You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

yagama Abinda zaiyi tafiya zaiyima.


Babu Abinda ta tsana kamar kai abinci a aikinnan nasu tafison abarta a hadawa suna dauka suna kaiwa sbd idan tana ganin masu kudi burinta sake hauhawa yakeyi.


Tsaki tasaki ta dauke baki ta dauka tana tafe tana qananun tsoki tana Harare harare.


VIP dinsu Yana can sama Saida tagama tsinewa manager ko kafin takai saman daukeda tray din.


Saida ta tsaya ta huta kafin ta nufi VIP 3 din tana isa security din dake gurin ya tura mata qofar gurin yana washe mata baki sbd mutuniyarsace ba ruwanta lafiyayyan takeaway take Masa idan zasu tashi shiyasa kowa gurin yake yinta Dan babu ruwanta bayarwa takeyi shiyasa lissafin nasu yanxu gurin kullum cikin rudarwa yake tunda aka dauketa aiki gurin.


Tana shiga ta tsaya cak tareda lumshe ido tasaki wata irin ajiyar zuciya afili tace'"


Hummmmm masu kudi turarensu ma qamshinsa na dabam ne,
Ya Allah ga amah da usi.


Bude ido tayi ahankali daidai wayarsa na daukar ringin batareda ya juyoba ya sanya dogon hannunsa da fatarsa ke sheqin hutu da haske ya dauki wayar tareda miqewa ya nufi window ya Dora wayar a kunne batareda yace komaiba.


Zare idanuwanta dake neman rufewa su suma tayi tana girgiza kanta ahankali tace'"


Ya Allah.


Table ta nufa ta ajiye tray din idanuwanta suka sauka kan wallet dinsa dake ajiye da kudi acike acikinta batasan lokacinda tayi saurin dire tray din ta dauki wallet din ta bude taba zaro ido tace"


Yau ranar sa'atace ya Allah nagode maka.


Kudin ta zaro gabaki daya tana musu kallon qurilla fuskarta cikeda farin ciki tace'


Kayi hakuri Dan balarabe Amma nafika buqatan kudin Nan.


Aje wallet din tayi ta juya da sauri cikin farin ciki tana damqe kudin ta fice tana sauri Dan karya gama waya ya juyo yaga ba kudinsa ya biyota yace kudinsa zai qwata itakuma bazata bayarba.


Ta glass din window dayake tsaye yake kallonta cikeda tsananin mamaki da qyamar halinta daya sanyashi kasa juyowa akaro na farko dayaga mace da irin wannan halin mafi Muni agaresa Wanda hakan yasahi kashe wayar wadda tunda ya daga baice komai sai sauraren zancen da ake Masa tacan Wanda kusan hakan dabi'arsa ce.
#mamuh#


#MIN QALB❤️
Mamuhgee


ZAFAFA BIAYAR


SIRADIN RAYUWA
safiyya huguma


MIN QALB
mamuhgee


YANKAN BAYA
billyn Abdul


KIBIYAR AJALI
Miss xoxo


ABINDAKE CIKIN ZUCIYATA
hafsat rano


Pay @09033181070
Or 09032345899
6/17/21, 8:01 AM - ': _*MIN QALB*_
_Mamuhgee_


2


Bazai iya ganiba
sunaji suna gani qaton saurayin yake kokarin keta rayuwarta dabata gama sanin ciwon kantaba,
Ita kukan datakeyi dannewar dayayi Mata akan duwatsu suna cin jikinta
Shikuma Usman kukan zabar dayasha yake tunowa itace zaayiwa amatu Wanda sanadin hakan sunzama 6arayi dole da qarfi da yaji.


Qoqrin bude qafafuwanta qaton keyi
Usman yayi wani yunkuri tareda kama hannun Wanda ke maqure dashi ya sakar Masa mugun cizo Mai qarfi da haqoransa dasuka gama bushewa da dau'da.


A gigice yasakesa Yana yarfe hannu sbd azabar cizon.


Wani qaton dustsi Usman din yadauka baiyi wata wata ba ya buga akan qaton dake kan amatu
Take ya sulale gefe kansa na tartsin jini sosai ko ihu daya beyiba ya zube agurin Yana wani irin Shure Shure.


Suna ganin hakan wani irin tsoro yashigesu da gudu ya kamo hannun amatu Yana cewa'"


Zo mu gudu amatu.


A firgice dayan ya riqesu Yana cewa'"


Kun kasheshi....a kidime yake fadar hakan cikin tsananin tsoron ganin abokinsa na Shure shuren mutuwa.


Qoqarin jansu yakeyi Yana cewa'"


Wlh police zan kaiku Kun kashesa,
Bazaki guduba ku barni cikin masifa akamani.


Jansu yakeyi da qarfi cikin firgici da tashin hankali suna kuka sosai suna rokonsa ya sakesu Amma Shima a rude yake kansa zai wanke kota halin Yaya.


Irin kukan dasukeyi Basu taba yinsaba arayuwarsu sbd jin wani ya mutu sbd su Kuma Suma kashesu dayan sukaji yanacewa zaayi.


Sosai suke kuka suna rokonsa ya sakesu Amma ko jinsu bayayi Dan Shima kusan kukan yakeyi na tsoro da firgici.


Wata qatuwar gora daga bayansu aka kwadawa qaton a tsakiyar Kai
Ya tsaya cak tareda sakin hannuwansu Yana qoqarin juyawa yaga ko waye ya yanke jiki yafadi jini nafita a qeyar kansa.


Jikinsu na rawa cikin tsananin tsoro da firgici suka juyo suna qanqame hannuwan junansu tareda ja baya suna kallon qaton dashima yake Shure Shure.


Cikin sauri megadin makarantar ya matso gabansu tareda riqo hannuwansu yasaka musu kudi Yana waige waige Yace"


Kuyi gudu sosai kuje can qasan layin gaban kasuwar baya akwai makarantar almajirai ku shige cikinsu ku kwanta ku boye zanzo idan ankwana biyu
Kuyi sauri karku taba dawowa tanan
Kuyi sauri kuje..


Kallonsa sukeyi suna sake sakin sabon kuka sbd sunqara firgicewa da Abinda yake fada,


Yaturasu Yana cewa'"


Kuje kuje kuyi sauri karku dawo.


Gudu suka Fara suna waiwayensa sbd akaro na farko da wani ya taimakesu arayuwarsu.


Tun suna waiwayensa harsuka bace suna gudu cikin Daren gashi yace karsu hau titi subi kwana kwana.


Koda suka Kai makarantar almajiran dare yayi sosai gashi karnika sai haushi suke musu duk inda sukabi.


Suna kaiwa bakin makarantar suka tsaya suna rarraba idon Ina zasu boye sbd almajiran gasunan kwance birjik a fili kowa da matacciyar tabarmarsa wasu Kuma da kwalaye wasuma hakanan suke kwance a qasa ga cinnakai da qwari da komai Amma ba ruwansu kwance suke abinsu suna bacci.


Hanunta usman yakama suka qarasa can qarshe yacire matacciyar rigar jikinsa data gama yagewa ta mutu ya shimfida musu suka kwanta kowannensu jikinsa na rawa numfashinsu na fita da sauri sbd tsananin tsoron dasuke ciki.


Asubar fari dukkanin almajiran aka tadasu suyi sallah
Wanda wannan shine karo na farko dasuka tabayin sallah Shima Suma dai sunyi yanda sukaga kowa nayi gurin bin Abinda malam yayi.


Ana gama sallah kowa yadauko allonsa Yana bita.


Gari yafara haske sai sukaga almajiran na kallon amatu cikin mamaki suna kallon kanta Wanda gashinta ke butu butu da dau'da da qazanta Wanda yake son nuna ita mace ce.


Daga dama sukaji wani almajiri yace"


Kai wallahi idan malam yazo yaga mace dukanku zaiyi wayace mace tana zuwa Nan?hmm
Korarki ma malam zaiyi yanzu Yana fitowa.


Usman najin kora ya kama hannunta suka miqe anabinsu da kallo suka fice a sanyaye.


Harsunyi nisa kadan yatuno da maganar kawu megadi na cewa karsu koma yayi saurin juyawa da ita Yana kalle kallen inda zasu fake Kuma.


Ganin har yamma tayi suna gararin gurin zuwa yasa ya lalubo kudinda kawun yabasu yaje shagon dake kallon inda suke yasiyo Rezar nera ashirin yadawo yajata suka zagaya bayan wani gida Yana cewa'"


Amatu zo muyi aski irin nasu almajiran malam saimu koma cikinsu tunda bamuda wani gurin.


Haka ta zauna yahau yimata aski
Saida ya aske kan tas Wanda duk kusan Rabin kan ya yayyakenta sai jini ke fita kadan kadan Amma Sam Basu damuba Shima sama sama yayi nasa askin rabi yayi rabi beyiba suka dunkule Rezar sbd gaba suka koma makarantar dama kayan jikinsu duk riga da wandone dasuka gama yayyagewa suka sauya kamanni.


Dayake makarantar ba qa'ida sukebi ba take malam ya kaebesu yaga sabbin alamjirai aka Basu tsoffin allon karatu take suka shiga sahun almajirai batareda kowa yasan cewa amatun mace ceba Koda malam ya tambayi sunayensu sukace Usman da amadu.


Ahankali suka Saba da rayuwar almajiranci duk da akwai wuya Amma tafi musu rayuwarsu ta baya dansu yanzu ganin sukeyi sunyi gata.


Akai akai Usman kemata aski sbd kar gashinta yafito musamman sbd tanada saurin tsirowar gashin,


Sunsaba idan sungama ayyukan gidan malam akayi karatu aka gama su fita yawon bara sai yamma sudawo karatun yamma sannan sufita barar dare daga Nan Kuma dare nayi zuzo su kwanta.


Yanzu suna samun yin wanka a sati ko so dayane shiyasa suka Dan Fara canzawa.


Tun suna qirgen kwanakin zuwan kawu megadi harsuka daina suka koma qirgen kwanakin zuwansu har lissafi ya batar musu.


Ko ayanxu dasuke cikin inuwar almajiranci abun dai 'dayane shine idan baka tsayawa kankaba Kaine a qasa ko yaushe,


Sunsha gwagwarmaya zamansu makarantar malam din,


Idan anyi sata su ake maqalawa,
Barna sune,
Laifi sune,
Hatta laifin cikin gidan malam su ake maqalawa shiyasa sunfi kowa azabtuwa sbd irin dukan da malam da ya manyan yaransa suke musu,


Shatin buloli ajikinsu yazama tamkar zanen fatarda aka haliccesu da itane,


Tun suna kuka a almari harsun qame sun daina sbd ganin rayuwar ahaka take koina na sama ya danne na qasan.


Duk hutunda akeyi sukam basa zuwa koina sbd basuda gurin zuwa shiyasa rashin tausayinsu yafi yawa sbd ansan ko an zalincesu basuda me tsaya musu.


Ahaka dai rayuwa taja tsananin rayuwa Yana qara musu yawa musamman yanxu da amatu take Fara nonuwa kullum cikin boye boye suke gashi yanxu abubuwan naqara tsanantar musu ne gashi amatu ko mgn batayi sosai da qarfi da yaji suke boyon mganarta kar agano mace ce.


Yanxu dasukayj wayo Usman shine me wahalar Abinda zasu ci duk da tare suke zuwa duk inda zasu gashi baqin jini tamkar a jininsu yake sbd duk inda sukaje tsanarsu da kyararsu akeyi shiyasa suka riqe aransu duniya kowa kansa kawai yasani basuda Abinda yafi musu junansu.


Wani hutu da akayi kamar daga sama saiga kawu megadi Wanda tuni suka Fara mantawa da kamanninsa,


Farin ciki da murnar dasukayi kamar shine danginsu da basuda musamman dasukaga yazo musu da gari kusan kwano buyi jikinsu har rawa yakeyi gurin yimasa godiya.


Amatu ya qurawa ido musamman kanta dake aske tas Yana qyalli ga wasu qananun quraje a jikinsu zuciyarsa na susa yaji dukkanin kuzarinsa ya karye sbd tabbas duk da baitaba haihuwaba ita 'ya mace ce bazaa jima ana boyeta ba amatsayin namiji.


Dazai tafi yasiya musu gwanjo kowannensu riga da wando masu Dan dama dama.


Tun daga lokacin yake Dan zuwa akai akai Yana dubasu sai rayuwar tadan Fara yimusu sauqi.


Awani zuwa da yayi
Baizo da niyar tafiya dasuba Amma atake tunaninsa ya sauya akan amatu sbd girma daya Fara zuwar Mata gadan gadan Yana tsoron amatsayinta na mace ta abalage acikin maza.


kallonsu yayi bayan sun zagayo bayan makarantar cikin karyewar zuciya Yana jinjina rabasun dazaiyi yace"


Usman kaga amatu tafara girma akwai hadari abarta cikinku anan..


Kallonsa sukayi atare cikin rashin fahimta.


Gyara tsayuwa yayi yace zantafi da ita zan kaita gurin me 'dakina idan yaso Kai saika riqa zuwa Mana hutu.


Atare suka girgiza Kai itada Usman din suna kallon juna idanuwansu na cikowa da hawaye.


Nasan zaa rina yafada cikin ransa Yana kallonsu zuciya a karye.


Kamo hanun Usman yayi yajasa gefe ya fahimtar dashi sosai ta yanda zai gane Abinda yake nufi
Harya gane Yakuma amince sbd har abada bazaiso Abinda zai samu amatu ba.


Daga haka suka hakura sunaji suna gani suka rabu da juna kawu yatafi da su kafin daga baya Usman yadawo makarantar malam.


Tunda amatu tadawo gidan kawu Bata taba haduwa da tsangwama ba saidai Kuma babuwa wani janta ajiki da iyami tayi.


Basuda qarfi sai rufin asiri da haka malam yasakata primary school dinda yake gadi wadda tuni aka maidata 'yar maigadi.


Usman shekara daya yayi batareda itaba ya tattara karatun yadawo gidan kawu Yana kwana a soro komai tsananin sanyi da zafi kuwa.


A haka kawu yasamar Masa aikin tsaron gidan wanka da bahaya a Tasha har Shima yashiga primary 2
Yana shiga primary 5 ya tattara karatun ya ajiye sbd gwagwarmayar rayuwa.


Kawu da iyami sune gatansu na farko,
Kawu da iyami sune wainda suka cirosu daga bola suka basu sunanda ake kallonsu da daraja ayanzu.


Shekakarda tashiga js 2 a shekarar suka shiga wata sabuwar masifar da akayiwa kawu sharrin satar cire winduna da qofofin makaranta ya siyar.


Duk inda ake zuwa roqo da Kai kuka sunkai akan alamarin Amma Abu ya agagara qarshe dpo nunawa yayi sai idan ita amatu kokuma matar kawun zasu kwana dashi tukuna zai taimakesu.


Akaro na farko da amatu ta tsani maza da taimakonsu.


Ranar dukkaninsu kwana sukayi kukan baqin ciki sunaji suna gani akayi gidan yari da kawu hukuncin shekara biyu dama Kuma abin hadda gayya sbd Shima alqali yaso amatun tabasa hadin Kai sbd irin wankewa da jikinta yayi gashi fatarta Ashe me irin hasken Nan ce ga jikinta daya gama fitowa ana mace tsaf yanzu iyakaci qarasa balagewa ne dabatayiba a cikakkiyar mace.


Tunda akayi gidan yari da kawu alamarin duniya yasakosu gaba ko abincinda zasuci ya gagaresu dole Usman ne yanaji Yana gani yake fita gwagwarmaya Amma sai ahankali.


Wata bakwai da zuwan kawu gidan yari aka koresu daga gidan dasuke suka rasa gurin zuwa ga iyami Dan cikinsa take dauke dashi wahala tasaka ya bare ko kudin asibiti basuda.


Akaro na farko da Usman yakoma sata kenan arayuwarsa ya kama musu daki buyi a wani gidan haya me dakuna goma reras a jere kamar shaguna,
Gidanda ya hada mutane dabam dabam masu halaye dabam dabam.
#mamuh#


MIN QALB❤️
Mamuhgee


ZAFAFA BIAYAR


SIRADIN RAYUWA
safiyya huguma


MIN QALB
mamuhgee


YANKAN BAYA
billyn Abdul


KIBIYAR AJALI
Miss xoxo


ABINDAKE CIKIN ZUCIYATA
hafsat rano


Pay @09033181070
Or 09032345899
6/17/21, 8:02 AM - ': *_MIN QALB 4_*
_Mamuhgee_




#ZAFAFA BIYAR#PAY@+234 903 234 5899 OR 09033181070




Tana fitowa dakin ta washe baki tareda daga kudin ta kallesu tana fitar fuskarta dasu tace"


Hmmm amah zakiyi kudi ki mallaki uwayen wainnan kiyi rayuwa yanda kikeso ki juya Wanda kikeso hhhh.


Kallon hashimu me tsaron qofar tayi tareda sakar Masa murmushin iko na nuna Masa itace agabansa tunda ita ke riqeda kudi,


Sake juyasu tayi tareda zaro Yan naira dubu 'daya 'daya guda uku tabasa tana cewa'"


Kana fadar Abinda yafaru yanxu to sunan aurenka matacce dan wlh sainaje nasa anhana.


Damqar kudin yayi da sauri Yana turawa cikin aljihu tareda washe bakinsa har iyaka yace"


Haba Hajiya amah kema kinsan hakan bazaitaba faruwaba,
Ko bomb akamin belt dashi bazan fadaba.


Dariya tasaki cikin girmama alamari da mutunci irin na kudi Wanda yasa hashimu fadar haka akan dubu uku kacal ma,
Sake kallonsu tayi tana dagawa tace"


Allah sarki kudi,
Kudi muna sonku
Bama gane kowane yare sai naku.


Juyawa tayi tana cusasu cikin wandon jeans dinta dake cikin doguwar jallabiyarta tana cewa'"


Hashimu bakinka qanin kafarka.


Kallon tray din tea dinda takawo yayi yanason kallonsa amatsayin tsarkakken Abu Amma apatite dinsa yakasa dauka take yaji gurin gabaki daya yafita aransa ya kwashi wayoyinsa da wallet dinsa ya fito ya fice batareda ya kalli ko gefenda Hashimu ke Masa asauka lafiya ba.


Tana saukowa ta sauya kayan aiki ta zari Jakarta ko sallama batayiwa manager ba sbd gabaki daya hankalinta yatafi a station sbd tasan usi nacan najiranta.


Adaidaita ta tsayar ta fada tana cemasa'


Central police station zaka kaini.


Bayan ta zauna cikin napep din ta zaro kudin daga aljihun jeans dinta ta qirgasu dubu ashirin da bakwai ne kenan hadida dubu ukun data bawa hashimu dubu talatin kenan,
Hmmm lallai wannan daga gani me kudine yau badan belin usi ba da kamawa kawu shago zatayi yafara Sanaa Koda ta awon su gero ne da gari.


Daidai gate din central din aka ajiyeta ta sallami me adaidaita din ta kalli gate din station din tana Jan siririn tsaki cikin quluwa tace'"


Tabbas da munada arziki da nafi qarfin zuwa gurin Nan Ina mace,
Amma haka qaddara tazomin inaga stations din jahar Nan Babu Wanda bana zuwa sbd irin haka.


Sauke numfashi ma qarfi tayi tareda Jan iska tana cewa'"


Amah bakida Wanda yadamu da mutuncinki Dan haka ki daina kawo tunanin komai bayan na maida hankali ki Gina rayuwarki cikin jin Dadi batareda kinsa damuwar komai ko kowaba arai.


Rataya qaramar Jakarta tayi tana nufar hanyar shiga tana karewa 'yan iskan kurtun police 'din dake binta da kallon qurulla saidai dayake sunfi kowa sanin waye ita yasa suka kama kansu sbd tsira da 'yan canjin dake aljihunansu sbd Suma a qone suke murus ba canji.


Kamar daga sama insfector Garba ya ganta tashigo fuskarta a daure.


Dan hadiye yawu yayi tareda shafa aljihunsa ya lalubo Yan kudadensa kusan dubu shida ya hadiye yawun qaqa nikayi sbd gskia yanason amah Amma Kuma duk lokacinda ya kusantota saita sanfesa tas har mamaki yakeyi yanda take zaresu bai saniba baikuma ganiba yanda kasan me aiki da aljanu haka take.


Togewa tayi bakin kanta tana sake tsuke fuska ta kalli wainda suke incharge tace"


Gurin USI nazo.


'Dayan dayake qule da ita tun wani zuwa datayi belin Dan uwanta ta samfe Masa dubu hudu yake haqe da ita Danma fitinanniyar Bata tabuwa sbd ogansu daya gama mutuwa kanta tana kassarasa Amma qaton banxan yakasa bude ido ya fahimci Babu Abinda amah keso arayuwarta idanba kudi da Dan uwanta usi ba sai kawu.


Saida suka gama harare hararen juna kafin aka fiddo da Usi din aka Fara rubuce rubuce akace dubu gama sha biyar zata bayar.


Bude jaka tayi taciro kudin batareda tace musu komaiba ta miqa musu tana yiwa kudin kallon bankwana cikin ranta tace'"


Insfector Garba Kaine wlh zaka biya tunda kanaji kana gani suka kama usi akan sunyi fada da wani Dan masu kudi shine shi USI aka kamasa.


Insfector Garba na ganin irin kallon datayi Masa ya fada office dinsa Yana zare dukkan kudadensa daga aljihunansa Yana turawa qarqashin lokar office dinsa Yana zazzare idanuwa sbd gskia yau bai shirya daukar asara ba.


Kallon usi tayi zuciyarta na qunar ganin yanayinsa daga gani uban duka suka Mai suka cire haushinta Dan tasan kowannensu a qule yake da ita.


Wata baqar €class0221 ce tashigo station din tayi parking atake duk suka ajiye Abinda sukeyi jikinsu na rawa suka miqe suna fadin'
MD ZABEERA ya iso.


insfector Garba ne yafito Yana cewa'"


Sargent salisu kufito da yaron Nan Wanda MD ZABEERA yakira yayi mgn akai Wanda sukayi fada da USI.


Yes sir"


Da gudu suka fiddosa tsaf dashi ba alamar antabasa ko kayan jikinsa fes suke.


Kallonsa tayi cikin mamaki jin shine abokin fadan usi atake taji haushinsu duk ya kamata ta kalli usi dayasha mugun duka tace'"


Usi uban waye yayi maka wannan dukan?
Ga abokin fadanka nan Babu alamar ko hararsa anyi bare duka.,


Wlh yau saina daukaka qara a kotu akan wannan abin......


Saurin katseta insfector Garba yayi sbd shigowar MD ZABEERA din Wanda qamshinsa yagama kame iskar gurin gabaki daya.


Batareda tajuyoba tace"


Bazanyi shiruba kodai abi Mana haqqinmu kokuma naje kotu wlh bazan yardaba...


Murmushin yaqe insfector Garba yasaki Yana dan satar kallon gefen MD din yace"


Kinga Dan uwanki shine baida gskia shiyasa Kuma Kinga......


Waro manyan idanuwanta tayi akansa cikeda mamaki tana cewa'"


Ni kake fadawa usi ne baida gskia??
To wlh ma nafasa auren naka daga yau ko sunan anguwar mu kakira Garba Allah saina raba aurenka da matarka me kamada bokiti.


Shiru dukkaninsu gurin sukayi musamman insfector Garba din sbd dai duk tagama bude Masa yawa agaban MD ZABEERA Wanda babban mutum da kowa ke matuqar respecting da matuqar karramawa sbd arzikinsa da mugun Jan girma da ajinsa bawai Kuma Dan shekarunsaba sbd duka duka shekarunsa bazasu fi talatin da buyar zuwa da shida ba aduniya,


Yarone Wanda ake Kira da abokin manya sbd dukkanin abokanan hurdarsa manyane wainda wasu sun haifesa,wasu sunyi jika dashi wasuma sun kusa haihuwar tasa,
A familyn daya fito su din wani babban family ne dasuke da girma da mutunci a idon duniya sbd kamannin kakaninsa da uwayensa Amma a yanzu kusan Rabin qarin girma da mutuntawar dasuke qara samu sbd shine shiyasa ko acikin familyn nasa wainda basa qaunarsa suka fi yawa.


Kasancewarsa baida hayaniya da son shiga sabgoginda Basu shafi Abinda yake gabansaba yasa yake qara shiga ran abokanan harqallarsa Kuma hakan naqara Masa girma shiyasa koina yashiga ake matuqar mutuntasa musamman dayake yana mallakar wata irin tarin dukiyarda ta tsolewa mutane da yawa ido.


Batareda yatsaya bi takan hayaniyarsuba ya kalli insfector Garba da idanuwansa dake cikeda da wani irin kwarjini
Atake jiki na rawa insfector Garba yace"


Ranka ya Dade Bismillah muje daga cikin office din"Â yaqarasa fada Yana basa hanyar shiga office din
Su Sargent suka Mara masu baya tareda yaron dayazo belin.


Wannan shine karo na farko arayuwarsa daya taba zuwa police station Dan haka bai tsaya Bata lokaciba ya kalli insfector Garba akaro na biyu cikin qosawa da zamansa cikin station din dayakejin kansa harya Fara juyawa ya bude baki cikin nutsuwarsa da kamewarsa datasasu Suma duk shiga nutsuwa yace"


Meye procedures din????


Da sauri insfector Garba yace"


Ba wani procedure sir just take him with u dama mun kamasane abisa rashin sani yanzu da safen Nan labari yazo Mana aishi din yaron amintaccen direbankane Wanda ka dauka kamar uba,
Muma ai tamkar ubane agurinmu
Ayi hakuri sir munsaka babban mutum kamarka zuwa Nan.


Zuba Masa fararen idanuwansa masu sake rikitarda Insfector Garba yayi Yana nazartar yanda mutanen duniya suke,
Wato Babu wata doka ko adalci shidai me kudi akoyaushe shine me gskia komai yayi daidai ne wat a life.


Miqewa yayi tareda kallon mal aminu dayake kallon 'dansa cikin rauni da takaicin yau sune sukayi sanadin zuwan mutum me matuqar girma da mutunci kamar MAHMOUD DAHEER ZABEERA a irin nan,
Shi mutum ne daya tsani mutanenda suka dauki kudi sune rayuwa
Saigashi a hukuma ma kudin sune dai aka fifita.


Ganin duk sun shige office din insfector Garba dayake shine DPO din Nan dama ana kiransane insfector sbd sunan yabisa tuntuni,
Ta kalli usi da isonsa daya harya kusa liqewa sbd kumburin duka tace'"


To da mutum ya mutu dai gwara yazama biri
Dan haka da Babu gwara ba Dadi tunda sum ringa sun maka wannan dukan gurinsu zamu samu na siyan magani" ta qarasa fada tana zagayowa inda suka saka kudinda suka karba hannunta aikuwa cikin saa taga kudin aikin ranar gaba daya
wani mugun murmushi tasaki tareda Kai hannu ta kwashe kudin gaba daya Wanda yayi daidai da fitowor MD zabeera cikin office din dpo Garba.
#mamuh#


Pay@
+234 903 234 5899
Or
09033181070
6/17/21, 8:02 AM - ': *_MIN QALB 5_*
_Mamuhgee_




##Zafafa biyar#pay@ 09033181070 or 09032345899


Usi ne yafara ankarewa dashi yaga yanda qarara idanuwansa da fuskarsa suka nuna tsananin qyama da takaicin Abinda idanuwansa suka gane Masa Nan ya fahimci cewar yarigada ya ganta yayi saurin dauke idanuwansa dga kallonsa yayi sbd tsananin kwarjini da cika masa ido da yayi yai saurin yin qasa da murya Yana cewa'"


Amah kiyi saurin barin Nan kokuma ki maida kudin.


Batareda ta fahimci Abinda yafadaba ta kallesa tana cewa'' oya yi sauri mutafi nagama ramawa kura aniyarta anan,
Insfector Garba Kuma zaizo yasameni a gida nasani acan zan fanshe wannan tozarcin dayamin agaban baqonsu da ko kallo bai isheniba bare na tsaya harsu gama kulasaba kafin su dawo kanmu.


Gaba tayi tana zuge zip din Jakarta data saka kudin usi na biyeda ita Yana satar waiwayen baqon dake bayansu fuskarsa a hade ko inda suke bai kallaba ua nufi motarsa Yana duba agogonsa dake nuna Masa lokacin ganawarsa da mahaifinsu yayi gashi shi mutum ne dayake aiki da lokaci komai lokacinsa yake ware Masa sbd tsari dayayiwa rayuwarsa.


Amah ko takan babbar motarsa batabi ba sbd gama quluwa datayi da Abinda Garba yayi Mata.


Usman kuwa suna fitowa tafiya kadan sukayi yaja ya tsaya jikin wata bishiya Yana sauke ajiyar zuciya ya zauna Yana jingina kansa jikin icen ya sake sauke numfashi ya kalleta yana sakin 'yar dariya kamar Babu rauni da tsamin duka a jikinsa yace"


Amah kina ganin akwai ranarda zamuyi rayuwa kamar sauran mutane masu daraja???


murmushi itama ta saki tana kallonsa cikin kulawa da rashin nuna damuwa kafin ta bude Jakarta ta shafo kudin dake ciki tana kallonsu tace"


Bama buqatar wani rayuwa ko gatan daya wuce muyi rayuwarmu ayanda take,
Karka saka wani Rai a wani rayuwan bayan kasan mu din asalin 'yayan bola ne,
Bamuda wani rayuwa bayan Wanda muke ciki a yanxu.


dariya Usi yayi hadi da miqewa tsaye yafara tafiya yana Dan dingyashi saboda raunin da akai masa a kafa sosai yake masa zugi
cikin sake quluwa Amah tabi shi da idanuwa tana tunano irin kalar rashin arzikinda zatayiwa Garba.

Tafiya sukeyi suna firarsu cikin nishadi sbd su Sam Babu Abinda suke ajiyewa arai ya damesu.




Suna shiga gidan da Aunty Salamatu suka fara cin karo aikuwa ta soma sakin numfarfashin masifa dan Sam bata manta dibar albarkan da Aman tayi Mata ba kafin fitarta,


Amah na ganin hakan ta fuske ko kallonta batayi ba ma tai wucewarta zuwa dakinsu jakarta ta ajiye hadi da cire karamin hijab dinta ta fito ta nufi qofar dakinsu kawu ta tararda
Usi zaune tare da Kawu wanda ke tambayar Usin" wane shegen kurtun Dan sandan ne yayi maka wannan ta'asar???

Qwafa yayi Yana taba qafarsa dake Masa zogi yace"


Ai kawu idona idon Sargent salisu saina saka anyi Masa zanen yarbawa har a goshi da qeya,


Shikuma insfector Garba duk Yakuma zuwa gidan Nan gurin amah saina Masa askin kwalba.


Cikin takaici kawu yace"


Shi garban me kama da an sulala naman Kai shine yasa aka maka wannan dukan? Kokuwa shi Sargent salisu din dayafi kama da danyar alala yayi gaban kansa yayima wannan dukan kamar wanda yayi kisa¿


Maman basiru dake kusa dasu tana aikin wanke rishonta ta tabe baki tana cewa'"


To meya raba dambe da fada¿


Tsuke fuska kawu yayi Yana kallon iyami dake fitowa daki daukeda robar garin tuwo dazata gyara yace"


Iyami kinajin matar nan nafadamin mgn bazakiyi Mata dukanda mijinta ba mijintaba ko yayanta bazasu ganetaba,
Waini iyami kodai auren dole ne mukayi?da kike wulaqantani ne kokuwa talauci haukane?


Dariya usi yasaki Yana cewa'"


Wlh kawu talauci haukane tunda gashinan duk bamuda hankali....


Butarda dake gefenda ya dauka a hasale
Usin na ganin hakan ya tashi

Please Login or Register in order to submit comment