You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

da yunwa ga gajiya da bakar azabar da kafafun su ke musu.



Bad'ejo kam tun tana amai da kuzarinta har ta koma kakari, dan babu komai acikinta, wata matashiya haka acikin wadanda suka tsira ta kalli yanda Bad'ejon ta lafe ajikin Mairoji tana sauke ajiyar numfashi da kyar, cike da tausayinsu tace"sannunku....ina kuka nufa daga nan?".



Cikin haki Samle tace"Rugar Saje muke son komawa, amman bamu san hanya ba daga nan".



Cikin kulawa, matashiyar tace"awane gari kenan, dan nan fa muna cikin Maiduguri ne, kuma ni haifaffiyar nan ce, ban taba jin sunan wannan garin ba".



Mairoji da tadan fisu sanin sunan garuruwa tace"amakartar mu dai nasan wani malami dayake zuwa daga Kano, yace mana babu nisa sosai tsakaninmu da da garin, kuma garin da yayan babata yake akwai duwatsu, sosai dan wani ma kamar ya fado miki idan kina tafiya".



Jinjina kai tayi , aranta tace"maybe irin yan mazauna kan karshen kanon nan ne, kuma garin da take nufi, ko can Dala ne, tunda ai akwai sauran duwatsu har yanzu acan.



Dafa Mairoji tayi ta mata murmushi, tace"shikenan ni ma wan babana yana kano ne, kuma nima can zan koma, inshaAllah sai mu tafi tare, kafin agano inda kuke sai akaiku".



Cike da murna suke ta mata godiya, sannan suka kuma daukar hanya suka nausa, dan so suke, su isa bakin titi kowa sai ya kama inda ya nufa.

Kuyi hakuri mutuwa aka mana sai yau na samu damar muku update, sory 4keep you waiting guys.=ØOÞ



   *RUGAR SAJE*



By Nusaiba Ayuba Suleiman



Wattpad@nusysa

IG@Nusaiba A.S. Sarkin zango.





*FITTATU 18=ØÚÜ 2 0 2 1=Ø¥Ü*





–&

*HOME OF QUALITIE'S WRITER'S ASSO=ØÚÜ*

```{{The Home Of Qualitative Writers That Are Educate Humanities}}```

https://m.facebook.com/story.php?story_fbid=106249334371950&substory_index=0&id=106248871038663&sfnsn=mo



*œ&þ{{H.Q.W.A=ØÚÜ}}
'þ*

(3E 'DDG 'D1 -EF 'D1 -JE.



_4_



    Sunyi nisa suna ta nausar hanya, wani abokinsu ne ya bada shawarar arabu, kar maharan su farga dasu, na'am su kayi da batunsa inda suka rabu kashi kusan biyar dan suna da yawa maza da mata, yara da manya, zugar su Mairoji suka nausa yamma, wasu kuma kudu, wasu arewa haka dai kowa ya nufi inda yake ganin matserata ce.



    Sai gab da magaruba su Mairoji suka iso bakin titi, zama sukayi suna haki dan sunyi matukar gajiya, sun dade anan ma kafin wata sharon  tazo wucewa sai daga mata hannu suke, amman bata tsaya ba, sai da tayi nisa sosai sannan ta dawo da baya direban ya kallesu yaga suna da yawa, dan sun kai kusan su ashirin, kallonsu ya kuma yi yace"kunyi yawa, da saina daukeku gashi can cikin gari ahargitse yake, amman idan zaku iyayin goyo ku shigo, nima nakai fasinjane, kuma ban samu na dawowa ba, sai wasu su zauna a boot".



   Gosiya suka mai matan suka yi goyon biyu, mazan kuma wasu a boot sai wasu agaba, suma sunyi goyon, koda suka ga sunyi nisa da tafiya sai kowa ya fara sauke ajiyar zuciya, gudu kawai direban yake shararawa basu shigo kano ba sai gabanin asuba.



   Atashar Kano line ya juye su sannan ya musu fatan alkhairi ya tafi bayan yasha dubban adduo'i daga bakunan su, dan ko kwandalarsu bai karba ba, zama sukayi awajen har gari ya gama wayewa , masu hankalin cikin su suka tashi sukai sallar asuba.

    Wajen shida da wani abun kuma kowa ya kama gabansa bayan sunyiwa juna fatan alkhairi, suma su Mairoji fitowa sukayi suka samu me napep fada musu unguwar da zasu matashiyarnan tayi sannan suka tafi, agaban wani dan madaidaicin gida suka tsaya , nan ta tsaida me mashin din kan zata karbo masa kudinsa, shi kuma yace bai yarda ba, kawai taje tayi zamanta, suna haka aka bude get din gidan wata bakar prado zata fita , kallon motar tayi tana sauke ajiyar zuciya, shima na cikin motar kallon ta yake da mamaki da sauri yai fakin ya fito ya karaso wajensu hannunta ya kama yace "Shahuda...kece da sassafennan, maza mu shiga ciki daman Kawu bai fita ba".



   Mai mashin din ta kalla tace" sallame shi tukun, sannan mu shiga da wadannan yaran".



Kallon su Mairoji yayi, yana bata fuska, zai magana ta kama hannunsa ta dan girgiza mai kai, shiru yayi ya karasa wajen mai mashin din ya tambaye sa kudinsa, bayan ya sallame shi ne ya kuma kallon Shahuda yace"Hudaa....wadannan yaran fa masu kama da bararoji, wai tare kime dasu".



   Bata kalle sa ba, ta kamo hannun su Mairoji tace"kumu je, akun gidan mu ya fara zuba".

   Awajen ta barsa yana ta bata fuska, kafin daga baya ya bisu shima, afalo suka tarar da matar gidan tana jera abin karyawa akan dinning, ai da gudu Huda ta saki hannun su ta isa ga matar ta rungume ta tana kuka, shafa kanta matar tayi tana murmushi"ya isa mana kukan, ya isa.....maza shiga ciki kiyi wanka sai kizo ki karya".



Kanta ta gyada tana share hawayenta, ta ce"Ammy tare nake da wasu yara, suna bukatar taimakon mu Ammy pls..."



  "Ba komai Huda, ai d'a na kowa ne, ki kaisu daya dakin su gyara jikinsu akwai kayan Laylah sai auyi amfani dasu, in kun gama sai kuzo ku ci abinci".



Cikin farin cikin Huda ta rungume ta tace " na gode Ammy na, Allah ya kara girma da daukaka".



Da "ameen "ta bita tana murmushi, daki Huda ta kaisu Mairoji bayan ta nuna musu yanda zasuyi amfani da kayan bandakin sannan ta fita ta tafi dakinta dan kintsa jikinta.







+++



    Karamin hauka yake musu agidan, duk ya hargitsa komai banda sambatu  babu abinda yake, babban yaron sa Lala shi ya samu ya kama sa zuwa daki, cikin kwantar da murya yave" haba oga...akan wannan yar tatsitsiyar yarinyar zaka daga hankalinkai, haba dan Allah ga mata nan manyan , ga hajiyoyin dake son hulda dakai amman oga ka maida hankalinka akan wadda batafi yar cikin ka ba zaka nemi shiga wani hali...."



    "Kai dalla kamin shiru, ita din yarinyar ruhi na ce, rayuwata ce kuma fitar numfashi na ce, akan na rasa ta, gwara na rasa duk wani abu dana mallaka, ba zaka gane son da nake mata ba, ina jinta har bargo na, ga kuma waccen dake dauke da jini na, d'ana ko y'ata bansan mai zata haifamin ba, tun kafin yazo duniya nake jin kaunarsa, kace wai dan me zan damu?".



    Abun da Lala bai taba gani ba kenan, hawaye a idon oga, ja da baya yayi ya zauna ya rasa ta inda zai fara lallaba ogan nasa, da kyar ya aro dauriya ya samu ya lallashe shi, sannan suka samu saukin karamin haukan daya fara musu.





+++++

 

     " Huda dan Allah meye hadinki da wadancen bararo din....? Allah ni ji nake basu min ba, ga karni idan zuka zauna awaje".



   Murmushi tayi tana kallon Ammy da Kawu dake shigowa falon, bayan sun zauna ne Kawu yace ta kira su Mairoji, suna zuwa zuka gaidasu da hausarsu dahar yanzu bata gama fita ba, nan suka nemi jin asalin su yan ina ne,ba wani bata lokaci Mairoji ta fada musu dun abin daya faru dasu, har zuwa gudowarsu, numfashi suka sauke Kawu yace"yanzu kenan ke Bad'ejo juna biyu ne dake, harna kusan wata biyu da wani kwananaki, ba komai Allah ba azzalumin sarki bane, kuma ba azzalumin bawansa bane, sai shi nawan ya zalinci kansa".



     "Ammyn su, ga amanar yara nan ahannunki, ki kula dasu kamar yaranki duk da bani da matsala dake ta wannan fannin, fata na Allah ya taya mu riko, kuma inshaAllah zan cigita anemo ahalinsu".



Kai Ammy ta gyada tana jin kaunar su dukansu tare da dinbin tausayinsu, Salman kuwa banda bata fuska babu abinda yake, dan shi kam baiji dadi ba zasu zauna musu agida, Allah yayi shi da dankaren tsantsani.



    Gwalo Huda take mai dan tuni ta gano sa, daman kuma gasu abokan fada.



Cikin dan kankanin lokaci sai ga rayuwarsu Mairoji ta fara sauyawa, awata biyu da sukayi har anyi musu cuku cukun makaranta, Salme zata fara daga primary 4, Mairoji kuma js 3  tunda dole sai an sake mata wasu takardun, Bad'ejo ce dai suka bari saita haihu, tunda ita tana js 2 daman abunnan ya faru.



++++



    Acan Rugar Na-ma'u kuwa Goggoji hawan jini ne ya kada ita, dan ta kasa fidda rai da ganin Mairoji, ada can tana yawan mafarki da ita tana neman dauki, amman adan kwanakin bayannan, batayi sai dai da zarar ta tuno ta gabanta zai ta faduwa.

    Ga Tako da take bata kulawa sosai, haka daga Dutse kusan ko yaushe Alhaji Badan yana hanya shida matarsa dan ganin lafiyar Goggojin, Ahmad tuni ya koma bakin aikinsa, sai dai ko yaushe suna waya da Tako yana jin yanda jikin kakar tasu yake, da kuma sanin halin da ake ciki akan Mairoji.



     Asalinsu.

Alhaji Muhammad Saje, haifaffen Borno ne, mahaifinsa shi ne shehin Borno, su biyar ne agun babarsu awajen uba kuma su goma sha daya ne, atsakanin iyayensu mata babu kazamin kishinnan, domin suna zaune ne lafiya.

    Kishiyar babarsu suna kiranta Hajja Yanzi, babarsu kuma Hajja Gana, yaran Hajja Gana biyar, Mahmud, Falmata, Baraka, , Sa'adatu, Muhammad.

   Ita kuma Hajja Yanzi tana da shida, Baba Gana, Hajja Yaana, Safiyya, Saminu, Lawal, sai Aliyu.

   Mahaifinsu wanda suke kira Ya Malam, yana matukar kaunar 'ya'yansa, kuma hakan bai hana ya basu cikakkiyar tarbiyya ba mai kyau, sun taso cike da son karatu na arabi dana boko, sai dai yan ubancin dake tsakaninsu ya musu katutu.



Muhammad kaf cikinsu shi ne karami, kuma sai Allah ya bashi farin jinin yan uwa dan dukda yan ubancin dake tsakaninsu yan dakin Hajja Yanzi suna sonshi sosai, ya samu yayi karatunsa lokacin daya gama sakandire Allah yaiwa Shehu rasuwa, bayan gama zaman makoki aka daura Mahmud shi ne zai gaje shi, da fari ya amince, sai da ya rage kwanaki a nada shi sai ya samu iyayenshi da zancen baya so abawa Baba Gana, Babarau bata ji komai ba, sai fatan alkhairi da tayi kawai , amman sauran yan uwansa sunji ba dadi dan sai da suka nuna hakan, bayan an nada Baba gana,  sai yazam kamar wani mulkin garin aka bashi gaba daya, sai ya fara takurawa yayan Hajja Gana, inda ya sa aka kullawa Mahmud sharri wanda yaja dole suka bar gidan, suka koma can wata unguwa daban, anan ma basu tsira ba, shekarsu biyu ya kuma hada musu wani tuggun daya fitar dasu daga borno gaba daya, yankin Hadejia suka yada zango, iya su uku, tunda matan suna gidajen mazajensu bada su suka tafi ba.



     Inda suka sauka kyauye ne sosai, can gaban wani kogi mai suna *Gilima*, sun dauki kusan shekara biyu sannan Mahmud yayi aure, yana zaune da matarsa bafulatana, mai suna Hasiya, sunyi haihuwa ta biyu Allah ya yiwa Hajja gana rasuwa, bayan nan da shekara biyar shima Muhammad yayi aure.



   Kasancewar Allah ya bawa Muhammad yalwar saje da cikar gashi afuskarsa sai mutan wajen suke kirkiransa da malam saje, tun baya son sunan har ya hakura ya ke amsawa, ahankali kuma sai ya fara tara shanaye da kananun kiwo, ganin yawancin fulanin kusa dasu duk sun dawo wajen da zama, kafin cikar shekara biyu sai ga shi ya zama babban gari, to kusan Malam Saje da Malam Mahmud su ne masu alimin cikinsu sai mutan wajen suka nemi da Mahmud ya zama shugaban yankin, amman yaki yace su bawa kaninsa shi yafi dace wa tunda shi ne matashi.



    Sunyi na'am jama'ar wajen, nan auka bashi matsayin shugaban yankinsu inda aka sawa wajen da suna *RUGAR SAJE*, kafin wani lokaci sai gashi rugar ta bunkasa dan harda yar kasuwa aka samu awajen, matar Saje tana goyon danta na Fari Badamasi, Allah ya karbi Malam Mahmud sakamakon motar shanu da tabi takansa, Saje yaji mutuwar nan dan ya tashi ba shida kowa nasa sai matar sa da yaran da Mahmud ya bari.

    Bayan Hasiya ta gama takaba ta koma garinsu mai suna Darai inda madakin garin ya nuna yana sonta, kuma daman abokin Mahmud din ne, Saje shi ya shiga ya fita yaga abun ya tabbata dan yasan kamar ta koma wa gidan Mahmud ne.

   Yaran dda ta bari, Maryam matar Saje ita taci gaba da rikonsu, Aminat, suna ce mata Tako, sai Mariya wadda taci sunan Hajja Gana, suna ce mata hajja, sai Sa'ada wadda taci sunan babar Hasiya kuma kanwar Mahmud, duk kan sau Goggoji matar saje ita ke rikeda su, lokacin tana goyon Safiyya.



    Bayan wasu shekaru yan matan duk sun tasa dan har aurar da Tako da Mariya, sai sa'ada da batayi aire ba dan ita kan dan uwanta take so Badamasi.



    _Wayyo....hannuna, wayyo ido na=Ø%Þ=Ø%Þ=Ø%Þ=Ø%Þ_

*Mmn Mu'ayyad.*





    *RUGAR SAJE*



  By Nusaiba Ayuba Suleiman



Wattpad@nusysa

IG@Nusaiba A.S.Sarkin zango



    *FITTATU 18=ØÚÜ 2 0 2 1=Ø¥Ü*



–&

*HOME OF QUALITIE'S WRITER'S ASSO=ØÚÜ*

```{{The Home Of Qualitative Writers That Are Educate Humanities}}```

https://m.facebook.com/story.php?story_fbid=106249334371950&substory_index=0&id=106248871038663&sfnsn=mo

         

            *œ&þ{{H.Q.W.A=ØÚÜ}}
'þ*

(3E 'DDG 'D1 -EF 'D1 -JE.



_Deducated to my sweet Mamah=Ø
Þ_



_5_



    Arayuwar Sa'ada babu wanda take so sai Yaya Badan, Allah ya jarabceta da soyayyarsa, yayinda shi kuma yake nuna bai san tana yi ba, bawai ko bata da kyau ba ko kyan kira, ah ah kawai dai shi baiji sonta acikin ransa bane banda na yan uwantaka, Malam Saje da Goggoji duk sun san da wannan abun amman sai suka zuba musu ido kawai, Sa'ada taci gaba da korar manema aurenta, shi kuma Badan ya maida hankali kan karatunsa da yake acan garin kano.



    Bayan ya kammala makaranta ne sai aikinyi ya gagare sa, tunda ba wani babba bane dashi daya sani bare ya kai masa kokon neman alfarma, ganin haka sai kawai ya koma sana'ar gado noma da kiyo, ina nan danan ya gida wani karamin gidan gona, ya zuba shanaye da tumakai, ga kaji da zabbi , cikin kankanin lokaci sai gashi Allah ya dafa masa, masu kudin makotaka dasu suna zuwa siyan shanaye dan shi baya kai dabba kasuwa, awannan kasuwancin daya fara ne, Malam Saje ya matsa masa da batun auren Sa'ada.



   Da fari, kin amincewa yayi sai dayaga bacin ran iyayennasa sosai kafin ya yarda, ba wani bata lokaci aka tsaida ranar biki, tunda abu ne na gida ba wani tsayawa za'ayi bata lokaci ba.



    Madakin garin Darai shi ya zama wakilin ango, Malam Saje ya zama na amarya haka aka bikin cike da farin ciki, da kwanciyar hankali, shekararsu biyu ta haifi danta na miji, ranar suna da yamma ciwon ciki ya turnike ta kafin akaiga asibita rai yayi halinsa, Badan yaji mutuwar kamar zaiyi hauka, haka aka share zaman makoki, aka watse,bayan kamar shekara biyu da rasuwar Sa'ada,  wani uban gidansa dake garin Dutse shiya sama masa aiki a ma'aikatar ruwa ta jihar, sannan ya hada da basa kyautar 'ya sukutum, wannan karon baiki ba ya karba iyayensa sunyi farin ciki sosai sukamai fatan alkhairi da dacewa.



   Yarinyar da aka bashi da wayewarta dai dai ta zamani kuma t ataso agidan dattijai, wanda suka san girma da arziki, bayan bikin ta nemi alfarmar ya dauko mata Ahmad dake hannun  Tako, ita zataci gaba da rikesa, da fari danginnasa sunki, amman da ta matsa sai suka yarda ya dauke sa ya bata, wani abin mamaki da farin ciki shi ne yanda ta dauki son duniya ta daurawa Ahmad, komai ta samu shi, gashi har kusan shekara da auren bata taba yin koda batan wata ba, Ahmad nada shekara hudu ta samu ciki danginnan sunyi murna sosai.



     Safiyya kanwar Badan, mai kimanin shekara sha shida ita tazo ta zauna mata saboda laulayin take yi mai matukar ban wahala, tana gidan kafin hutunsu ya kare, wan Anty Aisha matar Badan ya kawo musu ziyara anan yaga Safiyya ya kware mata, so abunka da duk gida ne shima ba'a dau lokaci ba aka aura mata shi.



    Lokacin ya'yan Goggoji biyar ne, Badan , Usman, Mahmud, Safiyya, sai autansu Abdulmalik, 'yayan Mama Hasiya kuwa, Aminatu, Mariya, Sa'ada, sai wadanda tayi agidan madaki, Rabi'u, Ibrahim, sai Salma. Kusan wadannan ahalin sunajin kansu ne kamar uwa daya ce ta haifesu, don wani irin soyayya da kulawa suke bawa junan su.



Aisha da danta na miji wanda yaci sunan dan autan su Badan kuma sunan mahaifinta Abdulmalik, tun da ta yaye shi take zuba idon ganin wani cikin amman Allah bai kawo ba, tun tana sa rai har ta hakura ta fawwalawa Ubangiji, dan tasan yana sane da ita, Ahmad da Malik sun taso da wata irin kaunar juna, ko kadan daya bayason gainn bacin ran daya, haka idan daya baida lafiya to tabbas zaka samu shima dayan yana tayashi, haka suke taso tamkar tagwaye, dan kuwa Malik badai girman gabba ba, babu wanda zai kalle sa yace Ahmad ya basa shekaru har biyar, abangaren halaye kam, Ahmad nada saukin kai, sannan kusan ko yaushe fuskarsa a sake take, da wuya kaga bacin ransa, sabanin Malik da Goggoji kemai kirari da 'Sa kake baka dariya sai hamma, duk wanda yaga dariyar ka yaga mutuwa' wannan kuwa haka yake dan idan kaga Malik na murmusawa to tabbas ya gano wani salon muguntar.



Abangaren ra'ayi ma sai aka samu banbanci, dan Ahmad koda ya gama karatunsa sai ya fara aiki ne da matattarar man fetur na kasa, inada ya koma Delta da zama bayan sun bashi gidan zama da masu mai hidi ma, ga kuma albashi mai tsoka, shi kuwa Malik koda yai digirinsa na biyu a business sai ya bige da buga kwallo, inda yake a babbar kungiya ta Arsenal, ba yanda iyayensa basuyi ba ya sake sana'a, amman sai ya nuna wannan din yake so, hakan suka kyale sa bayan sun mai fatan alkhairi.



Abangaren Safiyya ma tana zaune lafiya da maigidanta, domin irin tuzuran nanne, wanda sukan dade basuyi aureba, sosai kuwa yake nuna mata kulawa, dan har lokacin bata haura sha bakwai ba, suna cikin shekara ta kusan goma da aure sannan ta haifi danta namiji,inda yaci sunan Muhammad, bafa kuma ba sai daya shiga firamare sannan tayi mace, inda aka samu Maryam, irin yawon arba'in da ake bayan an gama wankan jego shi taje gida alokacin, kwanan ta daya da zuwa ta shirya zuwa inda Hajja take aure awani gari tsallaken ruwa, dukda Goggoji taso hanata zuwa amman sai ta nuna tana son zuwan tunda ai daman yawon arba'in ta fito, ba yanda Goggoji tayi haka ta hakura ta barta suka tafi, ita da dan autansu Abdulmalik, tafiyar da bata dawo ba kenan sai gawarta aka kawo, shi kuwa Abdulmalik ma ba'a gansa ba duk neman da akayi, kuma abin ta'ajibi shine 'yar tata babu abindaya sameta sai ruwa data sha.



Asibiti aka kai yarinyar inda Aisha matar Badan tayi zaman jinyarta, sukuma anan gidan sukayi zaman makokinta, lokacin kam Malik yaji mutuwar sosai, dan kaf kannen babannasa babu wadda suka shaku kamar Safiyya haka shima Ahmad sunan ji da ita sosai, bayan an shafe zaman makoki ne Maman su Malik ta nemi alfarmar Goggoji ta bar mata Mairoji ta ci gaba da riketa, duk da anga yanda ta rike Ahmad cikin gaskiya da amana kamar dan cikinta, amman haka Goggoji ta hana ta Mairoji dan Allah ya dasa mata kaunar yarinyar ne.



Malam Saje kaf cikin jikokinsa da yake dasu dana dan uwansa day mai dasu nasa, babu soyayyar wanda tafi ta Malik girma awajensa, yana son shi kamar ya maidasa ciki, zuwan da Malik din yake yi wajen sa yin hutu tun yana sakandari yake cemai"kaga Audu....indai ina da rai da lafiyata naga aurenka, to ka tabbata bakada mata sai Mairoji, ita nake son ka aura ka tsaya mata arayuwa, dan Allah ko bayan ba raina ka cika min wannan buri nawa kaji".



Ire-iren wadannan maganganu tun yana boyesu har ya samu Mamansa da maganar yake sanar da ita, sau tari idan yazo yana fada mata sai dai tayi dariya kawai, dan itakam Ahmad dinta take wa sha'awar aure Mairoji, yanda yarinyar take nitsattsiya ba tada rayan kai na yaran zamani ai da salihin dan ta ta dace ba da wannan baudadden ba, wani zubin idan yazo yana bata labarin hirar da sukayi da Mallam sai dai tayi dariya kawai, ko kuma tace"babana dan Maliki.....uwata fa babbar macece, ba matar yara bace, tanadin da nake mata babba ne yaro dan haka kaja baya".



Shima idan ta fadi irin hakan dariya yake yace"Mama ada idan Mallam yana fadamin Mairoji ce matata anan gaba, bana jin komai, amman yanzu idan naji bai fada ba har haushi nake ji, ajiyar Malam yanzu ta dawo ajiyata, ni ne dai wanda kike wa wannan tanadin".



Arananr daya fada mata haka, yini tayi tana mamakinsa, dan itace ta haifesa amman ba zata yarda ba idan wani yace mata shi ya fadi haka ba, yanayin sa kadai ya isa ka gane waye shi, irin yananin fuskarsa ma babu alamun wasa ko wargi aciki, amman wai shi yake fada mata abunda yazo masa haka kai tsaye, kenan soyayya ya fara ko me, ko kuma dai yanajin Mairojin ne aransa bawai yana sonta ba.





Rayuwar Mairoji ta tashi ne rabinta agidan Mama rabinta wajen Goggoji, da taimakon Allah dasa bakinsu Mama da Ya Ahmad Mairoji ta yi firamare, dan Goggoji da hanawa tayi, dakyar ta yarda tayi to kuma kutso kai da Mamuda dan gidan Tako yayi da sunan yana sonta sai, Goggojin ta kuma matsawa lallai aure za'a mata ai ta isa, tunda kawayenta wasu duk suna dakin miji, da kyar ta bari tayi karamar sakandari, tana gamawa kuwan ta fara neman yan uwa don maganar aurar da ita.



Hamma Gid'ad'o, watau Madakin Darai kusan shi yake tsayawa akan komai na gidan, dan tun bayan mutuwar Mahmud shi Malam Saje yake ganin amatsayin dan uwansa.



Agarin Hadejia akwai wani abokin Malam da yake aurar da jikokinsa, to ya gayyace shi, da fari ma yaki zuwa saida Goggoji tayi magana sannan ya shiryawa tafiyar, ranar daya tafi da kwana biyu mahara suka ritsa Ruggar inda auka yi ta'adin da barna sannan suka wuce da yan mata uku.



Yana can yaji labarin abindaya faru ba shiri ya juyo gida amman sai yazo ya tarar da wayam, dole shi ma sai gidan Tako yaje amman ya ce bazai zauna mata anan ba zai koma can garin Darai ya zauna kafin aga yanda hali zaiyi.







+++++++



Atafi-tafi dai su Maoroji sun dau wani lokaci agarin kano, dan sosai Ammy take basu kulawa da nuna kauna, yanzu har Mairoji ta fara makaranta ita da Salme, sai dai kayan da aka basu ne na makarantar har yanzu basu yawe da saka shi ba, siket ne iya gwuiwa grey calour sai milk din riga da grey din baby hijab, da safa doguwa da kombas.



A amakartar da Mairoji take akwai wani Fahad daya masifar takurata da shirar banza wai shi sonta yake, tun bata kulasa har tazo tana dan tsayawa suyi yar magana ta wuce.



Yauma sun fito break kawarta wata yar gayu yar kyakkyawa haka ta kamo hannunta tana mata nuni da kai, kallon wajen Mairoji tayi suka hada ido da Fahad daya harde yana kallonta, karasawa wajensa sukayi da sallama, amsawa yayi yana kafita da ido, kanta ta sunkuyar tana wasa da hannayenta, kallon wajen yayi yaga ba yawaitar mutani ya kamo hannunta ya na dan murzawa, cikin kasa da murya yace"baby...kullum kara kyau kike, kuma har yanzu kinki yarda mu zama abu daya, nifa dan love ne ya kamata ki gane wannan, gashi gobe ne birthday dina ina gayyatarki kizo, ki shirya zan aiko a daukeki za'a kawo ki wajen da muke, idan kinzo na tabbata kina so na, idan kuma baki zo ba, jibi zaki xo jana'izata dan zan ahi poisen ne, gwara na mutu na huta da naganki akoda yaushe amman kuma baki amshi tayi na ba".



Sakin

Please Login or Register in order to submit comment