You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

buk`ata
daga gare mu ?".

"Ta na buk`atar hutu ba ta san hayaniya, don haka mun kai ta d`aki na musanman ,sannan akwai the
same case irin wannan wanda ya ke a k`ark`ashi na don haka zamu d`orata kan irin wannan treatments
d`in har zuwa sanda za muga k`arshen abun da izinin Allah,Sannan da akwai shawarwari da zan ba ka
Wanda su ke da buk`atar a kula da su ,amma yanzu lokacin sallah ya yi zan je in dawo in ya so sai mu
sake zama anjima".

"To shikenan Doctor Na gode I will wait you", da haka dai suka sallama su ka fito domin zuwa su
gabatar da sallah azhur
*JADEEDAH*

STORY & WRITTEN BY :

(*Cwt~Sumiey*)

Marubuciyar littafin

MENE NE ABIN YI ?

KARAGAR MULKI

And now.....*JADEEDAH*

*YOTA*

BOOK 1

PAGE 18❤

"Wallahi Momynah kar ki so ki ga Matar,na yi mamaki matuk`a the same irin case d`in Uncle banbancin
d`aya ita it's minor ne".

" Ya Salam My son na tausaya ma ta nasan zafi da kuma yanayin jigata ga wanda Allah ya jarabta da
irin wannan ciwon na juyewar kwakwalwa, Allah ya bata lafiya ".

"Amen Momynah sauk`in ta d`aya Hedeache kawai ciwon ya fara sakar mata a matsayin sing d`insa".



" To da d`an sauk`i za ace sai ka natsu ka fara fahimtar a wanne mataki take akai shin
Epilepsy,ADHD,Multiple sclerosis ko kuma Autism Spectrum ne daganan sai kusan wanne mataki ya
kamata ku d`aura ta akanta".

"Eh na duba hakan sai dai na ga ta mataki na Epilepsy mataki Generalized seizures wanda hakan ya ke
sa tai loss of consciousness".

" Da kyau that's my boy,yanzu a cikin matakai uku da ake d`auka game da wannan cutar wanne
matakin za ka fara amfani da shi,Medications to control seizures,Surgery ko Lifestyle changes ?".

"Momy I think i chose the number one ,kamar zai fi in hakan bata faru ba sai mu janza da wani options
d`in".
Sai da Hibba ta nisa kafin tace,"Focus on the person first not their condition. Treat them with dignity
and respect ka ji ni?", ta cigaba ba tare da ta tsaya ba,"When referring to someone with a brain-related
issue, it's essential to use respectful and person-centered language.By using respectful language, we can
promote understanding, empathy, and inclusivity".

" In sha Allah Momynah zan kasance kamar yanda ki ka tarbiyantar da ni ina k`arami ba zan ba ki kunya
ba zan yi kamar yanda ki ka ce ".

" Momynah ko dai za ki zo ki yi takin over akan wannan case d`in"....

"A'a ba zan zo ba kai ma ka sani,kuma ni ma nasan you will do better"...." Mom da gaske na ke fa ".

" Hmmmmmm Jaheed ta ya zan bar Kano in taho Abuja in duba wata bayan nima ina da nawa patient
d`in ai haka ba mai yiwuwa ba ne ba".

"Momy please shi's in unconscious condition she need your help"

"Ka ga Jaheed abu d`aya ni ke ganin zan iya shima sai in ka ga `bullowar wata Matsala ne wacce ba ka
gane ma ta ba, ko dai ta ziyarci ni anan a Hospital d`in da na ke aiki ko kuma in cigaba da treating d`in ta
online while kai kuma kana monitoring d`in,shi ne kawai abinda zan iya".

" To au ba matsala tunda har za ki iya bata wani d`an lokaci daga cikin lokuttan ki ai hakan ya wadatar
mana,mun gode da wannan alfamar",ya kai zancen ya na mai saluting d`inta.

Murmushi ta yi kawai ba tare da ta ce da shi komi ba,sai shine ya ce da ita," Ina Uncle yau ba ki bani shi
mun gaisa ba".

"Jaheed kenan Uncle d`inka yananan yanda ya ke kamar kullum", ta kai zancen ta na mai maida akalar
Camerar wayar yanda zai samu damar ganin sa ta Video Call d`in da su ke,an samu canji akan da don
yanzu yana iya zama ba kamar da da sai an kwantar an tayar ba,ya kan nuna alamar in yana jin yunwa ko
k`ishir ruwa amma daga ba haka ba ba abinda zai iya yi maka ko kalma d`aya daga cikin bakin SA ba ya
iya furtawa.

" Momy mai yasa ba za mu yi jump to the next level ba akan Uncle, an kwashi tsawon shekaru masu
yawa ya kamata ace improvement d`in da aka samu ya fi haka".

"Hmmmmmm My son nima na yi irin wannan tunanin amma Dr Liyo ya dakatar da ni ya ce in bari
muga zuwa k`arshen wannan year d`in daganan sai asan abinda za ai".

"Hakan ya kamata domin ni kaina ma k`osa in ga Uncle d`ina ya dawo kamar yanda na san shi a
baya"...... Ya dakata sakamom jin knocking d`in da aka fara yi mishi,ya mutsa fuska ya yi kafin ya ce da
ita,"Momy i have a visitor ya katsemin jin dad`i na, Allah har na k`osa lokacin tashi yayi in tafi Gida don
ma matsalar ba zan iske daddad`an abincin ki ba mai kamshi da saukar da natsuwa ga wanda ya ke ci".

" Au za ka fara tsokanar ta ka ko,yaushe rabon ka ma da cin abincin nawa ?,bayan ga matan ka can
`yan zamani wanda su ka fi ni iya girki".....kasa hak`ura yai da cigaba da saurare ta sai d`aga mata hannu
yai yana mai cewa,"By Momy I will call you letter da zaran na koma Gida",Ya kai k`arshen Maganar ya,na
mai ending call d`in.

Sake Knocking d`in akai a wajen karo na uku,"Yes come in",ya fad`a ya na mai gyara fuskar sa ya,koma
asalin Iman kuma Dr Muh'd Jaheed,ka sa iya sakin k`ofar tai ta shigo sakamakon yin tozali da fuskar da
ba tai zato da tsanmani ba.

Ba ita da ta shigo office d`in ba har shi Muh'd Jaheed d`in sai da yai mamakin ganin ta.

"May I come in", ta sake tambaya muryarta a rarrabe," Yeah you can come in, have a seat",ya kai
zancen ya na mai nuna mata kujerar da za ta zauna.

"Da me zan iya taimaka maki",ya tambayeta yana mai tsura mata ido da tattara hankalin shi akanta.

Sai da Jedeeda ta tattaro d`an sauran natsuwa da kuma kwarin gwuiwarta kafin ta ce da shi," Suna na
Jedeeda Anderson mahaifina ne wanda d`azu ku kayi da shi zai dawo ka bashi shawarwarin hanyoyin da
za a bi domin kula da mara lafiyar,ya ce min ka buk`aci wasu papers a wurinsa don haka ya tafi Gida
domin ya d`auko daganan yace if possible ka sanar da ni advice d`in".tsura mata ido yai yana son ya gano
wani abu mai muhimmanci daga gare ta wanda yake jin yana jan shi zuwa inda ta ke amma kuma ya kasa
gano komi ye,dole sai haƙura yayi gami da zuba mata ido yana jin me ta ke cewa.

Cikin k`ank`anin lokaci yai mata bayanin irin su kula da shan maganin ta,rashin son hayaniya a inda
take,yawan lura da halin da take a ciki a koda yaushe,samun isasshen barci,aikata abubuwan da ta fi so
da dai sauran su,ya kai k`arshe zancen da wannan.

Jiki a sanyaye Jedeeda ta mik`e ta na mai cewa da shi,"Thanks a lot Doctor na ji dad`in bayanan ka
kuma by the will of God za a yi kamar yanda ka ce kuma za a kiyaye abinda ka ce".Hakanan ya ji
muryarta har a saman kan shi,har sai da takai shi ga kafeta da idanuwansa masu tasiri ga wanda ya ke
kallo.

Sai da ƙyar ya iya cewa da ita bayan ya samu ya mallaki kan shi, "Don't Mind in har da zai ku yi amfani
da duk abinda na ce in sha Allah a hankali a hankali za ta rik`a samun sauk`i,idan ba wani abu da yai
saura za ki iya tafiya".

Rasa me zata ce tai ta so ace ko Yaya ne ya bata damar da za ta yi magana akan abinda ya faru da`zu
amma ko da wasa bai ba ta fuskar hakan ba kamar ma ba da shi abun ya faru ba,har ta kusa k`ofar fita ta
ji ba za ta iya fita ba har sai ta ce da shi wani abu akan abinda ya faru,sai dai tana jiyowa da niyar ko
yunk`urin ta ce wani abu,aka banko k`ofar da k`arfi a ka shigo batire da an ba mai shigowar izinin hakan
ba.

Bakinta na rawa ta fara ambaton sunan shi da cewa," Papa lafiya what wrong with you,ko dai jikin
Momyn ne ya motsa ?".
Ko d`aya bai saurare ta ba domin gabad`aya hankali da tunaninsa ya na kan kan Dr Jaheed, "Dr kalla ka
gani na kasa yarda da abinda na gani a jikin this papers Anya da gaskene Gloria na sane da wannan cutar
sama da shekaru Ashirin,kai I can't believe this".

Amsa Dr Jaheed yai ya na duba paper's d`in na wani d`an lokaci kafin ya ce da shi," I'm sorry to say Sir
domin Maganar gaskiya Madam Gloria ta san da wannan lalurar har ma tana medication d`inta ka ga
wannan takardar shaidar ta ziyarci wani babban Asibiti ne U.s a shekarar 2018 wannan kuma photon
kwakwalwar kanta ne da aka d`auka a Paris in the year 2007 da kuma sauran test-test da ta gudanar
akan hakan".

"What Momy ta san da wannan ciwon at how", Jedeeda ta tambaya fuskarta d`auke da mamakin
abinda ta ji.

" Kun ga bai kamata ku tada hankalin ku ba domin hakan zai iya sake jefa ita patient d`in cikin wani hali
in har ta farka ta gan ku a haka,yanzu ba lokacin maganar ba ne ba,ta lafiyarta mu ke,mu gare mu ma
bayyanar wannan hujjojin wata sabuwar nasara ce domin zamu yi amfani da ita mu cigaba da d`orata
akan medication d`in da ya kamata".

"Kai .....hah....why are you doing that for me,how long mu ke a tare amma ba zaki sanar da ni wani
abu daya ya ke damun ki ba ,wannan wanne irin betraying ne haka shin dama can ba zaman amana mu
ke ba?"....

Dakatar da shi Dr yayi ta hanyar zaunar da shi kan d`aya daga cikin Seater's dake kusa da shi nan ya
cigaba da bashi baki har ya samu ya shawo kan shi hankalin shi ya d`an kwanta kafin ya maida kallonta
akan Jadeeda ya ce da,ita,''Am if possible ki d`auke shi ki mai da shi Gida yai wanka ya d`an huta ya ci
abinci sai zuwa anjima sai ki dawo da shi may be zuwa time d`in ma ta farka amma dan Allah na rok`e ku
Dan Allah kar wanda ya ta da wannan Maganar for now domin ta na buk`atar hutu".

" I promise you ba abinda zai faru ba wanda za sake tada maganar a dai yanzu mun gode da kulawarka
a gare mu,thank for your care, kindness and consent ".

Da murmushi ya amsa ma ta abinda ta ce d`in nan ta kama hannun Revered Anderson Wanda ya zama
kamar sick person su ka fita daga cikin Hospital d`in gabad`aya.




~~~~~~~




"My World da alama dai yau ka yi aiki da yawa domin ga gajiyanan duk ta bayyana akan fuskar ka".
Hannunsa ya kai ya na mai shafa kan shi har zuwa saman fuskarsa kafin ya ce," Ke dai bari Gimbiya ta
tamkar mutanen jirana su ke,ko kusa ban samu wani lokaci da zan huta ba".

"Eyyah I'm so sorry My World na ga hakan kwance akan fuskar ka,ga shi kuma ba kowa a tare da kai
sai kai kad`ai".

" Ayush kar ki damu I will be okay ,yanzu ba ga ki ba,in sha Allah komi zai koma normal ".

" A'a ni ba haka na so ba,iya haka bai wadatar da ni ba".

Murmushin gefan baki ya sakar mata wanda yake k`ara k`awata fuskarsa kafin ya ce da ita,"Ko za ki
taho yanzu ne kin san zan yi farin ciki da hakan ?".

Zaro idanunta waje ta yi tana mai cewa,"Rufa min asiri kar ka sa Ummu Nurain ta zo ta addabe ni da
masifar ta babu gaira babu dalilin".

"Matsoraciya ki taho mana"....sai da Gimbiya Ayush ta `bata fuska kafin ta ce da shi,"Ni wallahi ba
tsoranta na ke ji ba,kawai ba na biye mata ne don kar ajina ya zube,me ye zai sa ma inyi hayaniya ko
fad`a da ita sai ka ce ba Gimbiya Ayush ba,in ma ba dan k`addara da ta had`a ni Auren Miji d`aya da ita
ba ai da ko hanyar da na bi,ba ta isa ta bita ba".

Sosai ta zage sai zuba masifa ta ke,shi kuma ya tsura mata ido tamkar television,ganin kamar ya zuba
ma wuri guda Ido ne ya sa ta ta d`an dakata ,sai a lokacin ta fuskanci ita ya ke kallo.

" Wai har haka ake kishina kuma ake sona ban sani ba ?"ya tambayeta ba tare da ya tsaya ba ya
ce,"Ashe ni Muhammad Jaheed d`an gata ne har haka ban sani ba".

Bata iya ta ce mi shi komi ba sai sake tamke fuskarta da ta yi alamun har yanzu ta na kan k`adamin
fushi akan Maganar da ya yi.

"Ina son ki,ko fushi ki ka yi kyau ya ke k`ara ma ki,komi ki kai burge ni ki ke kuma k`aramin son ki ya
ke,kin can-canci a so ki,daga nan ina iya haikato daddad`an k`amshin da ke fita daga jikin ki,ke d`in ta
daban ce you are so classic woman".

Irin wannan dad`ad`an kalaman ne suka ribaci Gimbiya Ayush wanda tuni ta ma manta da wani batun
Ummu Nurain da yai mata har daga k`arshe take cewa da shi," Ya kamata fa ace ka zauna kayi dogo
tunani cikin jagorantar Al'umma `bangaren Addini ko kuma kula da lafiyar su wanne za kai ,ka ajiye
d`aya,ba na son in rik`a ganin ka cikin irin wannan yanayin, kwata-kwata ba ka samun hutu kullum cikin
aiki ka ke".

"Hmmmm Gimbiyata kenan ba abinda za a fasa walau jagorantar Al'umma ko kuma kula da lafiyar su
domin duka aikin taimako ne ,aikin Allah kuma kin ga bai kamata in janye daga wani `bangaren ba tunda
duka suna da buk`ata ta".

Bud`e baki Gimbiya Ayush ta yi da niyar za ta sake cewa da shi wani abu ya dakatar da ita da cewa,"
Addu'ar ki kawai na ke nema da kuma fatan nasara akan komi,sai dai ban sani ba ko hakan ya na sawa in
shiga hak`ink`i ba?",ya tambaye ta yana mai tsare ta da idanunsa"A'a ni ko d`aya ,kawai dai ba na son in
cigaba da ganin ka a yanayin da na ke ganin ka".

"Kar ki damu ba abinda zai faru da ni ,ina tare da Allah, kawai Addu'ar ki na fi so da kuma kulawar da ki
ke bani", da haka dai su ka kai k`arshe firar ta su da ita.

Gyara zaman laptop d`in da ya ke aiki da ita yai sai dai tun bai yi nisa ba wayar shi da ke gefan shi ta
fara rurin nai man a gaji,sai da yanayin fuskar shi ya sauya kafin ya picking d`in call d`in muryarsa d`auke
da sallama.

" Haba Abu Nurain wannan wane irin rashin adalci ne,me na aikata ma ka har haka da ka za`bi ka
wofintar da ni ka nuna ma duniya ni ba kowan kowa ba ce a wajen ka, kar ka manta nifa `yar'uwar ka
ce,ko ba so akwai zumta a tsakanin da kai ".

" Ya Allah Zeenat mai yai zafi har haka mai ya kawo irin wad`annan k`ananun zancen ?".

"Oh k`ananun zancen ma za ka kira maganar da na zo da ita,yau kwanan ka nawa da tafiya ba Kira ba
sak`o hasalima ban sa ina ka tafi ba kar ka manta ni ma fa Matar ka ce kuma Uwar d`an ka ina da hak`k`i
akan ka".

Cire wayar Jaheed yai daga kunnen shi yai kamar zai yanke kiran sai kuma ya fasa ya san hakan ba
K`arami K`ara rurar wutar rikici zai ba.

Cikin sanyi da kuma gajiyar da ya ke tare da ita ya ce da ita,"Ban san me ki ke so ki mai da ni ba
Zeenat,ke fa na zo part d`in ki ki ka rufe min k`ofa kawai dan kin ga na fara shiga Part d`in Gimbiya Ayush
bayan dawowata daga office,gabad`aya ki ka tashi hankalina,ki ka hanani natsuwar rai, Randa kuma zan
yi tafiya tun da farar safiya na na zo inda ki ke ina maki magana amma ki iya ki bud`e idanun ki ki kalle ni
ki ka kasa , balle har in sa ran za ki saurari abinda na zo ma ki da shi,haka na k`araci zamana na gaji a
haka ki ke iya bayyana ta ki Soyayyar ta hanyar wani mahaukacin kishi na ki marar amfani ?".

" Ni ban wani san ka zo ba,kuma kai ma ai kasan Nurain ba ya wani barina in yi barcin kirki,kullum cikin
fitina da k`iriniya da rashin ji ya ke,da safen kawai ne na ke samu in yi barci mai isata,kuma ai nasan
waccen Matar son ka sanar da ita kafin ka tafi sai ni da ba a bakin komi na ke ba"......

"Kin ga Zeenat ba na son tashin hankali ,in dai kin kirani don ki tada min hankali ne sai da safe".

Tana k`ok`arin sake cewa da shi wani abu ya katse kiran ya barta da wani sabon takaicin a cikin
ranta ,ba shi ya tashi daga nan inda ya ke ba har sai da ya kusa raba dare daga k`arshe ya tashi yai sallolin
sa kafin barcin wahala ya kwashe shi akan prayer mat d`in
*JADEEDAH*



(It's a story of two love birds who are so different from each other )

STORY & WRITTEN BY :

(*Cwt~Sumiey*)

Marubuciyar littafin

MENE NE ABIN YI ?

KARAGAR MULKI

And now.....*JADEEDAH*



https://chat.whatsapp.com/CWkZfMqvD4H0mtd7WW6Xbz.



https://whatsapp.com/channel/0029VapqU8C002T5Bz8RSQ0a




BOOK 1




PAGE 19❤




"Wow Gimbiya Ayush irin wannan Ado haka sai faman k`amshin da walwali ki ke sai ka ce wata sabuwar
Amarya,ko dai Doctor na kan hanyar dawowa ne?", Anisa ta tambaye ta na mai sake bin ta da kallo.
Sai da Gimbiya Ayush ta rausayar da kanta gami da jujjuyawa kafin ta ce da ita, " Ba d`aya k`anwar
biyu,wannan kwalliyar da ki ke gani na yi ta ne domin rad`in kaina ba,babu inda zani Doctor kuma sai nan
da zuwa three days zai dawo".

"Yauwa Gimbiya Fadeelah ina sak`on da Fulani ta bayar ta ce ki kawo min ?".

" Oh ya na motor na baro shi amma in zamu tafi sai in d`auko miki".

"Ina ba ki isa ba salan kuma ki manta ki sake komawa da shi Masarauta".

" Kai Anty Gimbiya yanzu fa muka zo ko ruwa ba ki bamu ba, ki ke Maganar tafiya sai ka ce wad`anda
ki ke kora".

"Na fa san halin ki Fadeelah tsaf za ki iya sake komawa da shi,kad`an ne daga cikin aikin da za ki
iya,kuma Gidan ai ba bak`on ki ba ne ba ba kin san hanyar da fridge d`in ya ke".

" Haba k`awata Fadeelah fa now is a big girl ta ya za ki rik`a mai da ta baya,ita ma fa ta san aikan Fulani
ne ba za ta yarda ta manta ba".

"Yauwa Anty Aneesa fad`a mata dai,kowa yasan yanzu na girma".

" Hmmmm kin girman dai Fulani ta gama sangarta ki ai".....,Anesa ta katseta da cewa,"Wai ke tsaya da
za mu wuto na ga k`ofar Part d`in waccan Matar kamar a rufe kar dai ki ce min da ita yai tafiyar ?".

Sai da Gimbiya Ayush ta zaro idanun ta waje kafin ta ce"Wai wa ki ke nufi kar dai ki ce min Ummu
Nurain, ai ko k`ofar Gida in ba ta zama dole ba ba zai tafi da ita ba balle Gari ya gaarara har Abuja".

"Ki ce har yanzu ta na nan da halin ta na k`azanta" ,"Ai in gaya maki sai abinda yai gaba,yanzu da za ki
shiga Part d`in ta ba lalle ki iya shak`ar iska ba,sai fitinannen kishin tsiya,kamar wacce ke had`iyar wuta".

"Ta`b aiko ta na ruwa,wa ya gaya ma ta yanzu mata na zama da k`azanta ai kai duk ya waye,ba irin
wannan duhun kan"," AI ko ban da ita ita da yanzu za ki fara yi mata complain kan bata yin tsabta sai ta
ce,maki ai Nurain ne ba ya barin ta zauna sakat,kullum cikin sa ta aiki ya ke, idan ki ka matsa sai ta ce
har da laifin Dr. da ya hanata d`aukar me aiki,har ma `yan'uwanta sun kai ga gajiya da yi mata magana
sun kyaleta,ke ni wallahi da ni Imam ya fara Aura na rantse zai yi wuya ya k`ara kallon wata mace bare
har ya kai ga yin sha'awar Aurenta".

"Ikon Allah warnder shall never end wai yau Ayush ke ce ki ke crushing akan d`a Namiji ki ke bayyanar
da mayatar son shi a fili abun akwai d`aure kai da ban mamaki".Cewar Anesa k`awarta ce tun yarinta sai
kuma Gimbiya Fadeelah da take k`anwarta.

" Hmmmm ba za ki gane ba Anesa,dagaske ina son Imam Jaheed so kuma ba irin na wasa ba,Wanda
har ya kai na kan iya mantawa da asalina ko ni wace ce idan ina zaune tare da shi rikid`emin ya ke ya
koma shine Yariman ni kuma a matsayin hadimar sa, duk wani abinda ya ce shi nake yi ,bana son
sa`bawa dokar sa,ki na gani saboda gudun `bata mishi rai ya sa Na sallami duk wata Baiwa da na zo da ita
Gidannan ".
Sake baki Anesa tai tana mai bin Gimbiya Ayush da kallo," Ki gane Anesa Soyayya da Ustaz akwai
dad`i da tsayawa a rai,idan ki ka samu irin wannan dama kar ki yi wasa da ita".....shigowar Hameed ita ce
ta dakatar da zancen na ta.

`Dan dakatawa yai kafin ya ce,"Anty Gimbiya bak`i ki ka yi ashe ?".

"Eh Gimbiya Fadeelah ce da kuma Aneesa,ka shigo ma na ka tsaya daga gefe".

" Au ashema ba baki ba ne `yan Gida ne",ya kai zancen ya na mai wara idanunsa a cikin Parlourn daga
bisa ni ya samu wuri can gefe ya zauna".

"Meet my friend Anesa sai kuma Gimbiya Fadeelah autarmu" cikin mutuntawa su ka gaisa da juna
kafin ya ce,"Ai na san Gimbiya Fadeelah amma a IG ina d`an ganin videos d`in ta haka", da d`an sauri
Gimbiya Fadeelah ta d`ago tana mai sauke idanunta akan shi.

Murmushi ya sakar mata kafin ya ce,"Eh Hameed Abubakar Mai Fata shine suna na har DM na ta`ba yi
maki so d`aya amma ba feedback,daganan ban sake ba ".ya kai ƙarshen ya na mai sakin fara'a a saman
fuskarsa

" Fiye da haka ma za ka gani kai ba a IG ba hatta a Gida cikin Masarauta haka Gimbiya Fadeelah ta
ke,sai ka zo ka ka gama abinda ka ke a Gidan ba tare da ka sa ta a cikin Ido ba"Cewar Gimbiya Ayush.



"A to Na yi shiru tunda abun haka ya ke", rasa me ma Gimbiya Fadeelah tai sai dai bin sa da kallo da
take,shi kuma a lokacin ya maida hankalin sa kacokan wajen Gimbiya Ayush ya na mai cewa da ita," Am
ki yi hak`uri tun jiya Yah Imam ya ki rani ya ce in zo in tambaye ki ko da akwai wani abu da ki ke so ko ya
k`are a cikin Gidan,sai in je in siyo ma ki".

"A'a ha ba yace ya kusa dawo fa?"," Eh haka ya sanar da ni,amma kin sa ko da ya dawo bai fiye zuwa
irin wannan wurin ba","Na sani na yi zaton ko ya d`aga Maganar dawowar shi ne","A'a yananan ko d`azu
da muka yi waya da shi haka ya gaya min".

"Okay akwai kayan abincin wadatattun a store fridge d`ina ne kawai kayan cikin sa su ka fara k`asa sai
kuma Vegetables, kai duk abinda ya kamata ka siyo ka siyo kawai".

Mik`ewa tsaye tare da cewa,"Okay bari in je yanzu in dawo fatan dai ba inda za ku don sauri na ke da
akwai inda za ni in na dawo?".

" A'a ba inda zamu,in ma da inda zamu sai in bar maka sak`o wurin gate keeper","To ba damuwa
hakan ya yi barin in je part d`in Ummu Nurain in ji na ta sak`on ".

"In ka shiga ka gaishe min da ita"..... Da sauri ya katse ta da cewa," Wa!?,Ni a'a ba dai ni ba ai wannan
sai ki ja in na shiga in fito da k`afa d`aya".

"Yo kai ko me zai ja maka fitowa da k`afa d`aya sai ka ce Wanda ya shiga wani bak`on wuri Gidan
yayan ka fa ne".


Please Login or Register in order to submit comment