You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

da ki kai rayuwa da shi tun k`uruciyarki wanda
ya ke da tarin Illimi na addini da na zamani?".
Sosai wannan tambayar ta girgiza ta,har ta rasa me ma za ta ce sai faman kame-kame ta ke,har sai da
Yah Mustapha ya ce da ita,''Kinga ki natsu ki fad`i abinda ke a cikin Zuciyar ki bawanda zai maki dole
za`bi a ka ba ki".

Muryarta na rawa ta samu ta saita kan ta kafin ta ce "Abbanmu shima fa ya ce ya na son yai ilimi,ba shi
da wani buri da ya wuce ya zama tamkar kai ya gan shi yana koyarwa kamar kai,yai koyi da duk
kyawawan d`abi'un ka".

Wani murmushi mai cike da kamala Baba Malam ya saki tare da cewa da ita,"Allah yai maki albarka ta
shi ki shiga cikin Gida ki turo min Uwar d`akin ta ki".

Har ta kusa fita daga cikin d`akin ta waigo ta sauke idanunta akan Daniel idanuwanta sun yi rau-rau
kafin ka ce me tuni hawaye sun fara zuba daga idanunta,shi dama tun d`azu ya kasa iya d`auke idanunsa
akanta,haka ta na ji tana gani ta sa kanta tai waje ,Zuciyar ta sai k`ara raunana ta ke ,game da tunanin
wanne irin mataki ne Baba Malam zai d`auka akan ta da kuma rayuwar ta.

Gyaran murya Malam Babba yai kafin ya Kira sunan Alk`asim ya ce da shi,"Alk`asim kasan matsayin ka a
gare ni,tamkar d`ana da na haifa ka ke,kusan a hannu na ka girma na san halayenka,Wanda su ne suka
kwad`aitar da ni akan had`a Auren ka da Hibba, to sai dai zuwan wannan lamarin ya kawo mana
tsaiko,Na yanke hukuncin bada Aurenta a ga wannan bawan Allah,ba wai don wata gazawa ta ka ba, a'a
sai dan kwaikwayon kyawawan d`abi'u na magabatan mu,idan mu kai duba da yanda mutanen Madina
suka kasance a lokacin da Annabin mu,Annabin da muke koyi da shi Annabi Muhammad (S.A.W) yai
hijira tare da muhajiran shi zuwa Madina,a wannan lokacin mutanen Madina matayen su na Aure su ka
rik`a saki suna bawa muhajiran su aure,duk dan nuna karamaci,d`abi'u da kuma halayen su ma su kyau a
gare su,kun ga kenan ba laifi in mun yi koyi da hakan,ina fatan hakan ba zai zama wani abu na daban a
gare ka ba?,idan har haka ta kasance ina mai Neman afuwar ks ,ka yafe ni dan Allah".

Sai da Alk`asim ya matsa kusa da Baba Malam ya kama mayafin da ke jikin sa kafin cikin girmamawa ya
ce da shi,"Haba Malam kai fa Uba ne a gare ni ka can-canci ka yanke min ko wanne irin hukunci,balle
kuma irin wannan lamarin mai girman gaske, ba wai sadaukar da Soyayya Hibba ba ko da fiye da wannan
buk`atar za ka zomin da ita zan kasance mai yi maka biyayya akai".

"Na gode sosai da jin wannan kalami daga bakin ka,shakka babu Allah zai musanya maka da wacce ta
fita".

Kallon sa ya maida kan Alaranma Sama'ila ya ce,"Ana son a gaggauta wasu abubuwa ciki harda
musulumtar da Wanda ya zo musulumta, don haka zamu lak`anta ma shi kalmar shahada a yanzu,dan
haka ka jagoranci lamarin".

Nan Alaranma Sama'ila ya fara lak`anta ma shi kalmar shahadar,"*Ashshahadu Allah ilaha illallah,wa
Ashshahadu Ana Muhammad rasulullahi,wa Ashshahadu Ana Isa Abdullah wa rasuluhu*",yana fad`a
Daniel na maimaitawa harshen shi a rarrabe.

Nan fa suka d`auki kabbara baki d`ayansu kowa a cikin su na farin ciki shigar shi muslunci gami da samun
k`aruwa da su kai.
Alaranma Sama'ila ne ya tambaye shi da cewa,shin kana da wani suna da ka ke sha'awar a maida maka
madadin Daniel da ake kiranka?".

Shiru na wani d`an lokaci Daniel yai,ya na mai tunanin wanne sunan ne ya dace da shi da ," Am am ina
son Abubakar zan so a kira ni da Abubakar saboda na samu labarin irin gudunmuwar da ya baiwa addinin
muslunci ".

"Tabbas ka yi dacen suna ina fatan kayi koyi da mai sunan,Allah ya albarkaci rayuwar ka ya baka ikon
zamowa cikin salihan bayin sa".

" Shin yanzu idan Na ce zan baka Auren Hibba, kana da wanda za ka gabatar a matsayin iyayen ka ko da
acan asalin Garin ku ne?",

Duk`ar da kan shi k`asa Daniel yai kafin ya ce da shi"I don't have any relative in this town, Na zo Garinnan
a matsayin bak`o aiki ne ya kawo ne,Ni d`an asalin Garin Jos ne,iyayena sun rasu a wani rikici da akayi su
duka biyun,sai dai muna zaune tare da Grandmother d`in mu da kuma Sister na".

"Eyyah Allah sarki na jajanta ma ka akan haka,amma ku na da wasu dangi haka bayan su ko?".

" Eh to ba na ce babu ba amma na san akwai wani Uncle d`inmu guda d`aya,ya na can Benin da zama ,ya
ta`ba zuwa inda mu ke sau biyu bayan rayuwar Parents d`inmu,in fact dai muna rayuwa ne mu biyu da
Grandmother d`in mu da ta tsufa sosai,bayan ita kuma bamu da kowa gaskiya ".

Shiru duk mutanen wurin su kai kowa na mamakin labarin da ke fitowa daga bakin sa,Sallamar da
Ummie Maryam ta yi ce ta ja hankalin su, Baba Malam ne ya bata umarnin shigowa gami da samun guri
ta ja ta tsaya tare da cewa cikin mutuntawa da girmamawa matsayin ss na sirikinta," Hibba ta ce in zo ka
na son ganina Baba","Eh haka ne ina son ki je ki sanar da mutanen Gidan cewa a yau zan d`aura ma
Hibba Aure dan haka da buk`atar ku san da hakan ku shirys mata `yan kayayyakin ta dan da an fito
sallahr magariba za ta bi mijin ta".

Ba Ummie Maryam ba hatta da su Malam K`arami da ke zazzaune da ya ja bakin sa yai shiru tun fara
fahimtar abinda Baba Malam ke shirin aiwatar wa,sai da yai saurin ɗago kansa bakin sa na rawa,saba
damar furta komi.....




*JADEEDAH*



(It's a story of two love birds who are so different from each other )
STORY & WRITTEN BY :

(*Cwt~Sumiey*)

Marubuciyar littafin

MENE NE ABIN YI ?

KARAGAR MULKI

And now.....*JADEEDAH*



https://chat.whatsapp.com/CWkZfMqvD4H0mtd7WW6Xbz

https://whatsapp.com/channel/0029VapqU8C002T5Bz8RSQ0a




BOOK 1

♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡




PAGE 3 ❤



Cikin rawar murya Ummie Maryam ta sake mai-maita abinda kunnuwanta su ka jiye mata amma ta sigar
tambaya.

"Eh abinda ki ka ji shi na fad`a zan d`aura Auren Hibba da d`an'uwanmu Abubakar", ya na mai nuna inda
Daniel ya ke zaune ba tare da ya tsaya ba ya cigabada da cewa,"kuma a yau yanzu ma bayan sallahr
magariba, kuma zata bi mijin ta a yau d`in ba sai gobe ba, don haka ki je ki aiwatar umarnin da na sa ki",
ya kai k`arshe zancen yana mai kaurara muryarsa.

Ummie Maryam na tafe na waigen inda Daniel ya ke zaune wanda ya sauya sunan shi daga Daniel zuwa
Abubakar .

" Amm K`arami shiga da shi sashen bak`i ka nusar da shi duk abinda addinin ya tsara, ya gudanar ya
tsarkake jikin shi,sannan ya sauya suturar shi izuwa wacce addinin mu ya koyar da mu musan ya".
Jikin Baba K`arami a sanyaye ba tare da ya so ba ya mik`e gami da nuna ma Abubakar hanyar da ta da ce
su bi,Alk`asim ne ya dakatar da shi ta hanyar cewa, "Baba K`arami ina so zan bika domin mu aiwatar da
wannan aikin ladan a tare".

" Ba damuwa mu je",ya bashi amsa a tak`aice,su kuma sauran duk su ka mik`e su ka nufi hanyar da zata
sada su da babban masalacin anguwa da suke gudanar da sallah a cikin sa kuma su ke jagorantar duk
wani abu da ya ta so a cikin sa.

"Ummien Jaheed lafiya na gan ki haka kin shigo jikin ki ba k`awari?", Anty Zulai Matar Yah Mustapha ta
tambaye ta .

Sai da ta sauke idanunta akan Mama Hadiza,gami da duk`ar da kanta k`asa kafin ta ce da su," Baba
Malam ne ya umarce ni da in had`a ma Hibba kayanta domin zai d`aura ma ta Aure yanzu bayan sallahr
magariba kuma za ta bi mijinta ".

Zumbur Umma Jamila tai ta mik`e bakin ta d`auke da salati ta na cewa," Auren kuma wacce irin magana
ce haka mai ya sa Malam zai yanke irin wannan hakunci cikin k`ank`anin lokaci sai ka ce wata mara
gata,to wai ma da wa za'a d`aura Auren? ".

Sai da Ummie Maryam tai k`asa da muryarta kafin ya ce," Da wanda ta kawo managern da ta ke IT a
Company d`in sa".

Mama Hadiza runtse idanunta da k`arfi tai alamun maganar da ta ji ta bugi Zuciyarta, Umma Hafsat ce ta
amshi zancen muryarta na bayyanar da rashin yarda da hukuncin da Baba Malam ya zarta,gami da
cewa"Ba zai yiwu ba,ta ya zai amince da abinda k`aramar Yarinya za ta zo mishi da shi,ba tare da yai
duba da zata iya cutuwa ba,bai fa san komi game da shi ba,ta ya zai ɗauki ƴa ya ba shi sai ka ce wacce ya
tsinto",d`an tsagaitawa tai gami da maida akalar zancenta akan Mama Hadiza, "Ya kamata ki sa baki a
wannan zancen ki dakatar da Malam Babba in kuwa ba haka ba ke ce wacce za tafi kowa zubar da
hawaye a cikin Gidannan,ba fa a san asalin wannan Yaron ba ahalin sa gabad`aya duk ba sa Sallahr,a
haka za ki bari ya zama Sirikin ki Mihaifin wurin jikokin da za a haifa ma ki anan gaba?".

Umma Hafsat ce ta amshi zancen da cewa," Kin fad`i gaskiya Yaya bai kamata mu zuba Ido mu bar
wannan lamarin ya tafi a haka ba,an sha yi ma na irin wannan yankan k`aunar a cikin Gidannan a d`auki
`ya`yan mu mata a bayar da su ga wanda aka ga dama ba tare da anyi duba da suna son mijin ko a'a
ba,ba tare da anyi shawara da wani daga cikin mu ba,amma duk da haka ba a ta`ba kawo mana mutum
irin wannan ba,don haka dole zamu had`a k`arfi a tare mu dakatar da wannan k`udirin na su".

Kauda kai gefe Mama Hadiza tai gami da saurin d`auke d`igon kwallahr da ta ke k`ok`arin zubowa daga
idon ta gami da cewa,"Hmmmm kun manta shima `yar shi ce ya ma fi ni iko da zartar da hukunci akan ta
kuma ma dad`in gushi ai ita gata a kai mata,wacce `ya ce a Gidannan ta kawo wanda ta ke so a ka bata
shi,sai fa ita,ko kun manta za`bin ta ne,don haka kar ku tada hankalin ku akan d`an wannan k`aramin
abun".ta d`an dakata gami da cewa da Ummie Maryam, "Yauwa Matar K`arami(da ya ke ba ta fad`in
sunan ta),bari in je in kwaso maki kayanta na cikin d`akina ki had`a da na wajen ki kar lokaci ya k`ure". Ta
na kaiwa nan ta wuce ta tafi d`akin ta hannayenta saman fuskarta.
Umma Maimuna ce ta niyar dakatar da ita Baba Asabe ta saurin dakatar da ita gami da girgiza mata kai
tare da cewa," A'a kar ki je ba za ku iya can za komi ba,domin ba ku Isa ku can ja wannan hakuncin
ba,kun san halin Baba Malam ciki ba hatsi ba, ba zai ta`ba can ja maganar sa ba, don haka ku ja bakin ku
kuyi shiru kar da kuma ku ta da wata fitinar".

Kamar wacce aka hankad`o haka Yaya Zaliha ta shigo cikin Parlourn sai faman haki ta ke ita ce d`iya d`aya
da Baba Asabe ke da ita sai kuma Alk`asim shi d`in k`anin ta ne

"Inna Hibban ta ke mayaudariya macuciya ki fito inji dalilin da ya sa ki ka fasa Auren k`anina,ki fito gani
tsaye ina jiran ki,sai da ki ka bari Yaro yai nisa akan son ki sannan ki zo ki ce kin fasa Auren sa akan
me,me ya aikata ma ki", cikin d`aga murya ta ke magana.

Saida gaban Hibba ya yanke ya fad`i sakamakon jin wannan kiran da Yaya Zaliha ta ke mata.

"Ko da ya ke ai barewa bata yi gudu d`anta ya rarrafe ba daga dukkan alamu d`aki aka sa ki aka hure ma
ki kunne akan ki guji d`an'uwanki na jini akan wani banzan bare kafirin banza wanda kaf ahalin sa ba mai
yin Sallah,to ki sani za kiyi danasani mai girma wacce ba za ki ta`ba iya gyara kuskuren da ki ka aikata
ba,za ki gani a k`ok`on shan ki ki jira lokaci"........

" Kar ki kuskura ki yi mata mugun baki,domin ita ba `yar da ki ka haifa ba ce ba,wannan ina son ki sa ni
ko kuma ince ina son ki tuna ita a kaf ahalin ta ba ta ta`ba aikata wani abun kunya ba balle har ki goranta
ma ta da shi,bugu da k`ari ita ai alfamar ta yi ma Alk`asim da ta amince za ta Aure shi",Cewar Yayah
Hanne da shigowarta kenan itama goye da `yar ta a bayanta, itace babba `ya mace a d`akin su Hibba.

Wata tsawa Baba Asabe ta dakawa Hanne gami da cewa,"Ahir d`in ki Hanne anan a tafin hannunna a ka
haife ki,don haka ba ki isa ki goranta mata akan abinda ba ta ji ba bata gani ba".

"Au ashe babu dad`i Baba Asabe mai yasa ba ki dakatar da ita ba a lokacin da ta ke k`ok`arin cin zarafin
Mahaifiyata"....

Shigowar Baba K`arami ne ya dakatar da ita ran shi a `bace ya ce da ita,"Au dama abinda Baba Malam ya
turo ki ki yi kenan,me ya sa ki ka zo in kinsan tada ma mutanen Gidan hankali za ki yi ?".

" Yayah ta ya inaji ina gani zan barsu su ci zarafin Mahaifiyata a gabana kuma in kyale su,wallahi ba ta Isa
ba in yanzu ta sake cewa wani abu sai na maida mata da martani ".....

" Ba ki da hankali ne Hanne Baba Asabe k`anwar Mahaifin ki ce ta ya za ki tsaya ki na sa'insa da ita".

"Na san da haka K`arami,amma me ya sa kaf cikin Gidannan ba su da abokin rikici sai Mahaifiyata, na riga
da na dad`e da fahimtar su daga ita har Baba Asabe ba wani son mu su ke ba"....

Cikin matsananancin fushi Baba K`arami ya daka mata tsawa" Ki `bace min da gani tun kafin in sauke
fushina akan ki,ko dai ki koma Gidan ki in kinsan fitinar za ki tada mana ko kuma kije ki aikata abinda aka
Kira ki domin shi,ku kuma lokacin Sallahr magariba yayi kuna iya tashi ",duk yana magabar ne cikin fushi.
Kowa tashi yai ya nufi d`akina sa,ba tare da wani ya ce uffan ba,kowa ya san halin Baba K`arami yana da
hak`uri da kawaici,amma idan ran shi ya `baci bai iya fad`a ko fushi ba, sanin hakan ne ya sa ba Wanda ya
sa ke cewa komi su ka tashi.

Shima d`akin da Hibba ta ke a ciki ya nufa ran shi na jin suyar abinda ta aikata.

"Haba Hibba mai ya shiga cikin kan ki ta ya za ki zo da irin wannan batun ba ki zauna kin yi tunanin
abinda ka iya biyo baya ba,wai me ya sa baki ta`ba zuwa kin sanar dani abinda ya ke faruwa ba har sai da
komi ya lalace ?".

" Yaya Hanne mutumin kirki ne fa ya na da dad`in zama da kuma kyawawan d`abi'u "....

" Au abinda za ki fara kafa hujja da shi kenan,shin ba ki san kaf ahalin Gidannan ba wanda ke son
wannan Auren ba,hatta da Baba Malam ya biye ma ra'ayin ki ne kawai,amma ba wai yana son Auren ba
kafin in shigo nan na biya d`akin Mama na iske ta na zubar da hawaye kuma duk akan wannan maganar
Auren ne,shin ba ki tunanin wani abun ka iya biyo baya sakamakon rashin amincewar da su ka nuna?".

Hankalin Hibba sosai ya tashi da jin batun Yaya Hannenta ,cikin muryar kuka ta ce,"Kuka....Kuka
kuma..Mama ke kuka akai na,na shiga uku,ina zan sa kaina inji dad`i,wallahi indai haka ne na fasa Auren
ina son Mamata tai alfari da ni ba zan so zubar hawayenta akaina ba ".

" Haba Yaya Hanne ya za ki fad`a ma ta haka kin ga fa hankalin ta ya tashi,da kin sa ni ba ki sanar da ita
ba",Cewar Ummie Maryam.

"A'a Ummien Jaheed gara ta sani tun yanzu ta san irin kuskuren da ta aikata tun kafin lokaci ya kure
mata"....

" Wallahi indai haka ne na fasa Auren,zan zauna a Gida ko ganinsa ma ba na so,ku sallame shi ya tafi ya
bani wuri".

"Hmmmmmm kin makaro domin kin fi kowa sanin Baba Malam ba zai ta`ba sauya maganar sa ba,Aure
ba fashi kamar anyi an gama".

Hannu Hibba ta d`ora aka gami da sakin salati ta na mai cewa," Na shiga uku na bani ni kuma yanzu ya
zan yi Allah ba na son sa na daina son sa ina son in zauna da ku ba na son Auren gabad`aya "...

Shigowar Baba K`arami ya sa ta dakata,Hawaye sha`be-sha`be a idonta ya iske ta, ta na hango shi ta nufi
wajen da ya ke,ta na mai cewa," Yayah dan Allah ka yi hak`uri ka dakatar da wannan Auren,Na hak`ura
na fasa Auren ba na Son shi,ka dakatar da Baba Malam Dan Allah, Na fahimci kaf ahalin Gidannan ba
wanda ya ke son wannan Auren na rok`e ka kaji Dan Allah".ta kai zance ta na mai had`a hannayenta wuri
guda.

"Ai kin makaro Hibba domin yanzu haka an d`aura Auren ki da Abubakar,ni da kaina Na ba da Auren
ki,shi kuma Baba Malam ya zama waliyinsa,yanzu haka ya na waje ya na jiran ki ki fito ku tafi Gidan ku".
" Innalillahi wa'inna ilaihir raju'un,Yayah wallahi na tuba ka sa shi ya warware Auren ba na son bin shi ni
anan zan zauna na fasa Auren ".

Wata tsawa ya daka ma ta gami da nuna mata hanyar fita daga d`akin ya ce da ita," Ta shi ki fita ki bani
wuri ki tafi can Mijin ki na can na jiran ki,shin da ba ki san da zuwan ranar da za ki bar Gidan ba sai
yanzu,don haka tun kafin in sa`ba maki ki `bace min da gani".

"Allah na hak`ura na fasa ba inda zani,ba na ma son shi yanzu ka bashi hak`uri Dan Allah,kasa shi ya
warware Auren, ka sa ya sake ni"....

Ranshi a matuk`ar `bace ya nufi ta,sandar Covebing ya ci karo da ita ya d`auke ta ya nufe ta da ita,ganin
yanda ya nufota yasa ta kasa da gudu ta nufi waje hannunta rik`e da mayafinta.

Ko da isarta wajen,Jan tunga tai ta tsaya tana mai kai hannayenta saman fuskarta gami da murza
idanunta,Anya kuwa idanunta gaskiya suke gane mata kuwa,duk da kasancewar duhun Magariba ya fara
amma hakan bai hanata iya gane shi ba

Tsaye ya ke jingine jikin motar sa sanye cikin jamfa riga da wando,an dai-daita sumar kansa ya kawo hula
jaddara wacce tai dai-dai da kayan da ya sa,hannunsa rik`e da casbaha ya na ja,fuskarta shi sai faman
fad`ad`a murmushi ta ke,hasken muslunci ya baibaye shi,da ka yi ma sa kallon guda za ka fahimci ya na
cikin,farin cikin natsuwa da kwanciyar hankali.




*JADEEDAH*



(It's a story of two love birds who are so different from each other )

STORY & WRITTEN BY :

(*Cwt~Sumiey*)

Marubuciyar littafin

MENE NE ABIN YI ?

KARAGAR MULKI

And now.....*JADEEDAH*
https://chat.whatsapp.com/CWkZfMqvD4H0mtd7WW6Xbz

https://whatsapp.com/channel/0029VapqU8C002T5Bz8RSQ0a



Wannan page naku ne massoya na Allah ya bar mu tare forever and ever



BOOK 1

♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡♡




PAGE 4 ❤




Duk ta tada ma shi hankali da kukan da ta ke,kwata-kwata hankalin shi baya kan driving d`in da ya ke,ji
ya ke kamar ya janyo ta jikin sa ya lallasheta ya tambaye ta abinda ya ke damun ta amma ina hakan ba
mai yiwu ba ne ba.

"Why are you crying, me ya sa hawaye ke zuba daga cikin idanunki ko na yi ma ki wani laifin ne ban sa
ni ba?", ya tambaye ta cikin hausar shi mara fita sosai.

`Dago kanta tai tana kallon shi da sauri tai k`asa da idanunta tana mai kasa cigabada da kallon shi
tai,muryarta cikin alamun wacce taci kuka ta ce da shi," Ni bana son Auren ka maida ni Gida na fasa bin
ka".



Sosai Maganar Hibba ta daki k`irjin Abubakar har sai da ya samun wuri yai parking gami da mai da
kallon shi kacokan akan ta ba tare da ya iya cewa da ita kumi ba,sai tsura ma ta idanu da yai.

"Why....why...Hibba me ya sa za ki ce haka,ko kin manta we are married now,mun yi Aure ni da ke,mu
d`in ma'aurata ne,mun zama Mata da Miji,ta ya za ki ce kina son ki koma Gida,yaune fa aka d`aura Auren
mu,kuma ki ce za ki koma Gida a yanzu,to ki ce da su me in kin koma ?".

Rau-rau tai da idanu,hawaye na sake zubo ma ta daga idaniyarta," To ai duk basa san Auren na mu da
kai,fushi su ke da ni,Mamana ma kuka ta ke,hawaye zuba su ke da ga idanunta akaina".
Shiru Abbakar yai na wani lokaci,Kafin ya cire baki ya ce da ita,"Ban ji dad`in jin Mama na zubar da
hawayenta akan Auren mu ba,amma ki sani na maki alk`awari zan zauna da ke cikin Soyayya da kuma
amana,zan kyautata ma ki in baki farin ciki fiye da yanda za ki yi zato da tsanmani,zan zame mi ki Mijin
kwatan ce,Mijin nunawa sa'a,ba zan ta`ba bari ki sake kuka ba,zan maye ma ki duk gurbin da ki ka rasa a
sanadin Aure na,kuma a sannu in mu ka yi haƙora,wata rana za su yafe mu su amshi Aurenmu da hannu
bibbiyu".

Kai ta fara girgiza ma shi alamun ba ta amince da duk abinda ya ce a yanzu ba.

Marairai ce mata shima ya yi cikin fuskar tausayi ya ce da ita,"Dan Allah kiyi hak`uri kar ki bar ni,ina
son in rayu da ke,kar ki bar ni,ban san wacce irin rayuwa zan shiga ba in ki ka bar ni,zan cika mi ki
dukkanin alk`awarin da nai ma ki,domin yanzu ba zai yiwu in maida ke Gida a wannan lokacin ba,ran
Baba Malam zai `baci sosai fiye da yanda da ki ke tunani,in Mama ce zuwa nan gaba sai mu je mu bata
hak`uri, hatta da sauran mutanen Gidan duk za su yafe mana zasu so Auren mu da ke,ki bani wani d`an
lokaci kad`an ba zan kunyatar da ke ba, ba zan bari wani abu guda d`aya da ahalin ki su ke tsoran ya faru
da ke,ya same ki ba,ba zan ta`ba cin amanar ki ba ko in juya ma ki baya,zan kasan ce da ke a kowanne
irin yanayin na dad`i ko akasin haka,ki amince da ni mu tafi tare dan Allah Hibba, you are one and only
that I have in my life so please don't live me",ya kai zancen cikin raunanniyar murya.

Kalaman sa sun yi tasiri a cikin Zuciyarta har hakan ya sa Zuciyarta ta fara yin sanyi,kukanta ya tsaya
amma duk da hakan ba ta iya ta ce da shi komi ba.

Cikin muryar shi mai sanyi ya ce mata,"My Wife please shall we go,dare na k`ara yi dan Allah, dan
Soyayyar da mu ka nuna ma juna kafin Auren mu ?".

Da idanu kawai ta ke binsa,gani ta ke kamar duk abinda ya faru ba gaskiya ba ne ba kamar duk mafarki
ne,sai dai ko kusa ko da wasa ba mafarki ta ke ba gaskiya ne,a zahiri komi ya faru cikin d`an k`ank`anin
lokaci.

"Shall we go,please dan Allah ?", ya sake tambayarta a karo na ba adadi,da kai ta bashi amsa ya ja
motar cikin farin ciki da annashuwa.

Cikin some minutes ya isa zuwa Gidan shi da ke Jan Bulo,ba wani babban Gida ba ne,two bedroom ne
sai kitchen,main parlour da`yar farfajiyar tsakar Gidan daga gefe kuma sai parkin space wurin da ya ke
aje motar sa.

Tamkar bak`uwa haka take raba idanunta a cikin Gidan duk da kasancewar yau ne zuwan ta na farko
cikin Gidan,da kan shi ya shigar da trolleys d`in kayanta da suka taho da su ita kuma sai bin bayan shi
take.

Har ya Gama shigar da kayan tana biye da shi,kai tsaye ta ke nuna rashin sakewarta,da amincewar a
cikin Gidan,sai a sannan ya nuna mata wuri ta zauna,idanu ya zuba mata yana kallon ta kafin ya
tambayeta,"Amm nasan kin gaji da yawa kamata yai ki fara yin fresh up kafin nan me ki ke son ki ci in
sama maki kafin ki fito?".
"Ni ba wani wanka da zan yi,kuma ba na son cin komi".

" Seriously ya kamata ki ci wani abu ko da ba zaki yi wankan ba,bazan iya barin ki ki kwana a haka
ba,domin ma san ba makawa za ki cutu,ni kuma ba zan ta`ba iya barin wani abu ya cutar da ke ba
madamar ina da hanyar da zan iya dakatar da hakan ta faru,don haka ki fad`a min me ki ke son ki ci
yanzu in gabatar ma ki da shi ?".

"To...to..Just I need a one cup of tea".

" Nop ban yarda ba,abincin za ki ci,kin san fa na iya cooking",idanu ta zaro alamun bata yarda da
abinda ya ce ba.

"Sincerely da gaske na ke,in ma badan kar ki ce na cika baki ba da sai ince I'm the one of the great
chief a garin kano", sosai maganarsa ta ba ta dariya,har ya ga alamun ta fara sakewa a cikin Gidan.

Gyara zaman shi yai sakamakon

Please Login or Register in order to submit comment