You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

Yola ɗan kuɗin da tazo dashi a hannunta ta aje cikin ɗaki akabi a ka sace ta nima tayi cigiya sama da kasa ta rasa, kuma su kaɗai ne agidan daga matar yayan ta sai ƴaƴan ta, amma tayi tan bayar duniyar nan sai matan yayan tace ta ɗaura musu sharri,
karshe tayi ta mata wulakanci na kin kari,
abincin da take bata ma sai ta daina bata, gashi kuɗin da zatayi kuɗin mota ta koma Narkuta babu tunanin HAMDAH duk yabi ya isheta.
ganan ta da taje dan ta saida shi ma taje ta samu wasu sunci gonar,
duk yan da tayi akan gonar akace sam ba nata bane karshe haka tabarsu da Allah.
wannan ɗakin da take zaune aciki ma tun lokacin da tace kuɗin ta ya ɓata matar yayan nata tace tafita mata a gida da kyar dai tasa mu tabarta tacigaba da zama acikin, wan da da ɗakin kiwon kaji ne zuwan tane ta share shi ta shinfiɗa taburman ta take kwana a ciki.

tana so tazo Narkuta taga halin da HAMDAH take ciki amma bata da kuɗin mota, naira goma wannan yafi karfin arzikin ta,
tayi yawon niman bashi gidajen da ta sani dan ta fara jarin awara a nan ɗin dan tasamu kuɗin motar da zata takoma sai dai bata samu ba,
tana zaune ta zuba tagumi yunwa duk ya addabe ta dan rabon ta da cin abin ci tun jiya da daddare yau kuwa ganin har 12 tayi bata samu abun da zata saka cikin bakin taba sai ta zarce da azumi.
yaron matar yayan ta yashigo da kwano a hannu babu ko murfi ya dangwara mata kwanon abincin a gaban ta, babu girmamawa sai zallar rashin tarbiyya, yajuya yafita.
tuwone tuwon datsa miyar bakar kuka da ko manja babu a cikin sa, tuwon ɗan haka agindin kwano tamkar ɗan yaye za'a baiwa abincin sabar kankantar sa.
kallon abincin tayi kawai ta girgiza kai,
batare da takuma kallon abincin ba ta mike ta ɗau mayafin ta tafita a gidan,
cikin unguwar tasu tashiga can ciki
gidan wasu masu kuɗi dake can cikin unguwar tasu tayi,
tayi sallama a gidan matan gidan suka amsa tashiga, bayan sun gaisa tace
"Dan Allah kan maganar ai kin nan nakuma dawowa ko Allah zaisa na samu, ko shara da wanke-wanke da girkin abinci ko wanki duk wan da na samu zanyi"..........!★





*Kuyi hakuri kwana biyu bana samun lokacin yin editing sai ku karanta da hakuri idan na samu lokaci zan yi editing cikin document*


Mommyn Twins ce



Mama mai awara tayi maganar cikin nuna jaddada rokon ta, har in zata samu ai kin tarika samun kwabon kashewa da kuma kuɗin motar da zata koma duba HAMDAH yau sati guda kenan take yayon zuwa gidajen masu kuɗin unguwar su,ko zata sami ai ki,
wannan gidan da tazo ma,sun mata alkawarin samin ai kinne tun sati ɗaya da ya wuce, shine yau ta kuma zuwa ko zata samu, ko wani irin aiki ne tana jin zata iya har in zata sami kuɗin mota.
Matan gidan suka ce mata Eh sun yi shawarwari zasu ɗauke ta ai ki,
amma aikin ba ai kin abinci bane. shara da wanke-wanke da kuma wankin kayan su da na kuma ƴaƴan su, dan suna da mai yi musu girkin,
tace ta Amin ce zata iya insha Allah,kuma yanzu zata fara in dai akwai wankin yanzu.
Nan aka fara fito mata da lodin kayan wanki ɗaki-ɗaki,
ɗakunan gidan kaf sai da suka fito da kayan wanki suka jibgeshi tsakar gida,
sannan sukace tafara da wanke-wanke da shara kafin tayi wanki, nan Mama mai awara ta tuɓe hijabin ta ta sha ɗan mara da shi,
cikin kankanin lokaci tayi wanke-wanke kana taɗa tsintsiya tasoma shara,
tana gamawa sannan ta dukufa wanki mai uban yawa.


Wankin take tun tanayi da karfin ta har karfinta yafara kare wa,
ga azumin da babu suhur yunwan tun jiya da rana, ta kwana da shi takuma wuni da shi.
haka dai tayi wankin cikin mawuyacin hali.
tana gamawa ta zauna zaman jiran bushewar sa, tana nan har wankin ya bushe, ta ninke tabi ɗaki-ɗaki tana kaiwa, kamar yan da taga an fito da kayan cikin ɗakunan gidan.
Wani ɗakin idan ta kai suka duba kayan su gaya mata maganar banza, suke kayan ma bai fita ba.
ɗakin ƴanmatan gidan kam da takai wata yarin ya budurwa da ta karɓi kayan tana dubawa watsa mata kayan tayi a jikin ta,
cikin gatsali da tsantsar rashin tarbiyya da sangarci irin na ƴaƴan wasu masu kuɗi tace
"Wannan kayan ne kin wanke? ke wata irin mata ce wata irin dakikiyar mata ce ke wannan an wanke wannan kawai tsomasa a ruwa kikayi kika ɓata min kaya kawai".
kai kawai Mama mai awara ta jinjina,
cikin takai cin jin yan da yarin ya karama wacce ta haife ta tajuya wai ita take zaginta,
kallon gefen ta tayi mahaiyar ƴar na zaune a gefen su amma tayi kamar bata nan.
"Allah shi kyauta".
Mama mai awara ta faɗa a fili tare da juyawa tabar gurin.
itako budurwar fuska ta yamutsa tare da jan dogon tsaki, tace
"Kayan a kasa zaki barmin kenan kiyi tafiyar ki?".
tayi maganar cikin rashin sanin darajar na gaba.
Mama mai awara batace komai ba ta juyo takwashi kayan ta mika mata, fizge kayan tayi a hannunta tajuya tawuce ciki...

Bayan tayi shara da wanke-wanken yamma daf magriba ta takoma gida,
kafin ta tafi kuwa sai da sukayi mata jawabin gobe da sassafe zatazo,
ko da ta koma gida da tasha ruwa tuwon da matar ƴaƴan ta ta ɗan sakura mata na tun da rana wan da ya wuni abuɗe ma shi tayi buɗa baki da shi.
washegari da sassafen tazo ta gidan masu kuɗin bayan tayi wanke-wanken da shara aka kuma jibge mata wanki har da na jiya da ta wanke aciki tayishi......
tun daga ranar kullum Mama mai awara na kan hanyar zuwa yin wannan aikin,
cikin kaskanci da wulakanci da rashin daraja ɗan adam, wannan gida basa da daraja babba duk da ta girme musu duka amma basa daraja ta ko dun girman ta, suna yi mata kallon kaskantacciya kullum cikin wulakancin su take a haka dai har tayi wata ɗaya a karkashin su,
ranar da tacika wata guda tana yi musu aiki suka ɗauki naira dubu biyu suka bata suka ce shine albashin ta,
Mama mai awara ta karɓa har hanunta na ɓari tanata zuba musu godiya.
tana komawa gida tahaɗa ƴan kayakin ta tafita sai tasha,
tashiga mota zuwa garin Jos tana isa direct Narkuta ta wuce,
ko da suka iso a bakin titi aka sauke ta kasan cewar ɗan kuɗin da ke hannunta duk yakare a kuɗin mota da kafa tashiga layin unguwar su direct ta ɗau hanyar gidan Malam Musa.
a sakar gida ta iske Zainabu zaune ta yi sallama tashigo, da sauri Zainabu ta mike tana faɗin
"Oyoyo Mama mai awara maraba lale barka da zuwa".
Mama mai awara ta yelwata murmushin fuskarta tace
"Yauwa Zainabu".
Zainabu ta kara buɗe taburman da take zaune a kai tare da faɗin
"Sannu da hanya ga gurin zama".
tazauna gefen taburman nan suka shiga gaisawa kana Zainabu ta mike ta ɗibo mata ruwa mai sanyi cikin randar kasa ta kaso mata.
tasha tana cigaba da mata sannu da hanya.
bayan ɗan gaishe-gaishe da tanbayar bayan rabuwa,
Mama mai awara takuma bin gidan da kallo akaro na ba adadi jin babu wani alamar motsin wani acikin gidan,
ganin yan da Mama mai awara take ta raba ido cikin gidan, Zainabu taɗan muskuta tadube ta tare da yin murmushi tace
"Um sai kawai kiga ɗiyar ki tabiyo ki, fir taki zama fa wai
ita bazata iya zama ba kawai zata biki, HAMDAH kenan ƴar Mama".
Ido Mama mai awara ta waro tare da faɗin
"Wa ɗin wai HAMDAH to ai ni ita nazo ɗauka".
Zainabu tace "A'a ita kuma kika zo ɗauka Mama mai a wara?, to ai HAMDAH kamma tun ran da kika bar nan da kwana biyar tabiki in ban mance ba".
wani irin zabura Mama tayi tare da buga kirji tace
"Tun tafiya ta da kwana biyar tabar gidan nan to ina taje?".
Zainabu tace "Mama kina nufin wai baku tare da ita?".
shiru tayi cike da tsananin damuwa a ranta take faɗin
"To ko ta koma gurin iyayin ta ne".
sai kuma tayi saurin kuma cewa
"Ina baza ta koma ba ko dun gudun ta sana diyyar ta Ummi ta tabar gidan Abba'n ta, ina bazata taɓa komawa gida ba".
cikin tsananin matukar tashin hankali Mama tace
"Ina Zainabu bataje in da nake ba!"
ido Zainabu ta waro tare da buga kirji tace "Bataje ba? nan fa ta shirya tace zata biki nace ta hakura ta barki kidawo tun da kince bazaki jima ba tace a'a zata biki kawai, to ina taje?".
Zainabu tayi maganar hankali tashe.
hankali tashe Mama mai awara ta mike tana faɗin
"Bataje ba Zainabu bataje ba".
tanufi kofa, Zainabu ma ta mike taɗau mayafin ta tabi bayan ta,
duk gidajen da Mama mai awara take tunanin ko HAMDAH zata iya zuwa gidan wato gidajen da suke mutunci da su anan cikin Narkuta.
amma duk in da taje sai suce ai su rabon su da ganin ta tun ranar sunan ta.
batun tashin hankali gun Mama ba'a magana,
tunani tafara tashiga mota taje Bauchi ta tuba ko ta koma can, sai dai bugu da kari batasan gidan su a cikin garin Bauchi ba,ita dai tace mata ita ƴar Bauchi ce amma bata faɗa mata ko awani unguwa take ba,to yanzu idan taje ta ina zata fara neman ta, Bauchi babban gari ne ba karamin gari ba, idan taje ta ina zata fara neman ta....


Ranar Mama mai awara kuka da hawayen ta tayi da shar-shar, tunanin ta bai wuce ina tatafi wani hali take ita da ƴaƴan ta.
kwanan Mama uku ta fara shirin komawa dan tana ganin zaman ta anan nauyi take ɗaura musu, duk yan da taso samun kuɗin mota tatafi batare da sunsan bata da shi ba abun yacu tura, karshe dai malam Musa shi ya bata kuɗin motar komawa.
a haka ta koma taje ta cigaba da rayuwar kunci da bakin ciki acikin gidan su wacce matar yayan ta ta mallake ita da ƴaƴan ta, kullum tana cikin tunanin HAMDAH da ƴaƴan ta da halin da suke ciki,
duk san da tatuna hakan sai ta zubda ƙwalla, sai dai batayi kasa a guiwa wajen yi mata addu'a ba, duk san da zatayi sallah sai ta sanyata cikin addu'o'in ta.....★
wannan kenan



Acan kasar saudi kuwa bayan sati uku da canza Diamond ɗin har yanzu muna cikin masarautar Saudi mun zamo tamkar ƴan gida,
Bappa yace bazamu koma ba sai munyi aikin hajji da yake dumfaro wa yanzu.
wata ranar juma'a bayan mun dawo daga masallaci shugaban kasar mu na Nigeria yakirawo wayar Mahmoud yahaɗa su da Bappa,bayan gaisawar da ya guda na sakanin su shugaban kasar ke magana kan cewa tun ranar da aka tura kuɗin Diamond baikuma jin wani magana ba,
shin akwai wanda za'a basa ATM ɗin bankunan da aka zuba kuɗaɗen ciki nan kasa Nigeria kafin su sudawo?.
Bappa yace
A'a yarike ATM ɗin a gurin sa dan bayida wan da zai iya cewa abashi sai dai bari yayi wa ita yarin yar magana,
yaji ta bakin ta ko da abun da zatace kan lamarin bari a nemeta aji ta bakin ta.

I na zaune cikin ɗaki ina sakawa su Naseem kaya da yanzu nayi musu wanka, cikin kayan da ɗazu Bappa yabani kuɗi nasiya musu da muke dawowa daga masallaci.
nan yake yimin bayanin yan da sukayi da shugaban kasar mu kana ya ɗaura da faɗin
"Ko akwai wan da kike ganin za'a bashi kafin mu koman?".
nace "A'a Bappa yan da kace ɗin hakan yayi".
yace "To madallh shike nan".
ya mike yafita....
da daddare duk muna hallare a katafaren parlour'n da yake masaukin mu, muna cin abin cin dare Mahmoud ya dube ni sannan ya nisa yace
"Bappa ya faɗa miki yan da sukayi da shugaban kasa ko?".
nace "Eh yafa ɗa min".
kai ya jinjina tare da faɗin "Ok to yanzu kina so a bar kuɗin cikin account banki surika juyawa ne ko da wani abun da zakiyi da shi?".
Bappa yace "Tan bayar da shugaban kasa yayi min ɗazu kenan da nace masa yabar ATM ɗin agurun su,
ni ma dai nayi tunanin ko za'a siyi wasu ƴan kaddarori ne in yaso sai abar sauran banki yarika juyawa".
baki na washe tare da faɗin
"Eh wlh Bapp a siyi wani abu da kuɗin".
Mahmoud yace "To me kike so a siyan".
hannayena biyu na dafe kumatu na, nayi sama da kwayar idanuna ina ɗan jujjuya su, naɗan yi
shuru alamun nazari, sai nakuma washe baki nace
"Bappa kasan me nake tunani kuwa".
kai ya girgiza tare da yin murmushi ganin yan da nayi maganar, Mahmoud ma sai da ya murmusa. cikin muryar dariya
nace
"Bappa kuɗin zai kai yasiya mota da gida?".
nayi maganar ina rufe fuskata da cigaba da dariyar,
Mahmoud yace "Me zai hana shi kai wan har abun da yafi gida da mota ma zai siya, gidaje da motoci ma ba gida da mota kaɗai ba har abun da yafisu ma kuɗin zai siya da shi har yarage".
da sauri nace "Yauwa to kawai a siya motoci irin manyan motocin nan wan da suke loda kaya aciki ana kaiwa garurruwa masu nisa ɗinnan,
da gidan mai".
yace "Gidajen mai dai". nace "To shi da kuma asibiti da masallaci, umm da kuma irin abubuwan sadakatuj'jariyan nan".
Bappa yace
"Rijiya bishiya masallaci bohul makaranta asibiti,da dai sauran su duk sadakatuj'jariya ne".
kai na gyaɗa da sauri nace "Yau wa Eh Bappa".
nakarashe maganar cikin muryar dariya,
yace "Gaskiya kinyi tunani mai kyau abun da yakama ta ayi kenan".
dariya kawai nayi dan ni ban ɗauki maganar da wata girma ba dan ni atunani na mun dai yi sa cikin rahane amma kuɗin bazai iya yin abun da na lissafan nan ba.
Mahmoud kuwa kai ya girgiza ganin yanayin yaranta cike taf cikin maganar tawa......

A daren Bappa ya sanar wa shugaban kasar mu abun da nace ina so ayi da kuɗin,
shugaban mu ya jinjina lamarin matuka yace nayi tunani dan hakan ma ci gaban kasa Nigeria ne kwari da gaske.
za'ayi abun da nace in yaso sauran kuɗin kuma banki sai ta rika juyashi.
bayan sun gama maganar Mahmoud yace to shifa gobe idan Allah ya kai mu zai koma bakin ai kinsa.
Bappa yace "To Allah yakai mu mukam muna nan sai munyi ai kin hajji tukun, idan kaje karika zuwa duba mahaifiyar ka akai-akai gobe ma zaka kuma kirowo min Isa ya hadamu mukuma yin magana da ita".
yace "To ba da muwa Allah yakai mu"....
washegari da misalin karfe 11 Mahmoud yabi jirgi zuwa Dubai in da daga can zai shiga wani jirgin zuwa Nigeria...



★★★★
*After 1 year*
★★★★


🙌🏻🙌🏻🙌🏻🙌🏻🙌🏻🙌🏻😹 *da yar dar Allah anan book 2 yakawo karshe sai mun haɗu a littafi nagaba wato littafi na uku wan da shine zai zamo littafi na karshe da yar dar Allah*



*Zazzaɓin gida-gida yafara kyarkyara ta*




Mommyn twins ce






🌺 *HAMDAH* 🌺
*WASA FARIN GIRKI!!*✍🏻


*NA*
*RASHEEDA S DIRECTOR*


_(Book 3)_


_(Bismillahirrahmanurrahim.) Alhamdulillah ina yiwa Ubangiji buwayi gagara misali godiya da ya kuma bani iko a karo na uku nakuma dawowa domin kawo muku cigaban labarin HAMDAH ina rokon Allah ya bani ikon kammala shi lafiya👏🏻_

(Afwan a karshen book 2 nasaka (After 1 year)
I'm so sorry typing ero ne👌🏻)




Littafin na siyar wa ne ki biya ki karan ta.
domin biyan kuɗin littafin sai ka-ki tuntuɓi wannan number 08034690723




🅿️1





Bayan wani lokaci.
Tuni ai kin hajji ya karato gamasu niyya tuni aka fara shirye-shiryen tafiya ai kin hajji. kan kace me kasar Saudiyya tacika tayi makil da al'ummar Musulmi.
yanzu bama samun wani zama kullum muna hanyar zuwa bautar Ubangiji, ba dare ba rana kullum Bappa na tasani gaba wani sa'in tare muke tafiya da su Naseem da Nasmah,wani sa'in kuma na barsu wa Mammaa mahaifiyar Ukhtee kawata da nayi anan cikin masarautar Saudi jika ga Masarautar Saudi. dan tare muke tafiya da Ukhtee ita kuma Mammaa ciwon kafa ke damun ta bana bazata samu daman fita afara aikin hajji da itaba.
acewar ta sai an zurfafa ibada sosai kan lokacin Abdul Malik yayan Ukhtee da yake karatu can jami'ar Madina yashigo zai fita da ita guraren ibada a kan keken zama irin na masu ciwon kafa. kasan cewar na yaye su Nasmah kuma suna cin komai gashi sun saba da matar sosai, shi yasa wahalar su ta ɗanyi min sauki ko zamu fita ban cika tafiya da suba....
cikin yarda da buwayar Ubangiji aka kamla ai kin hajji na wannan shekaran lafiya.★
tuni mahajjata suka fara komawa kasashen su,nan muma muka fara shiri damin ko mawa kasar mu.
ana gobe jirgin mu zata ɗaga. tun safiyar ranar jama'ar dake cikin masarautar sukayi ta zuwa sallamar mu. duk wan da yazo sai ya nuna baison tafiyar mu wasu ga fuskokin su wasu kuwa sai sun kai ga furtawa. Ukhtee da Mammaa da tun safiyar ranar muke tare da su a side ɗin mu,
suka tirje wai sam sai dai Bappa ya barni a nan, ai ko nan kowa yace ya barni shi ya tafi bayan wani lokaci sai na koma.
ni dai dariya kawai nake binsu da shi, sai dai zuwa yanzu jikina yayi sanyi ganin yan da Ukhtee take kuka.
bilhakki ta rungume Nasmah tana faɗin bazan tafi ba.
Bappa ko ido yake binsu da shi cike da mamakin ganin zunzurutun kauna gun waɗan nan larabawan.
ana cikin haka kiran Mahmoud ya shigo wayar Bapp.
nan yake sanar wa Bappa yasami masaniya daga shugaban kasar mu anfara duk ayyukan dana lissafa kuma bazai ɗau wani lokaci ba insha Allah za'a gama,
Bappa yayi fatan alheri kana yakashe wayar.
koda naji labarin daga bakin Bappa nayi matukar mamaki dan ni har yau ganin abun nake kamar wasa bazai yiwu ba.
Bappa ya mai da hankalin sa kan mutanen da suke cikin parlour'n, abun da ya lura shine suna matukar son ba'i musamman wata kabilar, bugu da kari wan da Allah ya ɗaukaka a cikin su, babu garin da zai waye wasu daga wasu unguwanni daban-daban wasu kuma daga ɗan garuruwan dake gefen gari basu shigo ganina ba, na zamo abun kallo da hira a gurin su, haka zasuyi ta hotuna da ni da su Naseem.
numfashi Bappa ya sauke ganin gabaki ɗayan su kalma guda suke nanatawa..
dun dole Bappa ya amsa musu badun yaso ba da sharaɗin zasu sako ni a jirgi nan da ɗan kwanaki kaɗan.
ai kuwa ihun murna Ukhtee ta sake ta rungume ni tana sunbata. gaba ki ɗaya parlour'n yakaceme da murna...
washegari da misalin karfe 4 na asuba jirgin su Bappa ya ɗaga suwa kasar mu ta gado wato Nigeria★.
kafin ya tafi sai da yayi ta min nasihohi da jan hankali mai ratsa jiki..
tun da Bappa ya koma kusan kullum sai munyi waya ta wayar Ukhtee har da su Inna wuro.
Alhmdllh bazan ce komai ba game da zamata anan cikin masarautar Saudi batun samin kula da tarairaya ni da ƴaƴana kuwa ba'a magana...




A can kasar Nigeria cikin garin Bauchi state.

Na'ima ce da kawar ta Raliya,tafe cikin mota suka ɗau hanyar wani asibiti dake nan cikin G.R.A wan da shine Na'imar ke zuwa awo.
Raliya ke jan motar Na'ima na zaune a gefen mai zaman banza.
Raliya ta ɗan muskuta ta dubi kawar tata kana ta mai da idanun ta kan titi tare da faɗin
"Aminiya yanzu yanda kika tsaran nan kina ganin hakan zai yuwu kuwa baza'a sami wata matsala ba dai ko?".
Na'ima tasauke numfashi tare da gyara zaman ta cikin karfafawa da gaskata muradin ta tace "Kada ki damu aminiya Nice fa Na'ima baza'a sami wata matsala ba tabbas zai yiwu zai yiwu, yau ɗin nan kuwa zan haihu, Raliya ina cikin haɗari dole ne kawai na ai watar da hakan, kinsan kuwa jiya da daddare muna kwance da SALEEM yaɗaga rigata yana duban cikin yace shi har yanzu baya ganin garman cikin ciki wata 7 amma har yanzu bai taso ba,
kin san me yafi firgitani kuwa?".
tayi tambayar tana duban Raliya.
Raliya ta girgiza kai cikin takai ci taci gaba da faɗin
"Aminiya sunan wancan ɓatacciyar yarin yar, ya kira min har da min misali da ita, wai lokacin da take da ciki bai cika wata huɗu bama amma yaɗan taso".
ido Raliya ta waro tace
"What! ya akayi har ya iya tunota? to gaskiya kawata kada kiyi wasa".
Na'ima cikin damuwa da bakin cikin tuno da HAMDAH da SALEEM yayi tace
"Shiyasa nake son bin duk wata kofar da zaibi ya tuno da wancan banzar ɓatacciyar da ko a muce ko a raye oho, duk wata kofar zanbi na toshe duk da nasan bayida wani kataɓus, ko da ya tuno tan ma, amma ni kwata-kwata bana son na rikajin kwatankwacin irin sunan ta a bakin sa,
bakiji abun da boka yace min ba, yana son yara sosai hakan zai iya yin tasiri wajen rika tuno ta da ita da abun da ke cikin ta duk da hakan ba wani abun damuwa bane amma ni dai sam bana son jin kalmar sunan ta kan laɓɓan sa,
to ko yau da safen nan ma muna kwance dashi yaɗaga rigata yana shafa cikin yace wai anya abun da ke cikin nan yana da lafiya kuwa shi baya ganin yana girma,
nace masa ai jikina yabi Allah ya taimaka ma ina da tumbi,ke nifa kullum a narka abinci nake aciki na in kika ga abincin da nake ci yanzu wai dun kawai tumbi na ya kara girma,
yanzu Raliya cikin nan wata 7 ne yana daf da shiga wata 8 yazama dole na ɗau mataki in ba hakaba komai zai iya ɓaci,
kin ga wancan hatsabibiyar kanwar tasa Rafee'at ranar da muka haɗu a gidan su har habai ci take min wai mai cikin tuwo, ni har na fara zargin ko ta gane ne".
Raliya ta saki dariya har tana dukan sitiyarin motar tana faɗin
"Ai wannan Rafee'at ɗin shegiyar gaske ce sai ana taka mata burki".

dai-dai nan suka isa get ɗin asibitin, hon Raliya tayi mai tsoron bakin get ɗin yawan gale musu get.

a gefe in da aka tanada dan ajiye motoci suka faka suka fito suka nufi cikin sibitin.
kofar wani office direct suka nufa tare da yin knocking,
daga cikin office ɗin aka basu izinin shigo wa.
wanda ke cikin office ɗin yana zaune cikin shigar likitoci yana ganin su ya washe baki tare da faɗin.
"A'a manyan kasa kune tafe?".
cikin fari da ido Raliya taja kujerar da ke fuskantar sa ta zauna tana faɗin.
"Kanana dai ai kune manyan kuna zaune AC na ratsa ku kuɗi na shiga yadda yakamata me yamuku saura?".
Na'ima ma kujerar taja tazauna kana suka shiga gaisawa,
suna ɗan taɓa hira da dariya sakanin su da kagan su kasan tabbas sunyiwa juna farin sani.
Dr Mukhtar Lawan abokin su Na'ima ne sosai abota ne na tun a makaranta duk kanin su gar tasan garne, duk wani iskanci da sheke ayar da sukayi lokacin suna makaran ta tare sukeyi, har kuma yanzu wani kullin tare suke tufke shi. acikin su shine kaɗai yaɗan maida hankali kan karatu har yake cin moriyar karatun da yanzu yake a matakin Dr, asibitin mallakin sa ne wan da mahaifinsa yagina masa bayan zamowar sa Dr.
duk hirar da suke Dr Mukhtar idanunsa a kan Raliya,yakafe kirjin ta da ido wan da ɗinkin rigar jikin ta ya bayyanar da nonuwan ta kusan rabi a waje.
fiki-fiki yayi da ido cikin yanayin shiga tarkon Raliya yadubi Na'ima kana yace
"Na'ima kawarki Raliya takini fa taki na ganta kwata-kwata yanzu ko waya na kirata muɗan haɗu taki ta bani da ma mu haɗu, sabo da tasami manya wan da suka fimu bata hurɗa da mu".
yakarashe maganar da mai da idanunsa kan Raliya wacce tadaɗa bankaro kirji tana wani fari da ido.
dariya Na'ima tayi tace
"Kai haba aminiya ai ko ba komai dai zakizo wannan haɗaɗɗen office ɗin kiɗan rika ɗebe maba kewa."
fuska Raliya ta yamutsa cikin salon kwarewa a harkar bariki takuma bankaro kirji yayin da yatsarta guda ke saman wuyan ta tana ɗan yawo da shi har zuwa kirjin ta, ta saman nonuwan ta,ido ta kanne a kansa kana tace.
"Dr kenan ku abun naku ai sai a hankali in ka shirya yanzu Na'ima ta wuce ta bamu guri amma yanzu zaka ajiye min rabin miliyan anan shima ɗin dai-dai azo sallama ne".
tanuna saman table ɗin gaban sa.
ido ya waro da karfi ya furta
"500k ai ko ai kina na wata guda bai kai rabin miliyon ba".
dariya duka suka saka.
Dr Mukhtar yace
"Ina kinji ko Na'ima kawar ki tafi karfi na sai dai mugani kawai mu latse baki, ko za'a ɗan taimaka min naɗan lallasa ne basai ciki ba iya waje kawai". yakarasher maganar da dariya haɗe

Please Login or Register in order to submit comment