You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

sai na ɗauke su mu tafi tare,
ko bacci nake ji har idan idon su biyu bana yar da natafi na barsu su idan su biyu,
dan duk lokacin da naje na musu wanka Naseem yarika zillewa yana son shiga ruwan yarika bori da shure kafafu wai sai dai na barshi yashiga ruwan,
shi yasa nake jin tsoro kada wata rana nayi bacci yace zai je yashiga ruwan bugu da kari ma zai iya tunkarar babban kogin nan,
to haka zan yi ta zaman gadin su har sai sunyi bacci kafin nima nayi.....


Zaune nake na buga uban tagumi nayi shiru ina lissafa kwanakin da mukayi a cikin daji tabbas yau idan ban mance ba kimanin watan mu biyu kenan acikin dajin,
wasu hawaye ne suka zubo min na share su.
Ikon Allah haka zamuyi ta rayuwa a cikin daji har mu mutu karshe namun daji sucinye mu,
tausayin kaina da na ƴaƴana ya kamani sai na rungume su na fashe da kuka.
ganin sunyi bacci na shin fiɗa musu abun kwanciyar su wato zanin goyon su,
na janyo hijabina na lulluɓe su,
na mike na soma tafiya..
kallon sama nayi hadari ya haɗu bakikkirin daga can kasa sai walkiya ake da rugugin tsawa da alama dai anata zabga ruwa daga can da nisa,
ina tsaye ina tsinko abun da zan ci daga can nesa narika jin kugin ruwan nan yana karuwa sosai ba kamar nasauran kwanaki ba ƙugi ne sosai mai matukar amon sauti sosai.
da sauri na juya na fito daga cikin bishiyoyin na nufi in da su Naseem suke kwance cikin hanzari.
Daga can na hango ruwan yana wani irin gudu da kugi daga can da nisa yana wani sama da kasa.
Huff na ɗaga Nasmah na goya ta kana ɗauki Naseem da gudu na juya ganin ruwan
yana haurowa a hankali inda muke yanata taruwa a hankali har ya wuce idon sawu na,
daga can cikin kogin kuma yana wani irin gudu yana yin sama da kasa sai ruwan ya haɗu da junan sa ya fansalu sai yayi sama sannan ya koma kasa.
gudu nake da iya karfi na nayi bayan dutsai cikin sansanin tashin hankali galin ruwan ya iso inda muke zama ya mamaye gurin wan da yake gudu daga can kuma sauran kiris yakaraso,
bayan dutsai da na ɓoyen ma tuni ruwan ya iso har gurin,
cikin kaɗuwa da tashin hankali nasoma hawa kan dutsan da ko a mafarki ban taɓa tunanin zan iya hawan sa ba sai gashi na haura kan sa da goyo da kuma wani ɗan a hannuna can kuma saman sa sosai.
kan kace me ruwan yataho da wannan kugi da ambaliyar da yake,
gurin da muke zama yadawo tamkar cikin ainihin kogin hatta bishiyoyin nan sai da ruwa yahaye kansu,
duk da girma da tsawon da dutsai ɗin nan yake dashi sai da ya kusa haurowa sama in da nake tsaye jikina na cirawa,
rumtse idanuna nayi nakuma buɗewa cikin ruwan da yake wani irin gudu da kugi, ina ambaton sunan Allah, yau kam nasan mutuwa ce yazo mana babu makawa ruwa ce zata zamo ajalin mu,zata tafi da mu mu kuma mutu a cikin ta.
kankame ƴaƴana na kuma yi nagama sadakarwa na mika wuya ga mutuwa gaba ɗaya.
wasu irin halittun ruwa narika gani daban-daban wani abun ma idan nagani rufe idanuna nake da karfi har sai ya wuce kafin na buɗe,haka sukayi ta wucewa a kan ruwan,
wani abun da yadaɗa firgita ni da bani tsoro daga can najiyo guɗa mai karfi a can tsakiyar ruwan guɗa mai tsawon gaske babu jan numfashi ko sauke wa,
ido na zuba sosai daga can in da guɗar ke tashi sai dai banga komai ba sabo da sakanin mu da nisa kuma da alama daga can kasa abun ke wuce wa.
sai narika jin kamar iska tana jana kuma karfin iskar tacikin ruwan ne,kuka na fashe dashi na durkushe kan dutsai ɗin na kankame jikina,ina ambaton sunan Allah.
har lokacin ban fasa jin iska na kokarin jana ba,
a hankali guɗan da ake yarika raguwa alamun yana yin nesa da ni,
iskar da ke jana kamar zai faɗar dani cikin ruwan sai yarika sassauta, lokacin da na dai na jin sautin guɗar nan gaba ɗaya iskar ta tsaya.
abun tun sassafe sai yamma can kafin ruwan yafara sassauta gudun da yake, yana sassauta yana yin kasa-kasa,
a hankali yarika yin kasa yana wuce wa har ya dawo in da yake,
Numfashi mai cike da zallar tsoro na sauke a sannu narika bin gurin da kallo har zuwa gurin da muke zama,
yashin ya daɗa wankuwa yayi fari soll sai dai har lokacin da jikan ruwa sosai a hankali nafara kiciniyar sauka daga kan dutsan nayi matukar mamakin yadda akayi na iya hawa saman dutsan,
daƙyar na iya sauka kasa.
a hankali narika takawa in da kafata har yana lumewa cikin saka sabo da har lokacin da dam shin ruwa,
a hankali na matsa can gefe in da shima akwai damshin sai dai ba kamar in da muke zama ba.
ranar a nan muka kwana cikin ciyawa,
sai dai ban yar da na rumtsa ba dan gani nake kamar ruwan zai dawo....

Washegari da safe gurin ya daɗa sha ya tsantsame sai dai har lokacin da ɗan damshin sai dai ba kamar na jiya ba,
sai da rana yafito sosai kana
a hankali na ɗauko su Nasmah muka dawo gurin zaman mu,
ido na kurawa kogin nan ganin yadawo yan da yake da, kamar bashi bane jiya yayi ta hauka Allah mai iko.
ɗan kwalin kai na na kunce na shin fiɗa a kasa kana na zaunar da Naseem a kai ina faɗin
"Zauna kada ka sauka kasa kaji gurin da sanyi".
da sauri na kunco Nasmah da take ta musu-musu tana kuka a abaya,
na zauna na basu abincin su,
sai dai har lokacin bata fasa kananan kuka ba,
jijjiga ta nashiga yi ina faɗin
"Yi hakuri Nasmah nasan wan ka kike so kuma nasan ruwan nan akwai sanyi kibari rana yadaɗa yin zafi idan ruwan yayi ɗumi sai na muku".
nayita jijjiga ta.
zuwa can an jima
jin rana yadaɗan yi zafi sosai sai na tuɓe su na dubi Naseem da ke zaune yana ta wasa da yashin gurin nace
"Zauna na fara yi mata wanka sai na ma ka ko".
na mike da ita a jikina na isa gurin ruwan da muke wanka, ruwan yada ɗa yin fari soll,
kasan cewar rana ya taso ruwan har yana kashe ido sabo da tsabar hasken da ya kara,
a hankali na fara yi mata wankan ina yi ina kawar da kai na daga kallon ruwan saboda kashe min ido da yake, tamkar hasken ranar a cikin ruwan yake.
koda na gama yi musu wankan.
babu jimawa sukayi bacci,
mikewa nayi na koma gurin ruwan domin yin al'wala, na sun kuya ina ta kare fuska ta da hasken rana ke haska cikin ruwan yana kashe min ido, na saka hannu cikin ruwan a hankali na ɗibo na fara yin al'walar, na kuma mai da hannuna a karo na biyu, da sauri na ciro hannun jin na taɓa wani abu,
sai kuma na mai da hannun a hankali jin kamar dutsai ne na taɓan, a raina nake ai yana cewa ai dutsan yashi ne,
na cusa hannuna nakuma ɗibo ruwan sai na haɗo da yashi da wani farin dutsai, ina ɗago hannuna hasken rana ya haska dutsan tamkar wutan lantar ki mai hasken gaske. da sauri na rumtsa idanuna jin hasken har cikin jijiyoyin idanuna, cikin hanzari na watsar da yashin gefe ina mammatse idanuna,
nayi al'walan da sauri na bar gurin...
koda yamma tayi da nazo yin al'walan la'asar lokacin rana tayi sanyi hasken ruwan yaɗan ragu,
ina saka hannuna cikin ruwan nakuma ɗauko dutsai ɗin,
A hankali na ɗago shi narika juyashi a hannunna dutsan fari soll mai kyau da shi sai kyalkyali yake duk da kuwa babu hasken rana,
narika kallonsa gwanin ban sha'awa.
A hankali na mika hannu na ɗauko ɗayan da ɗazu nayi wurgi da shi na haɗa su ina ta juya su cikin sha awa,
nakuma saka hannuna cikin ruwan nayi ta laluɓo duwasun ina ciro su sai da naciro guda takwas na haɗa da biyun hannuna suka zamo guda goma,
bayan na gama al'walar na koma gun su Nasmah a kan abun goyon su na zuba duwasun,
ina zubawa kuwa da sauri har suna rige-rigen ɗauka sukayi ta wasa da shi,
nima ina idar da sallar na zauna nayi ta tayasu wasan da duwasun gwanin ban sha'awa da kyau da ɗaukar ido.
dariya nayi ganin yanda suke wasa da duwasun su ɗauki wannan su wurga sai subi sukuma ɗauko wa,
nace
"Kuma yayi muku kyau ko ai dutsan mai kyau ne nima wlh yayi min kyau kuyi wasan ku da shi".
nafaɗa da murmushi ina daɗa tura musu duwatsun gaban su...

Washegari ko da rana yafito dukan su na kwasa naje musu wanka Nasmah na goye sai na fara yi wa Naseem ko da na gama mishi, sai na saka hannuna nayita laluma cikin ruwan can na ciro dutsai ɗin guda ɗaya na dunkule shi cikin hannuna na cusa masa cikin hannunsa ina faɗin
"Gashi na karo muku abun wasa dun kule shi a hannunka kar ya kashe mana ido".
na kunce Nasmah na goya shi itama nayi mata wanka kana na laluɓo mata guda ɗaya na saka mata cikin hannun ta nace
"Kema ga naki".....★


Zaune muke muna cin kayan itatuwan dana sinko mana shiru nayi tare da kasa kunne daga can da nisa nake jiyo muryar kukan shanu,
da sauri na mike tsaye ina cigaba da baza kunnena ina son gane in da kukan shanun yake fitowa,
duk da daga ji yana da nisa da mu sosai,
wani irin farin ciki ne da murna ya lulluɓe ni,
dan na tabbata shanu bazai zauna shi kaɗai cikin daji ba sai da mutum.
cikin tsananin farin ciki da murna na sunkuya da sauri naɗau ki Nasmah ina faɗin
"Kuzo muje naji kukan shanu a tacan wata kila mu sami ɗan uwan mu bil adam a gurin".
ina ɗago zanin goyon su duwasun da suke wasa da shi suka zubo kasa,
banko bi ta kan su ba na goya Nasmah da sauri na ɗau Naseem da sauri nasoma tafiya.
har nakusa fita daga cikin bishiyoyin sai na juyo ina juyowa kuwa,
na hango duwasun suna wani irin walkiya kasan cewar lokacin rana yafara tasowa,
Naseem dake hannuna kuwa tsalle yarika yi yana nuna duwasun da hannu yanata kokarin zame wa a hannuna,
murmushi nayi nace
"Oh Naseem dutsunan wasan ku ko bari naje na ɗebo muku".
na juya da sauri na ko ma gurin ɗankwalin kaina na ciro naɗibi duwasun duka na zuba cikin ɗan kwalin na ɗaure na rike a ɗayan hannuna,
na mike da sauri muka kama tafiya.
ta in da nafi zato da tunanin tanan kukan shanun ke fita na ɗau hanyar da sauri.
sai dai munyi tafiya mai nisan gaske amma ban ga wani alamun shanukai ba hasali ma kukan su da nake ɗan ji yanzu na dai na, har na fara tunanin wata kila ma kunnena ne yajiye min ba dai-dai ba.
a gajiye na ja na tsaya tare da waigawa baya a raina nake faɗin
"Zan koma kawai gara rayuwar can ya fiye min na ko ina acikin dajin nan".
ga mamakina sai naga nayi nisa sosai dan ko katon dutsai ɗin nan bana hangowa na juya da zummar komawa bakin kogin sai kuma na hakura ganin nayi nisa sosai.
gashi kuma yamma ta fara yi sai na zauna kawai a gurin a nan gurin muka kwana washegari da safe ina zaune ina ɗan gyangyaɗi dan jiya ban samu nayi bacci ba dan acikin sun kuru muka kwana, kukan shanun nan irin na jiya shi ya farkar da ni firgigit na nimike da sauri.........!★




*Na jiya da gobe na baku*👌🏻😆




Mommyn Twins ce



Zunbur na mike tsaye jin da gaske ba wai ko kunne na bane ke yi min karya kamar yan da jiya nayi tunani,
da sauri na ɗauki Nasmah na goya ta,
sannan na ɗauki Naseem na rike shi,
na ɗauki ɗan kwali na da na ɗaura musu duwatsun wasan su na rike a ɗaya hannuna.
cikin sauri mai haɗe da gudu narika bin hanyar da nafi sammani da tunanin tanan ne kukan shanun ke fi.
nayi ta tafiya idan naji shanun sun dai na kuka sai na tsaya na huta idan duka cigaba sai na mike da sauri nacigaba da tafiya,
haka nayi ta tafiya ina yi ina hutawa duk san da shanun sukayi shiru idan suka cigaba da kukan sai nima nacigaba da tafiya ta in da nake jiyo kukan su daga can nesa sosai.
nayi tafiya har na godewa Allah.
ina zaune a gindin wata bishi ina hutawa gaba ki ɗaya jikina yayi sanyi dan tun ɗazu da shanu sukayi kuka basu kuma ba,
har nafara cire rai da sake yin kukan nasu zunbur na muke jiyo sautin su daga can kasa kuma yanzu nafi jin murtar nasu yafi kusa dani akan na ɗazu.
da sauri na mike na soma tafi
ɗan tafiya kaɗan nayi da sauri naja
burki ganin rami a gabana,
in da nake tsaye kuma tudune mai tsawon gaske,
dan saura kiris na zurma kafata kasa.
daga can kasan shima duk daji ne da bishiyoyi,
daga kan tudun in da nake tsaye ina hango shanukai ɗin can da nisa suna ta kiwo kasan cewar a kan tudu nake.
kallon kasa nayi mai uban nisa da tsawo
"Taya zan iya sauka a nan gurin".
nafaɗa ina daɗa kallon kasan.
a hankali nafara bin gefe tacan ɗaya ɓarin gefen dama na,
ganin tacan ɗin bai kai in da nake tsawo sosai ba,
a hankali nafara sauka ina takawa a hankali,sam naki yar da na kalli kasa sai naga ya daɗa yi min nisa kaina kuma sai yarika juyawa sabo da nisan sa,
nayi rabin saka daga saunin sai kawai kafata ta sule na zame muka rika gungurawa kasa tuni su Naseem suka saki kara mai karfi,
kan kace me Naseem ya suɓuce a hannuna ya ganaga can yafaɗi kasa,
Nasmah da ke baya na kuwa mukarika gungurawa da ita, cak numfashi na ya tsaya dan ganin ina kokarin isan kasa da baya kamar an juyani sai kawai na faɗi da gefe a kan hannuna.
kara dukan mu muka sake da karfi cikin azabar jin yadda na faɗi kan hannuna tamkar hannun zai ɓalle yabar jikina.
nayi-nayi na tashi na gagara tashi nafi minti goma kwance ko kyakkyawar motsi na kasa, ina kallon
Naseem yashe a can gefe yana ta zandara ihu,
Nasmah ma sai ihu take tana goye a bayana har lokacin...

Nayi ta yunkurin tashi na kasa da kyar na kai ɗaya hannuna na kunce zanin goyon ta kwanta gefe tana cigaba da tsala ihu duk jikin ta ya kwakkwar jane,
hannuna da na faɗi a kansa na ɗagosa da kyar kana da kyar na iya mike wa zaune.
yayin da hannun da na faɗi a kansan ke min wani irin zugi da raɗaɗi,
da kyar na yunkura na mike ina ɗingishi nazo gun da Naseem yake kife a kasa yana ihu,
na zauna na ɗago shi da ɗaya hannuna mai lafiyar,
nashiga kakkaɓe masa jikin sa ina jijji gashi,
shima duk ya kukkuje a.
Nasmah ta rarrafo tana kuka ta zo in da muke na janyo ta na cigaba da rarrashin su,
duk abun da nake cikin dauriya kawai nake dan nima duk jikina a kukkuje yake,zafin raunukan jikina bai kai na hannun da na faɗi a kan sa ba.
duk raunukan jikin yaran sai jini yake fidda wa.
rungume su na yi tare da fashewa da kukan azabar da hannuna yake min, ko matsi nayi da hannun sai naji zafin har cikin raina.

Mun jima zaune agurin jin tamkar karamin zafin ake a hankali na lallaɓa da kyar na mike,
na kamo Naseem da hannun na mai lafiyar na ɗagoshi da kyar na iya goya shi, dan shi yafi Nasmah jin ciwo.
ina matse idanuna hawaye na zuba cikin jin azaba,
sannan na ɗauki Nasmah na rike ta
a ɓarin hannuna mai lafiyar,
gefe na na waiga in da ɗankwali na dana ɗaura musu duwatsun wasan su yafaɗi can gefe shima na isa na ɗau ka da hannuna mai ciwon,
Jin wani irin zugi da hannun yayi min sai na sake ɗankwalin kasa,
na juya ina faɗin
"Naseem Nasmah bazan iya ɗauka muku abun wasan kuba hannuna yana min ciwo idan na samu wasu zan ɗiba muku a hanya".
a sannu na soma tafiya ina ɗaga kafata ahankali-ahankali,
sai kuma na tsaya a raina nake faɗin
"To yanzu idan na tafi na bar ɗankwali na anan a ina zan samu abun da zan ɗaura a kaina idan na cire hijabi na na rufe su Nasmah da shi?".
nayiwa kai na tan bayar,
idanuna na rumtsa nasan idan na ɗauka hannuna zai min zafi.
a raina nake ayyana na kunce Duwatsun na zubdasu sai na ɗauki ɗan kwalina nasan shi bazai min nauyi ba.
na koma in da yake na ɗauki ɗan kwalin ina kokarin kuncewa nayi nayi na kunce na kasa saboda da hannu mai ciwon ne jin hakan yana daɗa kara ramin zugin hannuna ne sai na bari.
na zaunar da Nasmah a kasa Sannan naɗan kunce zanin goyo na cusa ɗan kwalin sakanin bayana da jikin Naseem,sai na mayar na ɗaura,
kana na ɗauki Nasmah muka fara tafiya a hankali.
dan yanzu bana iya tafiya da sauri dan duk jikina ciwo yake min ga su Naseem har yanzu suna ta kuka.

Idan muka ɗan tafi kaɗan sai na sauke su na huta kana muku ma ci gaba,
Abun mamaki munyi tafiya mai nisa amma har lokacin bamu iso in da shanun nan suke ba, daga can saman tudun da muka gangaro da nake hango su banyi zaton zanyi irin wannan tafiya mai ni haka ba kafin na iso su.
a haka dai nayi ta tafiya har na iso kusa da su,
wasu matasa Fulani ne guda biyu suke kiwon shanun,suna tsaye can gefe sai dai na lura basu san da zuwa na gurin ba duk da dai sakanin mu da ɗan tazara,
a sannu na isa gindin wata bishiya na zauna kana na sauke su Naseem,
nayita rarrashin su Nasmah har sukayi bacci.
muna nan zaune a gurin har yamma sai sannan makiyayan nan suka fara kaɗa shanukan,sunayin gaba,
Ganin haka na mike da sauri na ɗauki su Nasmah narika bin bayan su duk inda sukayi ina biye da su,idan suka tsaya na tsaya idan suka cigaba da tafiya nima na bisu.
haka dai mukayi ta tafiya har naji badaɗi gashi babu halin nace zan tsaya na huta sutafi su barni,
tafiyar nake ina matsar ƙwalla sabo da tsaɓar gajiya gajikina da ya daɗa kara yin tsami,
muna nan muna tafiya har guri yafara rufawa.
can naga shanun sun tsaya kana a sannu naga sunayin kwana can na hangi bukkoki gefen bukkar cikin wani gurin da a ka zagaye shanun suka shiga, nan makiyayan suka fara ɗaure su,
a sannu na karaso gurin sai na tsaya gefe da garken shanun ina ta raba ido,
Fulani mazaunan gurin sunata harkokin su wasu daga kusurwa daban-daban suna ta ɗaure shanukan su da alama suma yanzu suka dawo daga kiwo,
numfashi na sauke tare da yin murmushi cikin zubda ƙwalla gani na acikin mutane wan da nagama fidda sammanin yiwuwar hakan,
a hankali na tako na tsaya kusa da garken shanun....

wani dattijo ne yafito daga cikin wani gidan da ke gefe da garken shanun,
kana yashiga cikin shanun cikin girmama wa da ladabi matasan makiyayan nan suka shiga gai dashi cikin girmamawa,ya amsa cikin sakin fuska
kana yashiga tayasu ɗaure shanun.
jijjiga Naseem da yake ta musu-musu a bayana nashiga yi dan nasan yagaji ko kuma jikin sa ya masa tsami dan yabugu sosai,ina matse ido hawaye na zuba,
tuni Nasmah ma ta saki kuka, sai na cigaba da gargiza su ina hawaye,
yan da nake girgiza sun hakan yasa hannuna ke girgiza zafi har cikin raina.
da sauri dattijon nan yafito daga cikin garken shanu yana ɗan waige-waige da alama dai kukan yaran yaji yasashi fitowa duba da yan da yake ta ɗan waige-waige,
nan idanunsa ya sauka kanmu da mamaki yake kallona kana yace
"Ke wanene me kike yi a na?".
yayi maganar idanunsa a kaina cikin hausar sa da bata tsaya ba,
banyi magana ba sai masar ƙwalla nake,
"Ke wanene nace me yasa mi yaron?".
cikin zubda ƙwalla nace
"Munfaɗi ne shine yaji ciwo kuma yunwa suke ji".
"Yunwa?".
yafaɗa yana kallo na".
na gyaɗa kai na alamar Eh, yaɗan yi shiru yana kallona,
kana ya kalli su Naseem da Nasmah da kyau sannan yace
"Garin yaya kuka faɗi haɗarin mota ne ina zaku je??".
yajero min tambayar
nace
"Acan kan tudu muka faɗi kuma Yola zamu".
shiru yakumayi alamar nazari kana yajuya tare da faɗin
"Kubiyo ni".
ai ko da sauri na bi bayan sa.
ya shiga gidan tun daga bakin kofa yake faɗin
"Sumaye Sumaye Sumaye".
wata yarin yar dake zaune a tsakar gidan ta mike tana faɗin
"Inna wuro Bappa na kira".
wata dattijo war mata tafito daga cikin bukko da sauri tana amsa kiran sa,
tare da faɗin
"Gani nan Malam".
yace
"Zo ga wani bakuwa nan tazo kuma wai yaron ta ya faɗi a kasa kuma yana jin yunwa bashi abinci yaci".
tace
"Subhanallahi kawo shi nan mugani garin yaya?".
namatso in da take tana kokarin karɓar Naseem dake ta zandara ihu, garin cirosa sa a bayana sai ta bige min hannun,
yarfe hannun nayi tare da faɗin
"Wayyo Allah hannuna".
tace "Ayya Allah kam sansu ke ma hannunka na siwo ne?".
kai na gyaɗa cikin zubda ƙwalla nace
"Eh da muka faɗi ne nima na buga hannuna".
kallon yarinyar dake zaune a gefe tayi tace
"Zo Mero kikarɓa mata yaron hannun ta".
yarin yar ta matso da sauri ta karɓi Nasmah,
tace
"La Inna wuro itama taji ciwo".
Inna wuro tace
"Oh wani irin faɗuwa ne haka sai kace haɗarin mota".
tafaɗa tana roko hannuna tare da cigaba da faɗin
"Ko dai haɗarin mota kukayi ne".
yarfe ɗaya hannun nayi nace
"Wayyo Allah na".
Inna wuro tace
"Malam itama ta buga hannun ta inaga tayi targaɗe a hannun".
"Nima dai haka nace kamar wan da suka faɗi a mota".
yamatso kusa da ni yana faɗin
"Naga hannun".
naɗago haka na mika masa yarike yana ɗan jujjuyawa,
rumtsa idanuna nayi da karfi ina faɗin
"Wayyo Allah wayyo Allah".
yace "Sannu kinyi targaɗe ne".
sai ya saki hannun
"Bari nakawo magani nasha maku".
Bappa yafaɗa yana shigewa cikin bukko,
ni dai yarfe hannun narika yi ina matsar ƙwalla.
yana shiga yafito da wasu robobin mai guda biyu, ya dawo in da nake.
Inna wuro tayi sauri ta ɗauko taburma ta shin fiɗa tace na zauna,
na zauna shiko a kan kujera ƴar tsuguno ya zauna kana yaruko hannuna yaja yaja yajijjiga shi da ɗan karfi, kara na sake cikin jin azaba har cikin kokon zuciya ta, ina shushshure kafafu kasa kamar zan saki fitsari a jikina.
kana yabuɗe ɗaya daga cikin roban mai daya fito da su ya lakato maganin ciki yashafa min a hannun da tuni yahaɗa zufa,kana ya saki hannun yana yimin sannu.
Inna wuro tace
"Sannu zakiji daɗi har kiyi bacci".
kai kawai na gyaɗa mata ina matsar ƙwalla, na matsa baya na jingina da jikin garu ina rike da hannun da ɗaya hannuna...
ya karɓi Naseem yashafa masa maganin dake cikin ɗaya robar a duk kanin ciwukan jikin sa,
yana yi yana ɗan mammatsa jikin sa har ya gangaro kasan kafar sa ai ko yana rike guiwar kafar sa yakara sautin kukan sa yana kankame jikin sa,
kafar yarike da kyau yaja sai ga kafar tayi kass,
Maganin da yashafa min a hannu yashafa masa a kafar yana faɗin
"Gocewar kashi ne".
kana ya mikawa Inna wuro shi ta karɓe shi tana girgiza shi da yi masa sannu,
nan ya karɓi Nasmah itama ya sha fa mata bayan yagama dudduba jikin ta ko itama da buguwa ko gocewar kashin a jikin ta,sai dai ita ba a samu gocewar kashin ba sai dai buguwar kawai...


Ina zaune nayi jugum zuwa lokacin kam alhamdllh zafi da zugin da hannuna yake min sai raguwa yake,
ido na zubawa su Naseem da ke jikin Inna wuro sunyi shiru sunata rarraba ido,
Bappa kuwa tun da yagama shafa mana maginin yamike yafiya sai yanzu yashigo rike da kwarya a hannunsa,
ya karaso in da muke ya mikawa Inna wuro kwaryar yana faɗin
"Basu susha dan su daɗa jin karfin jikin su".
Inna wuro ta amsa
tare da faɗin
"Dama yanzu nake shirin aiken Mero taje ta tatso musu madarar".
ta aje kwaryar ta mike da sauri ta shiga bokkar dake gefe da mu tafito da kwarya da ludayi guda biyu,
ta raba madarar biyu ta mika min rabi kana ta zauna tana ɗibawa da ludayi tana baiwa su Naseem,
ai ko suka karɓa suna ta sha,
A hankali na ɗibo nadarar cikin lodayi nakai bakina,
lumshe idanuna nayi jin ɗumi da garɗin madarar ya ratsa ni,ai ko na gyara zamata sai gashi na shanye madarar tass har ina tanɗe baki...
Bappa ya fito da shirin tafiya masallaci ya dube ni yana faɗin
"To ni zan tafi masallaci

Please Login or Register in order to submit comment