You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

sa na jiyo yana faɗin
"Kada ki ɓata lokaci dai kinji ko, kisaka kaya kawai kada ki rasa jirgi ki hanzarta."
nace "To Bappa."
na sauke wayar na mika mata da sauri na koma gaban mirror, a gaggauce nakarasa shafa mai sai pauda da man baki.
na mike da sauri na isa bakin gado in da dama nan nacire kayan da zansaka na aje na ɗauka na sa, dan sai da na shirya su Naseem da Nasmah kafin na shiga wanka, shiyasa shirin yayi min sauki.
tun da Bappa yakira waya nalura da yanayin Ukhtee gaba ki ɗaya yanayin ta ya sauya tayi wani ziruu da ita,
kai na kawar dan bana son muhaɗa ido da ita, dan yanayin nata zai iya sa jikina ya mutu.
cikin hanzari na kammala saka kayana,
ina cikin sa kayan ban kai ga gamawa ba Bappa yakuma kira.
Nan ma kuma faɗin nayi sauri yace, cikin hanzari na kammala saka kayan.

Na dubi Naseem da Nasmah ina faɗin
"Kutashi muje ko." ido
Naseem ya kura min yayin da hannayen sa biyu ke dafe da kuma tun sa kana ya ce "Mommy mataiyaci amuje?".
Nasmah ma tace "Tayan kaya amuje ko Mommy?." kai na girgiza musu nace
"Ba siyan kaya ko masallaci zamu je ba, kasar mu zamu koma can kasar mu in da aka haife mu."
ido yaran suka ware suna kallona kana Naseem yakuma cewa "Mommy kasar mu in da aka haife mu?."
yy maganar yana zura yatsarsa cikin baki alamun mamaki irin na yara.
kai na gyaɗa masa tare da ruko hannunsu ina faɗin "Kutashi muje." dan nasan idan nabi na surutun su sai mu makara anan har Bappa yakuma kira.
Ukhtee kuwa tuni idanunta suka kawo
ruwa kan kace me hawaye yafara sauka,
hannunta na rike cikin rauni tare da girgiza mata kai dan nima idanuna sun fara tara kwalla.
cikin harhaɗa larabci nace
"Dan Allah Ukhtee kar kisa jikina yayi san yi, baga waya ba zamurika magana ai tafiya ba mutuwa bace ai dai bamu rabu ba tun da akwai waya zamu rika gaisawa, bakin ce zaki zo kasar mu ba?."
kai ta gyaɗa min alamar Eh nace
"To dan Allah kada ki karya min guiwa da tafiyar kizo muje kin ga Bappa sai kira yake."
jiki a sanyaye ta mike.
koda muka fito parlour sai gani nayi babu akwatin kayan mu in da nafito da shi na ajiye ɗazu bayan nagama shirya mana kayan mu.
nan Ukhtee take sanar min direba ne yashigo ya ɗauka.
koda muka fita farfajiyar masarautar, a tsaye jikin mota muka tadda direba da alamu mu yake jira.
da sauri na juya na nufi side ɗin su Ukhtee dan yiwa Mammaa sallama,
narika bin part-part na masarautar ina yi musu sallama duk in da na shiga sai na fito da ƙwalla dan suma da kwallar suke rako ni,haka narika bin side mafi kusa da mu ina yi musu sallama dan idan nace zanbi na nesa da mu sai na kusan sai na ɓata lokaci mai tsawo ban gama ba.
daga karshe nashiga can cikin masarautar in da lokacin da mukazo aka canza diamonds ɗin nan aciki.
direct cikin katafaren parlour wan da aka kawata shi da adon zinari mai matukar ɗaukar ido muka shiga, adalin shugaba na zaune a mazaunin sa na alfarma, yayin da Alkur'ani ke gaban sa yana bita cikin nutsuwa. a gaban sa muka rusuna, cikin ladabi nayi masa barka da war haka,kafin nakuma cewa wani abu ya ɗaura hannunsa a kai na yana yimin fatan isa kasata lafiya, nayi mamakin yan da yasan abun da ya kawo ni dan ni a zato na bai san da tafiya ta ba. naji daɗin addu'o'in da yayi min kwarai da gaske, na mike cikin jin daɗi yayin da jikar sa wato Ukhtee ta rufamin baya, bayan itama ta gaishe shi, gaba ɗaya cikin parlour'n suka shiga yimin fatar isa gida lafiya ina amsawa da amin har muka fita.
a jikin mota na tadda su Mammaa cikin matukar bege kowa sai hawaye yake har sai da suka sa hawaye na ya karu.
direba na ganin mu yayi saurin buɗe motar yariko hannun su Naseem yasa su cikin motar, rungume juna mukayi da Ukhtee muka saki kuka a tare, gaba ki ɗaya gurin hawaye suke babu mai iya rarrashin wani,
zame jikina nayi cikin sauri nashige cikin mota, direba yatada motar.
motocin da suke jere a gaban mu guda uku sai wasu biyu a bayan mu,
motar farko mai tambarin masarautar haɗe da jiniya, shi ya fara fita, kafin biyu suka bi bayan sa sai kuma motar da muke ciki.
motoci biyu da suke bayan mu suma suka biyo mu, kamar dai ranar da muka shigo masarautar sai gashi yauma a haka muka fita.
muna isa airport batare da ɓata lokaci ba muka shige cikin jirgi, nan motocin suka juya.
bada jimawa ba jirgin ta ɗaga...

Bayan wasu ƴan awanni jirgin mu yasamu sauka cikin yar dar Allah da buwayar sa, cikin babban birnin tarayya Abuja da ke cikin kasata ★NIGERIA★.
bayan saukar jirgen da kamar minti 15 fasinjojin ciki suka fara sauka.
da sauri ganin Naseem da Nasmah sun mike kan kace me sun rufa da gudu sunyi bakin kofar fita in da mutane keta sauka,
cikin hanzari na rufa musu baya da sauri ina faɗin
"Kai kutsaya fa kar kuje ku faɗi."
ai ko da gudu suka fara sauka daga matattakalar jirgin suna dariya.
bayan su nabi ina dariya ganin inda suke sauka cap-cap-cap daga matattakalar kamar zasu kefe kasa ina cigaba da faɗin.
"Zaku faɗi fa kutsaya."
kan kace me sun sauka kasa, sauri na kara ina sauke kafata kan shinfiɗaɗɗiyar kasan kasata abun alfahari na ƙasata Nigeria, naja wani irin numfashi tare da shakar daddaɗan iskar dake kaɗawa acikin ƙasata.
ganin suna kokarin cigaba da gudun nayi hanzari na ruko su tare da faɗin
"Idan yaro ya faɗi yayi min kuka zan kara masa."
baki suka washe cikin kyakyata dariya Naseem yace
"Mommy baya mu faɗi ba." goshin sa na dungure nace "Zaku faɗi mana in zaku faɗin zaku sani ne wan nan gudun da kuke ai sai dai kuji ku a kasa kuzo nan ku tsaya."
na janyo su gefe guda.

Daga can gefe guda
da sauri aka buɗe wata motar da suke jere ɗan nesa da mu, wasu mutane biyu suka fito da sauri suka karaso in da muke, sannu da hanya sukayi min, na amsa ina kokarin janyo su Nasmah mu matsa gefe, daya daga cikin su ya mika min waya, kallon wayar da yake mika min ɗin nayi kana na mai da duba na kansa,
kai ya ɗaya tare da faɗin
"Ana maga na." ya fada yana kallon kan screen ɗin wayar, a hankali na sake Nasmah dake rike a hannun dama ta na amshi wayar, shikuma yayi saurin ruko hannun ta yaɗan matsa gefe kaɗan in da ɗayan mutu min ke tsaya ya harɗe hannu da bakin gilashi a aidon sa,
a sannu nakai wayar kunne na tare da yin sallama, daga cikin wayar akace
"Barka da isowa kasa Nigeria ki bisu su isa da ke masauki."
ɗan shiru nayi kamar naso nagane muryar mai maganar, sai kuma na sauke wayar batare da nace komai ba na mika masa wayar.
a hankali na soma tafiya suna biye da ni har gurin mota, da sauri ɗayan ya buɗe min murfin motar muka shiga in da tuni suka saka jakar mu cikin motar.
jere motocin suka fita kamar yan da aka kawo mu airport a can kasar Saudiyya.
muna fita daga cikin airport ɗin muka ɗau hanya, shiru nayi cikin motar ina raba ido cikin ƙasata yayin da zuciya ta ke kunshe da ɗin bin farin cikin gani na cikin ƙasata, ina jin wani farin ciki tabbas ƙasata abun alfahari na ne.
munyi tafiya mai nisa kafin muka isa wani katafaren hotel, hotel ne irin wan da manyan kusoshin kasa suke sauka a cikin ta...

Awani haɗeɗɗen ɗaki aka sauke mu sai da suka rako mu har bakin kofar room ɗin kafin suka juya, wan da ke rike da jakar mu kuma yashi ga ya ajiye, kana ya miko min waya yace "Ana magana." na amshi wayar a raina nake faɗin
"To yanzu kuma ina zai kuma cewa na bisu."
a sannu nakara wayar a kunne na sai jin muryar Bappa nayi yana faɗin
"HAMDAH sannun ku da hanya ya gajiyar hanya."
washe baki nayi dajin muryar Bappa da sauri nace
"Laaa Bappa mun iso lafiya kalau Bappa kana ina?."
nafaɗa ina washe baki cike da murna jin muryar Bappa da nayi yace
"Kuhuta ku kwanta ku huta sosai ina nan zuwa."
nace "To Bappa." na mika masa wayar ina cigaba da washe baki, mutumin ya fita tare da jamin kofa, numfashi na sauke tare da bin ɗakin da kallo, na isa bakin gado na zube bakin gado, in da tuni Naseem da Nasmah suka haye gadon sai salle suke.
kokarin tuɓe kayan jikina nake dan so nake naɗan watsa ruwa, naji ana knocking mayafi na naɗauka na mayar jikina, na mike na nufi kofar na buɗe ma'aikacin hotel ɗin nagani tsaye rike da babban tray, baya naja na bashi hanya yashigo ya dire try ɗin kan table kana yafita na mai da kofar narufe na murza key.
na dawo bakin gadon na tuɓe kayana nashige bayi,
wanka nayi sosai nafito na tuɓe su Naseem suma nayi musu wan kan.
bayan na shirya su nima na sauya kaya, kana na zuba mana abinci mukaci.
muna gama ci muka koma gado...

bayan haka da kamar awa 2 akayi knocking na mike naje na buɗe, ɗaya daga cikin mutanen da mukazo tare nagani tsaye yace
"Madam kun kammala zamu iya tafiya?".
kai na gyaɗa masa, juyawa nayi dan kiran su Naseem sai ganin su nayi a bayana suna kokarin fita daga ɗakin,
mutumin ya ruko hannunsu nikuma na koma na ɗau mayafi na nabi bayan sa muka fita..
tun daga bakin get ɗin da muka iso na fahimci banki muka zo dan gashi a rubuce (First bank) buɗe baki nayi a raina nake faɗin "To me mukazo yi a banki." bakin na rufe jin yana faɗin
"Bismillah fito muje ko." sai lokacin na lura ashe ma har sun fita har ya buɗe marfin ɓarin da nake ban sani ba, a hankali na zuro kafafuna waje na fito.
direct cikin bankin muka shige batare datsaida mu ko bincike ba, akasin jama'ar da nagani tsaye bakin bankin an tsaida su an hana su shiga.
tun da nashiga cikin bankin aka bani gurin zama ban motsa ba, duk wani cike-cike da kai kawo wasu suke tayi su da wan da mukazo da su, sai dai abun da yakamata ni nayi da kaina shine nake tashi naje nayi, awa 1 da zuwan mu aka kammala komai aka bani ATM,
muna fita daga bankin zato na masauki za'a maida mu sai ganin mu nayi a get ɗin wani banki, shima kusan mintunan da mukayi a bankin da muka baro mukayi a nan ɗin kafin muka kammala, nan ma da ATM ɗin bankin muka fita. ina mai jin mamakin kuma zuwan mu wannan bankin.
mamaki na bai karu ba sai da nakuma sin tar kaina cikin wata banki, wunin ranar muka kare ta a bin bankuna dan sai da muka je banki biyar kuma duk wan da mukaje da ATM ɗin sa muke fita..
sai yamma liss muka dawo masaukin mu, a gajiye na zube bakin gado in da ɗaya daga cikin mutanen da muka tafi da su yashigo da su Nasmah, wata laidar dake rike a hannunsa ya mika min yana faɗin
"Gashi ance na baki."
bin laidar nayi da kallo kana namika hannu na amsa shiku yafita,
zamata na gyara tare da zuba ATM ɗin da suke hannuna kan table ɗin gabana.
a sannu nashiga buɗe laidar dan ganin abun da ke ciki,
kwalayen wayoyi ne har guda biyu nagani ciki a sannu na ciro su ina jujjuyasu, rabon da narike waya haka a hannuna a matsayin nawa har na mance, sai kuma cikin hanzari nashiga buɗesu dan tun ban ciro su ba wayoyin suka tafi da ni, da sauri na ciro cazar wayoyin duka namike cikin hanzari naje na saka su a cj, ina saka wa kuwa suka nuna min acike suke, da sauri na dawo in da na tashi na kunna wayoyin, ai ko ina kunna wa sai ji kake ɗuɗut-ɗuɗut alamun shigowar message alert akai-akai.
ido na kurawa musu ganin alat ne na kuɗi suke ta shigowa, na bankunan da muka buɗe ɗazu, ido na zubawa sarautar Allah ganin kuɗaɗen da suke ta shigowa ni bama zan iya kiyaste adadin su ba.
sai da naji wayoyin sunbar kara kafin nashiga latsa su, contacts nashiga da sauri sai gani nayi babu number ko ɗaya, jiki a sanyaye nake kallon wayar, abu na farko da ya fara zuwar min shine lokacin da Abbu ya siya min waya yasaka min number family na aciki,haka narika bin lambobin ƴan'uwa na ina kiran su.
hawayen da yagangaro kan fuskata na share ina mai jin kewar ahalina, a sannu na mike na isa in da jakata yake na buɗe naciro number Ukhtee da ke rubuce a takarda, na saka cikin wayat kana na dannan mata kira,
tana ɗaga wa dajin nice mai kiran atare muka saki ihun murna.
hira mukayi tayi da ita har magriba kafin na mukayi sallama...

Kasan cewar ina fashin sallah gado na haye nayi kwanciya ta cike da kewar ahalina daya baibaye ni lokaci guda...
washe gari da rana Bappa ya iso Abuja, nayi murna matuka da ganin sa har nake jin wani ɓari na kewar ahalina dana kwana dashi ya yaye da ganin sa.
isowar sa ba da jimawa ba muka bar cikin hotel ɗin har da kayan mu.
wani katafaren gida mai matukar kyau da tsaruwa gida ne babba wan da girmansa yakai ya kawo tsarin sa gwanin burgewa, a bakin ramɓasheshen get ɗin gidan motar gaban mu ya tsaya, wan da mutanen da suka ɗauko mu a airport da wan da muka haɗu dasu a banki jiya dakuma wasu karin mutun biyu da yau nafara ganin su, sune acikin motar, motar da muke ciki ke biye da su, sukayi hon, abakin get ɗin ramɓasheshiyar gidan........★








Mommyn Twins ce
























HMD
WASA FARIN GIRKI!!!✍🏻

_(Book 3)_





🅿️4









Asannu a ka wangale tamfatsetsen get ɗin gidan, motar gaban mu yakusa ciki, a hankali direban dake jan mu ya danna hancin motar cikin gidan, a tsakiyar farfajiyar gidan duk suka faka motocin, a sannu na zuro kafafuna waje, "Ya ilahi ya littahi".
abun da na furta kenan lokacin da na dai-dai ta tsayuwa ta a cikin gidan, bin gidan nashiga yi da ido har ina wai ga gefe da gefe na.
gaba ɗaya gidan da tsaruwar sa yatafi da ni, tsaruwan gidan yawuci misali komai an tsarashi a inda ya kamata yana ajiye a in da ya dace,gida ne babba mai ɗauke da part har huɗu, daga gefe can gabar da gidan side ne guda ɗaya sai kuma gefe ta hannun dama shima side ne guda sai kuma gefen hagu shima side ɗaya, sai dai ƴan madaidaita ne ba wasu manya ba.
daga tsakiyar gidan kuwa wani side ne na musamman wan da yazamo sauran side ɗin sun sashi a tsakiya shi kam gini ne mai hawa ɗaya babbane ya tsaru iya tsaruwa, daga saman side ɗin har kasan sa yaji ado da gilasai masu ban mamaki an kawata shi tamkar a turai,daga kasa kuma an zagaye shi da wasu flaw's masu matukar kyau da ɗaukar ido,
gaban side ɗin wani shinfiɗaɗɗiyar swimming pool ne wan da aka kawatashi da rubber grass malaye har bakin kofar shiga side ɗin.
gefe can kuma parking space ne ɗauke da lafiyayyun motoci da suka kai guda uhu a cikin sa,
daga farin shiga gidan kuma gefe da ɗakin mai gadi masallaci ne shin fiɗaɗe agun,
sai kuma ɗakuna guda ɗai-ɗai a jere guda uku a gefe da masallacin ta can.

Maganar Bappa naji yana faɗin
"Muje ciki ko HAMDAH." da sauri nadawo daga duniyar kallon gidan dana tafi, da murmushi kan fuskarsa dan ganin yan da na tafi gaba ɗaya na shagalta da kallon gidan.
na ce "To Bappa". a hankali nabi bayan su side ɗin da ke gefe ta hannun dama muka nufa a hankali nake taka kafata ina cigaba da baza ido cikin gidan har muka isa cikin side ɗin.
masha Allah ɗan madaidaicin side ɗin ya tsaru matuka.
side ne mai ɗauke da 3 bedroom ko wanne da banɗaki a cikin sa, ɗan madaidaicin parlour haɗe da dinning
da kitchen da komai da komai, an tsara komai yan da yakamata duk wani abun bukata an tanadar babu abun da babu.
ɗakunan cikin parlour'n muka rika shiga wan da komai akwai hatta gadon ɗakunan duk da shinfiɗar su, sunsha lafiyayyun bedsheets.
bayan mungama zagaye cikin side ɗin gaba ɗaya, muka fita ɗayan side ɗin dake gefen hagu muka shiga, shima kamar wancan side ɗin yaji komai. kowa sai faɗin masha Allah yake, nidai kasa magana nayi sai binsu nake inata baiwa idona abinci sabo da gaba ɗaya yanayin tsarin gidan yatafi dani.
daga nan ɗaya side ɗin dake can gabar da gidan muka nufa, shima tsaruwan sa da tsarin sa kamar sauran part biyun nan,
koda muka fito daga cikin part ɗin baki na washe nadubi Bappa dake ta faɗin
"Kai komai yayi masha Allah komai fa yayi yadda yakamata". baki nakuma washewa ina faɗin "Kai wlh Bappa gidan nan Allah yayi kyau kaga fa nan irin wancan can ma irin wancan kai tsarin gidan yayi kyau komai iri ɗaya, sai dai kawai kalolin kayan cikin sune daban-daban".
dariya Bappa yayi kana yace "Da gaske gidan yayi kyau ko?."
"Wlh kuwa Bappa." nafaɗa da sauri ina cigaba da washe baki, shima dariyar ya kuma yana girgiza kai kana muka rufawa mutanen baya in da suka nufi wannan kayatacce rantsatstsen babban side ɗin nan dake a tsakiyar gidan wan da yazamana da sauran side ɗin sun sashi a tsakiya.
a hankali muka isa bakin kofar da sauri ɗaya daga cikin mutanen ya isa bakin kofar side ɗin wan da yake na glass ya ɗaura hannunsa gefe kan wasu madannai ya daddanna sai ga glass ɗin yafara bada sauti ɗan baya yaja kana ya dubeni yace
"Bismillah Madam ɗan zo ki tsaya a nan."
ya nuna min kan step ɗin da yasauka akai wan da saika haura kansu kafin ka isa bakin kofar,step ne guda uku, nuna kai na nayi alamar ni?. yace "Eh." a hankali na matso na haura kan step ɗin, daga in da yake yamika hannunsa yakuma danna wasu lambobin kana yace na ɗaura hannuna kan nan yanuna min wani ɗan zagaye da hoton yatsu, a sannu nakai hannuna na dai-dai ta yatsuna kan zanen yastun, nan yafara bada sauri ɗit-ɗit sai kuma yakuma danna wata lambar data fito mai alamar Okay. nan take kofar tazuge gefe ai ko da sauri na ɗaga hannuna.
ya juyo yana duba na kana yace
"Madam wannan kofar special ne mai amfani da zanen yatsune mutum ɗaya ke amfani da shi, sai kuma wancan". yanuna wata kofar dake gefe ya isa gurin muma mukabi bayan sa,ni dai cikin rashin fahimta nake jin sa, yace
"Shi wannan common door ne kamar yanda aka sani kowa zai iya amfani da shi."
ya murɗa handle ɗin kofar yabuɗe muka shiga ciki.
sai gamu mun bayyana cikin wata katafaren parlour ya ilahi ya lilahi, har bansan san da na furta "Kai! amma wannan duk yafisu kyau!".
nayi maganar cikin hakikance gaskiyar abun da ke cikin zuciya ta wan da maganar fitowa kawai tayi,
Bappa ko karamar dariya yayi tare da jijjiga kai.
suma sauran dariya suka bini da shi, nan muka fara kusawa cikin katafaren parlour'n, baki da hanci gaba ɗaya na buɗe wajen kallon katafare kayataccen parlour'n, faɗan tsaruwar sa da misalta tsarin parlour'n ma ba zai misaltuba, yaji kayan alatu da more rayuwar duniya tsaruwan sa ya zarce sauran side ɗin da muka shiga babu haɗi ko kaɗan.
bedroom ɗin dake cikin parlour'n muka rika shiga ɗaya bayan ɗaya, bedroom ne zafafa har guda huɗu masu ɗauke da tsalatsalan bathroom,
daga gefe da parlour'n kuwa katon dinning area ne sai kitchen babba a gefe.
sama muka hauwa wan da shi kanshi step ɗin haurawan sama abun kallo ne domin kuwa shima an kawatashi na musamman.
wow masha Allah shima tsarin saman kamar kasan sai dai banbancin kalolin kayan dake cikin su, kalar kujeru da labulayen bedroom and parlour kasan white and ash da ɗan ratsin lemon-green. saman shima 4 bedroom ne a cikin sa kalan kayan bedroom and parlour'n kuma white and sky-blu.
Antsara komai yadda yakamata sai tashi da sassanyan kamshi mai haɗe da kamshin sababbin kaya yake.
kai gidan ya haɗu fa nidai bakina yakasa rufuwa wajen kallon tsaruwan gidan, bayan mun gama zaga lungu da sako na saman muka gangaro kasa anan muka yada zangon mu cikin parlour'n kasa.

Kowa sai yaba kyau da tsaruwar gidan yake, ɗaya daga cikin mutanen yadube ni kana yayi gyaran murya sannan ya ce
"Madam komai yayi ko? komai ya miki wannan gidan yayi miki? kokuma mu isa wani gidan?."
kallon sa nayi cikin rashin faminta sai kuma na maida dubana ga Bappa danaji yana faɗin
"Duk da dai bataga sauran ba amma ga yanda take ta washe bakin nan ai ba a magana."
da sauri nace "Bappa gidan..". bai bari na karasa ba yace "Gidan ki wannan gidan duk girman ta nakine akwai kuma ire-iren su suna nan".
ido na waro kamar a mafarki nakejin zancen, "Wannan ya miki?". mutumin yakuma jefo min tambayar, kai nashiga gyaɗawa da sauri sai kuma naruko hannun Bappa ina faɗin
"Eh wlh yayi-yayi Allah Bappa gidan yamin kyau sosaiiiii".

Dariya Bappa yayi yace "To sake min hannu kada ki ɓala".
ai ko sauran mutanen ma suka rika dariyar ganin yan da nake washe baki ina jijjiga hannun Bappa, Naseem da Nasmah dariya suka rikayi suna tsalle jikin Bappa kamar wan da sun san abun da ake.

Mutumin yacigaba da faɗin
"To masha Allah wannan side ɗin shine naki a yanda aka tsara ginin gidan, sauran kuma ke kikasan yan da zakiyi da su, yanzu mu zamu koma mubarki ki huta zamu dawo zuwa gobe, domin sauran baya nai."

Sukayi mana sallama suka fita, suna fita, na dubi Bappa ina waro ido nace
"Bappa wai da gaske wannan gidana?". Bappa yayi murmushi tare da faɗin "Daɗina da ke akwai shirme." hannu nashiga tafawa ina faɗin "Kai wlh gidan nan yayi min mugun kyau." ya ce "To sai ki goyashi kuta yawo tun da dai naki ne." ido na waro tare da sa dariya nace
"Bappa gidan zan goya?." kanshi ya jinjina yana murmushi.
rungume Naseem da Nasmah nayi cikin tsananin farin ciki, sai kuma na sake su.
da sauri nace "Bappa ina su Inna wuro da Fatu?."
yace "Suna can ruga". nace "Bappa shine bakazo da su ba kace su dawo nan suzo mu zauna da su a nan, kaji Bappa."
nafaɗa ina jijjiga hannun sa, "Kaji Bappa kace su zo". nakuma faɗa ganin yayi shiru bai ce komai ba,
yace "A'a HAMDAH su zauna acan zan koma ai nima".
ido nakuma warowa da karfi nace "Bappa ni kaɗai za'a barni a wannan gari gudan, da ni kaɗai zan zauna a gidannan ai dani daku zamu zauna."
nayi maganar ina nuna cikin parlour'n "Tap Allah bazan iya zama ba dan Allah Bappa kace su dawo nan, wannan gidan ai tsoro zai rika bani ni kaɗai a cikin sa, kaji Bappa?."
nafaɗa ina bubbuga kafafuna a kasa. "To babu damuwa zasu zo amma ba yanzu ba."
na ce "Bappa sai yaushe." ya ce "Bari dai mana a gama Hajiya HAMDAH."
dariya yake bani in naji ance Hajiya HAMDAH, ai ko na washe baki,
yace "To meyasa bakisa hakorin hajji ba acan?."
"Kai Bappa,hhhh to zan sa in na kuma komawa."
"Allah ya kai mu ai kamar yanzu ne shekara zata kuma zagowa Allah ya nuna mana cikin masu rai da lafiya."
yayi maganar yana mikewa tare da cigaba da faɗin
"To ni bazanje masallaci gashi ana ta kan kiran sallah, mutumin zo muje muyi sallah".
da sauri Naseem ya mike ya roko hannunsa suka fita.


Da sauri na mike inata daɗa waigen cikin parlour'n inshiga wan ɗakin in fita inshiga wancan haka narikayi, daga nan kuma naja hannun Nasmah muka haura sama ina faɗin
"Bari naje na zaɓi bedroom ɗin da yafi min."
koda muka haura ɗakunan duka na shiga kana nazaɓi ɗaki ɗaya, nan cikin bedroom ɗin nabuɗe bathroom ɗin sa na shiga mai girma da tsaruwa kamar ɗakin kwana.
kayan jikina na tuɓe duk da ban jima da yin wanka ba nacika ruwa cikin basin nashige ciki, lumshe idanuna nayi ina jin daɗin ruwan na ratsani, najima sosai a ciki kana na wanke jikina da sabulu mai sanyin kamshi da nagani cikin bathroom ɗin, sannan nafito.
Na sami Nasmah gaban mirror ta ɗauki

Please Login or Register in order to submit comment