You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

hanani samun damar lashe kanbun
Gimbiya da ta fi kowacce Gimbiya kyawu, Ado da kuma saka kaya masu tsada,bazan ta`ba barin wannan
damar da na samu ta kubce daga hannuna ba na sha wuya kuma na d`au lokaci mai tsawo kafin in kawo
wannan matakin dan haka ba zan yi wasa da ita ba".

" In ko har haka ne ki na da gaskiya bai kamata ki bar cikinnan ba domin ina da yak`inin ko Alkyabba ba
za ki sa ta yi maki kyau ba,balle a kai kan sauran kayan Ado,cha`b Ai ko mutum goma ba za ki samu
wanda za su ya ba ta ki kwalliyar ba,wata k`ila kuma a samu amma a cikin Bayi amma ba dai `yan cikin
Masarauta ko wad`anda ake gayyatowa ba".

"Na shiga uku in haka ta kasance da ni ban san ina zan sa kaina ba,ina mai tabbatar mi ki da ba zan
sake nuna fuskarta a irin wad`annan taron ba in har haka ta kasance".

Wani murmushin gefan baki Anesa ta yi kafin ta ce,"In ko haka ne kar`bi ki sha ya fito waje kowa ma ya
huta", ta kai zancen ta na mai d`auko ma ta ruwa a d`an k`aramin fridge da ke ku sa da ita.

Amsa Gimbiya Ayush tai ta aje ta na mai kauda kanta can gefe ba tare da ta ce mata komi ba,cikin
mamakin attitude d`in da ta yi Anesa ta ce da ita,"Me hakan ke nufi,kin sa ni a rud`u,ko dai so ki ke ce
min duk abubuwan da ki ke fad`a ba gaskiya ba ne ba,ko kuma maganganun Gimbiya Fadeelah ne suke
son wasa da hankalin ki,Fadeelah ba kowa ba ce face k`anwar ki,har ita wace ce,wanne matsayin ta ke
da shi,me ta taka".....

A fusace Gimbiya Ayush ta dakatar da ita,sai dai ba ta iya ta ce mata komi ba har Saida ta saita
kanta,ta rage fushin da take ciki gami da sassauta zancen da ke d`auke a bakin ta," Kin ga Anesa na gode
da shawarwarin ki da kuma lokacin ki da ki ka ba ni,Na gode da hakan ki zo ki tafi Gida ,zan kira ki daga
baya".

"Mene! ki na nufin korata ki kai daga Gidan ki,akan me,me na aikata,ko shine sakamakon kasancewar
da ke da na yi ?....ni...na ma rasa ne zan ce da ke".

Ko motsi Gimbiya Ayush ba ta sake yi ba,har dai Anesa ta gaji da kallonta da ta ke,ta zari Jaka da car
keys d`in ta yi hanyar barin bedroom d`in Na ta.

"Ki gaishe da Baba Waziri da kuma su Umma Karema", Gimbiya Ayush ta ce da ita,Ko jiyowa ba tai ba
balle ta sa ran za ta bata amsa.

Kwanciya Gimbiya Ayush ta yi hannunta d`aya a saman cikinta ta na shafa shi,a hankali kamar mai
rad`a ta ce," I'm sorry My Unborn Baby,ina son ka so mai yankan shakku dole ce kawai za ta sa in rabu da
kai,Zuciyata ba za ta ta`ba bani goyan bayan in barka ba,zan yi fatan nan gaba bayan wasu shekaru ka
sake dawowa a matsayin d`ana".



~~~~~~~~
"Momy kin tsorata ni,Na yi kuka na yi Addu'a,har sadaka na yi duk dan son in ga kin warke kar ki tafi ki
bar ni".

Gloria hannunta ta kai saman kan Jedeeda, cikin muryar majinyaci ta ce mata,"Haba `yata Jedeeda,
ina za ni in tafi in barki,zan yi ta rok`on Allah da ya bani tsawon rai inga har `ya`yanki".

Wata dariya ce ta kwace ma Jedeeda farinciki fal a cikin ranta," Zan so haka ta kasance ace har jikokina
kin ga ni ba ma iya `ya`yana ba".

"Momy I beg you kar ki k`ara barin ciwo yaci k`arfin ki har haka,mun shiga tashin hankali da damuwa a
saboda haka", Nora ta fad`a ta na mai sake shigewa jikin ta.

" I'm sorry kin ji Auta ta,I promise to you daga yau zan rik`a kula da kaina da zaran Na ji wani abu da
ban gane shi ba,zan yi saurin yin magana akai ba zan k`ara barin family na su shiga cikin tashin hankali a
kai na ba".

Shigowar Granny tare da Uncle Rechal ce ta sake dawo da murnar farkawarta ta sabuwa.

"Kin ba ni tsoro My Daughter Gloria, wannan wanne irin ciwo ne mai firgita ahali haka?".

Cikin muryarta ta majinyata ta ce,"Mom ai yanzu komi ya wuce tunda gashi yanzu na warke,kuma wai
kun manta da ake cewa,a woman who gets her strength from God can never ever be broken, don haka
ba abinda zai same ni tunda ina tare da albarka Yesu Almasihu da kuma ta ki".

Fuska d`auke da annuri Revered Anderson da shi da Martin su ka shigo ,hannun Martin d`auke da
sabbin magungunan da aka sake rubuta ma Gloria, da sauri ya aje ledan ya matsa kusa da ita suka sa ta
tsakiyar shida Nora.

" Papa ya ake ciki ya Doctorn ya ce wanne mataki take a cike yanzu?".

"Thanks to the Father Lord, ya ce kiji da sauk`i ,ga sabbin medicine nan ya rubuta mata ya ce ta sha na
kwana biyu kafin daganan sai a sake check up d`inta daganan sai ya sa mana ranar sallamah".

Fuskar kowa sai da ta nuna farincikin jin wannan batun,Granny ce ta kai dubanta kan su Martin ta ce
da su," Kun ga `yan jikokina ku taso ku bata wuri ta d`an huta in ta k`ara samun sauk`i sai ku je ko ciki ne
sai ta mai da ku,kun fa girma da wannan halin ak`allafa kun kusa 19 years ai kwa barma yara wannan
d`ab'ar ko".

Sake shigewa jikinta su duka biyun su kai,Wanda hakan ya sa Gloria ta sake rungume su kafin ta
ce,"Mom ki bar su suna kewata ne ,kwana nawa ba su samu irin wannan kulawar daga gare ni ba".

Jayayya ce ta `barke tsakanin Rechal da Revered Anderson kowa a cikin su na san ta fad`a mi shi me ta
ke sha'awar ci ya je ya siyo mata,ganin da gaske ba Wanda zai hak`ura a cikin su sai kowa ya je ya siya
abinda ya ke ganin za ta so shi.
~~~~~~



"A'ah Bibah yau ke ce a Gidan na mu", Ummu Nurain ta tambaya fuskarta d`auke da murmushi.

" Wallahi kuwa Aunty Zeenat, ya Gida ya aiki ina Nurain ya ke?".

Ta`be baki tayi kafin ta ce yanzu na kora shi ya bani wuri saboda ya dame ni,sai faman bari-bari na
ke,ya su Umma Hanne fatan duk suna lafiya ?".

"Eh ta na lafiya ta ce ma a gaishe ki,Yah Hameed ne ya je Gidan ya ce baki jin dad`i shiyasa ta ce in zo
in da wani abun da zan taimaka mi ki da shi".Bibah ta kai zancen ta na mai wara idanun ta cikin
Parlourn, tun kafin ta shigo cikin Parlourn ta tana tsakar Gida ta san yau za ta gaya ma `yan garinsu da
aiki.

" Shi Hameed d`in ne ya gaya miki ba ni da lafiya?",Ummu Nurain ta tambaya cike da mamaki.

"Eh haka ya ce,ya mace daga nan Gidan yake kuma "....

Tun kafin ta kai k`arshen zancen tai zumbur ta mik`e ta na mai nufar bedroom d`inta in da wayarta ta
ke,jikinta har rawa yake wajen lalubo Number sa ta fara Kira,Ringing d`aya biyu Ana uku yai picking,
muryar sa d`auke da sallama tare da gajiya isowar shi masaukinsa kenan daga Hospital.

" Yaushe za ka barni in huta ne,eyeh Abu Nurain, me na maka,shin ba ka jin tausayina ko kad`an,
k`aramin cikinka na ke d`auke da shi ga kuma hidimar Nurain da ta taru tai min yawa a kaina, amma duk
da hakan ba za ka barni in ji da iya wad`annan ba har sai ka koma kana had`a ni da iyaye da `yan'uwana,
so ka ke dole sai sun tsane ni kamar yanda ka tsane ni kaina ,so ka ke sai sun mai da ni saniyar ware
kamar yanda ka maida ni a cikin Gidan ka".ta d`an daka ta sakamakon jin wani abu na k`ok`arin tokare
mata mak`oshihakan ne ya bashi damar cewa da ita wani abu, "Zeenat me kuma ya faru wad`anne irin
maganganu ne su ke fitowa daga bakin ki,me na aikata maki bayan nisa da tazarar da ke tsakaninmu da
ke,ina ga fa tunda na zo wannan Garin wannan itace waya ta biyu da mu kai to me nayi maki,ina nan ina
ta fad`i tashi duk dan in samu abinda zan rufa mana asiri amma hakan be sa kin ji tausayina ko Addu'a
mai kyau ki rik`a biyo ni da ita ba,sai dai tashin hankali da fitina".

" Oh iya adalcin ka abinda ya gani ma ka kenan laifina ma ka ke gani,to na gode,amma ina so ka sani
daga rana mai irin ta yau kar ka k`ara turo min wani cikin Gidan in har da zummar ka zubar min da
mutunci da k`ima ne,ba sai ka k`ara `bata min suna kamar yanda ka yi a baya ba,in kuwa ba haka wallahi
zan hauka ce maka a cikin Gidannan "....

" Ki hauka ce mana Zeenat, Dan Allah ki haukace d`in wai ke wacce irin Mace ce, me ye a cikin
kwakwalwa da tunanin ki Anya kuwa kin ma san me kalmar Miji da Zaman Aure ta ke nufi,to ki sani Na
shirya tarbar duk kalan haukan da za ki zo da shi,dai-dai na ke da ke".yana kaiwa nan ya kashe wayar
gami da cillar da ita saman kujerar da ta ke kusa da shi,hanunshi ya kai saman goshi shi yana mai dafe shi
tare da furta kalmar Innalillahi wa'inna ilaihir raju'un a hankali,k`arar knocking d`in da ya ji ne ya sa ya
bud`e idanunsa wanda har sun fara sauya kala,haka ya ja k`afarsa ya je ya bud`e ma eanda ya ke son
shigowar.

"Lafiya dai Imam Na ga yanayin ka duk ya sauya", Doctor Nass ya tambaye shi bayan ya ra`ba ta jikin
shi ya shigo Parlourn.

" Uncle Nass Zeenat ce,nema ta ke ta tarwatsa min tunanina,so ta ke sai ta samin cutar damuwa ta
k`arfi da yaji,Wai Dan Allah haka dama Auren Zumincin ya ke,wannan bala'i har ina?".

Sai da Uncle Nass d`in ya kama shi ya zaunar da shi sannan ya ke ce mi shi,"Duka Mata kowa na da irin
na ta k`alubalen ba wai sai iya Auren Zuminci ne ake samun tasgaro a cikin sa ba ,ita Zeenat wannan
shine na ta k`alubaken,ka yi hak`uri ka dage da addu'a,in sha Allah komi zai wuce wata rana".

"Amma Uncle Gimbiya Ayush ba ta min irin abinda ita Zeenat d`in ta ke mani,duk da ita tafita a komi
ga dukiya ga Sarauta amma iya abinda na ce mata kawai ta ke yi".

Wannan Allah ne ya so ka da rahama ya sauya ma ka da ita don ka samu natsuwa daga gareta,don
haka sai kai Godiya kuma ka k`ara da hak`uri", da kai Imam ya amsa ma sa ba tare da ya kuma cewa komi
ba.

"Na je can Hospital d`in akace min ka taho masaukinka shine fa na zarto nan ga launch d`inka can
Madam ta ce a kawo ma ka".ya sanyo wani zancen da zai sa su bar wancan.

Murmushi mai tafe da yak`e ya yi tare da cewa," A mik`a min godiya ta wajen Aunty tawa ina ta sa ta
d`awainiya tun zuwana".

"Oh wannan Ai kun fi kusa,yauwa ya Maganar Mrs Anderson ya jikinta a wanne Condition ta ke
yanzu ?".

System d`in shi ya janyo ma shi tare da cewa," Ga file d`in ta nan duba ka gani kafinnan bari in d`an
watsa ruwa ina fito sai mu tattaunawa yanda ya kamata".




*JADEEDAH*



(It's a story of two love birds who are so different from each other )

STORY & WRITTEN BY :

(*Cwt~Sumiey*)
Marubuciyar littafin

MENE NE ABIN YI ?

KARAGAR MULKI

And now.....*JADEEDAH*

*YOTA*

BOOK 1



PAGE 22❤



"Momy mun yi waya da Papa ya ce ya Isa lafiya ya na saran tomorrow early in the morning zai baro
Lagos ya dawo ,domin gabad`aya hankalin shi yana nan ya na son ya ji yanda last result d`in nan zai fita".

" Eh nima ya kira ni amma tun bayan isar sa Airport ne daganan ba mu sake yin waya da shi ba,a
lokacin ina gab da shiga d`akin Test d`in".

Granny ce ta amshi zancen da cewa,"Ya kamata ya zuwa yanzu ma ace result d`in ya fito,tun fa safe
gashi 5pm na shirin yi".

"Uhm gaskiya kam nima tun d`azu abun na raina", Cewar Martin.

"Ko dai zan je in gano ,halin da ake ciki wata k`ila aiki ya yi masu yawa ne shiyasa ba su dawo ta kan
mun ba".

" Yauwa Aunty Jee ki je ki jiyo mana ko ma samu mu fita daga bakin tunane-tunanen da mu ke a
ciki",Cewar Nora da ke haɗa kayan da za su koma da su Gida.

"Okay bari in je Allah ya sa mu ji abinda zai kwantar mana da hankali ba ya k`ara tashi ba"," Ameen",Su
ka had`a baki su duka.

K`arar knocking d`in da ake ne ta sa yad`an d`ago ya kalli Door d`in ba tare da ya bar abinda ya ke ba
ya bada izinin shigowa.

"Good Evening Doctor", ta fad`a a d`an d`arare ,a hankali ya d`ago da kan shi ," Oh ke ce come in, ina
fatan lafiya dai?".ya tambayeta ya na mai cigaba da aikin da ya ke.

"Amm.....muna cikin jimami ne,muna ta dakon jin sakamakon test d`in da akayi ko zamu fita daga
cikin tunani da damuwa".
"Oh Sorry aiki ya d`an rik`e ni,test d`in are yet to be out amma zo zauna have a seat,akwai Maganar da
na ke son yi dake", ya kai zancen ya na mai nuna mata wurin zama.

Zaunawa yai ya na mai tattara hankalin shi wuri guda ya na kallonta," Ammm Mahaifiyar ki ta na
samun sauk`i sosai sai dai da akwai buk`atar taimakon ku a cikin lamarinta in har kuna son lafiyarta ta
d`ore,da akwai shawarwarin da na ke son baku ko Allah zai sa a dace".

"Doctor ina sauraron ka I'll do everything in har akan samun lafiyar Momynah ne",ta ce da shi a
ƙagauce.

"Yana da kyau a ce ta rik`a yawaitar yin exercise domin motsawar ga`bo`binta,sannan a rik`a kula da
abincinta ta rik`a samun wadataccen barci, a hanata yawaitar tunani ko barinta ta zauna ita kad`ai,
banda shan wani abu wanda ya danganci Alcohol da sauran su"....haka dai ya cigaba da jero mata
dokokin da ya kamata mai irin wannan ciwon ya kiyaye

" Thanks alot Doctor, ban san da wanne irin baki zan iya Gode ma ka akan irin kulawa da kuma
sadaukantar da lokacin ka daka yi akan Mahaifiyata ina maka fatan alkairi ".

" Don't Mind cause it's my duty kin ga kenan ya zame min dole in aikata abinda ya kamata".

"Duk da haka I'm really appreciate ba zan manta da hakan ba", ta kai zancen ta na mai mik`ewa za ta
fita,har ta fara tafiya ta dawo,gami da komawa ta zauna ta na mai fuskantar shi da cewa ta ce da
shi,"I'm sorry about the last day, I'm swear to the Jesus Name ba halina ba ne,a that day ina cikin tashin
hankali da firgicin rashin lafiyar Momynah,ina mai baka hak`uri akan hakan,ba ni da wani za`bi ne I know
Abuja Boys ba yaren da suke ji sai na kud`i hakan ya sa nai amfani da wannan policy d`in dan tak`aita
zancen amma har cikin raina nasan ban kyauta ba abinda na yi ".

" Kar ki damu na fahimce ki ,tun kafin ma ki yi bayani, Allah ya bata lafiya ".

Wayar shi ce tai k`ara ya d`aga na wani d`an lokaci kafin ya aje wayar ya na mai cewa," I'm sorry for
interruption da akwai wata Doctor ya na da muhimmanci idan zai yiwu ku ganta she is expert about
Neurogical disorder zai kyautu a ce kun kai mata ziyara ,idan har kuka aikata hakan za ku fahimci abinda
Na ke son sanar da ke".

Cikin zumud`i Jedeeda ta ce,"Why not me zai sa ba za mu iya zuwa inda ta ke ba,ai komin nisan inda
ta ke za mu je ,mu ke da riba akan hakan fa,mu ke Neman inda Momy za ta samu lafiya ta warke daga
lalurar da ta ke damunta,don haka a kowacce k`asa ta ke a shirye mu ke da mu je can,kai ko nawane za
mu kashe in har zamu samu damar ganinta".kasaƙe yai yana kallonta ya rasa me yake faruwa da shi,komi
nata neman rikita shi yake, murmushinta maganarta,tafiyarta hatta da motsi in tai sai ya riƙa ganin
kamar yasan wani ko wata da irin wannan ɗabi'ar, yanayin yanda ta ke juya idanunta tare da yanayin
yanda ta ke sarrafa bakinta wajen yin magana,sukan su na ɗaya daga cikin abinda ya ke sake jefa shi
cikin kokonto a cikin Zuciyarsa

"Ba wani Gari ko wata k`asa ta ke ba anan nan Kano ta ke da zama,sai dai ta na da k`a'ida guda d`aya
duk wani patient da za ta duba sai dai ya same ta a Gidanta ,ko kuma mutum ya bi ta Asibitin AKTH
Wanda ta ke aiki a cikin sa sau d`aya ko sau biyu a wata".ya ce da ita yana mai son gano wani abu daga
gare ta.

" Kano kuma ?",ta tambaya fuskarta na nuna rashin jin dad`in abinda kunnuwanta su ka ji mata.

"Eh haka na ke nufi ,amma ki bi komi a hankali lamarin it's about a choice sai fa kuna buk`atar ta,idan
kun ji ba kwaso ba dole ba ne ba, shi has experience about the case Neurogical disorder, yanzu haka ta
na da patient d`in da take kula da shi sama da shekaru Ashirin, kin ga kenan ta san hanyoyin da za a
samu sauk`in cutar".

" Na fahimce ka amma wani hanzari ba gudu ba,zuwan Momy Garin Kano kai tsaye zan iya ce maka
abu ne da ba zai yiwu ba,ba ma ita da kanta ba ko mu ba mu da damar zuwa wannan Garin, baza ta ta`ba
yarda da hakan ba,ka sani za mu iya kashe ko nawa ne in dai zata yarda ta zo ta dubata anan".

"Warnder shall never end me ye a cikin Garin Kanon da har za ku gitta irin wannan lafazin akan
shi,shin wani abu ya faru ne da ita a Garin wanda ba ta son tuna shi ko sake faruwar shi?".

" Ba ni da wannan masaniya gaskiya nasan hakan dai a matsayin dokar cikin Gidan mu,...amma ka
manta kawai mu koma kan Maganar yanda za mu shawo kan wannan Doctorn ta amince da buk`atar
mu".

"Hmmmmmm ki yi hak`uri amma dagaske ina mai sanar da ke ba zaki ta`ba iya sanyata ta zo Garinnan
ba,idan har kuna buk`atar taimakonta to ku kai mata ziyara ta na da dalilin mai matuk`ar muhimmanci
da ba za ta iya bari ta zo nan ba,abu d`aya na sani zan iya had`a ku da ita domin ta rik`a baku
shawarwarin da za su amfanar da ku".

" Ba wani taimako da zaka iyai mana akan haka,zan so in ga na samu wata hanya da zan taimakawa
Mahaifiyata na ga ta warke daga wannan lalurar da ta ke fama da ita,ciwon kan da take fama da shi yai
tsanani ba na son in ga ta na yanke jiki ta fad`i ko kuma ta fita a cikin hayyacinta, ba na son haka".

"Gaskiya babu", ya bata amsa a tak`aice, shiru Jedeeda ta yi na wani d`an lokaci, kafin ta d`ago ta kalle
shi ta ce," I'll do my best, zan yi iya me yiwuwa na ga nayi convince d`inta ta amince mu je ta had`u da
Doctor d`in, idan har kana da tabbacin samun sauk`in na ta","Allah shi ke da iko akan komi muna sa ran
faruwan haka","Hakan ya yi kyau ga wannan card d`in ta ne,za ki iya yin contacting d`in ta da zaran kun
shirya ma hakan,bata da wata matsala zan yi mata bayani",ya kai zancen ya na mai mik`a mata ta
amsa,tare da yi mashi godiya

"Lokacin tashina ya yi zan wuce,zuwa gobe in na shigo zan duba Test d`in na ta daganan sai in duba
yiwuwar discharging na tan".sannan su ka yi sallama ta tafi,shi kuma ya cigaba da had`a abinda zai tafi
da shi.

Tafe take ta na tunani hanyar da za ta iya shawo kan Momynta,da kuma tunanin dalilin da ya sa ta
hana su zuwa garin Kano bayan kuma suna da damar kai ziyara a ko'ina na fad`in k`asarnan kai ba cikin
k`asarnan ba har da k`etare suna da damar zuwa,ta kan nuna `bacin ranta matuk`a in taji ko firar Garin
Kano su na yi ,kai ko k`awa bata son ta ji sunyi in har `yar Kano ce,to meye ya jawo hakan,tabbas ta d`au
aniya binciko ko ma me ye ya ke binne a k`asa, ta yi maganin matsalar in har hakan zai zama sanadin da
Momynta zata samu lafiya ,da wannan tunanin ta isa Room d`in da su ke.

√√√√√√√√√

"Amm..... Ya ma ki ke da suna,Bibah ki ke ko wa ma ?,ki tattara inaki-inaki ki bar min Gida,tun muna
shaida juna ,ki je ki ce wa wanda ya turo ki na kore ki,ba na buk`atar taimakon na ki, shashashar banza,
munafuka kawai".

" Subahanallahi Aunty Zeenat me ya faru ,mai yai zafi har ka?".

"Ban sa ni ba,kawai abinda na ke da buk`ata ki fita ki barmin Gida,ki je ki sanar da munafukai da kuma
`yan gulmar da su ka turo ki,lafiyata lau ba abinda ya same ni".

" Amma Aunty Zeenat ".....kar ki kuskura ki k`ara cewa da ni komi,salin alin ki d`auki mayafin ki ki fice
min a Gida".

Ganin kamar ba za ta tafi ba yasa ta daka mata tsawa tare da fara fatali da duk kayan wanke-wanken da
ta fara had`awa ta re d`aga sautin muryarta ta na cewa," Za ki fitar min a Gida ta daɗin rai ko ko sai na
raunata ki?"

Bibah a firgice ta ɗago tana kallon ta gami da rasa me za ta yi, duk ta firgice domin ba ta ta`ba ganinta a
cikin irin wannan yanayin ba,sai ta kalli tarin wanke-wanken da ke gabanta wanda ta had`a za tayi da ita
Ummu Nurain ta warwatsar da su sai ta kalli Zeenat da ke tsaye a saman kanta sai faman huci da ta ke
tamkar wacce tai tsere,ganin cigaba da zamanta ba lalle ya haifar da d`a mai ido ba ya sa ta d`auraye
hannunta gami da d`aukar mayafinta ta bar mata Gidanta.

"Duk dai-dai na ke da ku munafukan banza da na wofi,ku ne fa kuka zuga shi ya Auro waccen mai
kama da karuwan,wacce ta dalilin ta na zama tamkar bola a wajen shi ,Na rantse da Allah ba zan bar ku
ba,ku dai jira lokacin da zan sauke abinda ke cikina ku ga irin matakin da zan d`auka ba shi ba hatta da ku
sai kun gane asalin wace ce ni".haka dai ta cigaba da maganganun ta har Nurain ya farka da daga barcin
wuyar da ta kora shi ya je ya yi,kan ta ya nufa sai faman murza idanun shi ya ke da hannayensa,ya ce da
ita," Umma yunwa Na ke ji ki bani abinci in ci".....tun kafin ya kai k`arshen Maganar tasa ta kai masa duka
tare da cewa,"Dan Ubanka wuce ka bani wuri ,in yunwar ta tashi ta kashe ka duk ba ta sanadiyar ka ake
yimin duk kalar wulak`ancin da ake so ba".

Ihu ya sakanmata da iyakacin k`arfin sa ya na kuwwa yana cewa shi yunwa ya ke ji ta bashi abinci,ta
tashi ta dafa mai ba zai ci biscuit ba ba zaici Noodels ba,dole ba dan ta so ba ta tashi ta d`ebi wasu daga
cikin kayan da za tai amfani da su ta wanke kafin ta d`ora masu girkin.
*JADEEDAH*




STORY & WRITTEN BY :

(*Cwt~Sumiey*)

Marubuciyar littafin

MENE NE ABIN YI ?

KARAGAR MULKI

And now.....*JADEEDAH*



*YOTA*

BOOK 1




PAGE 23❤




"Kar dai kace min nan ka fara sauka ba ka Isa Gidan ka ba,wai sai yaushe za ka girma ne,iyali ne fa da
kai ,Anya kuwa Jaheed ?".....

"Momynah Haba dan Allah,welcoming d`ina ya kamata ki yi ba ki tare ni da tarin tambayoyin ki irin haka
ba".

" Au nufinka in zuba ma ka Ido kawai ka dinga aikata duk abinda ka ke so ka ke ganin dai-dai ne,to
hakan ba zai yiwu ba,dole ne in nusar da kai gaskiyar kuskuren da ka ke aikatawa ".

Sai da ya maida fuskarsa kalar ban tausayi kafin ya ce," Momynah na yi kewar daddad`an abincin ki ne
me sa

Please Login or Register in order to submit comment