You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

ranki godiya bakomai bace.
Dariya anty zarah tayi tareda kallon Amatun tana jinjina sunan Wanda rabonta dataji tun zamansu asibiti jinyar Muhammad.


Yanason fita Amma sbd yakira Dr Fatima yasa ya jira harsaida tazo ta duba zarah din ta tabbar Masa da bakomai bane duk cikin laulayin cikine sai nauyi da cikin zai Fara shiyasa Dan haka bayan fitar Dr Fatima fita yayi shima ita Kuma Amatun ta Dan jima kafin ta tafi sbd qafafun anty zarah din ciwo sukai Mata sosai Sai data Dan tattausa Mata su tasamu tayi bacci kafin ta fito Takoma tayi sallah ta kwanta tanajin bacci.


Da daddare Takoma tasake dubo anty zarah din duk da ba wani Abu dake Mata ciwo kawai qafafun ne acan tabarosa tadawo Saida antyn tayi bacci yadawo sukai wanka suka kwanta.
Washe gari zai bar sashenta yakoma na anty zarah Dan haka tun safen bai fita ko Ina ba suna Palo suna shiririta ita ala Dole saiya lallasheta yasata bacci kafin yatafi haka dai suka shiririce har sallar magriba tayi ya tafi.


Zarah duk yanda tayi tunani da Shirin dauriyar abubuwan dazataita gani tareda daukarwa kanta alqawarin dangana tayi Shirin zaman hkr sai abin yazo Mata a baibai yabarta da mamaki sbd MD sauya Mata yayi daga MD ZABEERA zuwa asalin miji,
Ya sauya ta bangarori dabam dabam,
Babban mamakinta ayanxu shine zaman gida daya koya sosai yake zama agida wani lokacin Yana yini guda cikin zabeera bai fita ba Yana tareda iyalinsa ga yawan fara'a daya samu kansa aciki Abu daya datake maimaitawa shine Bata taba Tunanin ummanta datace Mata wata kishiryar kamar alheri ce sbd tana gyara maka mijin daka jima Yana wahalarda rayuwar aurenku hakama wasu yancin naki wata kishiyar itake kwato muku keda yayanki gurin miji ta hanyar sauyasa,
Tabbas ta yadda da hakan,
Akwai Abinda bazaka iyaba arayuwar zamantakewarka da mijinka sbd ka kashe zuciyarka Dan haka kodai duk wadda za'a auro kingama cutarta sbd kin sabawa mijin da yin shiru akan haqqinki Dan haka itama bawani dadinsa zataji ba kokuma kisamu wadda zata sauya mijin kisamu rayuwar dabaki samuba abaya,
Kishiya ko wace iri kasamu ta gari ko akasinta tasan da akwai ciwo Amma dai duk da hakan tana jinjinawa Amatu sbd ta taimaketa tanan Dan ita dai daza'a barta saidai suyi rayuwarsu sugama ayadda suka Fara bazata iya yiwa MD hayaniya ko yunqurin sauyashiba sbd yafison rayuwar kadaicinsa kamar tafi Masa nutsuwa takega shiyasa batason shige Masa sosai.
Abu dayane data lura dashi shine wen ever Amatu is around idanuwansa akanta suke sbd bazai iya Hana zuciyarsa Abinda takeso ba saidai Bata damuba sbd itama aduk lokacinda take kusa to hannuwansa bazasu iya zamaba sai acikin nata Koda Amatun na kusa Wanda hakan ya tabbatar Mata da tanada nata bangaren me mahimmanci a rayuwarsa.


Anasa bangaren kuwa yasamu kwanciyar hankalinda baitaba samuba a rayuwarsa tun bayan rasuwar mahaifiyarsa tabarsa,
Yasamu nutsuwar zuciya da rayuwa,
Yasamu kwanciyar hankali data ruhi,
Rayuwa cikin iyalin dakake matuqar so suke sonka tareda baka nutsuwa shine asalin Abinda baisaniba sai yanzu,
Amatu ce takawo sauyi arayuwarsa da zuciyarsa Amma Kuma zarah ce abar jinjinawa kwanciyar hankali da nutsuwar rayuwar dasuke sbd itace ta dauki komai da salama da dangana tareda sawa kanta nutsuwa batareda damuwa ko tashin hankali ba azaman Wanda yasa ake zaune kalau,
Da Bata bada wannan gudunmawarba da duk yanda suka Kai ga tsananin son juna shida Amatu bazasu samu wannan kwanciyar hankalinba da nutsuwar zaman lafiya.
Nuratu tazama tamkar aminiyarta yanzu sbd kusan kullum gurinta ma take yini hardai ranarda anty salamatu tazo gidan yini sukeyi fira USI ma da tintini yarinyar ta fice Masa arai sbd kusan itace silar komai tun Yana shareta har suka Fara sabawa sbd Amatu dakuma yaganta Dr salman dayake babban abokin shawarar USI dabaida amintaccen Dan uwa irinsa da hakan dai suka Fara sabo da ita sosai.




Satinta hudu da tarewa tafara Shirin komawa sbd school karatunsu yadauki zafi Dole zata koma Dan haka duk sukabi suka wani sukukuce musamman ita dazata Koma ita kadai ko Muhammad gurin umme zaiyi zamansa daqyar ma dadynsa yabari Dan acan yaso sanyashi school Amma ummen ta toqa hakama shima Muhammad din yafison gurin ummen yanzu sbd tana sakaltashi da yawa gashi Kuma yaga Yana ganin dadynsa anan.


Ita kanta anty zarah zatai kewar Amatun sbd sunyi sabon sabo duk da har abada zasu taba komawa yanda suke Ada ba Amma ko yanzu sunyi sabon shaquwarsu suna tsananin mutunta juna da gujewa Shiga haqqin juna.


A gidansu ta yini Daren ranarda zata koma canma Saida tayiwa su iyami kukan barin gida kafin yazo da daddare ya dauketa suka koma gida.
Washe gari Saida tayiwa kusan kowa dake cikin zabeera bankwana kafin suka wuce USI ne dakansa yakaisu airport suka wuce yadawo.


Sbd son cire Mata damuwar data sanyawa ranta yasa Basu koma Greece ba direct suka nufa US.
Wata irin rayuwar Jin Dadi da sakewa sukai a US tamkar turawan qasar Dan sai alokacin tasake sanin asalin waye MAHMOUD ZABEERA sbd wani bangarensa data gani na dabam wato Dan rayuwa.
Duk yanda zatai rayuwa bazata manta wainnan kwanakin dasukai a US ba sbd ya shayar da ita soyayyarda har abada bazata barta ba,
Ya sanyawa zuciyarta wani sabon maganadisun sonsa da qaunarsa.


Kwanansu takwas suka tattara suka nufi gida saidai Kuma kamar karsu dawo tunda suka dawo tafara zuwa school kwana biyu shikenan ciwon zazzabin dare ya sanyota gaba sunyi yawon asibitin hardai aka tabbatar musu da ciki ne Dan haka ba wani magani haka suketa fama duk wani aikinsa ya ajiyesu jinyar matarsa yake cikeda kulawa da tsananin qauna.


Ganin harya share kusan wata daya da rabi yasa ta daure ta bawa kanta qwarin ta nuna Masa ta warke sarai kafin yafara maganar komawa sbd tarin ayyuka da Kiran dayaketa faman Sha dazai tafi ita dakanta takaisa airport suka fito motar ya kamo hannunta ya matso da ita cikinsa Yana kallonta da fararen idanuwansa dake bayyana newarta tun kafin ya tafi ya bude baki ahankali Yana shafo cikinta cikin laushin murya yace"


I will miss you wife.


Dan dago qafarta tayi sbd yafita tsayi takai bakinta Kan nasa ta Dora ahankali ta zura Harshenta tabashi wani irin kiss tana kallon cikin idanuwansa tace"


I will miss you More.


Rungumeta yayi tareda sauke ajiyar zuciya Yana shafa Bayanta yace"


I love you.


Qanqamesa tayi kalmarsa na sake kashe jikinta.
Sun jima ahakan kafin lokacin tafiyarsu yayi yabata kiss a goshi ya wuce tana kallonsa harya shige ta juya jiki amace ta shiga mota tabar airport din tana Jin kewarsa kamar tabisa.
##Mamuh#




ZAFAFA BIYAR 2021


Hafsat miss xoxo🥰
KIBIYAR AJALI......!
   (Sulke baya tareta saita gitta).😋🤗
 Â
     Mamu gee🥰
MIN ƘALB!!😋🤗


    Hafsat rano🥰
ABINDA KE CIKIN ZUCIYA...!!😋🤗


    Safiyya huguma🥰 SIRAƊIN RAYUWA😋🤗


     Bilyn Abdull🥰
SARAN ƁOYE🤗😋


  Duka akan farashi mai rahusar gaske.


Kamar haka👇🏻💃🏻


Ɗaya___300
Biyu____400
Uku_____450
Huɗu____500
Biyar_____700


Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇


ACCOUNT NO 0812652655
ACCOUNT NAME- HAFSAT LAWAN GAMBO
BANK NAME: ACCESS BANK.


saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇


0903Â 234Â 5899


IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇


 09033181070


💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻
TEAM----ZAFAFA BIYAR🔥😘🥰😍


ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻.
6/17/21, 8:09 AM - ': *_MQ 50_*




https://youtu.be/1VyZ6f1GTWg
Please subscribe to our YouTube channel 👆👆👆






Tana komawa gida kwantawa tayi tun anan Palo tana waya da anty salamatu akan maganar zuwan datakeson tayi suna gamawa anan palon bacci ya dauketa.
Bacci me nauyi tayi sai kusan yamma ta farka ta tashi zaune tana Dan dafe kanta dayayi Mata nauyi sbd baccin datai dakuma Dan ciwon dayake Mata.
Miqewa tayi ta nufi daki Kai tsaye toilet ta wuce tayo wanka dan jikinta yasaki tayo alwala tafito ta sanya riga da wando me Fadi ta sanya dogon hijab tahau dadduma ta tayarda sallah.
Bayan tagama sallar kicin taje ta hado tea da biscuits tazo ta zauna Tasha tana kallon agogo tasan zuwa yanzu ya Isa sauka Amma bazata kiraba zata Bari idan yahuta yasamu lokaci zai kirata.




Washe gari da wuri ta wuce school sbd akwai asibitin dazasuje daga school din,
Tunda safe shine ya tayarda ita daga bacci suketa waya Saida zata Shiga wanka suka aje tana Shirin fitowa yasake kiranta harta Isa school suna waya har Anty zarah yabata suka gaisa tayi Mata ya jiki daga Nan daqyar tasamu yayi hanging wayar ta maida hankali Kan Abinda yakawota,


Sai yamma likis ta dawo gida amatuqar gajiye Dan haka ko abinci Bata tsaya Ci ba wanka tayi ta kwanta baccin gajiya da daddare data tashi bayan tayi komai tasake komawa ta kwanta suna waya ta rikice Masa akan sai anturo Mata anty salamatu wlh bazata iya rayuwa ita kadaiba.
Dole ya amince wa buqatarta yaje yasamu kawu da kansa yayi Masa roqon zuwan anty salamatun wannan karon hadda iyami ya roqa taje tadubota tunda batada lafiya zataji dadin ganinta sosai.


Kawun bedai cemasa ya amince da zuwan iyaminba tukuna Amma dai ita salamatun zataje itama bazata jimaba sbd maganar neman aurenta da Andi ya nemawa alhaji qarami Wanda yake autansu Modibbo basason doguwar bidia kamar a taqaice suke son ayi auren.


Da kansa yasa akawa anty salamatun shirye shiryen tafiya sbd kusan shima a matse yake dataje din yasamu me kula Masa da Amatun Dan gabaki daya hankalinsa ba'a natse yakeba Jin yake kamar yaje da kansa yayi jinyar abarsa Amma Kuma ayanzu zarah dake kusan haihuwa tafi buqatarsa shiyasa ma duk wasu tafiye tafiyensa ya rage saita haihu sbd Bata kulawar datake buqata.


Duk yanda yaso anty salamatu ta Isa cikin kwanaki qalilan bai yiyuba sai bayan sati biyu da maganar ta tafi tareda USI dazaiyi 6month program acan aikuwa Nan suka dasa sabuwar rayuwa a Greece hakan kuwa ba qaramin nutsuwa yabawa MD din ba Dan dama shineya tsayawa USI akan zuwa Greece din yin program dinsa acan infact ma shine yadauki nauyin komai sbd kawai Amatun tasamu Yan uwanta atareda ita hakan ne kawai zai bashi cikakkiyar nutsuwa sbd yanayin datake ciki.


Zaman USI agarin tareda zuwan anty salamatu ya kawarda duk wata damuwarta da rage Mata kewarsa sosai Dan haka saita kwantarda hankalinta take karatunta cikin kwanciyar hankali da bada himma musamman yanzu da cikinta yafara girma Dan kusan wata hudu cikin na biyar kenan ita Kuma zarah ayanzu tana gab da shiga cikin watan haihuwarta shiyasa Koda yazo gurinsu bai wani dadeba yakoma yasake barinta cikin sabuwar kewarsa Dan har wata qaramar tafiya sukai dayazo din.


Zaune suke apalo tana duba wasu textbook na school anty salamatu Kuma tana yanka Mata gwaibar data siyo daga wani superstore ahanayarta ta dawowa school suna Dan fira sama sama sbd Rabin hankalinta nakan books din wayarta tayi ringing tun daga Kan kalar ringtone din tasan waye me Kiran ta Kai hannu ta dauki wayar tana sake wata qaramar ajiyar zuciyar son mijin nata ta daga cikin kasalalliyar murya tace"


AMATULLAH's husband..


Duk da Yana cikin wani yanayi na damuwa Saida yadan murmusa hartaji sautin murmushin ta cikin wayar ahankali tace"


Barka da yamma.


Barka wife,
Hw are you and my baby?
Ya anty salamatu hope duk Kuna lafiya?


Yes lafiyanmu kalau it's just that we're missing you badly.


Numfashi ya sauke Wanda yasata Dan gyara zama tana ajiye books din jikinta cikin sauti me nutsuwa tace"


Lafiya kuwa? You sound worried.


Dafe goshinsa yayi cikin yanayi na damuwa yace"


Zarah na asibiti tun safe she can't deliver by her self itama aiki za'a yi Mata.


Faduwa gabanta yayi cikin tsoro da damuwar itama zatazo wajen ga tausayin anty zarah din sai jikinta yayi sanyi da rawar murya tace"


Yanxu tun cikin dare anty zarah take cikin wannan halin Amma baka fadaminba dady sai yanxu?
Wlh na tausaya Mata yanxu kenan suna ZABEERA specialist?


Yes yau sukeson ayi aikin sbd qarfinta harya qare nagaji da ganinta cikin wannan halin.


Kwantar da murya tayi cikin tausayawa anty zarah din da tausayinsa shi kansa sbd tana iya Jin irin damuwar dayake ciki a muryarsa tafara qoqarin kwantar Masa da hankali tana sake bashi qwarin gwiwa akan Allah yasa ayi aikin lafiya akuma dace.


Bayan sungama waya tana fadawa anty salamatu tana lalubo numbern umman zarah din ta Danna kiranta,
Tana dauka ta gaidata cikin ladabi ta Dora da cewa''


Umma Ashe anty zarah haihuwar tazo wlh bansaniba sai yanzu dady yake fadamin tun safe Kuna asibiti.


Amatu antynki Kam tanajin jiki kitayata da addua Allah yarabasu da bbyn lafiya.


Inshallah Allah lafiya kalau zasu rabu
Allah yasa ayi aikin cikin sa'a
Nasan bazata iya mgn yanzu ba Ina Mata sannu zuwa anjima zansake Kira naji Inshallah.


Shikenan Amatu angode Allah yayi albarka.


Amin umma ngd sai anjima.


Aje wayar tayi tana kasa cigaba da karatun ta shiga damuwa da tunani tasake Kiran MD din takuma kwantar Masa da hankali.


Haka Takoma sukuku tunda sukai Magana takasa sukuni sbd hadda tsoro tsoron zuwan tata haihuwar yake sake shigarta takasa zama sai kiransu takeyi akai akai tana tambaya har lokacinda aka shiga aikin da zarah Amatun kiransa takeyi tana Kiran umman zarah din harsaida umman tace Mata"


Amatu ki kwantarda hankalinki tunda kema bake kadaiceba kada ki daga hankalinki wata matsalar ta taso Kuma ku rabawa mijinku hankali Kashi biyu.


Ana fitowa sallar magriba aka fito da lafiyayyan jaririn zarah cikin qoshin lfy sai kuka yakeyi cikin qoshin lfy aka wuce dashi sukai duk aune unen dasuke buqata kafin aka shiryasa cikin fararen overall masu kauri nurse ta fito dashi fuskarta daukeda murmushi ta nufo inda MAHMOUD yake tareda mahaifinsa Modibbo daya iso asibitin alokacin tareda umme da Haj maryam.


Modibbo aka miqawashi ya karbesa cikin farin cikin ganin jikinsa 'da na farko ga MAHMOUD dinsa.
Addua yayiwa jaririn kafin ya miqawa MAHMOUD da idanuwansa suke Kan fuskar yaron Wanda tunda nurse tafito dashi kafin yashigo hannunsa zuciyarsa tagama cika da soyayyar 'dansa.
Zarah tabasa farin cikin rayuwarsa,
Ada baidamu da samun 'dan kansaba Amma tun Bayan haihuwar Muhammad zuciyarsa ta cika dason Tara zuriar me yawa kodan ya Gina tashi zuriar sbd fita rayuwar kadaici.


Addua yayiwa yaron tareda Masa huduba yakirasa da sunan Muhammad DAHEER Modibbo.
Godiya Modibbon yayi cikin Jin dadin takwaran da akai Masa.
Nan kowa yafara karban yaron ana Yaba kyawunsa da kamannin babansa daya Dan dauko.


Saida aka gama murnan samun Modibbo aka koma murnar samun nasarar aikin da akayi umman zarah kuwa farin cikinta a bayyane yake ganin yanda kowa ke murnar haihuwar 'yarta.


Babban tashin hankalin dasuka shiga na samun mugun labari daga bakin likitoci shine ba lallai zarah din tasake haihuwa ba sbd rashin qwarin mahaifarta data fashe kafin Cs din.
Hankalin ummanta yatashi sosai hakama da duk Wanda yake gurin Saida jikinsu yayi sanyi Amma ganin MAHMOUD dakansa ya dauki qaddarar ya dauki juriya yasa kowa ya hkr suka buge da tarairayar zarah wadda tayi kukan wannan mugun labarin MAHMOUD na aikin lallashinta cikin nuna Mata tsananin damuwarsa Dole qarshe ta dangana tabarwa Allah akan hakan shine qila mafi alkhairi.


Amatu data sake Kira kusan karo na biyar kenan bayan haihuwar sai yanzu tasamu damar Magana da anty zarah din Tai Mata barka tana sake Mata sannu daga Nan suka Dan gaggaisa da jamaar dake asibitin ta kashe wayarta.


Kallon babynta takeyi idanuwanta na cikowa da hawayen farin ciki Dana damuwa taji an zauna gefenta tareda zagayeta da hannunsa har ita har Modibbon Yana kallon Modibbo dake baccinsa cikin nutsuwa ya shafa fuskarsa tareda maido kallonsa Kan fuskarta Yana riqo hannunta cikin kulawa da nutsuwa yace"


Zarah ki daina damuwa akan Abinda ba Allah ne yafadaba,
Banson Baki empty hopes Amma Dan ance bazaki sake haihuwa ba ba lallai bazaki sake haihuwar ba sbd ba fadan Allah bane ki dauki qaddara ki rungumeta Allah nason bayinsa masu yadda da qaddara.


Dago jajayen idanuwanta dake tsiyayar ruwan hawaye tayi ta kallesa cikin tunani daban daban Wanda ya kunshi irin hope din data hangowa kanta na samun soyayyarsa ta hanyar Tara zuria me albarka dashi sbd gano burinsa da qaunarsa tason Tara Yara.


Kamar yasan Abinda take Tunani ta ganin irin kallon datake Masa ya rungumeta ahankali tareda shafa Bayanta cikin murya me taushi yace"


Zarah yanzu ke ba matata ce kawaiba ke uwar 'yayana ce,
Ayanzu kin riga kinzama wani sashe na rayuwata da zuciyata,
Samun haihuwa a tsakani wani alamarine me girma Dan kuwa kinriga kinzama tamkar jagoran zuriar dazan Tara a gaba ko ba naki yayanba,
A da ke zarah ce matar MAHMOUD yanzu Kuma ke zarah ce matar MAHMOUD uwargidansa Kuma uwar Dan haka ki cire kowane irin tsoro ne kikasa acikin ranki sbd mi MAHMOUD DAHEER ZABEERA Ina baki tabbacin mutuwace kawai zata cireki daga rayuwata.


Wani irin kuka tasaki tana sake qanqamesa zuciyarta na cika da farin ciki da nutsuwar zancensa....


Ahaka ummanta tashigo tagansu Dadi yasake kamata ta karba Modibbon ta fita dashi sbd su iyami dasu maman junior dasukazo ganinsa.




Kwanansu shida a asibitin aka sallamesu suka dawo gida inda kowa keta zuwa barka da farko gida taso komawa MAHMOUD din yace tazauna a gidanta bayason zuwanta ko Ina.


Amatu kullum tana kiransu Jin takeyi kamar tazo Amma Babu dama Dole saidai take ganinsu ta hotuna shikansa MAHMOUD din bataga alamar zai barta tabiyo hanyar zuwaba sbd ko school yanzu ya hanata tuqi da kanta anty salamatu ke kaita wani lokacin Kuma USI idan yanada time kenan sbd akusa da street dinsu yakama apartment yake zaune.
Ranar data Fara Masa maganar tanason zuwa Kai tsaye yace"


No,Babu inda Zan iya Bari kije until you deliver.


Dama tasan haka zai fada Dan haka Bata wani damuba ta bar zancen ta maida hankali Kan rainon cikinta da karatunta ta bangare daya ga MAHMOUD din dayanzu wani soyayya yakeji kodan itama lokacin haihuwarta ya matso ne Amma sam yanzu ko barinta bayayi ta sarara akan Kiran wayarsa.


Bayan sunan Modibbo da sati uku yayi daidai da Gama exams dinsu tana gida kwana biyu Babu inda take fita ga nauyin cikinta ya dameta ma gabaki daya.


Zaune take ita kadaice agidan anty salamatu sunfita da USI siyayyar wasu daga cikin kayansa na lefe dayake siya tun anan sbd Shi da Nuratu sungama daidaicewa tsakaninsu yana dawowa yakeson ayi idan son samunsanema to ahade aurensu danasu anty salamatu sbd dagashi har nuratun kamar zasu cinye juna sbd soyayya shiyasa itama yanzu nuratun kamar ta hadiye Amatu sbd qauna Dan sai yanzu take qara sanin mahimmanci Amatu agurin USI da irin tsananin qaunar junansu dake tsakaninsu.


Kallon wani tv program na likitoci takeyi a CWTv hankalinta rabi nakan waya sbd tun safe take kiran wayarsa Bata shiga Kuma shima tun Daren jiyan raban daya kirata.


Sake Danna kiransa tayi akaro ba adadi still Bata shiga tana qoqarin sake Kira taji ana qoqarin bude qofarsu ta shigowa ta juyo tana kallon qofar da waya a hannunta sukai Ido biyu itada shi ta Dan zaro Ido tana kallonsa tareda miqewa tsaye komai nata na bayyanarda mamakin ganinsa shikuwa kallonta yakeyi cikin kewa da soyayyarta ya tsaida kallonsa Kan cikinta dayayi girma cikin wata free doguwar rigar masu ciki data saka wadda batakai qasa ba sbd kada ta takurata ya ware Mata hannu Yana kallon fuskarta daukeda boyayyan murmushi da gudun dabatasan zata iyaba tayo kansa ta fada jikinsa ya rungumeta Yana Dan dagata sama cikin farin ciki da murna tace"


I love this surprise of urs Husband.


Sauketa yayi tareda Kama hannunta suka qarasa shigowa taso karban luggage dinsa ya hanata suka nufi dakinsa tafara gyarawa Yana tayata suka gyara dakin duk da Babu Abinda yayi 'yar qurace kawai.
Wanka yashiga ta fita zuwa kicin hada Masa abincin dazaici.
Cikin farin ciki tafara dafa Masa pasta da carrots sai beef meat ta hado Masa Kan tray takawo Masa har bedroom dinsa yaci tana zaune tanata tambayarsu Modibbo Wanda kamar ubansu daya da Muhammad sbd suna dibar kamanni.
Yana gamawa ta kwashe kayan ta maida ta dawo ta zauna Kan cinyarsa tana sake tambayarsa meyasa be fada Mata zaizoba.


Fuskarsa ya Dora kan tata Yana sauke ajiyar zuciya a boye yana kallon cikin idanuwanta da itama shi take kallo ya Dora hannuwansa Kan cinyoyinta Yana shafawa cikin malalacin sauti yace"


Sbd inason ganin farin cikin bazata a kyakkyawan fuskan matana.


Murmushin Jin Dadi tasaki tana sake shigewa jikinsa ahankali tana qara cukuikuyesa qasa qasa da murya tace"


Ko acikin barci MAHMOUD ZABEERA yazomin farin cikina bayyananne ne bare ganinka a zahiri so lovely husband zuwan bazatanka ya tafi da zuciyan AMATULLAH K.


sake matsota yayi cikin jikinsa Yana shaqar qamshin jikinta ya shaqi numfashinta dake sauka Kan fuskarsa sbd matsuwar dasukai da juna ya Dora bakinsa Kan nata Yafara kissing dinta Yana zame hannuwansa zuwa wuyan rigarta.


Koda anty salamatu suka dawo da daddare guraren 9 Bata tareda wata gajiya sosai sbd sun Dan bibbiya guraren hutawa sun shaqata bataga Amatun ba a apalo ta shige da kayan zuwa dakin Amatun inda sauran kayan lefen suke Nan na Bata ganta ba sai tayi tunanin toilet Dan haka dakinta Takoma ta fada toilet itama tayo alwala tazo ta tayarda sallah.


Jin shiru shiru ba motsin Amatu yasata fitowa tana zuwa kicin ta duba ko tana can,
Ganin anyi sabon girki a kicin din yasata bubbudewa tana dubawa tafito Palo ta nufa dining tana ganin plates da kayan da akai amfani dasu ta fahimci oga kwata kwata ya taho kenan ta fito kicin tana kallon hanyar zuwa dakinsa tasake tabbatarda shi dinne yazo ta wucewa daki tana cewa''
Naji dadin zuwanka nasamu yanzu nabi usi next week idan zaije gida.




Washe gari tana kwance cikin jikinsa tana bacci cikin nutsuwa sbd irin kyakkyawar rungumar da yayi Mata suna bacci cikin baccin tafara Jin kamar ciwo ciwon Mara na damunta Wanda yasata bude idanuwanta tana sake saurarawa Abinda takejin saitaji da gaske ciwon yake ta yunqura zata tashi zaune yabude idanuwansa Yana kallonta ta yunqura ta tashi zaune ya tashi shima Yana riqota yace"


Lafiya kuwa?


Kallonsa tayi da sauri tana dafe qasan cikinta a Dan tsorace tace''


Ina ganin labour ne..... kasa qarasawa tayi cikin tsananin azaba da firgici tace"


Hospital hospital hospital take me" duk arude take maganar a jujjuye batareda tasaniba
Ganin hakan ya sauko gadon ya nufi wardrobe ya dauko shirt da wando yasaka cikin sauri tareda dawowa ya dauko Mata riga kamata ya sanya Mata suka fito tana sake dafe cikinta cikin azaba tana Kiran sunan Allah Dana MAHMOUD din cikin ciwo.


Jin dogon salati da qarfi yasa anty salamatu fitowa daidai qarasowarsu tsakiyar palon a Dan rude ta kallesu tana maida kallonta Kan Amatun daketa faman salati ba qaqqautawa cikin mamaki tace"


Subhanallah haihuwar ce ko me?
Lafiya kuwa?


Muje asibiti"kawai ya iya furtawa anty salamatun Yana nufar qofa da matarsa.
A gigice suka Isa asibiti musamman da ciwon ya taso Mata gabaki daya suna Isa ruwan haihuwa na fashewa akai labor room da ita.


Zama yayi Kan kujerun jira Yana kashe wayarsa sbd baya buqatan ko hayaniyar ringing waya.
Suna zaune saiga USI shima ya iso Nan suka Fara zaman jigum jigum cikin zullumi da fargaba,
Wannan zaman jiran dayakeyi yau yana daya daga cikin ranakun tsananinsa na rayuwa sbd gabaki daya Jin yake kamar nutsuwarsa zata bar jikinsa Amma haka dai yake zaune shiru kamar ba Wanda ke cikin tension ba.


USI da anty salamatu ne ke samun damar waya da Yan gida sunajin yaya kota haihune?
Zaman awa uku sukayi cikin ta hudu kafin Allah yabata ikon haihuwar baby girl lafiyayya da ita saidai ba qatuwa bace sosai sai kuka takeyi aka shiryata aka miqowa familynta ita ya karbeta Yana kallonta cikin wata irin nutsatsiyar sonta da qaunarta ya shafa Dan qaramin kumatunta Yana Mata adduoi da murmushi akan fuskarsa yace"


De symbol of my love FADIMATU ZARAH MAHMOUD ZABEERA.


Aikuwa cikin farin ciki anty salamatu itama ta karbi babyn tana kallon fuskarta cikeda murna tace"


MAHMOUD wannan 'ya da yayunta take Kama.
Murmushi kawai yasaki zuciyarsa na sake wanzuwa da farin ciki sai alokacin ya bude wayarsa da atake Kira suka Fara shigowa ya fice Yana amsawa.


Yana dawowa ya tararda anfito da Amatun ankaita dakin hutawa ya shigo Yana aika Mata da wani irin kallon samun nutsuwa ya qarasa bakin gadonta ya zauna tareda Dan rungumota yabata kiss agoshi yace"


Thank you.


Murmushi tasaki tana Dan harararsa tace"


Bazan qaraba daga wannan.


Dariya maganar tabawa anty salamatu takuwa ringa qyaqyata dariyarta shikuma wani guntun murmushi ya sake Yana sake kissing hannunta dake cikin nasa batareda yace komaiba.


Acan Nigeria kuwa cikin both families din haihuwar ta Isa kunnen kowa akaita Sanya alkhairi da yiwa FADIMATU ZARAH adduar Allah ya raya Akan sunna,
Zarah da akaiwa takwara kuwa rasa abin cewa tayi sbd farin ciki shiyasa ma tace zatazo taga takwara da kanta.


Kwananta daya a asibitin suka sallamota suka dawo gida Nan anty salamatu tayita hidima dasu ganin suna hutu Kuma gashi umme da zarah hadda Nuratu since zasuzo yasa ya yanke shawarar su dawo gida

Please Login or Register in order to submit comment