi, kuma Allah ya taimake ta,"

Idiris bai dawo ba a lokacin.

"Duk yadda ummi ta so ta yi wa naima bayanin halin da take ciki, kasawa ta yi, ta ji abun yayi mata girma ta faWa, dan"

"haka ta yi shiru da bakinta, ta samu ta saya mata wanduna guda huWu, har da ribbon."

"Duk in da idris ya haWu da abokansa, suka yi masa kirarin ango, da tambayarsa yaushe za su cin girkin amarya, sai ya"

"hau masifa yana basu labarin halin da ummi ke ciki, na mummunan ciwon sanyi da yadda take bugawa, da ™azanta tare da ™orafin ragowa ce aka haWa shi da ita, su yi ta masa dariya, suna ce masa angon WoWWoya."

"Tare da tabattar masa, idan bai yi da gaske ba, sai ya kwashi ciwon."

"Sai dai ko sun tambaye shi dalilin fasa auren sa da Hindu, sai ya Soye musu gaskiyar zancen."

"Haryanzu kuma bai rabu da hindu ba, yana lallaSawa su haWu a wani wurin na daban, duk da tarin kashedi da"

mahaifinta yayi mata a kan idiris.

"Na'ima kuwa a ranar zata koma gidanta, suka haWu da magaji a hanya, suka haWu suka gaisa."

"Ta ce ""Yaya magaji ashe aure aka yi wa ummi babu labari?"""

"Hashim ya ce ""Ke dai bari na'ima, abun ne yazo babu shiri, ni kaina ban san da zancen ba sai ana gobe Waurin aure""."

"Na'ima ta gyaWa kai ta ce ""Amma, ka yi ha™uri da abun da zan ce, wallahi ku din ga gaya wa kakarku da Wan uwanka"

"gaskiya, ya za a katsewa ummi karatunta, kuma a haWata aure da wanda baya ™aunarta, dama ita ba bi ta kanta za ayi, aji ko tana son sa ba, gaba Waya a firgice take a cikin gidan nan, jikinta duk shaidar duka, ya korota daga Waki, Wakin da na tarar da ita, ba ™ofa babu taga, babu abun zama, ba ya bata abinci, wace irin rayuwa ce haka? A gidanku ba ta huta ba, an aurar da ita,

Please Login or Register in order to submit comment