You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

sai bedroom dinta Yana gaba tana bayansa.


Zaune take tana kallon wani Shirin girke girken larabawa da akeyi a mazzika taji shigowarsa tareda sallamarsa ta juyo fuskarta daukeda murmushin dake bayyanarda girman son datakewa Dan nata sai idanuwanta suka sauka akan wadda ke bayansa ta hadiye sauran murmushinta fuskarta na sauyawa zuwa bacin Rai da fushin ganinta ta tsuke fuska sosai tana dauke Kai daga bakin qofar.


Tsayawa Amatu tayi daga Inda take tana sauke Kai ganin irin kallon qyama da tsanar da ummen ke Yi Mata,


Qarasowa yayi gefen ummen ya zauna Yana kallon fuskarta data canza yaji ransa yaqara jagulewa ya sauke wani irin numfashi Mara Dadi Yana dafa hannun ummen cikin kulawa da sanyin jiki tareda sautin daya sakasu kallonsa duk su duka biyun yace"


Umme Meyesa Zaki dauki halayyar daba naki ba¿
Shin Amatu tanada wani banbanci ne da sauran mutane da Kika zabi qyamarta ita kadai?
Umme Amatu matar dazan aurace sbd Ina sonta da dukkanin zuciyata
Shin umme kodan son datakewa dan naki bazaki qaunacetaba kodan hakan?


Girgiza Kai tayi tana danne 6acin ranta ta kallesa tace"


Khalil kadaina cewa tana sonka wannan bayan kudi duk duniya Babu yaren datake ganewa,
Wannan Babu wani buri a rayuwarsu Bayan samun kudi ta ko wane halin Yaya,
Kudine kawai agabanta ta yanda zata iya yin komai akan kudi ciki ina fada maka harda mutuncinta zata iya siyarwa akan kudi,
Wlh khalil kaima sbd kudinka take sonka da bakada kudi bazata taba sonkaba
Irin wannan matar kakeson nabari ka aura Khalil???


Dagowa yayi ya kalli Inda Amatun ke tsaye cikin wani irin yanayi na damuwa ya sauke ajiyar zuciya tareda cewa''


Zo AMATULLAH,
Zo Nan kusada umme.


Kallon ummen tayi taga ko kallon inda take Bata qaunar Yi sbd qiyayya ta tako ahankali tazo gefensa ta zauna ahankali Kan carpet din dake gurin tana sauke kai maganganun ummen na sake jujjuyawa cikin kanta.


Numfashi ya Kuma saukewa cikin wani irin yanayi na damuwarsa dake bayyane wadda tasa dukansu su biyun kallonsa yasake riqo hannun ummen cikin sanyin murya yace"


Ummen banfara son AMATULLAH ba Sai danasan asalin wacece ita,
Nafara sonta ne bayan nasan batada kowa aduniya,
Banfara sonta ba saidanasan a bola ta tashi acan tayi wayo ta koyi gwagwarmayar rayuwa,
Banfara tsananin sonta ba saidanasan irin wahalalliyar rayuwar datayi amatsayin almajiri Mara yanci Wanda ta rayu cikinsu amatsayin namiji bayan tana matsayin mace,
Amatu bakowa mace face yarinyarda wasu bayin Allah suka taimaka suka daukesu Bayan sungama wahalalliyar rayuwa acikin bola da mataccin gidaje da shagunan daba'a gamaba,
Babu Wanda yataba kallonsu da idon Rahama,
Babu Wanda yataba duba yanayin shekaru da jinsinta amatsayin mace ya taimakesu,
Sun kwana da yunwa suntashi da ita,
Sunyi sata dan suci suyi rayuwa,
Maza da yawa sunyi yunqurin lalata rayuwarsu da sunan taimakawa shin umme Wanda yake ciki irin wannan qaddarar Dan yayi sata dan yaci ya Hana kansa Zina illa ne dahar za'a gujesa??????


Umme wallahi tallahi ina tsananin son AMATULLAH da dukkanin zuciyata bansan ta Yaya zanyi Miki bayani ki qaunaci Amatu ba,
Na shirya auren AMATULLAH na zamo gatanta itada zuriarta Wanda Babu wani Abu dazai sauya niyata akan hakan,


Shin umme kintaba zaunawa kinyi tunanin irin tarin Lada da farin cikin dazaki samu aduk lokacinda Kika kawo murmushi da farin ciki a rayuwar marayu?
Umme tarin ladace me yawa wadda zata iya gyara Miki ko wanke kurakurenki Kuma yabaki nutsuwar zuciya da ruhi....


Zuwa lokacin Amatu kuka takeyi sosai sbd Bata taba sanin khalil yasan asalinta ba daduk halinda suka Shiga arayuwa Kuma ahakan yake sonta tabbas yagama bawa rayuwarta girgizar data sauya zuciyarta akansa gabaki daya.


Umme ma hawaye takeyi sosai tsananin so da qaunar danta na ratsata...


Ahankali ya zamo qasa ya durqusa gabanta tareda riqo hannuwanta idanuwansa dasukai laushi na kallonta a karye yace"


Umme ayau gani na durqusa a gabanki Ina roqonki daki ajiye dukkanin wani burin rayuwa ko komawa Allah kodan samun nustuwar zuciya,
Umme Ina roqonki da ki qaunaci Amatu ki da zuciya daya sbd bazan iya ganinku acikin halinda kuke cikiba,
Umme......


Bata Bari ya qarasa ba tayi saurin dagosa tana rungumesa hawayenta na qara tsiyayowa tace"


Nayi maka alqawari Khalil wlh Babu wani al'amarin duniya dazan sake Bari na 6ata akansa,
Idan dai Amatu ce Kuma wlh na amince maka bazan qara qintaba idan har na tabbatarda har zuciyarta itama take sonka....


Rungumeta yayi da sauri Yana cewa''


Thank you ya umme.


Share Mata hawayenta yafarayi tareda juyowa ya kalli Amatu dake kuka sosai ahankali tanajin Sam Bata cancanci soyayyar khalil ba,
Zuciyarta batayi Mata adalci ba son wani 'da namiji a zuciyarta Wanda ba khalil ba...


Ahankali yakamo hannunta ya dawo da ita gefen umme dake kallonta cikin wani irin sabon yanayi ya zaunar da ita ahankali yace"


Amatu ga amanar ummi na ki kular min da ita amatsayinki na matar 'danta.


Dago jajayen idanuwanta tayi ta kallesa kafin ta kalli ummen ta daga Kai ahankali takasa cewa komai sai binsa takeyi da Ido zuciyarta na karban zazzafan baqon yanayi akansa Wanda ta tabbatarda sone me zafi.


Murmushi umme tasaki ahankali tareda kallon Amatun tana nuna Mata gefenta tace"


Kimin alqawarin zaki so shi fiyeda yanda yake sonki??


Murmushinsa me nutsuwa ya saki Yana kawar da zancen da cewa"


Umme wannan son Kaine zakice ta Soni fiyeda yanda nake sonta sbd bazata iya Sona yanda nake sontaba nawa me girma ne.


Murmushi sukayi Banda Amatu dake Jin wani babban al'amari me girma atareda ita hakanan taji gabaki daya nutsuwarta na barinta.




Haj maryam da Nuratu dasuka jima Bakin qofar palon suna jin dukkanin Abinda yafaru baqin ciki me girma yarufe zukatansu da idanuwansu musamman nuratu data gama zaucewa a fusace ta juya tana qoqarin sakin ihun baqin ciki da zuciyarta dake neman tarwatsewa da gudu Haj maryam tabi bayanta tana cewa''


Yau tunda Kika juyamin baya Aisha akan danki kowa ya shirya tashin hankalin dazai biyo daren Nan Dan wlh yau sai takardun asalin Amatu sun kwana a hannun Modibbo da Andi.
##mamuh#
6/17/21, 8:05 AM - ': *_MQ 27_*








Ko gabanta Bata gani ta qarasa sashensu tana qoqarin dafe qirjinta dake mugun zafi da radadi kamar zai tarwatse
Tana shiga palonsu ta zube qasa Kan gwiwowinta tareda fashewa da wani irin kuka me tsanani da zafin Rai,


Da sauri momynta ta qaraso ciki tana rikota tana Kiran sunanta cikin nata ciwon ran me tsanani da tausayin 'yarta tana sake kamota tace"


Nuratu please kada kiyi irin wannan kukan wlh karyamin zuciya zakiyi bazan iya ganinki cikin irin wannan halin ba Dan Allah kidaina kuka zamu samu mafita,
Bazan taba Bari Khalil ya auri wadda bake ba musamman wannan barauniyar karuwar yarinyar Dana Gama alwashin bazata taba aurensaba kodan yanda ya fifita sonta akanki.


Tsananta kukanta yayi tana girgiza Kai tana cewa''


Momy wlh inoson Khalil fiyeda yanda 'dan Adam zai iya lissafawa,
Zuciyata zafi takeyi sosai bazan iya kallonsa ya auri wata ba,
Gwara na mutu danaga wannan ranar.....


Da sauri momyn ta rufe Mata baki tana girgiza Mata Kai cikin tashin hankali tace"


Dan Allah Nuratu kidawo hayyacinki ki daina wainnan maganganun
Zan zamo Mana mafitarda zamu Kori Amatun daga rayuwarmu gaba daya da duk ahalin zabeera ma bama Khalil kadai ba.....


Dagowa nuratu tayi da idanuwanta dasukai jajir suna tsiyayo hawaye tana qoqarin fahimtar zancen momyn ta zabura da sauri tana tunowa da takardun data karbo hannun manager na kaf asalin Amatun harma da qarin rayuwar karuwanci datasa aka qara Mata akai,


Dakinta ta nufa kamar mahaukaciya ta nufi inda handbags dinta suke tahau wargazasu tana neman jakar da tasaka envelope cikin hauka,
Ganin yanda take wargaza Kaya yasa momyn saurin qarasowa tana sake riqota saigashi ta zaqulo jakar
Jikinta har rawa yakeyi ta bude ta dauko envelope din gaba cewa''


Momy yau Babu Abinda zai Hanani wulaqanta wulaqantacciyar rayuwarta,
Saina sakata kuka ninkin Wanda ta sakani tun zuwanta zabeera,
Ayau zata San asalin irin girman soyayyar Dana kewa Khalil.


Juyawa tayi ta fice tana share hawayenta dasuke sake bulbulowa cikin tsananin zafi da baqin cikin da zuciyarta ke ciki


Da gudu momy tabi bayanta tana Kiran sunanta sbd ayanda take yanzu ba acikin hayyacintaba komai lalacewa zaiyi Bata haka zasu tona asirin Amatun ba so takeyi harda umme ta fito cikin zancen....


A firgice ta biyo bayan Nuratun tana Kiran sunanta Amma tuni nuratun ta hada da gudu gudu tana sake sakin sabon kuka ta nufi sashen Andi inda tasan Modibbo nacan taredashi a daidai lokacin.


Ganin takasa cimma Nuratun data nufi hanyar sashen Andi yasa hankalinta mummunan tashi tuni ta firgice sbd wlh tasan Kwana zasuyi aciki Suma sbd zancen ba qaramin tashin hankali da masifu zai janyo ba,,,
Salman dake qoqarin parking yaga wucewar Nuratu da gudu gudu kamar tana kuka Yana qoqarin kashe motar ya fito saiga momynsu cikin sauri itama tanabin bayan Nuratun hankalinta amatuqar tashe daga ganinsu yasan ba lafiya ba bare ganin sunkama hanyar sashen Andi koma meyene to ya girmama dan duk Abinda yasa aka wuce Modibbo aka nufi Andi to da matsala babba.


Kashe motar yayi da sauri ya fito yana qoqarin bin bayansu saiga Dr khalil ya fito daga sashen ummen tareda Amatu da ummen zasu mayarda Amatu
Da sauri Khalil ya taresa ganin Yana Shirin gudu yace"


Lafiya likitan qashi???


Kallon hanyar Sashen Andin yayi cikin sauri sauri yace"


Inaga akwai matsala ne Naga Nuratu da momy sun nufi sashen Andi kowannensu Babu nutsuwa atare dashi Nuratu ma kamar kuka takeyi...


Juyowa yayi ya kalli khalil din cikin fargaba yace"


Ina Jin tsoron Abinda zaisa suje gurin anty musamman Nuratu nasan halinta da tsananin fushi da rashin tunani Wanda kowa yasan yawancin fushinta akan Abinda ya shafeka ne
Akwai Abinda yafaru yanzu a tsakaninku ne????




Dukkaninsu su ukun da sauri suka kallesa cikin wasi wasi da shakku


Da sauri umme ta kalli me aikinta dake fitowa dan kawo Mata wayarta dake ringin cikin sauri tace"


Shafa'atu Maryam da Nuratu sun shigo sashena bayan shigowar su Khalil????


Da sauri cikin tashin hankali duk suka zubawa shafar Ido jiran amsarta
Tace"
Eh da Kuna ciki sun shigo Amma.......


Bata qarasaba Salman ya juya da mugun gudu Yana cewa'"


Innalillahi-wainna ilaihirrajiun.....


Da sauri Dr khalil ya juyo ya kalli umme da zufa ya katse Mata ya kalli Amatu da tuni qafafunta suka Fara daukar rawar tashin hankali ya riqo hannuwansu duka su biyun cikin qoqarin bawa kansa nutsuwa Dan kwantar musu da hankali yace"


Umme duk tsanani karku Fadi asalin abinda yafaru na gskiar Abinda yafaru tsakaninku Kika kawo Amatu zabeera,
Amatu komai zai faru karki bude baki kiyi magana nine zanyi Magana ok???


Kallonsa umme tayi da sauri tana cewa''


Ta yaya Zan tsaya Ina kallonka ka dauki hukuncin Abinda bakaine kayiba...


Umme please kuyi kawai Abinda nace ku koma ciki Bari nabi bayansu tun kafin su Isa.


Da sauri yabi bayan su Yana share zufan goshinsa akaro na farko dayaji yanawa wani fatar faduwa ya Suma sbd Jin yake inama Nuratu kafin takai tafadi ta suma a hanya..


Kasa hakuri ummi tayi takasa komawa ciki ta tsaya gurin tana zarya cikin tsoro da fargabar Abinda zai biyo baya....




Bakin qofar shiga momy tayi nasarar damqe Nuratu da sauri tana sauke numfashin wahala da tashin hankali tace"


Nuratu kidawo hayyacinki kada kiyi Abinda masifarsa zata qare kanmu sbd wannan alamarin ba Abune me sauqi ba dazamu Bari Modibbo yaji daga garemu ba bare Andi
Maza kawo takardun Nan mukoma muyi Magana a nitse......


Qwacewa tayi tareda tura qofar palon zata shiga har lokacin kuka takeyi sosai tace"


Momy yau idan ban tona asirintaba duniya tasan ko ita wacece ba hankalina bazai taba kwanciyaba
So nake ta dandani 'dacin rabuwa da Abinda kakeso....


Fixgota Salman yayi da qarfi Yana qoqarin kwace envelope din ta fizge da qarfi tana cewa''


Kaima bayanta zakabi aci gaba da barin karuwa tana rayuwa acikin zabeera?
Me take Baku da duk mazan zabeera kuka haukace akanta??
Abinda take bawa sauran mazan waje........


Wani wawan Mari salman ya sauke Mata Wanda yasata haukacewa cikin tsananin firgici da masifa tace"


Wlh ka sake dasamin tsanarta me tsanani Koda Zan rasa Raina saina tabbatarda Andi da Modibbo sunsan karuwace ita,
Barauniya ce,
Yar bola ce,
Me aikin karuwanci a gidan abinci.......


Ba zata Marin dayafi na farko zafi da qara ya sauka akan inda Salman ya mareta
Wannan karon radadin yayi tsananin data kasa riqewa saidata zube a qasa ta dago ta kallesa idanuwanta na qarasa rinewa hawaye masu tsananin zafi da baqin ciki suna gangaro Mata murya na rawa tace"


Khalil duk akan wannan karuwar ce??


Cikin tsananin bacin Ran dabasu taba ganinsa aciki ba ya bude baki zaiyi Magana akai gyaran murya daga bakin qofar Shiga palon kusan duk atare suka juya cikin firgici da tashin hankali sukaga Andi ne da kansa a tsaye Modibbo na gefensa kowannensu kallo daya zakayi Masa kasan dukkanin fushi da bacin ransu a bayyane yake
Cikin nutsuwa Modibbo ya qaraso gaban Nuratu da itama tashiga firgici ya sanya hannu ya zari envelope din hannunta batareda yace qala ba ya juya yadawo gefen Andi Yana bude envelope din Wanda yasa tuni kowannensu ya shiga rawar jiki musamman momyn tuni ta durqushe qasa tan neman sakin kuka
Andi yayi wa gefenta kallo daya take ta hadiye kukan batareda yafitoba yakoma tana rawar jiki.






Duk inda tashin hankali da sanyin jiki yake Yana tareda Amatu da umme sbd kowannensu yakasa samun nutsuwa ta ja qafafunta dasukai nauyi ta nufi hanyar sashensu idanuwanta na sake kadawa bayan kumburin dasukayi na kukan data gama sha,


Tana shiga palon da anty zarah dake zaune tana qoqarin kiranta tayi saurin miqewa ta qaraso gabanta cikin tashin hankali da tsoro take Kiran sunanta tana tambayarta lafiya.


Kasa motsi tayi bare Magana sai kawai ta fashe da sabon kuka me shiga Rai tana zubewa qasa...


Innalillahi-wainna ilaihirrajiun" anty zarah ke maimaitawa tana zubewa qasan itama cikin tashin hankalin ganin irin kukan da Amatun keyi cikin rudu muryarta na rawa tace"


Amatu meya sameki kifadamin tun kafin kisa zuciyata fashewa itama Dan Allah,
Kukanki na bani tsoro tareda sani cikin tsananin firgici Dan Allah kiyimin mgn.....


Dagowa tayi ta kalli anty zarah din jajayen idanuwanta na tsiyayo da hawaye masu zafi tanajin tausayin kanta Dana zarah din sbd tasan lokacin rabuwarsu ne yazo,
Abinda Bata saniba shine zarah din zata tsaneta idan taji Abindake faruwa?
Koda zata tafi zatayiwa anty zarah adalcin fada Mata gskia da bakinta ko Dan zallar qaunarta gareta.


Wasu hawayen ne suka Kuma tsayayo Mata ta rintse ido zuciyarta na radadin Abinda zata fada ahankali tace"


Anty zarah ki gafarceni na zamo babbar butulu me mayarda alkhairi da cin Amana,
Na cutatar dake ta hanyar wahala akan Abinda Kika saka Rai da burika akansa,
Na hanaki bacci da sukuni gurin dawainiya Dani akan qarya yaudara...
Anty zarah banida ciki ajikina,
Bantaba daukar cikiba,
Bantaba sanin namijiba bare nayi Abinda zaisa nasamu ciki,
Dr khalil ba Mijina bane.........




Sakinta anty zarah din tayi cikin tsananin firgici da mamaki tayi baya tana zaman 'yan bori idanuwanta na silalo hawayen tsoro da karyewar zuciya ta Fara girgiza Kai tana son yin Magana takasa sai hawaye....


Anty zarah bantaba sanin a duniya akwai masu irin tsarkakakkiyar zuciya irin tasu kawu ba sai Dana hadu da Dr khalil dake da salman kuka kawo wani irin farin ciki da sanin mutuncin Kai arayuwata Amma Babu Abinda nakawo Muku sai yaudara da damuwa.....


Cikin rawar murya anty zarah dake rawar jiki gaba daya cikin firgici tace"


Idan duk Abinda Kika fada hakan ne to meya kawoki cikin rayuwarmu????


KUDI"""""tafada Kai tsaye tana sauke Kai hawayenta na qaruwa..


Son kudi da burin samunsu kota halin Yaya yasani shigowa rayuwarku
Saidai bayan haduwata daku na fahimci samun mutanen dake sonka da son farin cikinka tareda zama acikinsu shine asalin farin ciki da walwala Wanda kudi baya siya maka suba,
Anty zarah girmanki da qaunarki alqawarine da bazai taba gogewa azuciya da rayuwataba,
Anty zarah idan lokaci yayi Zan fada Miki gaskiyar duka Amma ayanzu iya Abinda Zan fada Miki kenan.




Miqewa tayi da sauri ganin irin hawayenda anty zarah din keyi tana bin cikinta da kallo burirrikanta akan cikin suna tarwatsewa daya Bayan daya,
Cikinda akai alqawarin Bata Abinda za'a Haifa Wanda tuni tafara kallon kanta amatsayin uwa Nanda lokacin qanqani.


Buga kofar da akayi da qarfine yasasu kallon kofar tun kafin su motsa aka sanarda saqone Andi nayiwa Amatu Kiran gaggawa.


Rintse idanuwanta tayi hawayen ciki suka gangaro ta juya ta nufi qofa.








A tsaitsaye suke Babu Wanda yasamu damar motsawa daga Inda yake sbd tashin hankali kusan mintuna suka share ahakan sbd shock dinda su Andi suka Shiga Bayan Gama sanin wacece Amatu dakuma irin qazamtacciyar rayuwar karuwancin datayi qarshe ta qare acikin zuria mafi tsafta da mutunci,


Umme da sauran manyan yaran Andi da Modibbo da tuni aka kirasu suka qaraso Babu wanda ya zauna duk tsaye suke cikin tashin hankali da jimanin abinda zai biyo Andi kawai ake jira yayi Magana.




Dagowa yayi cikin wani irin yanayi na tsanani yayiwa Khalil kallon dayasa kowa sake Shiga firgici cikin amo me firgitarwa yace"


Kowace tambay amsa daya nakeso,
Ka auri wannan yarinyar??


Aa,


Acikin takardan Nan anrubuta cewa
Ita din Mara asali ce,
Yar bola ce,
Karuwa ce,
Barauniya ce,
Gidajen abinci,hotels da gidan rawa take aiki,
Babu police station dinda batayi zamaba har gidan yari
Gaskia ne ko qaryane???????


Cikin tsananin firgici da tashin hankali muryarsa na rawa yace"


Gskia ne Amma Banda.......


Hannu Andi din ya daga Masa fuskarsa na nuna dukkanin fushinsa da bacin ransa.


Take yace kowa ya watse ya sallamesu ya juya yayi ciki 'yayansa na binsa abaya.


Kasa motsi kowa yayi sbd sanin abin bazaiyi kyauba.


Daga ciki kuwa kallon alhaji qarami yayi Kai tsaye yace"


Yarinyar da mariqanta a daukesu a rufe a central station dinda Khalil zaifi shekaru goma Yana nemansu baigansu ba a sanarda commissioner laifin datayi ta yanda zasusan girman laifin Bata sunan zabeera.
##Mamuh#
6/17/21, 8:05 AM - ': *_MQ 28_*






Cikin nutsuwa da girmamawa Modibbo ya kalli Andi a natse yace"


Kama yarinyar da mariqanta kamar su ba'a musu adalci ba sbd da yiyuwar qila bada masaniyarsu ta aikata hakanba kamar yanda shima Khalil Babu saninmu yaje ya kwaso Mana ita..


Tsit Sukayi kowa na kallon Andi da yanayinsa sbd maganar da Modibbon yayi ana jiran jin me andin zaice.


Zama batareda ya dagoba ya kallesu yace"


Alhaji qarami na damqa case din a hannunka a shigar da qara me qarfi akan yarinyar da mariqanta idan ka Gama binciko zancen gaskia ne ko aa akan laifin qage da shirin batawa zabeera suna ta hanyar qage akan cikin qarya,
Hakama asaka likitoci masu kyau suyi bincikenta aduba idan da akwai ciki a jikinta ko Babu,
Kada abari Khalil yasan inda aka Kai case din duk tsanani hakama MAHMOUD ZABEERA kada abari ko kadan yasan Abinda yake faruwa tunda baya Nan sbd acikin minti biyu zai iya saka agano wa Dan uwansa inda yarinyar take.


Cikin biyayya alhaji qaramin yace"


Angama Inshallah Andi.


Sahirtaccen numfashi Modibbo ya sauke zuciyarsa na daci da alamarin sbd baiso komai ya lalaceba.


Amatu na isowa sashen motar civil defense din na fakawa bakin qaton gate din ZABEERA
Alhaji qarami ne yafito daga palon ya kalli khalil yace"


Ka shiga ciki Andi na zaiyi magana da Kai.


Kasa motsawa yayi ya juya ya kalli Inda Amatu ke tsaye yanajin kunyar kansa daya Bari har suka tsintsi kansu a irin wannan Matsin dabai samo mafita ba tuna farko sukai aure tun kafin zuwan wannan ranar.


Kallonsa itama takeyi zuciyarta na sake karyewa da wannan masifar
Itadai komai tsananin hukunci da zafinsa zata dauka matuqar ba rabata za'ayi da Khalil din ba.


Sake maimata Masa alhaji qarami yayi Yana kallonsa cikin fushi Wanda yasashi dauke idanuwansa daga Kan Amatun yafara takawa ahankali ya nufi qofar palon yashige.


Yana shigewa alhaji qarami ya kalli Amatu dake tsayayo hawaye masu ciwo tanajin zuciyarta na sake karyewa ya nuna Mata hanya alamar suje.


Da sauri umme tayi gurinta tana qoqarin riqeta anty zarah data biyota tayi saurin rungumeta ta baya tana sake sabon kuka sbd su duka sun San matuqar aka tafi da Amatu ba lallai su Kuma ganinta arayuwarsu ba.


Daga umme har anty zarah din da Amatu kuka sukeyi sosai musamman umme datasan idan Amatu ta tafi rayuwar Khalil dinta na cikin hadarin rasata.


Haj maryam ma a katse take har lokacin sbd Basu Gama sanin inda Rana zata Fadi ba gashi dai Nuratun ma kuka takeyi sosai sbd wannan fitinar tasan shikenan Khalil bazai taba sonta ba yanda take fata komai yagama lalace Mata.


Matane su biyu da uniform dinsu na civil defense manya manya dasu kowacce tanaji qarfi da rashin Imani sbd Babu kalar bahaushiya acikinsu bare ace musulmai suna qarasowa alhaji qarami ya nuna musu Amatu sukayi kanta suka kana hannuwanta biyu suka Fara janta umme da anty zarah suka bisu abaya suna roqonsu cikin tsananin kuka Amma tuni suka wuce da ita,
Salman kuwa cikin palon yayi da sauri ko sallama baiyiba ya tsaya gabansu Andi ya kalli khalil dake sunkuye da Kai yace"


Dan Allah Andi a sassauta Amatu a tsaya a fahimci zancen ta hanyar nutsuwa mace ce ita wlh rayuwarta zasu lalata idan aka Bari suka tafi da ita aka kulleta Dan Allah....


Da sauri Khalil ya juyo ya kalli Salman din cikin tsananin firgici bai tsaya gama sauraren Abinda yake fadaba ya turesa ya fice da gudu ko gabansa baya gani.....


Ba Andi kadaiba hatta Modibbo Saida ya kidima da wannan alamarin,
Yaransu da Basu taba dago Kai sun kallesuba idan suna musu Magana,
Yaransu da Babu Abinda suka sani arayuwa bayan yimusu biyayya da bin umarninsu Koda baiyi musu daidaiba Amma ayau akan mace kamar abinda sukai shekaru suna Dora 'yayansu akai na neman rushewa,
Yau Andi da kansa Yana zaune ake tafiya abarsa yana magana hakama shima wannan yau shi Andi da kansa yake kalla Yana cewa ba'ayi Abinda yakamata ba....da matsala,da matsala babba ma kuwa.




Juyawa Salman yayi yabi bayan Khalil Yana fasa maganar da yayi niya cikin 'dacin Rai idanuwansa na sake sauyawa.


Koda suka Isa bakin qofar zabeera tuni aka wuce da Amatun motar alhaji qarami nabin bayansu.


Cikin tsananin tashin hankali Khalil ke qoqarin bin motar da gudu da qafafunsa Salman yayi saurin riqesa Amma ya fizge yabi motar da gudu Salman da umme na kiransa cikin tashin hankali umme ke cewa''


Salman dauko mota da sauri kabisa idan yayi gudu ciwonsa zai tashi Dan Allah kabisa kada kabari komai yasamu Khalil shikadai nakedashi.


Ciki yakoma cikin sauri jikinsa har rawa yakeyi yafada mota yajawo da gudu yabi Bayan Khalil din.


Koda ya cimmasa harya Fara galabaita numfashinsa yafara sarqewa.
Da sauri ya tsayar da motar ya fito yakamasa yasaka motar ya zagayo ya shiga Yana qara Masa sanyin AC din motar Yana janyo tissue da yawa ya miqa Masa yana qoqarin daidaita muryarsa yace"


Dr kada kayi Abinda zai kaika kwance sbd kana buqatar tsayuwa da qafafunka gurin fitarda Amatu cikin wannan matsalar.


Kasa Magana Dr khalil din yayi Yana fitarda numfashi cikin yanayi na azaba ya lumshe idanuwansa dasukayi jajir ahankali yace"


Muje gidansu kawu Ina buqatan daukesu daga gidan yanzu.


Hanyar gidan suka kama Yana tuqi Yana kallon Khalil din daketa fama da numfashinsa Dan daidaitawa kada yabari yaci qarfinsa.


Koda suka Isa Salman ne ya bude Masa motar yafito Yana sake qoqarin daidaita numfashinsa ya share zufansa suka nufi cikin gidan.


Zaune kawu yake Yana sauraron radio iyami na zaune gefensa tana shafawa qafarta daya Jan lalle sai gasu sunshigo da qaramar sallama suka qaraso iyami na ganinsu ta ajiye lallen datake qoqarin sawa dayar qafar tana musu maraba da zuwa duk da dai yanayinsu yasata fargaba musamman sbd zufan da kowannensu yaketa sharewa bama kamar Dr daketa fama da numfashinsa Yana dannewa sbd kada agane halinda yake ciki.


Kallo daya kawu yayi musu yasan ba lafiya ba
Ya tashi zaune daga kishingiden dayake ya janyo radionsa kusa ya qure murya sbd kada aji zancen dazasuyi ya kalli khalil daya zauna gefensa yace"


Likita lafiya naganku kamar 'yan saqon mutuwa???
Salmanu lafiya kuwa??


Numfashi Dr ya sauke Yana lumshe ido sbd azabar dayake ji ya kalli kawun cikin taushin murya yace"


Kawu zanyi maka bayanin abindake faruwa Amma Dan Allah yanzu inason ku biyoni muje wani guri muyi maganar.


Kallon juna kawu da iyami sukayi suka sake maido da kallonsu kansa cikin rawar murya iyami tace"


Akwai Abinda yasamu Amatu ne?
Meya faru ne kafara fada Mana mu musulmaine zamu dauki qaddara koma menene.


Ajiyar zuciya salman ya sauke cikin sake bawa kansa nutsuwa yace"


Ba Abinda kike tunani bane iyami Amma dai yanzu muna buqatar barin Nan ne tukuna.


Kallon Dr khalil kawu yayi da kyau kafin ya miqe Yana cewa'


Iyami sanyo hijabinki muje na yarda da Khalil fiyeda kowa arayuwata Dan haka koma menene Yana mahimmanci barin Nan din tun sun fada.


Jiki mace iyami ta miqe ta wanke qafa dayar dakeda lalle ta fada daki ta sanyo hijabi hannuwanta na rawa sbd hakanan takejin tashin hankali tun kafin suji koma menene yake faruwa.


Babu Wanda suka fadawa suka rufe dakunansu suka fice.


A mota Dr khalil yakira babban yaronsa na asibiti Ibrahim ya sanar dashi Yana buqatar gidansa daya Gama be tare ba na kwana biyu,
Cikin sauri yace angama likita.




Anguwar can take nesa kusan hanyar wajen gari

Please Login or Register in order to submit comment