You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

mama "toh mama insha
Allahu" khadija ta runtse idonta se hawaye
tausayinsu duk ya cika mata ciki...
BAYAN SATI 1
A yau aka salame su,Gwamnati ce dama ta dau
nauyin duk wata dawainiyar sh,,Da zasu tafi aka
basu wheel chair da kuma forearm crutch,kyauta
shima,se godiya suke yi,,AISHATUL MUBEENA
kuwa ta warware har dariyar ta takeyi,,Amma
rannar data koma normal se data kalli ma'u tace
"Umma,kinga kafata yadda ta dawo,A haka zatai
ta zama?" Ma'u ta fashe da kuka a hankali duk da
tana k'ok'arin kada ta gane ta dage tace "a'ah
aishatul mubeena zata warke yi hak'uri,," Tayi
murmushi tace "toh umma"
A rannar da suka koma yan'uwa da abokan arziki
suka dinga zuwa dubiya,kowa ya zo se yaji
tausayin aishatul mubeena,ita kuwa dayake da
yarinta haka take dariyarta tana harkar ta ba
ruwanta,ita a wayonta ta zata kafar tata zata
warke ne kamar yadda mamanta ta fada mata,,,
Mal ne ya shigo gidan yana masifa 'Bazan iya
bafa,baze yiwuba,Ayi ta zagina a gari anacewa
inada ya gurguwa! Ma'u a fusace tace "Mal ya
isheka fa,Waye ya ja mata? Ba kaine ba,Azzalumi
kawai,Me bak'ar zuciya! Ya juyo da mamaki "lallai
ma'u kin rik'a,Amma saurara kiji,Yau din nan
zanyi maganinki!" Ma'u wani murmushin tak'aici
tayi ta tana kallansa,,Ina sauraronka,,
Yayi wata dariyar mugunta sannan yace............
Comment as:
Publish Preview
No comments:
AISHATUL MUBEENA 45-60
[12:22AM, 14/10/2016] Miss_Hafcy: ◆◆◆AISHATUL MUBEENA◆◆◆ NA MSS HAFCY
®ONLINE HAUSA WRITERS [45]-[50] Likita ta
ganni tsaya a jikin mota yana murmushi,,kasa
magana tayi ta tsaya kawai tana kallansa cike da
mamaki,,Dayaga shirun yayi yawa se yace
'Malama ma'u ya kika tsaya anan k'araso mana"
jiki ba kwari ta karaso ya durk'usa ta gaishe shi
ya amasa tare da murmushi sannan yace "nasan
zakiyi mamakin ganina" Ta gyda kai alamar eh Ya
cigaba"Hak'ik'anin gaskiya tunda na ganki ke da
yarki nake tausayin ku,inason taimakon ku kuma
Cikin ikon Allah Se akamin transfer na koma
Asibitin aminu kano,Shine kwanaki na kawo ziyara
garin nan se nake tambayarku se ake cemin ai kun
rabu da mijiniki,,To gskia bazan boye miki ba tun
daga nan nake jin sonki a zuciyata daga baya
shine na yanke hukunci nazo na nemi amincewarki
dan Da aure nake sanki ba da wani abu ba! Ma'u
tayi murmushi "Toh likita zanyi shawara insha
Allahu nagode kwarai,Se dai kuma bansan sunan
ka ba", Likita yayi murmushi sannan yace "
Sunana DR MUHAMMAD AMEEN" Ma' u tace
"Toh Dr nagode,' yayi murmushi sannan yacr
"Inason zanyi magana da magabatanki in har kin
amince dan na dinga zuwa wajen ki" tace
"Bakomai Insha Allahu ba matsala" yace "Masha
Allahu amma nagode da wannan tarba me kyau
da kika min,, ma'u tace bakomai ai,,,Yace "ina
yartawa take? Ma'u tace tana ciki bari na fito
maka da ita" yace toh ya bude motarsa ya dauke
wata leda sannan ya kulle motar Ma'u bata dade
ba se gata da aishatul mubeena tana turota,Ita
kuwa tana murmushi tace "Ina wuni" yace lafiya
lau my daughter, Ya jikin naki? Tace da sauki,, Ya
mik'a mata ledar da kyar ta karba ma'u tai ta
godiya Sun dan yi hira Kadan yana bata shawara
akan yadda zata dinga kula da aishatul mubeena
dagabaya sukai salama Bayan ta koma gida tayi
wa mama bayanin komai mama ta ji dadi ta kuma
ce zata fada wa kawaunan ta da kuma yaya basiru
Abu kamar wasa zancen har ya mik'a yau Dr yazo
da magabatansa bayan sun Gaisa kawu na katsina
(Kawun su ma'u) yace,"Zamu iya sanin ka sosai"
dr yayi murmushi yace "Nidai sunana DR
MUHAMMAD AMEEN inada mata daya da yaya
guda hudu : Ameen(Abba) ,Abdulhafeez,Se
Husna da Aisha,,Ni baban likita ne yanzu a aminu
kano ina zaune a kano da iyalaina unguwar
lamido cresent,,Wayan nan kuma (ya nuna
kawunansa) daya k'anin babana ne dayan kuma
k'anin mamana ne wannan kenan Kawun katsina
yayi murmushi "Masha Allahu"Yanzu zamu kirawo
ita ma'u muji daga gareta kaga tunda bazawarace
in ka amince yau se a daura auren,Amma se munji
daga bakinta "dr ya gyda kai "toh bakomai" Yaya
basiru ne yaje ya kirawota kanta na k'asa ta
gaida su cikin girmamawa suka amsa ,,Kawun
katsina yayi mata bayanin komai sannan yace
"Yanzu yardar ki muke neman in kin amince se a
daura aure!" Gaban ma'u ya fadi ashe dai da
gaske ne ita bata zata abun ya kai ga haka ba har
ana cewa za'a daura auren yanzu,,Ta sunkuyar da
kanta tace..................
Like · 4 · Repl
Share
[12:22AM, 14/10/2016] Miss_Hafcy: ◆◆◆◆AISHATUL MUBEENA◆◆◆◆ NA MSS HAFCY
®ONLINE HASA WRITERS [50]-[55] Tace "To
shikenan Allah ya zaba mafi alheri"Dr wani dadi
yaji a ranshi,Tana gama fadan hakan ta fita daga
falon,,kawun katsina yace "To Masha allahu tunda
ta amince yanzu se muje masalaci tun dan naga
ana kiran sallar la'asar bayan an idar se a daura
auren,ince dai a shirye kuke(Ya kallesu)? Dr yace
eh mal muje" Cikin K'ank'anin lokaci aka daura
auren Muhammad ameen da Asma'u (ma'u) akan
sadaki dubu10,Ango yayi alkwarin wani satin ze
aiko da Kayan lefe se ta tare.. Tuni dama ya
sanar da matarsa Hajiya Hadiza,Dayake tana da
mutunci sosai kuma ba ruwanta addu'ar fatan
alheri tayi masa,Ta kuma ce inshaAllahu zasu
zauna lafiya,Indai ta bangarenta ne baza'a samu
matsala ba Yau ne tariyar ma'u,Bayan tayi yar
walima a gidansu,,Ita kadai aka kai gidan mijinta
banda Aishatul mubeena a cewar mama insunyi
sati 1 se akawota,Dan dr da kanshi yace ze dauke
ta ya dau nauyin komai dinta kamar yarsa ta
cikinsa Gida Masha Allah me kyau da shi bene ne
sama da k'asa,Hajiya hadiza tana sama yayinda
ma'u ke k'asa falo ne dan madaidaici da kuma
dakuna biyu se kitchen da bandaki da dan tsakar
gida ,,Dan yaya basiru da su kawun katsina sunyi
mata kayan daki ba laifi,,,Kowa se yi mata murna
akeyi mama ta mata nasiha sosai akan ta zauna
lafiya da uwargida ta kuwa dauka dan ita ba
ruwanta bata san hayaniya ma Dr ya tarasu yayi
musu nasiha baki daya kuma sun nuna mai sun
dauka suka mai alkwarin zasu zauna lafiya,, Bayan
sati Dr da kansa yaje ya dauko aishatul mubeena
da kayanta tana ta murna za'a kaita wajen
ummanta,Rannar da'aka kaita suka fara sabawa
da husna ;Sa'arta kuma akwai san mutane tafi
aisha san mutane sosaii nan da nan suka saba
kamar dama sun San juna,Husna tana shekara 4
ita kuma Aisha shekara 6 Suna zaune a falo dasu
husna YA ABDUL ya shigo fuska ba yabo ba
falasa, masha Allah kyakyawa ne sosai,Ga shi
akwai tsayi,duk da befi shekara 15,Ya gaida
Umma(ma'u)ta amsa da fara'arta tana mai sannu
da zuwa dan boardn skul yake yi yau ya
dawo,,Husna da Aisha da sauri suka taso zasu
mai oyoyo cak! Suka tsaya sakamakon muguwar
hararar da ya wurga musu,,"ku meyasa ba kuda
hankali ne ni zaku zo kuna wa oyoyo ?banzaye
kawae" ya fada cike da fushi daidai shigowa haj
hadiza(ummi haka suke cemata) tace "kadai abdul
Allah ya shirye ka ,kai da yan -uwanka Kana
hantararsu kaji kunya wlhy" Yace "To ummi akan
meye zasu zo suna min oyoyo se kace yaro
sa'ansu!" Umma datake dariya se a lokacin tayi
magana " Anty na ,ai da gskiyar sa ya girma fa"
ummi tayi dariya "halinsa ne kenan fa,ni rasa
gane irinsa,Haka yake,hira ma basa yi ,Suna mai
magana ya hantaresu wai shi baya san raini,dadai,
YA AMEEN,,kikace shine ba ruwanshi,yaranan
kamar k'awayensa haka ya daukesu,,suyita hira
suna raha abinsu abin sha'awa" umma tace "
shima ai yanason su,Da alama magana ce bata
dameshi ba ,(ta kalleshi)Rabu da ita Dana bari na
kawo maka abinci kaci,, Yayi murmushi "Toh
nagode" be sake magana ba ,umma ta tashi ta
nufi kitchen dan zubo masa abincin,,,yayin da ya
zauna a kujera yana jiranta,, se a lokacin ya lura
da Aishatul mubeena dake kan wheelchair tayi
tsuru-tsuru,dan har ta fara tsoronsa,, Ya kalli
ummi da mamaki "Ummi wannan waccece??
L
Share
[12:23AM, 14/10/2016] Miss_Hafcy: ◆◆◆AISHATUL MUBEENA◆◆◆ NA MSS HAFCY
®ONLINE HAUSA WRITERS [55]-[60] Ummi tayi
murmushi "k'anwarka ce,Yar antynka ce" yace
"Allah sarki,But yana ganta a wheelchair ciwo taji
ne? Ummi ta kada kai "A'ah polio victim ce! Ya
zaro ido ya maimaita "polio victim kuma??!,garin
yaya? Ya akai ta samu? Ummi tace "Kai kaga
bansan tambaya nima bansani ba, Allah ne ya
dora mata,ya isheka haka, yace toh ummi,, Kallo
daya ya mata ya kauda kai a fili yace "Sannu kinji
ya sunanki? A tsorace tace "Aisha..tul..mubeena"
ya gyda kai "nice name" Daidai lokacin umma ta
shigo da tray na abinci a hannunta ta dire mai a
gabanshi yayi godiya ya kai loma daya kenan
daga waje suka jiyo murya "Salamu alaikum
Ummina my lovely sisters kuna ina?? Hakan ya
tabbatr musu da cewa YA AMEEN ne,, Da gudu
aisha da husna suka tashi suka nufi wajen sa, ya
ware hannunsa suka taho da sauri suka rungume
shi Yayi murmushi "Nayi missing dinku Deariz"
suka amsa muma munyi missing dinka bros Ya
rik'e hannunsu suka k'araso wajen su ummi ,
ummi tayi murmushi ta kalli umma "kingani ko
dama na fada miki wuyata ya dawo,shi ba
ruwansu ba kamar wannan sakaran ba!" Umma
tayi murmushi ya k'araso wajen ummi ya
rungumeta, Da sauri ta kwace "kaga ni bansan
wannan shashashacin" yayi dariya " ummi nayi
missing dinki dayawa" tace "nima haka dana"
Yace "Finally dai mun gama secoundry skul Nan
da yan shekaru zan zama PILOT,, Ummi tace
"Insha Allahu munan muna ma addu'a yace "Dats
my ummi" Ya juyo ya kalli umma ya gaisheta da
girmamawa ta amsa,,Tare da yi masa sannu da
zuwa da kuma murna kamala sakandire,,Yayi ta
godiya,,Se a lokacin ya lura da Aishatul mubeena
Ya kalle ta yace "Fine girl bakida lafiya ne? Ya na
ganta a wheel chair? (Ya kalli su ummi)Umma tayi
murmushi ta sunkuyar da kanta,, Da mamaki se
sukaji tace "Ni polio victim ce!" A tare ummi da
ya abdul suka zaro ido,,Lallai yarinyar nan daga
fadan abu har ta gane ta haddace,, Haka Ya
abdul yace a zuciyarsa"Ya ameen yace 'Eyyah
Subhanalahi " ya kalli ummi " Ummi da gaske
take? Umma da sauri tace"Da gaske take Ameen,
kawai se ta fashe da kuka,, Ummi ta shiga
rarashinta shikuwa ya ameen be san sanda
hawaye suka fara zubo masa ba nan da nan
tausayinta ya cika mai zuciya,, yaji kuma wani
santa a zuciyarshi,,jinta yake tamkar k'anwarsa
uwa daya uba daya ! ya matso kusa da ita yayi
murnushi "Ya sunanki" ta wangale baki "Sunana
Aishatul mubeena! Yace wow nice name " zaki sha
sweet?" Tace ' eh" yace " toh zomuje na siya
miki, umma da sauri tace" aah ameen ka bari ka
huta mana, daga dawowarka? Yace bakomai
umma yanzu zamu dawo Ai nan kofar gida ne,,
Ya ja wheel chair din suka fita Jin haka husna da
aisha suka ce zasu je suma,ba musu yace su taho
yaja wheel chair din yana mata murmushi "Muje
na siya miki sweet koh? Tace "Ehh tana wangale
baki" suka fice Abdul kuwa tabe baki yayi, ya
cigaba da cin abincinsa ,Umma kuma dadi taji a
ranta sosai Basu dade ba se gasu sun dawo Kowa
da sweet a hannunshi se wangale baki
suke,,Aishatul mubeena ta kalli Ya ameen kainu
wajen umma,,Yace toh yaja wheel chair din wajen
umma ta wangale baki "Ummana kinga ya siyamin
sweet" Umma tace"nagani angode" Ya ameen
yace "Niwa? Ya sunana? Tace "Bansan sunan kaba
ni" umma tace "Auu baki san sunan shi ba?" Tace
"Eh ya sunanka" Yayi wani murmushi sannan
yace...
AISHATUL MUBEENA 60-80
[12:23AM, 14/10/2016] Miss_Hafcy: ◆◆◆AISHATUL MUBEENA◆◆◆ NA MSS HAFCY
®ONLINE HAUSA WRITERS [60]-[65] Sunana Ya
ameen amma kin san me zaki dinga cemin? Ta
gyada kai "A'ah" Yace toh ki dinga cemin "Bros"
ya abdul dayakr k'ok'arin tashi ya fashe da
dariya,"Wayaga bros! Su bros manya" ya tsuke
fuska kamar ba shi yayi maganar ba sannan ya
tashi ya fita,, Ya ameen yace "Ka dai ji dashi dan
rainin hankali" Aishatul mubeena kuwa maimaita
sunan ta shiga yi "Bro...s Yau ma kamar kullum
bayan sallar magariba suna zaune gabadayansu a
falon Abba suna hira ,,Ya ameen yace "Abba
nikuwa inada shawara" abba yace inaji "Abba me
ze hana aishatul mubeena ta dinga gwada tafiya
duk da dai tafiyar bazata zama daidai ba? In ba
haka wlhy tafiya da Forearm crutch din nan ze
mata wahala sosai" Abba ya numafasa sannan
yace "To ka dinga koyawa mata takawar
muga,Indan tana takawa shikenan ba matsala
idan kuma ta kasa kaga dole sai dai tayi amfani
da forearm crutch din" yace to insha Allah za
dinga gwada mata,, Umma tace "Angode fa Allah
saka da alheri" yace "Bakomai umma" Yau da
yama ya ameen Ya sauko da ita daga wheel chair
din yana koya mata tafiyar,Ba laifi ta na dan
k'ok'artawa yaji dadin Haka kullum addu'arshi
Allah ya taimake ta,Ta fara cangala kafar tata
dan a ganin shi hakan yafi da yawo da sanda"
YAU DA GOBE SAI ALLAH yanzu dai Aishatul
mubeena tana ss2,tana iya takawa amma saidai
tafiyarta ba irin ta masu lafiyar kafa bace cikin
ikon Allah tana iya cila kafarta tayi tafiya,,,, Ta
k'ara girma ta zama yan mata,,Tana da shekaru
16 Duk da ba lallai ka gane hakan ba saboda yar
k'arama ce kuma gata Ba k'iba saboda cutar
polio ta k'ara motse ta,,Amma duk da hakan
kyanta yana nan akwai kyau Masha Allah,,, Ya
abdul yana final year dinshi a university inda yake
karantar Engineering danshi dama burin sa kenan
ya zama engineer yayin da Ya ameen Ya zama
cikaken pilot har ya fara aiki ma Allah mai baiwa
duk da nakasa irinta Aishatul mubeena,,Amma
Kuma Allah ya bata kwakwala Tanada masifar
k'ok'ari mussaman ma a fanni Ilimin addini harda
na bokon ma,,,sannan kuma cikin ikon Allah,Allah
se ya bata fasahar yin ZANE yanzun zata kalli abu
ta zana shi tsaf kuma ya zanu sosai tayi fice A
makarantarsu a harkar zane sosai,,Kuma cikin
ikon Allah Ya ameen ne ya fara gano haka kuma
ya bata kwarin gwiwa sosai,,Duk wani abu datake
buk'ata a harkar zane da kudinshi yake siyowa ya
bata! AISHATUL MUBEENA ce t zaune akan Farar
kujera a compound din gidan,Kur'ani ne a
hannuta tana karantawa a hankali,,, YA ABDUL ya
shigo da motarsa ya faka ta a wajen fakin din
motoci,,Sanye yake da Bakin wando da riga sky
blue yayi bala'in kyau,,Ya k'ara girma ya kuma
k'ara kyau A hankali ya tako wajen datake karatun
yana sauraron k'ira'arta me masifar dadi,, Taji
kamar alamar mutum da sauri tajuyo suka hada
ido,,Bashiri ya kauda kai,,ya tsuke fuska yace "
Ke me kike yi anan? Murya na rawa tace "Daman
karatu nake yi," yace "Toh shi karatun ba'ayinshi
a ciki ne? A sanyaye tace "Saboda naga suna
kallo ne banason na dame su" yayi dan k'aramin
tsaki sannan ya bar wurin,,Ita kuwa ajiyar zuciya
tayi ta cigaba da karatunta Ba'a dade ba sai ga
Ya AMEEN nan ya taho daga dakinsa yana ta
mata murmushi(Dan bashida aiki week din) Tana
ganinshi tayi wani yalwatatacen murmushi ya
k'araso yana mata murmushi "SIS karatu ake ne?
Tayi murmushi "ina wuni bros" yace "Lafiya lau
sis karatu ake ne? Tace "Eh suratul khaf nake
karantawa kasan yau juma'a kuma sannan jibi
insha Allahu zamu yi musabak'a ! Ya wangale
yabaki "Masha Allah my l sister am very very
proud of you,,Allah ya bada sa'a insha Allahu ke
zaki ci,, Tace "ameen nagode bros" Yace "Ga
wani albishir din kuma;, tace inaji bros" yayi
murmushi " Yanzu uncle hashim(teachern su
aishatul mubeena) yace min aiy an zabe ki a gasar
zanen da za'ayi a Schools din dake kano wanda
kuma idan kinci shi ze bada damar ki wakilci kano
gabadaya a gasar da za'ayi da states din dake
nigeria.... Ta zaro ido da gaske bros? Yace
"kwarai kuwa! Tace anya zan iya kuwa? " yace see
you! Zaki iya mana insha Allahu se kin cinye
mudai kawai mu cigaba da addu"a,, Tace
"Nagode bros" Ya harareta "To meye na godiyar
kinsan dai banaso
Like · 3 ·
[12:24AM, 14/10/2016] Miss_Hafcy: by Hafsat
◆◆◆AISHATUL MUBEENA◆◆◆ NA MSS HAFCY
®ONLINE HAUSA WRITERS [65]-[70] Ta sa hannu
ta rufe bakinta toh shikenan na dena, yace
"Yauwa ko kefa" Bayan sallar isha,Aishatul
mubeena na zaune akan sallaya tana
muraji'a,Husna ta shigo da kur'ani a hannunta,Ta
zauna kusa da ita tace " Sis pls biya min nan,Ko
sau daya ne" Aishatul mubeena na k'ok'arin
dauka sai ga ummi nan ta shigo,Ta kalli husna"
Ke husna me yasa zaki dinga damunta kinsan dai
Musaba'ka garesu gobe ki barta tayi tilawa mana"
Husna tace "Kai ummi kawai fa cewa nayi ta biya
min shafi nan sau daya" Ummi tace "eh duk da
haka,Kije umma ta biya miki mana" Aishatul
mubeena tace 'Ummi dakin bari ma na k'ara
mata" ummi tace "Aah dai gwanda ta barki kiyi
karatunki" Husna na zumbure zumbure ta bar
wajen......... To Yaune dai zasu tafi musabak'ar
tun safe ta shirya tsaf cikin hijab har k'asa
uniform din makarantarsu Tayi kyau sosaii,,Ya
ameen ne da kanshi ze kaisu,, ita da su husna da
kuma k'aninta Amir( Yaron da Umma ta haifa a
gidan) dayake duk makarantarsu daya.... ,,(Da
harda su umma za'a amma zasuje Gaisuwa zaria
wani dan uwan abba ya rasu) A lokacin da suka
isa Mutane an taru sosaii,Makarntar dazasu yi
gasar da ita har daliban sun iso da kuma wanda
zasu kara da Aisha....Bayan an bude taro da
addu'a,Aka fara.... Cikin ikon Allah kuwa Aishatul
mubeena tayi kok'ari sosai,,Gyra da aka mata
basu da yawa,,bayan an kamala aka Aka kirawo
malam salisu(Babban malami ne shi) dan yazo
yayi jawabi sannan ya fadi sakamako,,,,,Sai da
malam ya fara jawabi ya kuma ja hankalin dalibai
da su dinga maida hankali wajen karatu sannan ya
fara karanto sakamakon kamar a haka: "A
musbak'ar Alkur'ani mai girma da muka gabatar
tsakanin makarantar,khalid ibn walid islamiya da
kuma Nana khadija Islamiya,, Makarantar nana
khadija islamiya wadda ta samu wakilcin Aliyu
sani tana da maki sha biyar (15) a cikin maki
talatin( 30)A mata kabara,,(Dalibai suka dauka
Allahu akbar) Sannan makarantar Khalid ibn walid
islamiya wadda ta samu wakilcin AISHATUL
MUBEENA MUHAMMAD AMEEN tana da maki.....
ashirin da biyar(25) a cikin maki talatin(30)! ku
musu kabara(Dalibai suka wage baki Allahu akbar)
Aishatul mubeena dake gefe wata ajiyar zuciya
tayi tare da Hamdala bata san sanda ta fara
hawayen murna ba,, Mal ya cigaba ' Wannan ne
ya tabbatar mana da cewa makarantar khalid ibn
walid itace ta cinye wannan gasar karatun
Alkur'ani me girma,, ku sake rangada musu
kabara(Dalibai aka dau kabara da karfi,nima
danake gefe wage baki nai nace Allahu akbar)
Dan haka an shirya kyautuka masu tsoka ga
wandanda suka yi Musabak'ar domin mu k'ara
k'arfafa musu gwiwa dama sauran dalibai,, Dan
Haka yanzu zan fara da Aliyu sani,, Alhaji Abdu
mai nerori ya bada kyautar Dubu Da kuma
Alk'urani me girma izu sittin ya kuma ce a bawa
wanda ya zo ta biyu a wannan gasar karatun
Alk'urani me girma,, Aliyu sani sai ka fito ka
amshi kyautar ka,, Ba dadewa aliyu sani yazo ya
karbi kyautarsa ana ta masa kabara Malam ya
cigaba sannan Zamu kira AISHATUL MUBEENA
MUHAMMAD AMEEN domin ta amshi
kyaututukanta,,Ba'a dade ba sai gata ta taho
tana cangala kafarta malam ya cigaba " Alhaji
Audu mai nerori ya bada kyautar Naira dubu dari
(100),Ga duk wanda yazo na daya Sannan
Shugaban kamfanin jirgin **** ya bada kyauta
kujerar umara shima ga wanda yazo na daya,Sai
kuma haj asabe ta bada kyautar atamfa guda uku
(3) itama ga wanda ya lashe gasar karatun
alkur'ani Dan Haka Malama Aisha se kizo ki karbi
kyautarki ta matso ta karba ana ta daukan
hotonta mussaman ma da'aka lura da nakasar
dake jikinta,, Ita kuwa se hawayen murna takeyi
hannu na rawa ta karba aka dinga kabara,, Malam
daga k'arshe yace,Dan haka sai muyi wa bayin
Allah nan addu'ar Allah ya saka musu da alheri ya
kuma k'ara budi.... Yayi addu'a sannan ya koma
ya zauna.... Tana dawowa daga wajen Karbar
kyautar kai tsaye wajen Ya ameen ta nufa ta
mik'a masa kyautar sannan ta koma ta zauna ta
kifa kai a gwiwa tana kuka,Ya ameen kuwa
rarashinta ya fara "Haba sis ki dena wannan
kukan mana Godewa Allah ya kamata kiyi ba kuka
ba! Ta dago idonta ta share hawayen sannan tace
" Toh bros insha Allahu na daina " yace "Toh
yimin murmushi mana" Batasan sanda murmushi
ya kubce mata ba,,Shima murmushi yayi yace
"Yauwa ko kefa" mutane se zuwa yimata Allah
sanya alheri suke mussaman ma dalibai da kuma
malaman makarantarsu kai hadda baki.... Bayan
an rufe taron Har zasu tafi gida tace a tsaya ta
zata je ta dawo,Suka ce toh......Kai tsaye wajen
shugaban makarantarsu ta nufa ta tsuguna har
k'asa ta gaishe shi ,Ya amsa da murmushi "Tashi
mana Aisha,Gaskiya kin burge mu sosaii muna
alfahari dake Allah ya saka miki da alheri ya k'ara
buda miki kwakwalki ,,kin k'ara fito da
makarnatar mu ba abinda zamu ce miki sai
godiya da fatan alheri"" Tayi murmushi "Malam
aiy nice da godiya,Nice ya kamata nayi muku
godiya ma,,Nagode nagode Allah ya saka muku
da mafificin alheri Ameen" Malam yace "Ameen
Aisha,Allah ya sa sauran dalibai suma suyi koyi
dake" Tace "Ameen" sannan ta bude jakarta ta
zaro envelop din nan da aka bata na Naira dubu
dari(100)....
Like · 2 · Reply · Ed
[12:25AM, 14/10/2016] Miss_Hafcy: ◆◆◆AISHATUL MUBEENA◆◆◆ NA MISS HAFCY
®ONLINE HAUSA WRITERS [70]-[75] Ta mik'awa
Malam Iro (Sunan shugaban makarantar tasu)
murya a sanyaye tace "Malam ga wannan kai da
sauran malamai ku kasa sauran abinda yayi
ragowa kuma a siyo butoci da tabarmu akai
massalacin makaranta " Malam ya zaro ido "Haba
a'eesha(Dayake haka yake ce mata) Ai kudinki ne
ba namu ba,Ki rik'e kudinki kinji Allah ya samu su
albarka mukam mun gode bama karbi kudinki ba
gaskiya" ta ja numfashi sannan tace "A'ah malam
dan Allah ka k'arba,Ba a maida hannun kyauta
baya!" Malam yayi murmushi " To sai da mu dauki
dubu ashirin(20) ta ishe mu" tace "A'ah malam
dan Allah ka karba duka" Yace "Toh shikenan
raba a biyu ki bamu rabi Allah ya sa albarka" ta
wangale baki " Yauwa malam gashi(Ta mik'a masa
kudin duka) ya ciri dubu hamsin (50) kamar yadda
Yace sannan ya mik'a mata yace "Gashi nan
a'eesha mun gode sosaii Allah ya saka miki da
alheri ba abinda zamu ce miki sai godiya" tayi
murmushi "Godiya nake malam Allah ya biyaku"
Sannan ta koma wajen motar tasu suka nufi gida
Suna isa gida a harabar gidan ummi da sauri tazo
ta rungume ta,Tana ta murna "yata kin burgeni
gaskiya,Am soo proud of you My daughter,Ina
alfahari dake Yata, aishatul mubeena tayi dariya
"Nagode ummina" Umma itama ta zo wajen cike
da murna Ta rungume yarta ta,Batasan sanda taji
hawaye na zuba ba duk iya kok'arin datayi na
ganni hawayen basu zuba ba amma sai da suka
zuba,,A firgice ta kalli umman tata "Umma kukan
me kike yi?" Da sauri ta share hawayen nata
"Kukan murna ne mubeena kukan murna
nakeyi,,Dama na dade ina jiran irin wannan
rannar Sai yau Allah ya nuna min,, ina ma
zanga........Da sauri ta canza zancen nata ,,muna
alfahari dake Allah ya k'ara buda miki
kwakwakarki,,Dake da sauran yan uwanki!" Su
Husna dake tsaye suka ce Ameen..... Ya abdul ya
fito daga dakinshi,Ya tsaya turus Yana kalonsu
"Meya faru ne? Ummi da sauri tace "Abin arzik'i
ne ya faru,,k'anwarka ce taci Gasar karatun
Alkur'ani me girma " Yace "Masha Allah wacce a
ciki?" Ummi tayi murmushi "yo waka sani banda
mubeena,Kasan wadanan sakarkarun(Ta nuna su
husna) Ba abinda suke tsinanawa" ya tabe baki
"Okay" ummi tace Sai kayi mata murna ai,Ya juyo
ya kalleta ya k'irk'iro murmushi yace "Congrats"
yana rufe bakinsa da sauri ya koma dakinsa,,Ya
ameen har a zuciyarsa beji dadi ba dan haka ya
yanke hukuncin yaje ya sameshi ya mai
magana,,Ya bishi dakinsu yayin dasu ummi suka
shiga ciki (Abinda yasa suka san itace ta lashe
gasar shine, Ya ameen ne ya kirasu ya sanar
dasu,,jim kadan bayan an gama fadan
sakamakon) Ya murda kofar ya shiga a zaune ya
ganshi yana kallon system dinshi dake kan
Bedside drower,,Ya shigo da salama sannan ya
zauna a kusa dashi, Yace "Ahki(My brother
dayake haka yake cemai) Gaskiya abinda kayi yau
baka kyauta ba"" Ba tare da ya kalleshi ba yace
"Me nayi" Ya ameen yayi murmushi,, "okay
bakasan me kayi bama? Ya kallesa "Yes
eh,Bansani ba" Ya ameen yace "To abinda kayi
yanzu a harabar Gida nasan nasan cewa umma
bataji dadi,Dan Allah ka dena yiwa yarinyar nan
haka kodan nakasar ta ai ka sota,,Kamar
k'anwarka fa take,,Dan Allah ki dinga janta a jiki
ka dena hantararta dan Allah na rok'e ka" Ya
abdul ya nisa sannan yace "To bakomai,Amma ni i
dont knw why(Bansan meyasa ba) kwatakwata
bata burgeni,Inaga jinin mu ne be hadu ba!!
Kuma dama kasan halina ai,,ni ban cika san
shigewa mutane ba and kar ka dauka wai ko dan
ba blood sister dinmu bace,No ko su husna ma
kasan ba wani sakar musu fuska nake ba Ya
ameen yace "To shikenan amma ya kamata ka
rage wannan halayar,Wani in ya fahimce ka wani
baze bayi ba,Dats why(shiyasa) mutane ke maka
Kallon me girman kai " ya abdul yace "Wannan ya
rage nasu ni ban damu cuz nasan ba halina bane"
lets keep this aside (mu aje wannan gefe) Wai ni
ina maganar FATY ne naga yanzu baka
maganarta,, Ya ameen ya bata fuska "kai ni daina
min maganarta mu b'ata" ya abdul ya kalleshi da
mamaki "Why meyasa" ya ameen ya nisa sannan
yace "Waifa daga taga pics dinmu da Mubeena
shikenan ta dau zafi, Wai budurwa tace,,inata
k'ok'arin na mata bayani amma tak'i yanzu bata
daga wayana ma" ya abdul yace "Tayiwa
kanta,Amma i bet you dakanta zata dawo tace ku
shirya" Ya ameen yace "oho mata" Ya kalli ya
abdul "Kai dama wayo kake min ko da wasa baka
min maganar budurwarka" ya abdul yayi
dariya"Wayaga me budurwa,, Hhh ni banda
budurwa ai" ya ameen yace "Ban yadda ba,Duk
yan mata dake binka kace bakada budurwa
wannan shayi ne kake mun" Ya abdul ya k'ara
dariya sannan yace ................ Kuyi hak'uri kunji
ni kwana2 biyu shiru
Like · 1 · Reply · E
[12:27AM, 14/10/2016] Miss_Hafcy: ◆◆◆AISHATUL MUBEENA◆◆◆ NA MSS HAFCY
®ONLINE HAUSA WRITERS [75]-[80] Yayi dariya
sannan yace "Kasan Allah? Ni har yanzu ban ga
wadda tayi min bane,Ni kaga ba kula mata ma
nake ba,In banda yan-uwa sai kuma classmates,"
ya ameen yace "Kuji shi kamar gaske" ya abdul
yace "Wallahi da gaske,," ya ameen yace " To
shikenan Allah ya zaba mana mafi alheri, nidai
kaga a shekarar insha Allahu zan yi aure na barka
(yayi masa gwalo)" Ya abdul yayi dariya,,wayar sa
ce tayi ruri da sauri ya dauka" Yace salamu
alaykum" dayan bangaren akace "wslm abdul ka
fito ina kofar gida" ya kashe wayar ya kalli ya
Ameen "Hafeez ne frnd dina bari naje ltr zamuyi
magana" Ya ameen yana k'ok'arin tashi yace
"okay nima bari na tafi". Kai tsaye falon umma ya
nufa inda ya tarada Nana(Aysha) Na chatn a
waya,Husna na kitchen,Aishatul mubeena Na
zaune Tana koyawa amir assignment,, Ya shigo
yana murmushi hade da kallan Mubeena' Hafizar
mu" tayi dariya "Kai bros" yace "Ko nayi k'arya?"
Da sauri Nana tace "a'ah bakayi k'arya ba ya
ameen, gaskiya ce" Yanzu kaga yan islamiyar mu
sai cemin suke nace suna taya ta murna da fatan
alheri, hadda masu sa pic dinta lokacin suna
musabaqar a display Picture(Dp)kaga(Ta mik'a
mai wayarta) ya karba "Masha Allah,Ai

Please Login or Register in order to submit comment