You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

kansu.
baki Nasmah ta washe ta mike tsaye a kangadon tace
"Mommy yau Aunty'n mu tayi mana haka."
tarike kugu tare da girgizawa, dariya nayi ina faɗin
"Au kice yau Aunty rawa tayi muku."
"Ba haka bane haka ne".
Naseem yafaɗa tare da mike wa yarike kugu yasoma tsalle.
ido na ware nace "Kai kuce yau kunsha rawa." cikin tsallen yace "Eh ai hadda chocolate ma."
tsai da tsallen da yake yayi sai kuma ya dira a godon da gudu yafita sai gashi ya dawo da School bag ɗin sa, a tsakiyar gadon ya zazzage School bag ɗin sai ga Chocolate masu yawa haɗe da littattafan sa sun zubo,
da mamaki nace
"Yau kuma Talatu kayan zaki tacika muku a jakar."
nakai hannu na ɗibo chocolate dasuka kai guda biyar kala daban daban, ga kuma wasu a gaban sa, da ɗan mamaki nake kallon su dan asanina babu kalar waɗannan chocolate ɗin acikin kayan cime-cimen su kalar nasu ba irin wannan bane.
"Kai Naseem a ina ka samo waɗan nan chocolate ɗin?."
nayi maganar ina duban sa, da sauri Nasmah tace
"Nima akwai nawa." ta dira agadon da gudu tayi waje, Naseem ko bai bani amsa ba sai kokawar buɗe laidar chocolate ɗin yake.
ta shigo da school bag ɗin ta itama ta zazzage, nace
"Kai wai waya baku wannan abun haka, Talatu Talatu."
nashiga kwaɗawa Talatu kira dan na fara tunanin ko rikici sukayi mata gun shirya su tabuɗe wani katon ɗin chocolate ɗin daban.
Naseem da yakai Chocolate ɗin baki ya kutsura yana ɗaga kafaɗa alamun yana jin daɗin abun yace
"Daddy yace mucinye wannan duka dai kaya mana wani."
"Ai yace idan ka kaiɓa min baye kaya maka ba ni de bani da yawa."
cewar Nasmah tana kai wan da ta ɓare baki.

Ido da baki na waro da mamaki tuno wan da suka taɓa kiran sa da Daddy a makarantar su nace "Wani Daddy mutumin nan ko?, a ina kuka san shi dan gidan ku da har zaku rika ce masa wani Daddy."
Naseem daya cika chocolate a bakin sa yace
"Ai Daddy yace kuma dai jo ya auke mu ya kai mu can guyin kifi babba."
cikin tsawa nace "Bana ce muku kada wani yasake baku abu ku karɓa ba? ashe bakuji ba so kuke nazane ku ko?, bana ce muku nice Daddyn ku nice Mommy'n ku ba, shi ba Daddy'n ku bane, baku san shiba shima bai sanku ba, bakuda Daddy nice Daddy'n ku, kuna jina dai ko?."
nariko kunnuwan su ina jijjigawa a hankali, suka gyaɗa kai.
shiru nayi tare da komawa na jingina bayana da jikin gado jiki a sanyaye nashiga maganar zuci
"Kuhi hakuri ƴaƴana ni zan cigaba da zame muku uwa kuma uba a duniyar na."
jin kwalla nakokarin zubomin nayi saurin dakatar dashi...

A ranar nasa aka kawo musu chocolate dawsu kayan makulashe aka kara kan wan da yake gida.
washegari ranar asabar bamu wuni a gida ba yawon guraren shakatawa muka tafi, ni Faty Naseem Nasmah da kuma Talatu, sai direba. sai yamma muka dawo niki niki da kayan makulashe, washegari ranar Lahadi ma muka kuma fita, shima sai yamman muka dawo a part ɗin su Inna wuro muka yada zango sai bayan isha muko koma side ɗin mu, ai ko muna shiga su Nasmah suka ɓingire da bacci.
koda gari ya waye dakyar nata da su Talatu ta tafi da su dan yimusu wan ka da shirin makaranta, dan tare jiya muka kwana da su.
kamar kullum na rakosu muna ɗagawa juna hannu suka fita.
ina komawa ciki wanka nayi nashirya cikin les copie colour da ɗan ratsin gold ajiki,
da misalin karfe 10 da rabi nasauko kasa da mayafi akai na sai ƴar karamar jaka mai ɗauke da wayoyina da wasu ƴan kuɗi dana saka ciki,
dinning area na nufa, in da na tadda Zulai tagama shirya komai na breakfast, a ɗan gaggauce nayi breakfast ɗin, ina yi ina duba agogo, dan fita zamuyi da Bappa zuwa asibitin da ake ginawa dasunan Inna ganin yan da ai kin ke tafiya, ina saurin ne dan jiya nace mishi karfi goma da rabi zamu tafi nasan kuma yanzu haka yagama shiri ni yake jira.
koda na fita a kofar masallaci dake ta nan cikin gida na taddashi zaune, na karaso in da yake tare da gaida shi, daga nan muka shige mota muka nufi asibitin.
masha Allah asibiti yayi kyau saura kaɗan a kammala aiki, bamu bar asibitin ba sai wajen karfe 12:20pm nacewa Yakubu muwuce makarantar su Nasmah mu ɗauko su.

Abakin get ɗin makarantar Yakubu ya faka mota yafita da sauri yana faɗin
"Bari naje na fito da su". yayi cikin makarantar da sauri, muna nan zaune can yafito da sauri kamar zai kife kasa yakaraso gefen da nake yace
"Hajiya wai an zo an ɗauke su."
ido na waro da mamaki nace "Wa yazo ya ɗau kesun bayan kai muna tare da kai ina ce kai ne me zuwa ɗaukar su."
Bappa yace "Zancen banza kai wani direban akayi musu sabo ne da zaizo ɗaukar su? ko dai bakaji abun da suka faɗa da kyau bane?."
yace "Wlh haka mai gadin yafaɗa Bappa."
da sauri Bappa ta buɗe motar yafita ai ko nima da sauri nafita narufa masa baya har ina haɗawa da sassarfa.
babu kowa cikin makarantar sai mai gadi da masu kula da tsaftar makarantar sai shara da goge-goge suke, hankali tashe Bappa ke tambayar mai gadi, mai gadin yace
"Ai ko minti goma basu da tafiya ba duk ɗazu muna tare da su anan da wasu ɗaliban mota tazo tafaka nan bakin get suna ganin motar suka zuba a guje zuwa gurin motar suna murna, da naso hanasu dan ganin ba ɗaya daga cikin irin motocin da ake zuwa ɗaukar su da shi bane, to ganin yan da suke ta murna sukayi gun motar a guje yasa nayi tunanin ɗaukar su a kazo, dama badaga gida akazo ɗaukar su ba!."
maigadi yakarashe maganar yana buga kirji.
Yakubu da gumi yafara keto mishi kamar zai fashe da kuka yace
"Ina ni ke zuwa ɗaukar su kuma gani a gaban ka sai kuma hajiya wata rana,ko mutumin yasako irin fuskata ce ya zo."

Bappa yace "Amma kuwa abun da mamaki amma ya kamata lokacin da kaga ba ɗaya daga cikin motocin da ake zuwa ɗaukar su da shi bane yazo kama yayi kaje kaga ko waye ne,amma wani abun mamakin da kace wai sun je gurin motar da gudu kuma suna murna to ko wani ne daga gida yazo ɗaukar su tun da sun san mun fita har da direba?."
ni dai kasa magana nayi sai ɓari da jikina yake cikin matukar tashin hankali tuni idanuna suka kawo ruwa kan kace me hawayen suka fara sauka.
murya na rawa Yakubu yashiga tafa hannu da salati yana faɗin
"Dama ance yanzu masu garkuwa da mutane sun canza salo akwai wani abun da suke yi sai dai kaga mutum na ta binsu kamar ya sansu harsu tafi da shi, wayyo Allah Naseem da Nasmah ko dai sune."
cikin gwalalo ido mai gadi yace
"Wayyo Allah nashiga uku wayyo ai kina shikenan dama ance idan aka sami matsala to abakin ai kina, ashe dama tsarin da masu garkuwa da mutane suka fito dashi kenan? shi yasa yarannan sukayi ta tsalle kamar doki suka ruga in da motar take, ashe jansu ake taciki kamar kuran karfe."
ɓarin jikina ne yakaru yayin da zuciya ta ke bugawa da karfi gudun hawaye na yakaru.
Bappa yace "Kai ya isa haka Falyakum khairan au yasmuq, in sha allahu babu abun da zai faruku muje gidan mugani wata kila daga gida ne akazo aka ɗauke su tun da sunsan bama gidan."
yadube ni yana cigaba da faɗin
"Kice Innalillahiwa'inna'ilaihirraji'un."
kalmar nashiga nanatawa kana muka juya gun mota, muka bar maigadin nan tsaye yana ta rafka salati dafaɗin shikam yau yasan ai kin sa yazo karshe har in sace yaran akayi.
acikin mota Bappa yarika zuba addu'o'i yakuma hanani kukan danake shirin yi yace nayi ta faɗin
Innalillahiwa'inna'ilaihirraji'un.
a haka muka isa gida.

Muna isa Yakubu yayi hon maigadi ya wangale get yana kokarin wucewa parking lot nace
"Ka sauke mu anan."
dan gani nake kamar motar bata tafiya da sauri tsabar tashin hankali.
tun kan ya dai-dai ta parking muka fito daga motar maigadi yakaraso yana mana sannu batare da dukkanmu mun amsa ba Bappa yayi saurin cewa
"Wayaje ya ɗauko su Naseem a makaranta a cikin ku?."
maigadi yace "Gaskiya babu wan da yaje ɗauko su dan tun da kuka fita ma babu wan da yafita, yau kam sunsha zama a makaranta Yakubu yayi hanzarin zuwa ɗauko su."
"Innalillahiwa'inna'ilaihirraji'un an ce anzo an ɗauke su kuma kace ba wan da yafi tun fitar mu an sace su kenan."
nayi maganar tare da fashewa da kukan da Bappa ketasa ni danneshi, nacigaba da faɗin
"Ina suke ina suka shiga waya ɗauke su.".
maigadi ya walalo ido tare da faɗin
"Iye! ansace su!."
Bappa yace "Ka tabbatar da babu wan da yafita."
yace "Wlh babu wan da yafita tun fitar ku ina bakin get ɗin nan........!





Mommyn Twins ce







7



HMD WASA FARIN GIRKI!



Littafin na siyar wa ne kibiya ki karan ta my no 08034690723




Mai gadi yashiga jan hanci yanaci gaba da faɗin "Sam babu wan yafita ai da nasani dana shiga ciki naje na karɓi makullin mota naje na ɗauko su ai, na ɗan iya mota ba sosai ba amma da wasu su ɗauke su gara ni naje a haka na ɗauko sun, wasu matsiya tane masu niman jaraba suka ɗauke su, duk tai makon da akewa mutane baiyi musuba har sai sun haɗa da sata, wayyo Allah Naseem wayyo Nasmah, ashe da rabon ragowar shayi da nama gobe bazan shaba, kullum sai sun kawo min na haɗa da nawa duk na kallame."
zuwa yanzu tashin hankalin Bappa yafara bayyana yashiga faɗin
"Kanu innalillahiwa'inna'ilaihirraji'un Allahumma ahjirni fi musibati²."
bakina na toshe da tafin hannuna jin kuka mai sauti yana son suɓuce min najuya ina kokarin barin gurin Bappa yakira sunana najuyo ina hawaye yace
"Je ki zauna kada ki ɗaga hankali sosai na tabbata zasu kira kuma bazasu cutar da su ba dan kuɗi suke bukata za'a kuma basu babu komai."
kai kawai na gwaɗa najuya nasoma tafiya, maigadi yabiyo ni yana cigaba da jan hanci yace
"Anyi bako Hajiya."
ban iya juyowa ba bare nabashi amsa Bappa ne yace "Ina bakon?." yace "Gashi can a mota yana shigowa kuma kuka shigo,"
"Wanene?." cewar Bappa, yace
"Gashi can cikin mota ai da naso hanashi shiga ganin baiyi kama da irin waɗan da za'a dakatar ba shine na barshi ya shigo."
yayi maganar yana nuna wata mota dake fake gefe a farfajiyar gidan.
Bappa ya girgiza kai kana ya soma tafiya yana faɗin.
"Ana cikin wani hali ta ya za'ayi a saurari wani bako."
Cikin matukar da muwa da tashin hankali nake tafiya, "Me zaisa su ɗauke su in dai kuɗi ne akan su ɗauke su ni da sun faɗa min ko nawa ne zan basu, me yasa suka zaɓi su cutar da yaran da basujiba basu gani ba.
wlh Allah sai yabi musu kadin su tun suna ciki ake cutar dasu da zaluntar su, har suka fito duniya."
wasu zafafan kwalla ne suka rika wanke min fuska bana ko iya ganin gabana, tunani na ɗaya awani hali suke yanzu..
Bappa har ya wuce motar da mai gadi yace masa bako ne ciki, sai kuma ya dawo sanin da yayi kan cewa bako rahama ne,
gilashin motar ya kwankwasa, a hankali aka zuge glass ɗin.
cikin matukar mamaki Bappa ke lallon mutumin da waɗan da ke tare da shi, yana zaune a mazaunin direba waya na rike a hannunsa yana ta faman latsawa, Nasmah na zaune a gefen sa tasaka kanta jikin kafaɗar sa tana ta cin chocolate, Naseem kuwa na zaune a gefen mai zaman banza rike da waya a hannunsa yana buga game yana kuma taunar chocolate.
cikin tsananin matukar mamaki Bappa ke cigaba da kallon mutumin da mamakin ganin sa tare da su Naseem,
tabbas bazai taɓa mance wannan fuskar ba, mutumin daya samar musu da ingantaccen ilimi a rugar su,mutumin da ya yayi ruwa yayi tsaki wajen ganin an cafke ƴan ta'addan da suke shiga rugar su suna kaɗa musu shanukai su kashe musu makiyaya.
cikin girmamawa mutumin yashiga gai da Bappa, Bappa ya amsa fuska ɗauke da annuri yana yi masa kallon sani, shiko mutumin ga duk kan alamu bai gane shiba, cike da al'ajabin ganin su tare da su Nasmah Bappa yace,
"Ikon Allah kai ne nan tare da su Naseem da muke zaton ko ƴan garkuwa da mutane ne suka ɗauke su."
da sauri Bappa ya juya yana faɗin
"HAMDAH taho gasu nan."
cak naja na tsaya dai-dai lokacin dana ke kokarin ɗaura hannuna jikin kofar side ɗina, najuyo da sauri, magana Bappa yaci gaba dayi yana nuna cikin motar.
"Gasu nan cikin mota Allah yayi ikon sa."
dagudu na nufo gun motar ina share hawaye na da bakin mayafi na,
ina isa gun motar nawuce gaban Bappa da sauri batare da duban cikin motar ba duk da glass ɗin motar a sauke take, hankali na nakan murfin motar dana saka hannu ina kokarin buɗe motar sai jin ta nayi a rufe, da sauri na ɗago karaf idanun mu ya haɗu da juna, da mamaki nake kallon sa sai kuma nan take naji raina ya ɓaci,
mutumin da yace wai arika turo mai wayo yarika ɗaukar su Naseem a school ba ni ba, wan da kuma suke kiran sa da Daddy yayi ta tara musu chocolate kamar sun zama shazumame sar kin shan zaki.
fuska na ɗaure tamau ina duban su Nasmah nace
"Ku sauko nan!." nayi maganar cikin tsawa da zare idanuna.
Bappa yaɗan matso yana faɗin
"Wlh mun shiga tashin hankali sosai da akace wani mota daban yazo ya ɗauke su ba ɗaya daga cikin motocin gidan nan ba, mungama zaton masu garkuwa da mutane ne, suka ɗau ke su."
kai ya jinjina tare da yin murmushi wan da yayi sana diyyar bayyanar kyakkyawar dimple ɗin fuskar sa, batare da yayi magana ba ya kai hannu ya buɗe marfin motar, baya na ɗan ja kaɗan ya buɗo marfin, ya zuro kafafun sa waje, Nasmah dake gefen sa yaɗago ta cak yafito da ita ya aje ta kasa, kana asannu yafito daga cikin motar,tsayuwar sa ya gyara kana yaɗan sunkuya jikin kofar yamika hannu cikin motar Naseem ya rike hannun nasa yaɗago shi cak yafito da shi, sai da ya ajiye Naseem kasa kana ya ɗago da murmushi yace.
"Idan za'a cigaba da barin su har kowa ya watse a makaranta ba'a je ana ɗaukar su kan lokaci ba to kuwa zasu iya fuskantar hakan,domin su masu garkuwa da mutanen babu ta in da basa nan."
kai Bappa ya jinjina cike da gamsuwa da maganar sa kana yace
"Tabbas kuwa, Allah yashiga sakanin nagari da mugu."
a kufule nace
"Babu ranar da ba'a zuwa ɗaukar su kan lokaci in ban da ranar da nayi ta kiran Yakubu bai ɗaga ba, sai kuma yau, yau ɗin ma ai bawani makara akayi ba tun da karfe 12:50pm muka isa makarantar kuma karfi 12 da rabi ake tashin su, kuma tun kan ɗalibai su watse mai gadi yace aka ɗauke su, to ashe dai ba'a makara zuwa ɗaukar su, ana zuwa ɗaukar su tun shabiyu ajira su har sai an tashe su a ɗauko su a dawo da su, babu wani ɓata lokaci a zuwa ɗaukar su, kai kuwuce mushiga ciki!."
nayi maganar cikin haɗa haushi biyu zuwa uku, akan me zaice ba'a zuwa ɗaukar su kan lokaci. sannan kuma wace dalilin ne yasashi zuwa ɗaukarsu ina ruwan shi dasu dakuma rayuwar su, yasa nayi kuka da tunanin ansace su ne. sannan ganin yan da yaran suka manne masa sai kiran sa da sunan dana hanasu suke.
tun da nafara maganar idanunsa akaina yayin da yake shafa sajen fuskar sa, kafaɗa yaɗaga kana yace
"Kinyi kokari, kiyi wayon sanin hakan tukun dan da kaɗan kikafi yaran wayo."
ido na waro amma lallai mutumin nan yana da rainin wayo karo na biyu kenan da yake cemin wai bani da wayo, yaran dana haifa yake cewa wai dakaɗan nafisu wayo. wani kallo na watsa masa tare da murguɗa baki nace "Allah yasa wayon suka fini, mece ce matsalar ka?."
nayi maganar tare da kuma murguɗe baki.
Bappa yace "Um to hakane kam amma ana zuwa ɗaukar su akan lokaci sai dai ɓacin rana, amma akiyayen shiyafi, mun gode sosai, in sha Allahu za'a kara azama wajen zuwa ɗaukar su."
hannunsu na fizgo ina faɗin
"Kuzo ku wuce ina magana kuna tsaye."
najanyo su fuuu muka nufi ciki anan na barsu shi da Bappa, cikin haushin jin Bappa yana saurarar sa, har shi zai gwada wa mutane yan da zasuyi da rayuwar su, ina ruwanshi, irin mutane masu shegen shishshigi kan abun da bai shafe su ba.
sai da muka shiga parlour kafin na sake hannun su, na zauna kan kujera, ina duban su sukam ma ko a jikin su sai wata tsafgar su suke.
kunnuwan ko wannen su na rike naɗan murɗa da karfi, suka haɗa baki wajen cewa "Wayyo Mommy."
nace "Sai na sinke kunnen har idan baku dai na abun da na hana kuba, wato duk hanaku da nake tayi bakuji ba ko shine yau abun naku yagirma har da binsa, kunsan shi ne? baku san mutum ba kukama binsa har da shiga motar sa, ina kuna so a yanka kanku ne?."
kai suka girgiza da sauri tare da faɗin
"A'a-a'a Mommy." nace "To ban hanaku ce masa Daddy ba bana ce muku ku bakuda Daddy nice Mommyn ku nice Daddyn ku ba?, ban ce kada wani ya sake baku abu ku karɓa kuci ba?, shine har yau zaku bishi kushiga motar sa, kunsan shine?,
to sai nayi muku duka yau sai na kaiku wa ɗawisu ta caccake ku bari ku gani."
namike tsaye tare da ruko hannun su ina cigaba da faɗin
"Ɗawisu kawai zan kai ku wasu sune zasu yin maganin ku."
kuka suka sake da karfi suna faɗin "Wayyo Mommy kai ki kai mu."
"Ai bazaku bari ba sai na kai ku gurin su su hana ku da kansu."
nayi maganar ina jansu.
ihu sosai suke suna faɗin
"Mommy mun bayi." komawa nayi na zauna kan kujera ganin sun tsorata sosai najasu jikina na rungume su, ina faɗin
"To kuyi shiru nafasa kai ku amma idan kuka kara sai na kaiku, zaku kara ko?".
kai suka girgiza da sauri nace "Kada ku sake zuwa gurin wan da baku sanshi ba bare har kushigs motar sa, kuma kada ku sake ce masa Daddy shi ba Daddyn ku bane nice nan Daddyn ku kunje jo?."
kai suka kuma gyaɗa wa suna jan shashsheka.
a hankali narika shafa kansu cikin tsananin tausayin su, wasu zazzafan kwalla ne suka ciko ido na, ban dakatar da su ba har sai da suka gangaro kan fuskata ta, nakai tafin hannuna na goge, yayin da nake daɗa mannna kan su a kirjina, ina jin tausayin su na daɗa shiga na.
maganar zuci nafara yi yayin da zazzafar hawaye mai cike da ɗin bin kuna ke cigaba da zuba a ido na.
"Kuyi hakuri bana so ku sanya wa ranku abun da babu shi a rayuwar ku, nafiso ku tashi da sanin cewa bakuda shi ni zan zame muku garkuwa uwa uba."
daɗa rungume su nayi ina jin kuna cikin raina lallai tabbas ba shakka anyi min tabo mai muni ni da ƴaƴana wan da bazan taɓa mancewa da shi a rayuwa ta ba.
kwallar idanuna na share tare da kokarin danne damuwa ta.
ɗago wa nayi jin sallamar Bappa na amsa ina mai cigaba da kokarin danne damuwar dake azalzala ta cikin zuciya, naɗan gyara zamata cikin dabara na share ragowar hawayen idona, ya karaso ya zauna. huf su Nasmah suka mike a jikina Naseem daya dubi Bappa yace "Bappa Daddy fa yana waje?." sai kuma ya juya da sauri yana faɗin
"Dan je guyin Daddy." ido na ware da mamaki kamar ba yanzu nagama masa barazana har da kukan sa ba amma gashi ya tashi yana faɗin zai je gurin mutumin.
Bappa yayi murmushi da faɗin
"Dawo nan mutumina, ai yatafi." yafaɗa yana ruko hannunsa kana ya cigaba da faɗin
"Yaro kenan shi kamar dabba yake duk mai kyautata masa to zakaga yana son kasan tuwa da shi,
wlh nayi mamakin ganin Ahmad Tijjani Sabil, nakuma yi mamakin ganin sa tare da yaran nan, koda yake hakan ba abun mamaki bane."
da ɗan mamaki na dubi Bappa jin sunan mutumin a bakin sa, Bappa ko daɗa faɗaɗa murnushin dake bayyane kan fuskar sa yayi kana yaci gaba da faɗin
"Yaron kirki ne sosai kinga ma bai ganeni ba sai da nayi masa tuni,
ai wannan yaro Allah dai ya masa albarka yakawo babban gudunmawa cikin rayuwar mu a Ruga, ya inganta mana rayuwa yakawo haske cikin rayuwar mu kwarai da gaske, lokacin da ɓarayin shanu suka addabe mu babu dare babu rana, sukashe mana makiyaya su kaɗa mana shanukai, kwasam sai Allah yajefo mana shi, wata rana yazo rugar mu a matsayin bako watan sa guda tare da mu, ranar da yazo ɓarayin shanu suka shigo rugar mu, suka saci shanukai suka raunata mana makiyaya Allah yatakai ta kwanan su na gaba, sai dai mun rasa makiyayin mu guda ɗaya kuma mun san su suka sace shi, ya kwashe su yakai su asibiti cikin gari, ranar hankali yatashi muka ɗau aniyar ɗaukar mataki da kanmu.
ranar da ya cika sati uku, har lokacin ɓarayi basu kara kawo mana hari rugar muba sai dai rugar da muke makota da su,
da yammacin ranar an je kai masa abinci kamar yadda aka saba sai aka iske shi da wani makiyayin mu cikin ɗakin da aka bashi yake kwana ciki, makiyayin da muke tunanin ɓarayin shanun nan sun tafi da shi, ya ɗaɗɗaure shi, yanata gana masa azaba da wani irin na'ura.
wan da yakai abincin yakurma ihu nan da nan jama'a suka taru munyi mamakin ganin makiyayin mu tare da shi yana bashi azaba,nan ƴan gari suka rika cewa a kashe shi ashe shima ɓarawon shanu ne muke tare da shi.
cikin tsawa yace duk mudakata yace kunzo nan kuna ta wani har gowar ku mara amfani kuje ku tare ƴan ta addan da suka dunfaro rugar ku domin kona ku su kuma tafi da dukiyar ku. cikin rashin fahimtar abun da yake nufi muka shiga kallon junar mu, shiko ci gaba da baiwa makiyayin mu azaba yacigaba da yi, dai-dai lokacin kuwa muka soma jin karar bindiga daga can nesa, nan fa hankali yatashi jama'a suka fara kokarin watsewa domin ɗaukar makamin kare kansu.
wani irin gigitaccen kara makiyayin nan ya saka lokacin da ya datse masa yasar hannun sa guda,
cikin tsawa yace masa, Ta wani kusurwa zasu shigo,? su nawa ne kuma?, wasu irin bindigogi ne a hannunsu?!!.
cikin tsananin jin azaba yasoma magana cikin matukar wahala yashiga bashi amsar tambayar dayayi masa.
munyi matukar mamakin jin abun da makiyayin nan yafaɗa to me haka yake nufi?, a lokacin bamu sami damar jin amsar tambayar muba,
sai muryar AHMAD Tijjani Sabil mukajiyo da karfi yana faɗin.
Kowa ya koma gidan sa kada wani yafito waje,duk abun da zakuji kada ku fito. kamar yadda yafaɗa kuwa haka mukayi batare da musu koni man jin ba'a si ba kowa yayi gidan sa, sai dai bamu zauna haka ba kowa da makami a hannusa domin kare kai.
ranar tashin hankalin da muka shiga ba zai faɗu ba, dan muna shiga gida ƴan tadaddan nan suka karaso cikin rugar mu, wasu suna kunce dabbobi wasu kuma suna ta harbi.
shigowar su dakamar minti ashirin, muka jiyo jiniyar sojoji ta ko ta ina suka sanya rugar mu a tsakiya.
nan suka shiga bata kashi ranar kamar rugar mu zata fashi dan harbin bindiga, an ɗauki tsawon mintina 30, kafin kikaji guri yayi tsit.
sai hayani ya da magana da turanci haɗe da hausa ake,
can aka fara magana da abun sauti irin wan da hukuma suke magana da shi domin sanar wa ko bada umurni wa al'umma,
aka ce kowa ya fito, nan muka fito cikin ɗar-ɗar duk da asanar wan nasu sun sanar mana da cewa hukuma ne ke magana,
amma a tsorace muke kuma bamu fito haka kawai ba sai da makaman mu, domin kare kai, duk da kuwa munsan su bindiga ne a hannusu mukuma akasin haka sai dai munsan Allah yana tare da mu.
koda muka fito ganin hukumar ne da gaske nan hankali yaɗan kwanta kaɗan, Allah yabasu nasarar cafke ƴan tadaddan nan wasu daga cikin su sojojin sun harbe su gasu kwance cikin jini, wasu kuma gasunan kwance a ɗaɗɗaure bindigogin su a zube a gefe.
Ahmad Tijjani Sabil yana tsakiyar hukuman nan yayin da wannan makiyayin namu ke kwance a gabansa shima a ɗaɗɗaure.
bayan jawabi da ban hakuri da hukumar nan sukayi mana, da

Please Login or Register in order to submit comment