You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

ba mai zai sa ki furta duk abinda ki ka furta ko
so ki ke ki zama silar tashin wata sabuwa fitina a cikin Gidannan wacce ba zamu iya kashe ta ba,in kuma
rikicin Addini ki ke son tadawa sai ki sanar da mu mu sani tunda wuri".

''Au Alk`asim me nake gani haka,ashe kai ma an shanye ka ban sani ba?"Baba Asabe ta tambaya cike da
mamakin abinda ta ga yayi.

" Ka ga Alk`asim ka fita a cikin wannan maganar kar abun ya girmama,don wallahi hak`uri na yafa
k`arewa".cewar Hibba

"A'a Hibba Dan Allah kar kice haka, kiyi hak`uri kin ji", kallon shi ya maida hankalin shi kan Cecelia da ke
ta faman `bata rai,da son barinta ta bi kadin laifin kofin zarafin da akai mata.

"Kin ga please and please Sis kiyi hak`uri,don't mind her shi's out of her senses,please Dan Allah", sai a
lokacin Zuciyar Cecelia ta fara yin sanyi ,kallonta ta maida kan Yayah Zaliha yanda taga tana ta `ba`batu
da hayaniya yasa ta yarda da Maganar Alk`asim cewar bata da hankali, bai bar su ba sai da ya tasa
k`eyarsu ya fitar da su daga Gidan daga ita har Hibban,daga k`arshe ma har cikin motar shi yasa su ,shi sa
kan shi ta maida su Gida,bai bar Cecelia ba har sai da ya ga ta yarda gami da sakankancewa Yaya Zaliha
ba ta da isasshiyar lafiya sannan ya tafi,gami da gargad`ar Hibba akan kar ta kuskura ta sake tada batun
ta bar shi su tafi a haka,.
Ko bayan tafiyar Hibba ta je da niyar ta bata hak`uri, dakatar da ita tayi gami da nuna mata ta riga da ta
fahimci daga inda matsalar ta ke,komi ya riga da ya wuce a wurinta.

Sosai Hibba ta ji daɗin hakan nan ta barta domin ta je ta sauke Sallahr da ke kanta,ita kuma ta fad`a
bathroom don tai wanka,tun kafin ta fito ta fara jiyo wayarta Na faman ringing a gurguje-a gurguje ta fito
ta nufi inda wayar ta ke.

"Oh my friend Gloria how fa now ya ki ke,I miss you".

"Ina lafiya k`awana gobe nake son in taso saboda ina son ayi komi na bikin ki tare da ni"," Yeehhh Na ji
dad`in haka sosai shi yasa na ke k`ara sonki".

"Hmmmm ai dole ne in yi ina Broth Daniel yake fatan dai yana lafiya, kin san har da son sanya shi a Idona
da nake ya sa nake son halartar bikinnan da wuri,bana so a ce ya zo bamu had`u da shi ba,kin san har
yanzu ina jin sa a cikin raina na kasa iya mantawa da shi"...." Gloria Anya kuwa...,wai me ya ke damun
ki,kin fa san Broth Daniel yayi Aure yanzu ma haka yana d`iyarsa ba za ki kyale shi ki huta ba,ki samawa
kan ki lafiya Kema ki fiddo Miji mai sanki ki aura ba,kar fa ki manta ba addinin mu d`aya da shi yanzu ba
".

" Cecelia ba zan iya ba,ba zan iya cire son Daniel daga cikin Zuciyata ba kuma ni Addinin shi bai dame ni
ba,in har zai Aure ni,kuma wai tsaya ba Mace ce ta yaudare shi har ya bar Addinin sa na gaskiya ba,to ba
kya tunanin haka nima zata kasance ta nawa `bangaren ba".

"Hehhh Gloria I'm swear ba ruwana ,kin san yanda yake Son Matarsa da `yarsa kuwa,domin yanzu haka
ina Gidan su Gobe za mu tafi Jos d`in tare".

Zumbur Gloria ta mik`e zaune daga kwancen da ta ke,tace," Seriously da gaske ki ke Cecelia ",sai da
Cecelia ta d`an `bata fuskarta kafin ta bata amsa da cewa," Eh mana da gaske nake kin san ai ba zan maki
irin wannan wasa ba".

"Na sani....na sani Cecelia, but ina neman alfarma a wurin ki na had`a ki da Allah kar ki cemin a'a, ban
san mai zai faru ba in baki amince ba".ta kai zancen muryarta na marairaicewa.

" Shikenan shikenan faɗamin me ki ke so a garuni,amma ki sani idan har abun akwai cutarwa a cikin sa
ba zan yi ba".

"No...no there are no any harm in it,kawai dai ina son zan biyo flight gobe ya sauke ni nan Kano, ke kuma
sai ki san yarda za ki sa Broth Daniel ya yarda ya amince mu tafi tare da shi zuwa Jos a motar sa"....

" Wait.. Wait.. Kina nufin gobe tare da ke zamu yi tafiya tundaga nan Kano har zuwa Jos ?".

"That's my friend haka nake nufi",shiru na wani d`an lokaci kafin tace," Anya Gloria ba wani abun a `boye
ki ke shiryawa ba da har ki kai saurin yanke wannan hukunci a wannan short time d`in ba".
"Oh Jesus na rantse maki ba abinda nake shiryawa kin san ni fa you know me,duk abinda zan iya aikata
kin sani,just one thing I know ina son ganin sa,ina son in ganni a kusa da shi kin san mun yi taking d`in
long time ban gan shi ba".

Shiru Cecelia tai tana,mai son gasgata abinda Gloria tace da ita,horns d`in motar sa da ta ji ne ya sa ta
yanke hukunci cewa da ita," let me try but amma ki sani ba zan wani zafafa duk hukuncin da ya yanke ya
yanku,zamu d`auke shi a haka kawai ".

" Eh I'm agree Na yarda",Gloria tace ta na mai saurin a je wayar tana mai rufe idanunta gami da had`e
hannayenta wuri guda ta fara addu'ar samun nasara.

"My Broth har ka dawo?",ta tambaye shi tana mai kama kanta alamun tana da abinda take son cewa,"
Are you OK Cecelia, ko da akwai wani abun da ki ke so ne?".

In'ina da kame-kame ta fara Wanda har sai da ya sa gaban Hibba fad`uwa don ita a tunanin ta ko abinda
ya faru a Gidan su zata sanar ma sa da shi,kafin ta bud`e baki ta samu damar dakatar da ita har ta riga da
da cewa.

"You know my friend Gloria wannan neighbor d`in nan ta mu,...wacce na baka labarin sun koma Lagos
da zama?"ta,kai zance a d`an d`arare.

" Oh Gloria your best friend ?","Yauwa ita mun yi waya da ita ne d`azu take cemin gobe zata bi flight
daga can Lagos d`in zuwa Jos don tai attainding my wedding ceremony ,amma yanzu cikin rashin sa'a ta
kirani ta ce bata samu ba sai flight d`in zuwa nan Kanon,ta ce min tana son zuwa amma ba ta da wata
hanyar,da zaran ba ta samu wannan damar ba shikenan ba za ta attainding ɗin bikin ba, shine na ce in ba
damu in tambaye ka ta biyo flight d`in zuwa nan Kanon in yaso sai mu tafi can Jos d`in tare da ita,idan ba
damuwa,domin na dakatar da ita na ce sai na tambaye ka".

"Oh Cecelia me ye abun damuwa a cikin wannan, bikin ki fa zata zo,AI ko daga Lagos d`in tace inje in
d`aukota ai zan je in d`aukota balle kuma daganan zuwa Jos, kar ki wani damu ki ce mata ta shirya ta
taho kawai abinta zamu jirata", wani tsalle Cecelia ta daka tana mai fad`awa jikin sa gami da jero nasa
godiya kala-kala.

" Kin ga sake min Miji kar ki je ki karya min shi",Hibba tace tana mai k`ok`arin rabata da jikin sa,"Kai Sis
duka ni d`in nawa na je da zaki ce zan karya shi ?","A'a ba anan take ba,yanzu sai ki ga tsautsai ya gifta ki
bar ni da Allah yai abun,bayan ke kuma fa naki Ango na can sabo dal yana jiran ki".

Rufe fuska Cecelia tai ta nufi d`akinta tana mai had`awa da gudu ,wayarta ta d`auka gami da kiran Gloria
kamar jira taje ta d`aga tare da cewa,"My friend what is the feed back fatan dai anyi nasara ?","Yeeee
we succeed mun yi nasara",wata k`ara mai k`arfi Gloria ta saki gami da mik`ewa tsaye ta fara tsalle akan
gadonta,Wanda wannan k`arar ce tasa Cecelia saurin kashe wayar ta.
*JADEEDAH*



(It's a story of two love birds who are so different from each other )

STORY & WRITTEN BY :

(*Cwt~Sumiey*)

Marubuciyar littafin

MENE NE ABIN YI ?

KARAGAR MULKI

And now.....*JADEEDAH*



https://chat.whatsapp.com/CWkZfMqvD4H0mtd7WW6Xbz

https://whatsapp.com/channel/0029VapqU8C002T5Bz8RSQ0a




BOOK 1




PAGE 12 ❤

"Wawooooo my friend you look so awesome, kin ga yadda skin d`in ki ke shining and glowing wai
mene ne sirrin ?".

"Yeehh Thanks my dear it's a God luck,bayan haka ba wani abu,amma na gode da yabon ki", ta kai
zancen ta na nai jujjuya jikin ta,ta d`an dakata ta na mai cewa," Ina my love yake na ji ban ji motsin kowa
a Gidan ba".
`Bata fuska Cecelia ta yi kafin ta ce da ita,"Za ki fara ko,kin san na fad`a maki bana son irin haka tunda
farko,Na gaya maki Broth Daniel yana san Matar shi,kuma ma Matarsa na son shi,Matanan fa
bahaushiya ce kuma kin san halin Hausawa ba sa da kirki ko mutunci in dai akan Mazajensu ne".

Yamutsa fuska Gloria tai kafin tace,"I swear bata gabana,haka kuma duk abinda za tai ba zai tsorata ni
ba ko da ko kan bala'i da masifa zata rik`a cizon sama ne,muddin Daniel zai nuna yana sona ta nayi
alk`awari sai na Aure shi ba tare da duba da ita ba,Matsala d`aya ace bai nuna interest d`in sa a kaina
ba"..

"God for bid in dai Broth Daniel ne ma ba zai nuna ba domin kin san ni bana son tashin hankali, ba zan
so ki zama silar tarwatsa farin cikin da yake samu a Gidan shi ba".

Cikin mamakin jin abinda ya fito daga bakin,ta ce" Cecelia me wannan maganar taki take nufi ,kaddai
ace kina nufin kin fifita wannan baren kaina,kamar fa haka maganganun ki su ke nunawa,in ko haka
ne".....ta dakata sakamakon jin nuryar Hibba na cewa, "Ba dai har bak`uwar tamu ta iso ba,a sannu da
zuwa your highly welcome".

"Yauwa sannu Aunty ya Gida mun same ku lafiya,ya kuma shirye-shiryen biki ?".

" Alhmdllh kumi na tafiya yanda ya kamata, ki samu wuri ki zauna Cecelia ya akai ki ka barta a
tsaye ,yauwa gama breakfast can ki had`o mata may be ko tana jin yunwa kinsa ba kowa ke son ya ci
abinci a yayin da zai tafiya ba",ta kai zancen tana nai maida kallonta akan Cecelia.

"Muna gaisuwar yaushe gamo ne shiyasa, amma bari in had`o mata", tayi hanyar derning d`in har ta
fara bud`e wermars d`in abincin ta dakata ta na mai cewa," Amma dai Broth fita yai naga kamar ban ga
motorn sa a waje ba?".

"Eh fita yai ya samu urgent call ne a office shiyasa ya tafi can ko breakfast bai yi ba".

"Eyyah nasan hankalinsa nanan domin ya ce min baya san mu yi dare a tafiyarnan"....

Cikin rarraba zance Gloria ta dakatar da ita da cewa," Am...uhmm...ki bar zuba abincin ina so zan yi
using resting room,in..Na fito sai ki zuba min".

"OK badamuwa muje na raka ki",koda shiga Gloria bathroom kai kawo ta farayi tana mai cewa," Ya
zanyi,ta ya zan iya dakatar da Cecelia daga zuba abincin nan I need to eat with Daniel, Na kwashe almost
a year ban had`u da shi ba,yau na samu damar da zanci abinci tare da shi ya za ai in wasa da ita,No haka
ba zata faru ba I will use this opportunity I can't not lost it ".

Shiru-shurun da Cecelia ta ji ne yasa ta fara knocking bathroom d`in ta Na mai kiran sunan
Gloria,"Are you ok,Na ji shiru har yanzu ba ki fito ba ?"," I'm coming" ta bata amsa a tak`aice.

"Dem it,wai me yake damun Cecelia ne,Anya kuwa zata Goya min baya in samu hanyar da zan mallaki
Daniel kuwa I don't think so,bana tunanin haka,amma ko in har ta juya min baya ta biye ma wannan
Hausa girl d`in nan ta ci amanar zaman tare,dan haka ba zan barta ba,dole zan bi komi har in gano
abinda ke cikin Zuciyarta sannan in yi maganin su gabad`aya", wannan duk maganganun da Gloria ke yi
ne a cikin Zuciyarta.

K`arar bud`e Gate da shigowar Motar shi cikin farfajiyar Gidan ne yasa Gloria saurin nufar hanyar fita
daga bathroom d`in bayan murmushin cin nasara ya bayyana a kan fuskarta.

"I'm sorry Beb I keep you wait cikina ne ya d`an `baci that's why", Gloria ta kai zancenta tana mai sosa
k`eyar ta.

"Hhhhhhhhh my friend kenan k`ya gama `boye-`boyen ki I know you,I kno everything, ke dai kawai ki
ce kina son ki yi breakfast da my Broth,ba sai kin shiga bathroom kin rufe kan ki ba".ta kai zance cikin
yanayin tsokana.

" Au Abar tsokana ma Na zama wurin ki ko,za ki shiga hannuna ne"...."Oh sorry ba haka nake nufi
ba,biside ma ai ni banga laifin ki ba you can fight for you love,but I beg you kar ki tada mana wata fitina
ki bari mu gama wannan bikin lafiya lafiya daga baya sai musan me zamu yi".

"Okay I promise you babu abinda zai faru,har mu gama wannan bikin lafiya, dama babban burina ki
bani goyan baya a cikin wannan tafiyar nasan in har hakan ta faru zanyi nasara",sai da Cecelia ta dafa
kafad`arta kafin ta ce," Don't worry I'm with you always, I will support you hundred percent, zamu shirya
komi yanda ya kamata,sai mun dawo da Broth Daniel kan hayar da ta dace,ko kin manta shi kad`ai ke
gare ni da zan iya Kira da sunan family taya zan barshi ya su`buce min,sai dai ki sani a can k`asan Zuciyata
ina jin tsoro kar Garin ean in dawo da shi cikin rayuwata ya su`buce min gabad`aya ".

"In Jesus name haka ba zata faru ba,komai zai tafi smoothly yanda muka tsara".

Shigowar Hibba sa`be da Jadeeda da ta koma barci ta dakatar da su daga zancen da suke yi," Am kuyi
hak`uri Na shigo muku without a knocking ba na son in yi knocking k`aryar ta tashi Jadeeda daga
barci,domin barcin bai nisa ba,ku fi to muyi breakfast d`in Abban Jadeeda ya dawo yana jiran mu".ta kai
zancen Zuciyarta na son hasko mata wani gi`bi da ta hango a cikin zancen na su,A'uxiyya tai gami da
watsar da zancen da Zuciyar ta ta take tsamata don son kyautata masu zato,kamar yanda Addini ya
koyar.

"Am sorry Sis mun tsaya firar yaushe gamo ne,kin San an kwana biyu ba a had`u ba", murmushi Hibba
tai tana mai juyawa tayi gaba a tare su ka nufi hanyar zuwa dining d`in,tunda idanun Gloria suka sauka
akan fuskar Abbakar k`afafuwanta su kai mata wani irin sanyi,kwarjini,kamala da haibar da ta gani
kwance akan fuskar suka sa Zuciyarta ta fara bugawa da sauri da sauri,a d`arare ta iya zama kan d`aya
daga cikin kujerun wurin,muryarta hard`ewa ta ce da shi," Brother Daniel Good morning "

"Morning Gloria how are you and how about you journey ?".

"Bro everything are okoy,kasan flight Na biyo so that's why tafiyan bai wani wahalar da ni ba"," That's
good Na ji dad`in hakan,what about Pastor Emeka,Momy Rebecca and your brother Richal ?",'Ahhh
they're fine duk suna lafiya,kasan Dad ya samu k`arin girma tun da dad`ewa, Momy ta zama woman
leader a Church d`in da Dad ke jagorantar,My Brox kuma ya na Canada karatu".
"Masha Allah labarin yayi min dad`i komi na tafiya yanda ya kamata,what about you,wanne mataki ki
ke, je a yanzu?".

Wannan tambayar ba k`aramin dad`i tai ma Gloria ba har wani blushing tafara yi gami da k`ara gyara
zaman rigar jikin ta kafin ta bashi amsa da cewa," Na fara masters anan Herbal institution dake nan
Lagos "....

" Haba mana my Brox,ya isa haka mana ,ku dakatar da wannan hirar mana ko kun manta muna da
tafiya mai nisa a gaban?","Hehhh Cecelia mene ne haka,shin kina son raba hirar zumunta ne komi ?,mu
fa d`au long time ba mu had`u ba".

Dariya Abbakar yai kafin ya shiga tsakanin su da cewa,"Bar ta zumud`i take ta na son zata ga groom to
be d`inta kin san ta yi spending almost a ten days ba tare da ta gan shi ba".

Baki sake Cecelia ta bisau da kallo ita kanta mamakin jin zancen da ya fita daga bakin sa tai,sosai suka
zage shi da Gloria suna tsokanar ta,duk abinda ke faruwa Hibba na can tana son barcin Jadeeda yai k`arfi
bata san abinda ke faruwa anan Parlour ba.

Abbakar ne ya cire baki ya na nai kiranta da cewa,"Madam a zo a bamu abinci we are felling hungry
",sai da Hibba tai k`asa da muryarta kafin ta mai do mashi da amsa da cewa," Please I'm sorry ina so
barci Jadeeda yai k`arfi ne,but please Cecelia ki yi sarving d`in ku kafin in zo ".

Zaraf Gloria ta mik`e tana mai cewa,"A zauna bari in Sarving d`in ,Na hutashshe ki", Jiki a sanyaye
Cecelia ta koma ta zauna ta bar Gloria da sarving d`in su domin ba zata so suyi jayayya a gaban Broth
Daniel ba,don gudun kar ya fahimci da akwai wata a k`asa,tunda yasan ba hakan a tsakanin su a can
baya.

Gab da Hibba za ta isa dinning wayar hannunta ta fara ringing, ganin kiran Mama Hadiza ya sa ta
fad`ad`a murmushinta kafin ta d`aga ta fara gaishe ta," Ina lafiya Auta ashe har yanzu baku tafi ba ?","Eh
Mama yanzu dai muke shiri zamu tafi ya mutanen Gidan ?","Duk suna lafiya yanzu ma Babanku ne ya ce
in sanar da ke ranar bikin Ummien Jaheed, Yayar ku (Yayah Hanne ta ke nufi bata fad`in sunan ta),da
kuna Umma Jamila za su zo nan Jos d`in su taya ku murnar gami da Allah sa alkairin ".

" Kai Mama na ji dad`in haka sosai Allah ya saka maku da alkairi ya biya buk`ata ya kuma baku aljanar
fiddausi","Amen Allah ya kai ku lafiya ya dawo da ku lafiya","Amen Mama,kin ga kuwa da na sani ai da
na kawo Jadeeda nan in su Ummie Maryam zasu taho sai su taho min da ita"......"Ahir d`in ki Hibba, ba ki
da hankali ne Yarinyar `yar shekara d`ayar za ki aje ki tafi wani waje har na tsawon kwanaki ba tare da ta
Isa yaye ba".

Cikin rawar murya Hibba ta fara bata hak`uri,"Mama Dan Allah ki yi hak`uri,wallahi haka nan na ji bana
son in tafi da ita,kamar wani abun zai iya samunta,gabana sai fad`uwa yake ".

"Addu'a za ki yi tayi,in sha Allahu ba abinda zai faru da ke,dole za ki hak`uri ku tafi tare can ma inda za
ku ahalinta ne danginta ne,suna da hak`k`i ki kai ma su ita su ganta suma,su Santa su Saba da ita".
" To shikenan Mama zan yi ta yin Addu'ar kamar yanda ki ka ce,da zaran mun Isa zan kiraki","Yauwa
`yar Albarka ki shafa min kan `yar rigima mai kukan banza,au na manta yau Jaheed da zazza`bi ya tashi
shiyasa bai zo maki sallama ba ",

"Ayyah Allah ya bashi lafiya zan kira Ummie Maryam sai in yi mashi ya jiki","To hakan yayi kyau amma
ki bari sai kun isa don da yaji ba ku tafi ba zai sanya rigima", To Mamma", da haka suka yi sallama ta
k`arasa zuwa dinning d`in.

Zuwan Hibba dining d`in ne ya rage ma Gloria rawar kan da take,cikin k`ank`anin lokaci suka gama
breakfast d`in suka sake had`a `yan sauran kayan da zasu had`a,Hibba ta goya Jadeeda, wacce har yanzu
take barcinta kana suka d`au hanyar zuwa Jos daga Kano

Sai da su kai tafiya mai nisa kafin Jadeeda ta tashi daga dogon barcin da ta sha,minti kad`an bayan
Hibba ta yi feeding d`inta ta fara kai hank`oran zuwa Inda mahaifin ta yake,"A'a Jadeeda yi zaman ki nan
wurin Momynki,ba zan iya d`aukar ki ba alhalin ina driving".

Duk yanda Abbakar ya so dakatar da Jadeeda k`i tai,babban burinta ta isa gare shi,ganin an hanata ya
ta fara kuka gami da ƙara son sai ta isa inda ya ke.

" Dama Na sani abinda nai ta gudu kenan ke ko kusa ba ki iya zama wuri guda tsaf",Ai ko kamar ta san
fad`a ta K`ara tsandarewa da wani sabon kukan.

Cecelia ce ta fara cewa,"Kai³ Momy ce tai miki fad`a to yi hak`uri kyaleta ba zata sa ashoben bikinnan
ba,kyauta za mu yi da nata",ta kai zancen ta na mai mik`a mata hannu,ba musu ta tafi wurinta
kasancewar ta Yarinya mara k`iwa.

"Wawooooo beautiful girl, ai sai yanzu naga fuskarta sosai,kai she's so beautiful,Babyn tamu
kyakykyawa ce ta zarcewa sa'a", cewar Gloria,da ita sai yanzu ta gamda dominsanda ta zo ta yi barci.

Murmushi kawai Hibba tai ba tare da tace da ita komi ba," Ai tukunna ma sai ma nan da wasu shekaru
za ki ga asalin kyau a wurin my daughter "," Maganar ki gaskiya ce Our Father Lord ya bamu Ikon ganin
wannan lokacin","Amen...Amen Gloria zan yi farin ciki in na riski wannan ranar kar ma ace in ga ranar
bikinta hohoho",Cecelia ta kai zancen ta na mai d`aga Jadeeda sama wacce sai faman wasa da gashin
attache da ke kanta ta ke.

"Yama sunan ta ?",Gloria ta tambaya ta,na mai amsar ta d`auke ta,Cecelia da take kusa da ita ta bata
amsa da cewa" Am sunan ta Jadeeda ",duk yanda Gloria ta so ta mai-maita suna kamar yanda Cecelia ta
fad`a amma ta kasa,madadin ta ce Jadeeda sai ta ta ce Jedeeda.

Sai a lokacin Hibba ta waigo tace da ita," Ba Jedeeda sunan yake ba Jadeeda ne, J d`in harafin a ne da
ita ba e ba".

"Oh Jedeeda, Na gane thanks for your correction", Gloria ta ce tana mai sakin fara'a akan fuskarta da
tunanin ta faɗa dai-dai.

"Ba Jedeeda ba fa Jadeeda", Hibba ta sake gyara mata a karo na biyu.
Duk yanda Hibba ta so ta gyara ma Gloria sunan ta fad`a dai-dai amma hakan ya faskara,kuma wani
abun Allah ita kuma ta kasa hak`uri ta barta ta kirata da Jedeedan,ita kuna sai faman mai-maitawa take.

A karo na ba adadi ta sake bud`baki ta gyara mata.

"Please Hibba ki barta ta kira da iya yanda bakin ta ya iya mana, tun d`azu sai faman abu d`aya ake
yak`i ci yak`i cinyewa"....

" Kamar ya in barta,kana nufin in barta ta cigabada da kiran sunanta da duk sunan da ya zo mata
komin munin ma'anarsa".Hibba ta katse shi k`asa Zuciyarta Na yi mata zafi from no way,ba tare da ta san
daga inda ya zo ko kuma dalilin zuwansa ba.

"No no no I don't mean that, but she try,she can't pronounced it very well, sai ki barta haka".

Sororo Hibba tatana kallon sa ba tare da ta iya cewa da shi komi ba,ba wai don ba ta da abin cewa ba
ne ba,a'a mamakin furcinsa take.

"Kin ga ba wai ina nufin wani abu na daban ba be ba,a'a just bana son abun yai nisa ne,but I'm sorry
naga ranki ya `baci I don't mean that, kuma ke ma ai kin san ina son a kirata da sunan ko,son sunan da
kuma ma'anarsa yasa na yarda har aka sa mata sunan".

" Hmmmmmm si shiyasa ka bada damar da za a rink`a kiranta da kowanne suna ba tare da la'akari da
kyawu ko munin sa ba,`yata fa muslmace ta ya zata rik`a kiranta da sunan kafu".....ta kasa k`arasawa
sakamakon zazzafan kallon da ya jefe ta da shi.

Ita kanta nan take danasani ta rufe ta, gabad`aya ta diriri ce ta rasa me ma zata ce.

"Kiyi hak`uri sister it's my mistake I'm regret ba zan k`ara furta sunan ba, har sai na iya,please I'm so
sorry".

Ko ta,kanta Hibba ba ta bi ba,babban burinta taga ta samu hanyar da zata bashi hak`uri amma ina ko
kallon inda ta ke bai sa ke ba,ranshi a `bace ya cigaba da driving d`in.

Kamar a mafarki wata babbar mota ta nufi kansu,damuwa,firgice da kuma rud`u duk sune suka
rufesa,gashi yana k`ok`arin sauke ko danne damuwar da yake a ciki,ga kuma firgicin abinda take
tunkararsa,amma ina duk yanda ya so ya hana hakan faru bai yiwu ba,sai fa gani yai su suna yawo a
sararin samaniya.




*JADEEDAH*
(It's a story of two love birds who are so different from each other )

STORY & WRITTEN BY :

(*Cwt~Sumiey*)

Marubuciyar littafin

MENE NE ABIN YI ?

KARAGAR MULKI

And now.....*JADEEDAH*

*YOTA*

https://chat.whatsapp.com/CWkZfMqvD4H0mtd7WW6Xbz

https://whatsapp.com/channel/0029VapqU8C002T5Bz8RSQ0a




BOOK 1




PAGE 13 ❤

Da k`yar mai motar da ke bayansu ya iya dakatar da tashi motorn,a gaban idon shi komi ya faru,rud`u
da tashin hankali duk sun baibaye shi,abun tashin hankalin shi kad`ai ne a cikin tashi motar,iya tashin
hankali ya ga tashin hankali, sai da motar ta tsaya dan kanta sannan ya nufi inda take, a yashe a k`asa ya
iske Hibba sai Cecelia da Abbakar da ke kwance cikin motar face-face da jini,da k`yar ya iya matsawa
kusa da su saboda hayak`in da ke tashi a cikin motar yana haki yana tari ya

Please Login or Register in order to submit comment