You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

ga ɓarawon wayar ya dawo a guje, yana zuwa ya zube gwiwowinsa a kasa a gabansu, yana kuka yana basu hakuri, a nan ne Imran ya koma gefe ya kira Rimsha a waya, shi kuma Lion hannu yasa ya karɓi wayarsa, dan dama yasan ba wanda zai iya riƙe wayar sai shi, dan ba waya ce kamar ko wace waya ba, sannan kuma idan suka kunna wutar screen ɗin to ya zama dole su razana su dawo mashi da wayarsa shiyasa bai wani damu ba, hankalinsa a kwance lokacin da aka kwace wayar.

Abin da ya faru yasa suka dawo da wayar shine, ɓarawon da ya kwace wayar ogansa ya kai mawa, yana faɗa mashi sun yi babban kamu, ogan yana karɓar wayar tun bai kunna wutar screen nata ba sai da ya ranaza, bai san lokacin da ya furta "Wannan wayar bata irin ƴan Nigeria ba ce, ban taɓa ganin irinta ba". Bai gama rufe baki ba, Michael ya sake kiran wayar domin da suna waya ɓarawon ya kwace wayar sai ya daina jin Lion hakan yasa ya katse kiran ya sake kira.

Suna riƙe da wayar kirar Michael ta shigo nan fa suka ga abin mamaki, domin wayar ba ringin take yi kamar ko wace waya ba, no gaya mashi ta ke yi ga wanda ya kira ga kuma number da ya kira sannan ga daga location da aka kira, shine a matsayin ringintone na wayar, kasa ɗaukar kiran suka yi, domin ma ba za su iya ba, ita ba ɗaukarta ake yi kamar sauran wayoyi ba, a'a idan ba Lion ba ba mai iya picking nata, sai kuma idan akayi Sa'a aka samu masu danne danne suyi ta latse jikinta har su samu su yi picking, haka suka riƙeta har kiran Michael ta katse.

Bayan ta katse ne, sai suka samu wayar ta kawo wutar screen ɗin da kanta, wani mahaukacin razana ogan nasu ya yi lokacin da ya halli abin da yake a gaban screen ɗin wayar, Hoton Lion ne a fuskar wayar, wadda kowa ya san shi da shi, wato da face mask, shi da James da Michael ne, shi kaɗai ya sanya face mask a cikinsu, suna tsaye a saman balcony ɗakinsa, sun rungume juna, sun yi kyau sosai, da sosai. Sun shagala da kallon hoton kiran Michael ya sake shigowa a karo na biyu kuma Vedio call ne na yanzun, rashin sa'ar su yasa ba su san ina suka danna ba, dan ya dakumi wayar da hannunsa, suna picking sai ganin Michael suka yi yana zaune saman dining table na palon kasa yana cin abinci, domin shima ya yi azumin litinin, ihu ogan nasu ya kurma tare da bawa wanda ya sato wayar a kan ya mai dawa mai waya wayarsa.

Abin da ya faru suka dawo da wayar kenan.

Cikin harshen turanci ya ce "Me yasa kake kwacewa mutane abu?" Shiru ɓarawon ya yi domin baya jin turanci ko kaɗan, sai da Imran ya gama magana da Rimsha ya dawo wajan ne ya shiga yi wa ɓarawon fassara yana mayarwa Lion da amsa, daga ƙarshe dai Lion ya ce a mai da shi makaranta a bashi sana'a, domin alamu sun nuna jahilci yasa yake sata, bai samu ilimiba kuma babu sana'ar yi, shiya jefa shi shaye-shaye da kuma sata, da haka suka yi sallama Imran zai je har gidan su gobe ya duba shi, dan ya karɓi address ɗin sa.

Kamar yadda suka fito gida a tare haka suka koma, kai tsaye bedroom na Imran suka wuce. Suna shiga ya nufi toilet dan yin wanka, komai na cikin ɗakin Imran daga waje aka kawo su, hasalima daga kasar su wato Usa aka kawo su, amma Lion ya ce ba su yi mashi ba, shi gidan nema gaba ɗaya ta yi mashi kama da keji kaji, dan haka shi ba zai zauna ba, dole adaran nan a sama mashi katafaren gida wadda aka gama gina wa aka zuba komai na kasarau, ya saya ya koma can, cike da zolaya Imran ya ce "Idan ka sayi wannan gida ka zama ɗan Nigeria kenan?". Karisa shiga cikin Toilet ya yi ba tare da ya sake yin magana ba, wucewa saman bed Imran ya yi ya kwanta yana mamakin yau Lion ne a Nigeria abin da bai taɓa zato ba, a Nigeria ma a gidan su.

A daddafe ya yi wanka ya fito, gaba ɗaya tsadaddun Towels dake a cikin toilet ɗin wai ba su yi mashi ba, da nashi da su Tga suka sanya mashi a cikin trolley sa ya yi amfani, ya saba da shiga dressing room ya shirya, amma yau daga cikin trolley ya ciro kaya, hakan yasa ya sake tsanar gidan su Imran, ba iya gidan kawai ba, gaba ɗaya kasar bata yi mashi ba, ransa ya ɗan ɓaci, haka ya shirya cikin wandon jeans fara tas da riga polo t-shirt blue, ya feshe jikinsa da perfume nasa mai bala'in kamshi bayan ya shafa mayukansa kenan, daga nan ya gyara gashinsa. Bakin gado ya koma ya zauna kusa da Imran yana ganin gadon ma wani local, ko gadon Bradyn sa ta fi wannan kyau.

Ni kuwa nace yau dai ba yadda zaka yi Nigeria ka zo ato, dole ayi hakuri da mu.

Shiru suka zauna domin Imran ya yi degree a sanin halin Lion, yasan baya son magana, dan haka suke zama shiru kamar kurame.

After 1 hour.

Suna zaune a in da suke ba su motsa ba, kuma ba wanda ya ce da ɗan uwansa uppan, kamar gumaka, zama da Lion sai an kai zuciya nesa, karfi da ya ji sai ya mai da ka kurma

Da sallama ɗauke a bakinta ta shigo cikin ɗakin, still hijabi ne a kijinta, hannunta na ɗauke da wani kyakkyawar katuwar tray mai ɗauke da kyawawan kololin abinci, da su plates and spoons da sauransu. Wani irin lumshe idanuwanta ta yi lokacin da ta shaki Kamshin perfume nasa, ji take kamar bata a duniya, ta lula sama jannati, zuba mata ido Imran ya yi, sai da ta shaki kamshinsa son ranta sannan ta buɗe idanuwanta karaf a kan fuskar Imran, wani irin kunya ta ji ya kamata, shi kuwa bai damu ba, dan yasan daɗin kamshin perfume ɗin Lion abin so ne, kowa zai so ya yi ta shaƙarta kada ya daina. Da hannu ya yi mata nuni da shi akan ta kai mashi gabansa, jikinta sai kerma yake yi ta nufe shi, banda hasbunallahu wanimal wakil babu abin da take nanatawa a cikin zuciyarta.

Gaban sa ta zo ta tsgunna cikin natsuwa ta buɗe kular abincin ta fara zuba mashi, yau ga Rimsha ga Lion waje guda, yana duke da kansa kamar yadda yake tun farko, da alama ma bai san da mutun a wajen ba.

Tana tsaka da zuba mashi abin ne, a zafafe ya yi wani irin ball da gaba ɗaya tray ɗin abinci, ciki kuma ya haɗa har da hannunta, domin hannun nata yana kan tray ɗin alokacin. Tarwatse abincin ya yi har saman bed, kular miya kuma da jikin bangon wajen mirror ya bugu miyar ta watse, kusan rabi na miyar ya watsun mata a jikin milk color hijabinta, ga shi kuma miyar steew ce, su cabbage and cucumber da ta yayyaka gaba ɗaya sun watse sama suka warwasu a cikin ɗakin, a takaice dai ball da tray ɗin abincin da ya yi ta watsa komai. Abin da kuma yasa ya yi ball da abincin a cewar sa ta kawo mashi wari gaban fuskarsa ta canza mashi iskar da yake shaƙa, dama kuma da kyar yake shakar wannan iskar ba dan yana so ba, tazo ta wani kawo mashi warin steew a gaba.

Tsabar razana Rimsha bata san lokacin da ta miƙe jikinta na kerma ba, a guje ta juya zata fice sai dai kuma ina tsorata ya yi mata yawa, numfashin ya rigata fita daga jikinta, saboda bala'in razana yasa ta zube kasa a wajen, shi kuma wayarsa da laptop nasa ya ɗauka ya fice daga cikin ɗakin, Imran ya rasa wajen waye zai je ɗaya daga cikin su, ga Rimsha a sume ga Lion ya yi waje da alama kuma ransa a matukar ɓace.

Ganin tunani ba nashi bane yasa ya ɗauki Rimsha ya ɗaurata saman bed nasa ya fita waje dan ya bi bayan Lion. Sai dai ko da ya fito babu Lion babu alamarsa, hakan yasa ya dawo cikin gida da sauri ya ɗauki wayarsa, member Lion ya fara kira dan ya ji a ina yake ya biyo shi, amma ina har 3 miss call ya yi mashi Lion bai ɗauka ba, daga karshe dai ya hakura a ajiye wayar ya kira su Akila domin su gyara mashi ɗakinsa, ita kuma Rimsha ya yayyafa mata ruwa. Baiwar Allah nan a matuƙar razane ta farfaɗo, gaba ɗaya ta fice a hayyacinta, numfashinta sai fita yake da sauri-sauri, idan baku mance ba, tun ainahi tana mutuwar son shi kuma tana bala'in tsoron shi, hakan yasa zuciyarta ta kasa jurar ɗaukar ganin fuskarsa, haka zalika ta kasa iya cire tunanin lokacin da ya zo zai yi mata kiss a mafarki, hakan kuma ba karamin birkita mata kwakwalwa yake yi ba, Allah sarki.

Wani irin kuka mai tsuma zuciyar mai sauraro ta saki, sosai Imran ya shiga rarrashinta yana bata hakuri tare da gaya mata kada ta damu shi Lion haka halinsa yake, Allah ya kiyayye ma yanzu bala'in zafin zuciyar nan tasa ta ɗan ragu saboda hasken musulunci da kuma imani da ta ratsa shi, amma ba dan haka ba, da Rimsha bata isa ta zo in da yake ba, yanzu ko ba komai yana ɗaukan mutane da daraja kaɗan, haka zalika yanzu ya san Allah ke yin komai, kuma laifin wani baya shafan wani.

Imran bawan Allah bai san da tsohon soyayyar da Rimsha ke yi wa Lion ba, ya ɗauka iya ball da ya yi da tray ɗin abincine ya sanya ta suma, a ɗazun kuma da ta suma lokacin da ta kawo mashi ruwa, ya tauka ta razana da ganin face nasa ne, wadda hakan ba wani bakon abu bane, domin dayawa daga cikin mata matsorata suna suma idan suka yi ido huɗu da shi, to shi Imran ya zaci ita Rimsha tana daga cikin su ne, shiyasa bai wani damu ba.

Sosai ya rinƙa rarrashinta, da kyar ya samu ta dawo daidai, da kansa ya tasata a gaba suka nufi Palo, a nan ta isko su Akila sun yi wanka sun dawo suna jiran ta zo su ci abinci, ai kuwa abincin da bata ci ba kenan baiwar Allah, daren ranar dai da yunwa ta kwana, haka zalika daren ranar bata yi barci ba sai wajen karfe 2 na dare sannan ne barci ya ɗauke ta, sai ajiyar zuciya take sauƙewa cikin barci.

Babban abin bakincikin kuma shine, tana fara barci ta fara mafarkin shi. Wai tana zaune a palo ita kaɗai, ta yi shiru ga kamshi da sanyin Ac na tashi, su Imran basu nan sun fita, ita ka ɗai ce a cikin palon, jikinta na sanye da wando da riga sun kamata sosai, tana rungume da pillow ta shagala da kallon Tv dake a gabanta, bata ankaraba sai ta ji hannun mutun a saman wuyarta, bata wani razana ba domin kamshin perfume nasa ya isar mata da sakon ko wanene, hannu tasa ta fara shafo nasa hannun, kwanto da kansa ya yi a saman kafaɗarta yana sauƙe mata numfashinsa a hankali hankali, sai faman lumshe idanu suke yi duk kan su biyu.

Sun ɗan jima a haka kafin ya zagayo ta gabanta ya zauna gefenta yana janyota saman faffaɗar kirjinsa, kwanciya ta yi ta lafe a kirjin nasa tana mai da numfashi, hannu ya zura cikin rigarta ta daidai kugunta yana ɗan shafa plat tummyn ta, sai wani yauki take yi mashi tana kara shigewa jikinsa, hakan da take yi kuma ba karamin kara birkita shi yake yi ba, dan haka sai ya cigaba da wasa da cibiyarta, a hankali ya sanya ɗayar hannunsa ya ɗago haɓarta suna fuskantar juna, gently ya matso da fuskarsa sai tin tata, tun bai karisa isowa ba, ta kurma ihu tare da farkawa daga barci, wani wahalallen zufa ne ke tsastsafo mata daga gefe da gefen fuskarta, ta yi sharkaf da fitsari sabida tsoro, wannan masifa da me ta yi kama, dafe kanta ta yi ta fara hawaye tana rokar Allah da ya sawwaƙa mata wannan bala'in kada hakan ya zama sanadiyyar taɓuwar ƙwaƙwalwarta ko kuma ma mutuwarta baki ɗaya, innalillahi wa inna ilaihir rajiun shine abin da ta fi yawan furtawa a ransa.

Tana zaune a wajen ta kasa motsawa har karfe 3, sannan ne ta ja jikinta da kyar ta iya sauƙowa kasa daga saman gadon ta nufi toilet, da kyar ta iya yin wanka tare da ɗauro alwalla ta fito, doguwar riga ta zura a jikinta tare da hijabi, ta shinfiɗa dadduma ta fara sallama tana kai wa Ubangiji kukanta, dan tasan ba mai cireta a cikin wannan azabar sai shi, baiwar Allah sai kugin yunwa cikinta yake, saboda bata ci abincin dare ba, da kyar ma take iya kai sallar saboda jiri na yunwa dake ɗibarta, abin ya taɓa ta sosai, har wani ramar lokaci guda ta yi, duk ta fita a hayyacinta, kuma duk wannan masifaffen son da take yi mashi tun tana yarinya ne ya ja mata hakan.

A daddafe ta yi sallah raka'a shida sannan ta rufe da shafa'i da witiri, ta zauna saman dadduma tana karatun Alkur'ani mai girma kasa-kasa, har lokacin yin raƙatainil fajir ya yi, haka ta miƙe ta gabatar da raƙatainil fajir ɗin ta, a raka'ar farko ta karanta Kulyahayyuwalkafirun, na biyu kuma ƙulhuwallahu ahad, domin Manzon Allah Sallallahu alaihi Wasallama ya ce falalar yin sallar raƙatainil fajir tafi duniya da abin da yake a cikinta, amma idan ka karanta wayan nan sururo guda biyun wato ƙulhuwallahu ahad da Kulyahayyuwalkafirun, falalar da zaka samu sai ya kai girman duniya sau biyu, dan haka kada muyi wasa da wannan dama, Allah ya bamu dacewa.

Bayan ta idar da Sallar raƙatainil fajir, ta ɗan zauna kaɗan, kafin ta gabatar da sallar asuba, yin hakan da ta yi kuma yana daga cikin sunnunin manzon Allah Sallallahu alaihi Wasallama, tsakanin sallar raƙatainil fajir da kuma asuba, annabi yana zama ya ɗan bada tazara na ɗan lokacin, yin hakan ma ba karamar falala bace.

Bayan ta yi sallar asuba sai ta yi askar nata, amma bata kai ga kammala askar ɗin ba barci ya ɗauketa a wajen, dan ta samu sauki sosai acikin zuciyarta, ta samu peace of mind, Alkur'ani mai girma maganin cuta komai girmanta, sallar nafila mai kawar da damuwa duk min girmanta, ta yi sallar ta roki Allah da ya shiga lamarinta hakan ya sanya ta samu peace, Baiwar Allah yana barci tana sauƙe ajiyar zuciya.

A haka Akila ta iskota misalin karfe 8 na safe, yau bata samu damar tashi ta yi shara ba bare kuma wanka da gyaran ɗaki har a kai ga girki. Akila ta sha mamakin ganinta a hakan, gabanta ta karisa tana ƙoƙarin taɓa ta, sai ta ji muryar Imran daga bayan ta yana faɗin "No heartbeat kada ki taɓa ta, ki kyaleta". Cikin sauri Akila ta juyo da kallonta kanshi, yana tsaye a bakin kofa jikinsa sanye da kayan barci riga da wando, da alama yanzu ya tashi daga barci, kuma da alama da tunaninta ya kwana shiyasa yana tashi ya nufi ɗakinta kai tsaye.

"Yaya Imran lafiya? Ko dai bata da Lafiya ne?". Juyawa ya yi ya nufi waje ba tare da ya yi magana ba, dan baya son su tashe ta daga barci, da sauri Akila ta miƙe ta bi bayansa, a palo ya tsaya yana bata amsa "Akila nima dai bansan meke damun Rimsha ba, amma dai tabbas na lura tana da damuwa, jiya ina da tabbacin bata samu barci ba, shiyasa take barci yanzu kada ki tasheta ki kyaleta idan ta tashi ta yi wanka muka samu natsuwa sai in ji menene damuwarta". Lokaci guda yanayin Akila ya canza, mood nata ya juya, sosai ta ji ba daɗi tana son jin meke damun yar uwarta.

Ganin ta shiga bad mood yasa Imran ya ce "Heartbeat kada ki damu ba komai In Sha Allah yanzu dai zoki gyara mana palo ko?".

To ta amsa mashi da shi, amma dai jikinta duk a mace, ta ji wani irin yanayi mara daɗi, ita bata son jin ance wani yana cikin damuwa ko kaɗan, hakan ba karamin ɗaga mata hankali yake yi ba. Ganin ya juya zai koma bedroom nasa ne yasa ta yi saurin cewa "Yaya Imran jiya waye ya zo ɗakin kan nan? Na gan shi da face mask ban iya ganin face nasa ba, amma dai daga ganin ga shin kansa nan ba ɗan Nigeria bane".

Ba tare da ya juyo ya ce "Heartbeat kin iya gulma ashe, to Saif ne, kuma ma ya tafi abinsa, sai na je nemansa yanzu, ki yi mani addu'ar Allah yasa na gan shi". Cikin sauri ta ce "In Sha Allah zaka gan shi" Allah yasa ya faɗa tare da wuce wa cikin bedroom nasa, ita kuma ta fara aikin da Rimsha take yi, dan yanzu ita ma ta iya.

To a ɓangaren su Michael kuwa, Wato Washington DC.

Yau zai koma school, tun safe ya shirya tsab ya haɗa duk abin da zai buƙata, suka yi sallama da Musharraf ya fito, da motarsa ya wuce school, kuma kamar dai a baya da su copper ya tafi, Lion ya ce 100 level zai koma, bai wani damu ba, ya yarda dan yanzu ilimi yake nema ido a rufe.

Michael na tafiya ba jimawa Tga ya shigo cikin ɗakin ya ce da Musharraf ya zo su ta fi, ba musu Musharraf ya biyo bayansa suka fito palon kasa, kai tsaye waje Tga ya nufa, dan yasan akwai camerori a cikin gidan, duk abin da ya yi Lion zai gani, hakan yasa suka nufi waje kawai.

Kai tsaye gym ya wuce, Musharraf na biye da shi, kuma bai kawo komai a ransa ba. Tsabar tsanar da ya yi wa Musharraf, baya son shi ko kaɗan, hakan yasa ya fara bashi horon sojoji, manya-manyan karafuna ya sanya shi ya fara ɗaga wa, Bawan Allah bai iya ba, amma saboda sanin bakin hali na Tga yasa ya fara koya, kullun Michael yana bashi labarin bakin halin da mugunta irin na Tga, yau kuma ga shi nan ya tabbatar.

Wani zabgegen bulalla Tga ɗin ya ɗauko ya ajiye a gefe, sannan ya ɗaurawa Musharraf wasu mayun karafuna a hannunsa ya ce dole sai ya yi tsayuwar minti talatin da su a hannunsa, Innalillahi wa Inna ilaihir rajiun, a wannan hali John ya zo ya same su, cikin halin nuna ko in kula John ya ce "Uncle T what is going on here?".

A kule Tga ya ce "John this guy ashe musulmi ne" a sukawane ya juyo da karfi ya furta "What??!!" Yayi maganar yana zaro ido waje.

"Yes John musulmi ne, ɗazun by 5:30 na shiga bedroom na Michael zan tasheshi daga barci ya zo ya fara gym, na shiga bedroom nasa baya nan, har zan fita part ɗin sai kuma na ce bari na leƙa ɗayar ɗakin ko yana can, to a nan na gan shi yana bautansu, shi kuma Michael ban gan shi a cikin ɗakin ba, a lokacin na kira Lion bai ɗauka ba, sai daga baya ya kirani da na gaya mashi sai cewa ya yi wai na bari sai ya dawo, Musulmi fa a gidan nan, amma Lion yana cewa abari sai ya dawo, to ba zai yi wu ba, kafin ya dawo dole na fara bashi horon, sai ya yi dana sanin zuwan shi gidan nan, kai sai na ma ji dalilin da ya sa ya zo gidan nan, dan daga gani kasan turoshi aka yi, kasan musulmai yan ta'adda ne, wata kila wani abin suke shiryawa, to mun fi karfinsu, shima Michael dole ya rabu da mutumin nan, yana dawowa idan na gaya mashi musulmi ne, dole zai rabu da shi, bakin shaiɗani, mugaye yan ta'adda mu dai mun fi karfin ku" ya kai karshen maganar yana wani huci kamar zaki.

Rai a matukar ɓace John ya ce "Tabbas Uncle T wuya zaka ba shi ba ɗan kaɗan ba, sai ya yi danasanin zuwan shi duniya, sai ya gwammaci da bai san familyn William jacop" ya kai karshen maganar tare da ɗaga kafa ya taka Musharraf ɗin a kirjinsa da karfi.

Baya baya Musharraf ya yi Allah sarki ya faɗi kasa ga kuma karafuna a hannunsa, suka danne mashi hannun, wannan zabgegen kafuran bulalar Tga ya ɗauko, ya fara zana mashi a jikinsa wai ya faɗin, bulaka biyar masu lafiya ya yi mashi sannan ya ɗage shi ya tsaida shi, ya sake sanya mashi karfen ya ce wai sabon kirga za'a fara.

Bawan Allah shi zane shi da suka yi ma bai wani dame shi ba, abin da ya dame shi nauyin wayan nan karafuna.

Cike da bada umarni Tga ya fara zuba mashi kashedi da kuma dokoki kamar haka "Daga yau kullun karfe 5 na safe ka tabbatar ka zo nan ka fara ɗaga karafuna kafin na fito, na biyu kuma da yamma dole ka kasance a wajen ruwan kankara, da daddare idan kowa yana barci, dole kai ka zo wajen tsere da doki domin ku yi tsere da dawakan, ba zaka taɓa yin barci ba sai ka yi tsere da dawakan kafa 30, da rana kuma ka kawo kanka da kanka cikin tsakiyar rana ka kwanta kana kallon sama, ka kalli rana sosai, idan kuma ka sake ka gayawa Michael sai na kashe ka, ko da yake ma shima Michael ɗin idan ya san kai Musulmi ne to ba zai barka ba, zaka karɓi nasa horon". Bawan Allah da kyar ya iya amsawa da to, haka Tga ya cigaba da zabtar da shi da horon sojoji har zuwa karfe 11 na rana sannan ya kyale shi ya wuce cikin gida domin ya je ya shirya ya wuce wajen aikin

Zama a wajen Musharraf ya yi ya kasa motsawa saboda gaba ɗaya ko ina na jikinsa ciwo yake yi mashi, hannunsa duk sun kumbura, da kyar yake iya numfashin, daga karshe kwanciya ya yi a wajen saboda bala'in azaba da ya sha.

Allah sarki, idan muka waiwaya gida Nigeria kuma, Akil yana fita daga part ɗin Imran kai tsaye bedroom nasa ya nufa, Umaisha bata ciki, fitowa ya yi ya duba Kitchen bata nan, abin ya bashi mamaki, haurawa sama ya yi izuwa ɗakin Ammie, ton daga bakin kofa ya fara jiyo kukanta kasa-kasa, cikin sauri ya tura kofar ɗakin ya shiga, tana tsugunne a tsakiyar ɗakin, ta haɗe kai da gwiwa sai kuka take yi, hannunta na ruƙe da tovel na goge goge, ita kuma Ammie tana hakimce a saman gadon ta ɗaura kafa ɗaya bisa ɗaya tana latsar waya.

Da karfi ya furta sunan ta "My wife!" Cikin sauri ta ɗago, fuskarta duk ya yi jaga-jaha da hawaye da majina, da alama dai wani abin mugunta Ammie ta yi mata.

Kasa magana ta yi ta mai da kanta kasa ta cigaba da kukan da take yi, da sauri ya kariso cikin ɗakin ransa idan ya yi dubu to ya ɓaci, dan bai son abin da zai taɓa mashi ita,. Yana zuwa ya sa hannu ya ɗagota ya rungume kayansa, ba tare da ya yi magana ba ya wuce da ita suka fice daga cikin ɗakin, ko sannu Ammie bata ce mashi ba, shima kuma bai ce mata ba, sai bayan ya kai Umaisha bedroom nasu ne ya dawo ɗakin Ammie ɗin, a bedside drawer ya zauna, cike da girmamawa ya fara magana.

"Ammie me ya faru yau kuma tsakaninki da yar taki?". Shiru ta yi mashi bata kula shi ba, ganin haka yasa ya riƙo hannayenta yana bata hakuri.

Ta ɗan ɗauki lokaci kafin ta ce "Ka sakar mani hannu, tun da matarka ta fini muhimmanci, wato ni ban isa in hukuntata idan ta yi mani laifi bako? Shine zaka zo ka gwada mani isa akanta ko? To ka je, ina dai mace ce zaka gani iya ganin idanunka". Kara yin kasa da murya ya yi cikin sigar bada hakuri da rarrashi ya fara magana "Ammie na san ban kyauta ba, amma kiyi hakuri sharrin sheɗan ne, kuma

Please Login or Register in order to submit comment