You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

motocin su,
tun kan mukarasa sauka sukayi hanzarin nufo in da muke,
Nan suka samu a gaba mu da jagororin da shugaban kasar mu yahaɗo mu dasu,
sauran sojojin da ke tsaye jikin motar sukayi hanzarin buɗe mana mota, muna karaso wa muka shige ciki, yayin da Ni Bappa Mahmoud Naseem Naseem, muke mota guda sauran motocin kuma jagororin mu suka shige ciki.
batare da ɓata lokaci ba sukaja motar mukayi gaba,
Ido nayi ta bazawa kan shahararren titin da muke tafiya kansa da kayatattun guraren da muketa wucewa,
Kai jama'a na rantse babu kasar da takai Saudi kyau duk tafiye-tafiyen ka duk wani yawon buɗe idon ka zuwa wasu kasashe daban-daban har in bakaje Saudi ba,
to Tabbas bakayi kallo ba, baka kuma baiwa idanunka abinci mai kyau ba.....


Wani kayataccen masauki aka sauke mu,
bayan munci munsha munyi su wanka, Bappa yace muje masallaci muyi sallah,
wasu sojoji uku sukayi mana rakiya zuwa Masallaci sai bayan sallar isha muka dawo masaukin mu a gajiye dan munyi sallole kam ba iyaka, tun a cikin masallaci su Naseem sukayi bacci,
a cikin parlour sojojin suka dire su saman kujera,
ɗaukar Nasmah nayi na nufi ɗakin da a ka sauke ni ɗazu,
shin fiɗa Nasmah da ke hannuna nayi kan lafiyayyen gadon, da ɗan sauri na juyo jin an turo kofa,
Mahmoud ne rike da Naseem, gefe na ja tare da soma cirewa Nasmah takalmin kafarta, ya karaso bakin gadon ya shin fiɗa shi,
Ina ɗagowa muka haɗa ido da shi, saurin kawar da kaina nayi,na lura tun a mota yake ta satar kallo na sai ya rika niman yimin magana musamman idan muna hira da Bappa sai ya rika saba ki ciki, yana fara sa baki cikin maganar ni kuma zanyi shiru haka kawai nake jin mogun nauyin sa,
gefen sa na bi ina kokarin wuce sa yace
"Shima kicire masa takalmin zai masa nauyi ai".
yafaɗa tare da nufar kofa yafita, a sannu na isa na cire masa takalmin, zubewa nayi a gefen su dan bacci ne tam ido na..

Washegari bayan mun dawo daga masallaci muka tadda an cike mana parlour da breakfast kalolin abinci iri-iri irin na gida Nigeria da kuma irin na nan kasar Saudi,
bayan munci munsha mukayi su wanka, aka kuma ɗiban mu da sojoji jama'a sai gamu a fadar Saudi,
Ya ilahi ya lillahi na ga karrama wa naga karamci daga gurin larabawa, gaskiya larabawa akwaisu da karrama wa,
nan da nan ina za'a saka akarika yi da mu tamkar mu wasu ne, anawani kafa-kafa da mu.
Nan da nan aka cike mu da kayan cime-cime irin na larabawa....★
Bayan maganganun da ya gudana sakanin fadar Saudi da jagororin kasar mu da shugaban kasar mu yahaɗo mu da su,
nan fadar ta bukaci ganin Diamond ɗin,
nan Bappa ya ciro sa cikin lajuhu wan da suke ɗaure cikin laida ya mikawa ɗaya daga cikin jagororin mu,
kana shikuma ya mikawa wani na kusa da shi sannan shi kuma yamika wa da dukkan alamu hukuma ne, ya karɓa kana ya taka zuwa sakiyar katafaren parlour'n saman table ɗin dake gaban wani farin dattijon balarabe yana zaune cikin kamala da dattako fuskarsa ɗauke da annuri,
ya aje laidar, tare da yin magana cikin harshen larabci.
shugaban shima yayi magana cikin harshen larabci da sauri wani da ke zaune a kasa kusa da kafar sa ya mike ya shinfiɗa wani farin gyalle kan table ɗin kana yashiga kunce laidar,
ya juye Lu'ulu'u'n kan farin gyallen.
wani dake tsaye taɗan can gefe rike da wani ɗan karamin a kwati ya maso da sauri tare da buɗe ɗan karamin a kwatin,
yaciro wani na'ura kana yamaso kusa da table ɗin,
ya ɗaura na'urar kan Lu'ulu'u'n nan na'urar ta kawo haske tare da bada ɗan sauti, idanun mutumin tar a kan na'urar, yaɗau mintuna da ɗan dama kana yaɗago,
cikin garshen larabci yayiwa wan da nafi tunanin shene shugaban magana,
kai ya jinjina tare da duban mu da murmushi ɗauke a kan fuskar sa,kasan cewar bama jin bama jin larabci shima bayajin yaren mu, sai ya juya cikin harshen turanci yake magana,
"To a binciken da akayi yanuna wannan asalin *LU'ULU'U* ne muna tayaku murna".
yafaɗa fuskarsa ɗauke da yelwataccen murmushi,
ai ko gaba ɗaya gurin yakace me da hayaniya kowa yana faɗar albarkacin bakin sa, sai faɗi ake wai wanene yasamo Diamond kuma wai a Nigeria.
mutanen saudi suke maganar, nan jagororin mu suka nuna ni, nan aka rika nuna Ni a na faɗin nice nasamo diamond ɗin, sai kawai nadawo abun kallo, sai nuna ni ake wasu kam ma sai sun zo har kusa dani suna tayani murna,
wasu cikin harshen larabci suke magana sai dai bana fahimtar su gara waɗan da suke magana cikin harshen turanci suma ɗin dakyar sabo da harshen su yanuna da Larabci turancin nasu da kyar nake iya ganewa.
nawo abun kallo har hotuna sukarin ka ɗaukawa dani, wani zaizo kawai yatsaya yaɗauki hoto da ni,
mutane suka rika shigowa suka rika kallo na ni da yarana suka rika ɗaukar su Naseem da Nasmah,suka rika magana cikin harshen larabci idan suka juya da turanci ne nake ɗan fahimtar su,
sukayi ta yabawa yaran da kokari da gararabba da sukayi a bakin ruwa kafin mu samo Diamond ɗin,
hatta shugaban sai da ya jinjina min.
nan da nan ya umurta aje banki a kawo kuɗi, muna nan zaune har waɗan da sukaje kawo kuɗin suka dawo aka rika shiga da gana masgo-masgo cike tam-tam da kuɗi, aka tarasu a tsakiyar parlour'n.
ido na ware cike da tsananin mamakin ganin yan da ake buɗe gana masgo ɗin ana ciro kuɗi a ciki, kuɗi irin na kasar su.
"Sai kace kasa ko kuɗin ganye, to me zamuyi da wannan kuɗin?".
nafaɗa a fili har sai da Mahmoud dake kusa da ni yajuyo ya kalleni,
wasu larabawa ne suka shigo da sallama,in da shi shugaban yayi maga da harshen da muke ganewa wato turanci yake cewa sune masa na farashin Lu'ulu'u, nan suka ƙiyasta kuɗin Lu'ulu'u'n batare da ɓata lokaci ba.
nan da nan aka fara zuba kuɗin cikin na'urorin kirga kuɗi da suka kai guda goma, wan da duk da su akazo daga banki da kuma ma ai katan bankin. bayan an shafi tsawon awanni ana kirga kuɗin
masana farashin Lu'ulu'u' sukayi magana da shugaban,
kuma umurtar su yayi a koma a karo kuɗin dan basukai kuɗin Lu'ulu'u'n ba,
wannan karon har da zinari aka haɗo.
aka rika kirga kuɗin duk gana masgon da aka kirga kuɗin cikin sa sai a maida kuɗin ciki a rufe a kuma zubuta a dadin kuɗin cikin sa,haka akayi tayi anayi ana rubutawa.
ni dai ido na zubawa sarautar Allah ni ban ma iya kirga tulin gana masgo ɗin da suketa tura kuɗi ciki kamar takardu ba,har naji na gaji tamkar nice na'urar dake kirga kuɗin, da mutanen da suketa sakawa cikin gana masgo ɗin.
bayan da aka gama kirga kuɗin a ka jibgesu a sakiyar parlour'n haɗe da
gwala-gwalai da sauransu....



Wannan dattijon balaraben da ke bada umurnin duk abun da za'a yi, yayi gyaran murya tare da nuna kuɗin kana yasoma magana cikin harshen turanci,
"Wannan shine kuɗin Lu'ulu'u'n".
nan kuma ya bukaci a kira masa shugaban kasar Nigeria,
cikin hanzari na kusa da shi yaɗaga waya ya danna kiran lambar shugaban kasar Nigeria,kana ya haɗa shi da shi,
nan yake sanar masa an ƙiyasta kuɗin Lu'ulu'u'n sannan kuma gashi an kirge shi, nan shugaban kasar mu yabukaci a haɗa shi da Bappa,yace yaya za'ayi da kuɗin,
Bappa yace kawai a sashi a sanunun banki dan bamusan yanda zamuyi da wannan kuɗin ba.
shugaban kasar mu ya turo da number account ɗin da za'a saka kuɗin ciki.
nan shugaban yabada umurnin a tafi da kuɗin banki,
nan da nan aka fara fita da kuɗin,
a ka kwashe su zuwa banki,
a ka zuba su cikin account ɗin da shugaban kasar mu yabada na bankuna daban-daban.....★
masauki a ka kuma mana acikin masarautar, kwanan mu uku a gurin naga halacci iya halacci, nadawo abun kallo har daga waje ana zuwa kallo na duk wan da yazo kuwa sai yayi hoto da ni.
har nayi kawaye ƴan matan larabawa ƴan cikin masarauta.
idan naji suna larabci sai nace su koya min, nace an ya ma kuwa zan iya?, sai suce zan iya babu wuya.....★



Acan cikin garin Bauchi kuwa, zaune Ya SALEEM da Na'ima suke a parlour'n sa........!★








mommyn Twins ce


Suna zaune cikin parlour'n Ya SALEEM,
yayin da shi Ya SALEEM ke zaune saman 1str ya tasa system a gaba yana ta faman latsawa,
Na'ima ko na kwance saman doguwar kujera, lodin yankakkun Apple da kankana da abarbane cikin plt a kan table ɗin da ke gaban ta,
daga kwancen take mika hannu cikin plt ɗin tana ɗibar yankakkin Apple da kankanar tana kaiwa bakin ta,
yamusa fuska tayi sannan ta mike daƙyar tana cigaba da yamusa fuskar,
sai kuma ta mike da sauri ta nufi toilet dake nan cikin parlour'n, tazubar da yawon da ta tarashi cikin bakin ta kana tajuyo a hankali,
ɗagowa Ya SALEEM yayi yana binta da kallo, da kyar take ɗaga kafa, tarike kugu da duka hannayenta tana wani tafiya da kyar, ta dawo gurin zaman ta tana wani yamusa fuska,
bin ta da kallo yake har ta zauna ,
zaman sa yaɗan gyara yakuma duban ta tare da faɗin,
"Amai kika kuma?". cike iya kirsa da makirci takuma yamusa fuska kana tace
"Banyi amai ba amma dai inajin zuciya ta na tashi sai dai nakasa yin aman sai yawu da yabi ya dame ni".
yace "Subhanallah duk kayan zakin da kike ta sha ɗin na bai sa kin dai na jin aman ba?".
baki ta yamusa tace
"um to dai gashi ni dai ina jin wannan abun da nake tashan bazai sai da min aman da nake jiba".
"Oh sannu". yafaɗa ya juya tare da ci gaba da abun da yake.
ido ta waro a kanshi ganin ya juya cikin ko in kula da damuwar ta ya cigaba da abun da yake, a kasan ranta take faɗin
"Idan boka na kan tudu ya kasa juya wannan bahagon halin naka, zan kaika wa wani bokan ya juya min wannan halin ko ohon naka".
cike da kwarewa a makirci ta marairaice fuska cikin shagwaɓe murya tace
"Haba My SALEEM iya abun da zakace min kenan,sannu kawai ai yakama ta kayi wani abu nifa wlh wannan cikin yana damu na, ciki da masafaffen laulayi haka, nifa cikin nan yana bani wahala wlh ni kam gara acire shi kawai na huta".
tayi maganar ne cikin kirsa da son gano yan da yake jin son cikin a ransa.
da sauri ya juyo ya kalleta tare da faɗin
"What! azubar fa kikace?".
kai ta gyaɗa cikin shagwaɓa tace
"Wlh ni wannan cikin yadame ni wai ace duk abun da nace baya min daɗi, duk abun da naci sai na rikajin zuciya ta na tashi ni,babu abun da zanci naji daɗin sa kawai ni dai inaga cire sa shine samun kwanciyar hankali na".
da sauri yace
"Ke bakida hankali ne zakice azubar, cikin ne za'a zubar Na'ima?".
kai ta kawar dan ba haka taso ba, har yanzu takasa gane SALEEM duk asirin ta da makircin ta, har yanzu takasa juyashi yan da take so,
yan da taso tarika juya shi yan da take so sai dai har yanzu bata sami damar hakan ba,
duk wani makircin ta da surkullen ta kuwa,
bata taɓa iya juya SALEEM son ranta.
sai dai wani lokacin takan ɗan sami yadda take so daga gurin sa sai dai ba duka yan da take bukata ba.
a yanzu takan ɗan sami nuna kuwalar sa a gare ta,
uwa uba bukatar sa yanzu baya barin sa a jikin sa, kullum sai ya sauke sa a mararta, hakan ba kara min da ɗi yake mata ba dan yanzu ma da kan sa yake niman ta, akasin da da sai ta nima da kanta.
A son ta tana so ya nuna mata kulawa fiye da kulawar da yake nunawa HAMDAH a da,
sai dai ina duk yan da taso hakan bai samuba, ko kwatan-kwatan yan da yake nuna kulawa da rawan kafa lokacin da HAMDAH take da ciki, da kafin ma samun cikin,
baya yi mata.
system ɗin gaban sa yaɗan ture kana yamiko hannunsa yaɗan shafi gefen fuskarta yana faɗin
"Sorry da ma ai an ce duk mai ciki haka take ji har fiye ma da hakan, so hakuri kawai zakiyi har Allah yaraba ku lafiya, yanzu kam ma ai kin kusa hutawa tun da yashiga wata huɗu kenan,
kinga ko kin ɗau gangarar hutawa tun da an ce wuyan ta ciki yafara kwari ne da zaran yafara girma zaka fara hutawa da laulayi,to kin ga kuwa kin kusa hutawa kenan".
rass. taji gaban kirjin ta ya buga shiru ta ɗan yi tare da tafiya cikin tunani a kasan zuciyar ta.
sai kuma da sauri tadawo da kallon ta san sa jin yana faɗin
"Wannan cikin dai ina ga shine a ke ciwa mai bin jiki,to ina ga shima yabi jikin ki ne gashi dai har watan sa huɗu amma bai fara bayyana ba,wata kila in yafara girma yanuno kansa nan zaki ɗan ji daɗi".
hannu ta mika taɗauki yankakken Apple takai bakin ta tana tauna cikin nuna rashin jin daɗin abun da take ci tace
"Ni wlh tsabar wahalar da cikin nan yake bani bansan har yashiga wata huɗu ba".
tayi maganar yayin da zuciyar ta ke tunano mata lallai wannan watan ne yayi dai-dai da cikin watan sa huɗu kenan.
murmushin gefen baki yayi kana ya mai da idanun sa kan wayar sa da ya ɗauka kan hannun kuje rar da yake kai.
sannan yace
"Ai abu na jikin ki ma kina mance kwanakin sa? tun lokacin da na sami labarin cikin nake lissafin sa".
ɗan dimm tayi sai kuma tayi saurin kawar da maganar da faɗin
"Wlh ni ina jin kwaɗayin gwaten gauta, ina ga abu mai ɗan ɗaci-ɗaci yafi gyara min baki".
"Gwaten gauta kuma to ke meye zakiyi da wani gwaten gauta?".
yayi maganar har lau idanun sa nakan wayar sa.
tace "Allah ni shi nake jin sha'awar na sha zan dai na jin bakina ba daɗi, kasan fa tun ranar da Raliya tayi ta kawo min na sha ranar na wuni ban zubda yawu ko amai ba,har nakuma ci abinci lafiyar Allah babu jin rashin daɗin nan,
gashi yan zu Raliya batanan tayi tafi bansan yaya zanyi ba,
bansan wama zai yi min in sha ba."
cikin fara gajiya da surutun ta da son sashi yawan magana da take yace
"Kiyi da kan ki mana har sai wani yamiki kafin kisha, tun da ciwon bai kwantar da ke ba kina iya tashi mai zai hana kiyi da kan ki, sai a samo miki gautar kiyi ai,
ko kuma kisa Rufa'ila tayi miki ko sauran ma'aikatan gidan".
yana gama faɗa ya mike tsaye yana rufe system ɗin sa.
Ido tawaro tace
"Rufa'ila? Rufa'ila'r ce zata yi min girki wlh bazan ci girkin Rufa'ila ba, kawai kasa dai a yimin".
takarashe maganar tana bubbuɗe kofofin hanci.
da ɗan mamaki yajuyo yakalleta ganin yan da tayi maganar a tsaye kana yace
"To wa kike so ya miki ni kike so naje nayi miki? babu masu girki ne a cikin gidan da sai na nemo masu yi miki?".
ganin yan da ya sauya fuska sai kuma ta shagwaɓe fuska tana faɗin
"A'a kai kuma haba dai kadai sa ayi min dan Allah my SALEEM ina so na sha".
"Wa kenan zan sa yayi mikin?".
yafaɗa yana kokarin barin gurin.
da sauri tace
"Dan Allah kayiwa Mamie magana dan nasan ita zatafi iya yin gwaten tun da dai abincin gargajiya ce, ita zatafi yin mai daɗi ma dan Allah kayi mata magana sai tayi min".
bai kuma cewa komai ba har ya juya zai bar gurin sai kuma ya ɗago wayar sa ya laluɓo lambar Mamie ya dan na kira.
bayan sun gaisa yaɗaura da faɗin
"Mamie wai Na'ima ce ke son shan gwaten gauta ko zakiyi mata".




daga cikin wayar Mamie tace
"Yanzu ma haka shirin fita unguwa nake, tasa ma'aikatan ta suyi mata mana in bazata iya yi da kan taba, kaganni nan fita ma zanyi".
Mamie na gama faɗar haka ta kashe wayar.
duk abun da suke Na'ima na ji dan wayar a speaker yasa ka,
batare da yajuyo ba yace "To kinji abin da Mamie tafaɗa bata nan zata fita so kawai kisa ayi miki".
yafaɗa tare da gyara rukon system ɗin sa ya nufi bedroom ɗin sa.
wani irin kololon bakin ciki ne ya tirni ke ta,
wato koma damuwa baiyi ba, shidai yakan nuna yana son cikin amma irin rawan kafa da yake nunawa lokacin cikin HAMDAH sam bayayi a kan cikin ta.
tsaki taja ta tare da mike wa, sai gatanan ta ware tana tafiya normal bakamar irin yanda ɗazu tayi da taje zubda yawo cikin toilet ɗin parlour'n ba.
ta nufi side ɗin ta da sauri ta shige ɗakin ta tana shiga,
ta ɗau wayar ta takira kawarta Raliya, Raliya na ɗagawa tace
"Aminiya ya kike ya gida ya cikin mun dai?".
Raliya tayi maganar da dariya
dariya duk suka saka kana Na'ima tace
"Him kedai bari aminiya ciki yana nan, ke ni ba na mance ba ashe dai cikin yashiga wata huɗu ni bana gama sakarkancewa ba kwata-kwata ni na ma mance da lissafin ashe ɗan batalikan nan yana nan yana rike da lissafin".
dariya Raliya ta fashe da shi.
tace "Ke da abu ke jikin ki baki rike lissafin sa ba".
Na'ima tace
"Himm ke dai bari ai ni na wasar da lissafin tun wancan ranar ashe dama haka mukayi lissafin cikin yanzu yake cemin wai cikin wata huɗu kenan yanzu yakusa shiga biyar kenan,
to idan yashiga biyar ba'aga ciki yana tashi ba yaya kenan, karfa asiri ya tonu".
Raliya tace "Haba dai sai kace ba Na'ima da na sani ba ya kike wani abu kamar ba kece Na'ima ba,ta ya za'ayi ya gane da zaran cikin yakai wata biyar in yaga baigirma ba sai muyi hanyar da zamuyi sai kawai ace ya zuba".
"Kwarai kuwa haka za'a yi kawata kin kawo mafita amma bazai taɓa zuba ba sai ya bani miliyan 5 ɗin na yanzu ma zan shirya in ce masa zanje awo ina zuwa kuma zan kira sa in haɗa sa da Dr Hashim Wargi in tsara masa yan da tafiyar zata kuma ci gaba".
kuma shekewa da dariya sukayi, Raliya tace
"Kai kawata kina fa tsula tsiyar ki".
tace "Yan da nake so kuwa in juya acikin gidan yanda naga dama".
sai kuma taɗan sassauta maganar tare da cigaba dafaɗin
"Amma ki san meye aminiya?".
Raliya tace "Sai kin faɗa". tace
"Allah yanzu ina son cikin nan da gaske narasa yan da zanyi ne kawai kinsan rannan naje gurin boka nace mishi yasake duba min yagani anya kuwa bazan haihuba, yace min maganar kenan fa ɗaya tas koyayen haihuwa ta na gama da su,wai ashe sauran sa kenan zuwan mu akan mahanar kuɗin da nake so SALEEM ya banin nan, yabaiwa aljani durkus jinin duk cikin da zanyi nan gaba kin san wai ashe bayan dawowar mu da wata biyu nasami ciki banko sani ba aljani durkus da akayi masa sadakar jinin yaɗauke cikin yaje ya shanye jinin,
dama wai shike nan ya rage duk na wanke sauran tun muna makaran ta,to ni yanzu abun yafara dami na kin gafa SALEEM yana son haihuwa yana son yara,
narasa yadda zanyi kinga fa ta sana diyyar ganin hankalin shi naga yafara komawa kan yara idan abokan sa sukazo da yaran su karkiga yan da yake yi da su,
gudun kada ya tunu cikin wancan ɓatacciyar shegiyar yarinyar nan HAMDAH da kuma abun da zata haifa ko ta haifan ko ta mutu da cikin oho mata shiya sa fa na laune nace ina da cikin nan, sabo da kawai hankalin shi yadaɗa dawowa gare ni,
yanzu tsohuwar sa ma wai an kira ta dan rainin wayo nace inaso nasa gwaten gauta kinsan me tace? tace wani wai zata fita unguwa to in yi da kai na mana,
kiji matan nan lokacin da wannan ɓatacciyar HAMDAH'N take nan kullum ita ke mata girki tasa akawo mata,
amma wai yanzu nace inaso nasha gwaten gauta tace wai nayi da kaina,wato ko da ɗanta ya narka min cikin da gaske haka zatace kifaji matar nan".
Raliya tace
"To ai yanzun ma na gaskiyar ce tun da koshi uban gayyar bai isa ya karyata ko yagane karya bane,
kirabu da ita kawai kin san har yanzu sunajin abun aransu sai dai bazasu iya yin komai a kai bane".
Na'ima tace
"Ah to sumayi mana ai sai dai abun yakashe su a ransu amma zancen suyi magana kam karyansu,
SALEEM yarigada ya zama nawa ni kaɗai idan sukayi wasa ma sai na rabasu da shi in ga ta faɗin su".
dariya suka saka dukan su
Raliya tace
"Yi hakuri dai kada ki raba su bassu a haka kawai aje zuwa tun da babu abun da aka rage ki da shi".
tace "Kwarai kuwa SALEEM nawane yazamo nawa, amma kinsan maye ne,
Raliya inason magana da ke kizo gida muyi ta, Raliya inason ɗa".
Raliya tace
"Kinason ɗa kuma?". tace "Kwarai kuwa ina son ɗa ɗan da zai zamo da na SALEEM duk da nasan ni bazan taɓa haihuwa ba,amma ina son ɗan da zai zamo na SALEEM kuma a madadin ni nahaife shi magajin SALEEM yashe zaki zo?".
Raliya tace "Zan shigo gobe dan yanzu bana ma gari nayiwa wani saurayi na rakiya, yanzu haka ma muna hotel ne da tun ɗazu kika kira ma bazan sami damar ɗagawa ba,nashiga wanka ne ma yanzu shine kiran ki yake shigo wa."
Na'ima tace
"To shike nan yanzu yaushe zaki dawo".
tace "Gobe ko jibi zamu dawo".
tace "To Allah yakai mu kida gobe dan Allah tabbas ina son ɗa wan da zai gaji dukiyar SALEEM".
Raliya tace "To an gama ina hanya kuwa".
nan sukayi sallama.
bayan da Na'ima ta sauke wayar daga kunnnen ta zama ta gyara tare da faɗin
"SALEEM dole zan samo ɗan da zai zamo naka yakuma gado min dukiyar ka".
tayi maganar a fili yayin da take girgiza kanta alamar yar da da duk wani shirin da ta tufkeshi yanzu a ranta....



a ɓangaren Mamie kuwa
tun lokacin da sukayi waya da SALEEM tana zaune a ɗakin ta, bawai fita unguwar zatayi kamar yan da tafaɗa mishi ba, tafaɗi hakan ne kawai dan a ranta tanajin bazata iya girkawa Na'ima abun da zataci ba koda ƴaƴan cikin ta sunkai guda goma ne.
tana zaune gan ɗeɗiyar mata da ita wai tana laulayin ciki har da niman mai yi mata girki duk da tulin ma'aikatan da ke gidan su.
kai Mamie ta girgiza "Wato dan taga lokacin na HAMDAH ni ke mata girki ko,
to ai HAMDAH yarin yace karama tana bukatar tai mako".
Mamie tayi maganar a can kasan ranta.
yayin da take jin Na'ima wata annoba ce acikin rayuwar su sai dai babu yan da suka ɗiba suka iya da ita.
Mamie na nan zaune har Abbu yashigo yakaraso ya zauna a bakin gadon da take zaune,
ya dube ta cikin kulawa tare da faɗin
"Yaya dai Hajiya Maryamu na ganki shiru haka".
murmushi tayi kawai tana faɗin
"Babu komai".
amma acikin kasan ranta tabbas tunanin HAMDAH ce yazo mata.
shima kuwa a ɓangaren Abbu haka abun yake dan tun shigowar sa da yaga tanayin ta shima yashiga irin yanayin datake cikin wan da baki baya iya furtashi sai dai yayi ta kona zuciyoyi...

a can cikin part ɗin Ummi kuwa
zaune take a kan sallaya kamar koda yaushe tana jan jarbi,
bayan tagama yiwa ɗiyar tata addu'o'in samun kariyar Allah a duk in da take.
Aunty Rafee'at da Aunty Jaleela kasan cewar yau Saturday ne duk suka tattaro da ƴaƴan su sukazo gida wuni, duk suna part ɗin
Ummi da ƴaƴan su, suna zaune suna ta tayata hira,
Ummi dai na zaune tana jin su wan da rabin hankalin ta ma baya tare da su.
Aunty Rafee'at da ke ta danne dan ne cikin wayar ta har tashi gurin adana hotuna,
shiru tayi tare da kurawa hoton HAMDAH sai ga hawaye ya cika mata ido kan kace me yafara gangara kan fuskarta,
ido Jaleela ta waro ganin Rafee'at na share kwalla tace
"Aunty Rafee'at yaya dai?".
fuskar wayar ta nuna mata batafe da tayi magana ba, da sauri ta karɓi wayar yayin da itama kwalla suka ciko idon ta,a fili Aunty Jaleela tace
"Ko ya take?". tayi maganar cikin rauni da damuwa sosai.
"Sai Allah Allah ka kare ta".
cewar Aunty Rafee'at, Ummi ma kwallar ce ta cika mata ido dan tasan mahanar kan HAMDAH suke.
ganin Ummi tayi shiru da alamun bayyanar damuwa sosai a tare da ita.
sai sukayi saurin kawar da zancen da wani hirar da ban...



acan cikin garin Yola kuwa
Mama mai awara na hango acikin family house ɗin su, wan da matar yayan ta ta kanainaye gidan yazamo nata dole da ƴaƴan ta.
tana zaune cikin waɗi ɗan karamin ɗaki karami sosai, acikin ɗakin take zaune da taburman ta.
tazuba uban tagumi, tunanin HAMDAH da halin da take ciki yanzu kaɗai take.
lokacin da ta iso

Please Login or Register in order to submit comment