You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

kallon y’ar ficilar rigar da take jikin Amanin da ta bayyana duk wata sura mai nuna
cikar d’iya mace. Ta gyara mata gashinta sannan ta tasheta zaune. Dahdan yana tsaye yana kallonta abin
duniya duk ya dameshi so yake ya yi nazari ya gano bakin zaren don an zo gab’ar da ya kamata ya binciki
al’amarin mai kama da Almara. Amani kasa ha’da ido da shi ta yi ga kunyar rigar da take jikinta wacce da
ita da babu duk d’aya. Imaan ta sha yi mata fa’dan kwana haka amma bata ji. Dahda ya juya yana fita
daga d’akin da saurinsa.




Tunda ya shiga d’akin bai zauna ba, zagaye kawai yake zuciyarsa cike da tunani… Dole akwai ayar
tambaya me yasa al’amarin yake faruwa haka? Bai bar tunanin ba sai da ya ji kansa yana neman tsawa
sannan ya zauna rik’e da kan nasa yana danna numberr Muhammad Alwan don kamar shi ya kamata ya
tambaya. Me yasa abubuwan suke tafiya a haka kamar wani sihiri? Duk da san dalili. Ya ja fasali a hankali
ganin Alwan d’in bai d’aga waya ba ya saki tsaki ya yi cilli da wayar. A lokacin kamata ya yi ya mik’e ya Yi
sallah sai dai ya kasa. Hannu kawai ya saka cikin sumar kansa yana yamutsawa a hankali.




A safiyar ranar da al’amarin zai faru. Safna..ta ziyarci wani Daji a Bidda da ke jihar Neja.

….. Motar su tana tsayawa a k’aramin Dajin Safna ta saki ajiyar zuciya tana jin tazo inda duk wata
buk’atarta zata biya. Boss lady dai kallonta take tana sake jaddada mata “Ki nutsu Safna ki gaya masa duk
abinda kike so, wallahi aikinsa kamar yankan wuk’a ne.” Ta d’aga kai “Dole ma ai, nifa naga abinda na gani
k’awa. Tsawa fa Moddi yake min kamar ba wanda da yake tsoro na ba. Ba ma wannan ba, ni yanzu burina
na cikawa Alwan buk’atarsa ko na samu ya zube min manyan ku’din da ya alk’awarta min. Idan har na
samu haka wallahi Boss lady ni da duk wani nawa mun yi hannun riga da talauci.




Tunda suka shiga wajen suke jin tsigar jikinsu na tashi sabida wasu irin abubuwa da suka dinga karo da su
a bukkar.
Sun kusan minti biyu zaune kafin matar ta ‘dago da jajayen idonta tana kallonsu. “Mun san

Me ke tafe da ke… Kin yi wani kuskure a rayuwarki, da baki zo nan ba ina tabbatar miki komai zai iya
faruwa… Kin amince da ya yi arziki duk da duhun da aka ce miki an gani a k’arshen arzikin nasa….Me
kike so a yi?” Safna ta ha’diye wani yawu mai kauri ta furta “Burina kawai a mallaka min shi mallaka ta
har abada….kuma ina son na haihu da shi abin ya fara damuna…” “Ba zaki haihu da shi ba har abada!”
Bokanyar ta fa’da da k’arfin gaske. Za mu mallaka miki shi irin mallakar da kike so sai dai mahaifiyarsa a
tsaye take a kansa sai kin yi takatsantsan.” Haka Bokanyar ta zauna ta ha’da mata duk wasu surkulle ta
bata tana jaddada mata yarda zata yi amfani da su. “Kada a samu kuskure!” Safna ta gya’da kai. “Sai
yaransa ina son a raba shi da su ya ji ya tsanesu…” Bokanyar ta buga wani abu da sauri ta wurgar ta furta
“Ba zamu yi aiki akan haka ba an garga’demu ku tashi ku bamu waje…” Safna yawu ta ha’diye da k’yar
me yasa duk bokan da ta je masa da son irin wannan aikin sai ya ce ba zai iya ba. “Ni dai ki taimaka ko
karuwai ku mayar da su… sannan ina son a

Azalzala soyayyar junansu a tsakanin Amani da Moddibo har su kusanci junansu na cika burin Alwan, ko
nima

Nawa burin zai cika, duk

Inda na je har yanzu ban samu

Cikar burina ba.” Wani kallo Bokanyar ta mata tana furta “Wannan an gama, ki je zaki ga abinda zai
faru…”Safna ta mik’e jikinta na rawa duk da farin cikin da yake cin ranta sai ta ji tsoro da fargaba kuma
sun shigeta. ta furta a ranta “Duk bala’i sai na mayar da yaran nan karuwai ko ta halin k’ak’a kuwa, tunda
ni ba zan haihu ba gwara kowa ma ya rasa. Ai Hajjan ba zata yi alfahari da karuwan jikoki ba. Musamman
a ce Uba ne ya kusanci y’arsa, ya aikata zina da ita, kuma ita zan saka ta yi ta bibiyarsa.Ta fa’da a ranta
tana cije leb’enta. Boss lady ta kalleta “Lamarin yaran nan abin mamaki. Me yasa duk cikar bokaye basa
iya aiki a kansu, sai yanzu burinmu zai cika. Safna lumshe idonta ta yi tana furta “Da sannu zan samu inda
zaa min wannan aikin, don na sha alwashin in dai ina raye sai na mayar da su karuwai musamman
Amani…” “Ina bayanki wallahi, ni kaina na tsani shegiyar yarinyar nan, ga kyan tsiya kamar ita ta k’era
kanta…”




A haka suka koma gida suna ta aikata mugun abin su. Tana zuwa gida kuma ta aikata duk abinda
Bokanyar ta ce, sannan ta fara shirin komawa gidanta cikin farin ciki da tunanin yarda zata juya
Moddibo…
…….



Da safe basu tashi da wuri ba, dalilin rashin samun isashshen barci da ba su yi ba. Har Mama Talatu ta
gaji ta shiga d’akin nasu wajen k’arfe 11:30 don ta tashe su.



Iman ta bu’de ido da k’yar ita ta fara tashi sannan Amanin. Mama Talatu tana kallonsu ta furta “Ku kuwa
yau lafiya kuke? Ku baku tashi ba shima mai gidan har yau bai fito ba?” Iman bata yi magana ba sai shiga
toilet da ta yi. Amani Kuma ta d’an rik’e kanta tana jin a yau dai kam kunya ba zata barta ta fita ta ga
Dahda ba. Mama Talatu ta ce “Amma dai Magajiya baki da lafiya ko?” D’aga mata kai kawai ta yi. “Ko da
na ji, don ga idonki nan ya nuna haka, Allah ya baki lafiya ki yi wanka sai na kawo miki abincin karyawarki
cikin d’aki” D’aga mata kai ta yi don bata jin yau zata iya fita su yi ido biyu da Dahda.




Dahdan yana zaune a parlor Iman ta fito cikin shigar casual shirt. Ta durk’usa ta gaishe shi daga gefe. Ya
amsa mata yana sipping hot coffee a hankali, idanunsa akan Laptop d’insa ya furta “Amani fa? How is she
feeling?” Iman kanta kunyar Dahdan take ji ta furta “Da sauk’i.” “Ki tasota ta sha tea, idan kun gama shan
tea d’in kuma zan yi meeting da ku..” Iman kanta sai da ta ji fa’duwar gaba. Ya d’ago yana kallonta ya ji
dalilin shirunta. “Ki je mana..” Da sauri ta mik’e har tana yi kamar ta kifa ta tafi da sauri wajen kiran
Amanin.




A zaune Amanin take ta tafka Uban tagumi, tunani ne kawai ya cika mata kwanya irin tunanin da idan
kana yin sa kake jin kamar kwanyarka zata tarwatse.. “Ki zo in ji Dahda..” Sai da cikinta ya wuntsila tsabar
shiga firgici ta ‘dago da k’yar ta furta “Ki ce ina barci..” ragowar maganar ta mak’ale mata ganin Dahdan a
tsaye a bakin k’ofar ya rungume hannunsa a k’irji. Tun kafin ya yi magana ta mik’e da sauri tana fidgeting
yatsunta. Ido kawai ya k’ura mata ya juya ya fita daga d’akin. Amani bata san ta saka Hijab ba tsabar
razana ta bi bayansu da sauri tana jin kamar zata fa’di sabida yarda k’afarta take har’dewa. Dinning ya
nuna mata bayan tazo ta tsaya masa a kai. Duk da idonsa a lumshe yake ta san me yake nufi ta je ta ci
abinci. Ba musu ta isa dinning d’in.. Duk ta zama wani sukuku kamar ba Amani Uwar tsiwa ba. Cin abincin
take kawai ba tare da tana banbance taste na zak’i da gishiri ba. Ta dai samu ta caccakala ka’dan ta kurb’i
ruwan tea d’in. Kafin ta ajiye cup d’in ta kifa kanta a saman dinning d’in. “Ku zo nan.” D’in da Dahda ya ce
ya k’ara mata bugun zuciyatta. Ta ajiye ta mik’e a hankali ta bi bayan Imaan.
Suka zube a gabansa. Tsawon mintuna biyar yana danna wayarsa. Kafin ya ‘dago Imaan ya fara kallo kafin
ya mayar da kallonsa kan Amaan da gaba d’aya bata da nutsuwa. Yana zagaye fuskarta da kallo yana
tambayar Imaan d’in. “How long ta ‘dauka tana kalar wannan mafarkin?” Ba Amani ba hatta da Iman sai
da tambayar ta razanata. Ya sake furta “Are you dumb Amani?” Ta girgiza kai “Ta da’de zai kai One
year…” Ya mayar da kallonsa kan Imanin ya furta “How is she react a cikin mafarkin…..” Imaan ta ha’diye
wani yawu mai d’acin gaske. Ta ja baki ta tsuke don wallahi ko me aDahda ya mata ba zata iya bu’de baki
ta gaya masa ba. Shi bai san jiyan ma mugun k’ok’ari ta yi wajen yakice kunyar ta yi ta gaya masa ba.
Dahda ya mayar da kallonsa kan Amani da ta cukuikuye gefen mayafinta ta matse shi tsam a hannunta.
“Hakan ya nuna aure kuke so? Tunda kun fara irin wa’dannan mafarkan?” Imaan ta ware ido Amani kuwa
ji ta yi zuciyarta ta daina bugun da ya kamata don Kallon da Dahdan yake mata jefa ta yake cikin wani irin
yanayi. “Na baku dama ku fitar da Miji nan da sati biyu, ku tashi ku tafi ku ba ni waje..” Imaan ta ‘dan
bu’de ido “Dahda karatun fa?” “An fasa..” Ya fa’da yana lumshe ido ha’de da murza goshinsa…




𝔍𝔦𝔨𝔞𝔯 𝔑𝔞𝔰𝔥𝔢★ ✍️HADARIN GABAS…..👌


NAZEEFAH SABO NASHE★ ✍️

08033748387.




_*🔥BRIGHT PENS...🔥*_
2nd batch

Zazzafar tafiya mai abin ban mamaki, tawayen jerin marubuta huɗu a sabuwar tafiyar ta second batch.
*HADARIN GABAS*

Nazeefah Sabo Nashe



*ƘARFE A WUTA*

Ayushercool



*ZAYTOON*

Zee kumurya



*MUTALLAB*

Nimcyluv Sarauta.




Page 16.




Ganin yarda yanayin launin idonsa ya sauya ne yasa suka San a duk maganganunsa ba wasa. Jikinsu a
salub’e suka mik’e da niyyar barin wajen. Dadan ya bi su da kallo da lumsassun idanunsa kafin ya saki
ajiyar zuciya. A zahiri ya furta “Ya Ilahi! What is this?”




Tunda suka shiga d’akin zama suka yi a gefen gado kowa zuciyarsa cike da tunani. Imani bata da fargabar
aure don tuni zuciyarta ta aminta da Mus’ab d’an gidan Umma J.. Amani ce mai fargaba. Fargabar da ta
kasa b’uya a saman fuskarta ta dinga sakin huci a hankali k’irjinta na wani irin bugu. Tabbas ta San
wannan ranar zata zo ranar da zata auri wani ba Dada ba, Amma ta ya zata iya yakice bahagon tunanin
soyayyar Dada a ranta. Abinda take ganinsa da kamar shirme sai dai a yanzu ta tabbatar da gaske son
Dada take… Imani ido ta bita da shi ganin yarda take zubar da hawaye idonta a lumshe ga k’irjinta yana
sama da k’asa alamar sauyawar bugun zuciyarta. Cike da rauni ta dafa cinyarta tana furta “Ama….” Bata
amsa ba sai dai ta Ware idonta da suke cike taf da hawaye akan Imanin. Kallonta take irin kallon cikin
k’wayar ido, tana girgiza mata kai. Ta furta “Ya kamata ki San Decission d’in da Dada ya yanke shine
abinda ya kamata. Ga duk wanda ya ganki a yanayin jiya kuma zai tabbatar da aure kike so don haka
auren shine abinda ya dace da ke wallahi, ina bayan Dada a wannan gab’ar nima.” Idonta ta sake
lumshewa cikin wata irin dasashshiyar murya ta furta “Wa zan aura?” “Mahmud.” Iman ta amsa mata
kanta tsaye. Amani ta girgiza kai tana furta “bana jin son sa a raina ko ka’dan.” A zafafe Iman ta ce “Dole
ki koyi son sa, idan ba ki so shi ba wa za ki so? Gwara ma ki farka daga shirmen mafarkin ki, ki sani ba
aure a tsakaninki da Dahda ba mamaki shai’dan ne yake son shiga cikin zuciyarki ya jefa miki ru’dani.
Menene aibun Mahmud d’in? Yana da kyau, ku’di, hankali da duk wani abu da za ki so a tattare da
namiji….” “Duk da haka bana son sa,sai dai a yanzu ba ni da wata mafita da ta zarce ta Auren Mahmud.
Shikkenan hankalinki ya kwanta?” Iman ta saki ajiyar zuciya tana furta “Alhamdulillah, sai ki kira shi ki
sanar da shi kin amincewa aurensa…” Amani ji tayi zuciyarta na mata wani irin zafi. Ta runtse idonta
kawai tana cije leb’enta kamar yarda Dahda yake yi a lokuta da dama idan yana cikin tashin hankali. A
komai na Dada wannan kawai Amani ta d’auko. Shiru ta yiwa Imani ba tare da ta kira Mahmud d’in ba, sai
dai a k’asan ranta tana jin tabbas amincewa Auren Mahmud shine solution na matsalarta.




Tunda ya sallamesu ya lumshe idonsa yana jin yarda zuciyarsa ta sauya launin bugunta zuwa matsanancin
bugu. A lumshe idon nasa yake kafin ya d’au wayarsa ya danna kiran Alwan. Kamar yarda zuciyar tasa
take ta uzzira masa ya aikata hakan. Kamar Alwan ba zai d’aga ba sai kuma ya ‘d’aga har yana sakin sautin
murmushi da Imaam ya sanya shi a mizani na rainin hankali, Eeh rainin hankali mana. “Ina jin ka Imaam,
me ka yanke a kan maganar mu?” Imaam ya runtse idonsa yana jin har idan zai bu’de baki ya yi magana
to zagin Alwan zai yi. Sai ya girgiza kai ya furta “Me ka aikata Alwan?” “Babu!” Alwan d’in ya fa’da cikin
ginshira tsabar takaici Moddi bai San sanda ya kashe wayar ba. Ya jingina bayansa da kujera. Cikin
zuciyarsa yake jin ba zai tab’a iya abinda Alwan yake so ba.




Sai dare sannan Amani ta kira Mahmud. Kamar kuwa jiran kiranta yake ya d’auka daga bugu guda kawai.
“Princess yau wace rana? Ke da kan ki kika kira ni.” Ta runtse idonta kawai tana jin yarda bugun zuciyarta
yake k’aruwa. “Talk mana Amaa…” ya furta cike da zakwad’in son jin muryarta. A hankali ta furta “Za ka
samu zuwa gida gobe?” Wata irin zabura Mahmud ya yi cike da farin ciki ya ce “Why not today…” Amani
ta lumshe idonta yana daga dalilin da Har yau bata ji tana son sa ba saboda Mahmud ba shi da Aji irin na
mazan da take so bata sani ba ko don yana matsanancin son ta ne? Murya a cunkushe ta ce “I Said
tomorrow Mahmud.” Ya lumshe idonsa yana furta “Shikkenan Princess Allah ya kai mu? Amma kafin nan
ba za ki gaya min ko menene ba? Kada ki saka na kasa barci.” Bata yi magana ba ta datse kiran kawai cikin
b’acin rai, me ye zai uzzira mata tunda ta ce gobe ba sai ya bari sai goben ba ita fa bata son naci.” A daren
dai Kam Amaa bata yi wani barcin kirki ba juyi kawai ta dinga cikin wani irin hali. Bata tashi Imani ba don
bata son ta ganta a yanayin da take. Hoton Dada ta zubawa ido kawai tana jin feeling d’in abinda take ji
yana sake zafafa. Idonta k’uri akan hotunan da take da folderrsu guda a cikin wayarta ta lumshe idonta a
hankali cikin wani irin yanayi ta kifa fuksar wayar a saman fuskarta ta saka bakinta daidai na Dahdan tana
sumbata da gaske dai kamar a haukace take. Hauka mana mahaifin da ya haifeka? Ita kanta ta fara
tunanin ta haukace. Hawaye wani na bin wani take shafar fuskar Dahdan tana furta “I Love you….”




Da safe da suka tashi dukkansu ba wani walwala a tare da su. Imani kam lalurar y’ar uwarta ce ta dameta
don duk abinda ta yi jiya da daddaren ta ji shiru kawai ta mata don bata son ta San idonta biyu ma.
Amma abin ya dameta ya kuma tsaya mata a zuciya don haka ta ji kawai gara ta gayawa Umma teey idan
ma magani ne a samar mata idan kuma Aljannu ne a yi gaggawar rabata da su. Suna fita suka tarar da
abin Mamaki Mommy ce cikin zafaffiyar kwalliya Dahda a gefenta tana cin chewingum tana ganinsu ta
gintse fuskarta. Ba su san ta dawo ba musamman Amani da ta ji wani bak’in ciki da rashin jin da’din
dawowar Mommy gidan. Wani irin kishi mai zafi ta ji yana shirin sark’afe mata numfashi ganin Mommyn
a jikin Dahdan sosai shi kuma idanunsa a lumshe tana sosa masa gashi. Kansa a saman cinyarta. Ganinsu
bai saka ta fasa abinda take ba. A hankali Dahda ya bu’de idonsa jin kamar ba su ka’dai ba ne. Da sauri ya
mik’e ganin twins d’insa. Fuskarsa a d’aure ya ce “Ba ku iya sallama ba ne?” Imani ta yi saurin yin k’asa da
kanta tana furta “Am sorry Dahda ba mu San kuna zaune ba.” Ama kuwa turo bakinta ta yi kafin ta juya ta
koma hanyar d’akin. Mommy ta bita da kallo baki sake tana furta “Mhmhn.” Dada ya d’an kalleta ya ce
“What?” “Hamshak’iyar y’arka na gani ji fa abinda ta maka, wai Imaam me yasa baka son hukunta
yarinyar nan? nema fa take ta raina ka ji yarda ta yi da baki.” Lumshe idonsa ya yi kawai ba tare da ya ce
komai ba yana jin Mommyn na ta masifa kamar zata ci babu. A hankali ya ja ta jikinsa ya manne bakinsu
wuri guda yasan hakan kawai zai mata ta yi shiru. Shirun kuwa ta yi tana jin dama ya kusanceta wata irin
zazzafar sha’awarsa ce take fusgarta sai dai ta San ba dama don a k’aidar wancan sirrin nasu yau ba ranar
da Dahdan zai kusanceta ba ne. Bata manta kashedin Alwan a cikin kunnuwanta “Kin amince sau d’aya zai
kusanceki a sati biyu? A wata sau biyu kenan?” Bata yi wani tunani ba ta ce ta amince don burinta ku’di a
wancan lokacin sai dai ba a kai ko ina ba ta fara gane shayi ruwa ne, don Kharija ce ita mai tsananin
buk’ata hakan yasa bisa dole ta fara bin mata don su gusar mata da kewar Dada sai dai basa iyawa don
Dada na daban ne a cikin maza na musamman bata jin za’a iya samun irin Moddin Didi guda biyar a cikin
d’ari. Jikinta Har rawa yake tana jin kamar ta saka kuka so take kawai Moddi ya kusanceta amma ba dama
a lissafin ta ma sanda suke da damar kusantar junan tana cikin ranakun ta na al’ada hakan yana nufin sai
wani watan kenan? Ga matsala guda rashin haihuwa abin ya dameta bata san Moddi ya bayar da
mahaifarta ba. Yana ganin yarda jikinta ke rawa janyeta ya yi kawai daga jikinsa yana murmushin k’asan
baki, dariyar mugunta ce fal a ransa don ita ta jawowa kanta son ku’di ya ja mata a lokacin sai da Alwan
ya bata zab’i idan ba zata jure ba ta bari a mata kishiya da matar da zata jure Amma ta ce bata son
kishiya. Ta dinga bin Moddi da ido da yake takunsa kamar ingarmar doki sam ba abinda ya damesa. Duk
da a saninta Moddi ma yana da zafin sha’awa sai dai yanzu bata San inda ya kai k’arfin sha’awar tasa ba.
Bin Mata! Ta ji zuciyata ta haska mata. Ta runtse idon madadin ta ji zafin abin sai ta ji hakan yafi mata da
kishiyar gida gwara ta waje. Abin kunya ne a wajenta a ce yau Moddi ya mata kishiya dariya y’an group za
su mata don ba’a tab’a ba ba kuma za’a fara a kanta ba.




Imaan a hankali ta gama shirya komai a dinning Ama kuwa tunda ta shige d’aki bata fito ba. Takaicin
dawowar Momny ne kawai yake nuk’urk’usar zuciyarta ji take kamar ta hallaka matar saboda tsananin
zafin zuciya. Mommy na kallon Imaan ta ce “Ina hamshak’iyar?” Imaam ta ajiye tea flask a saman dining
kafin a hankali ta ce “Bata da lafiya.” Mommy ta tab’e baki tana girgiza kai ta zauna a saman dining d’in.
Banda yanayin da take ciki yana damunta ba abinda zai hana yau ta yiwa yarinyar duka. Sai dai komai ya
kusa zuwa k’arshe idan har ta bi shawara k’awayenta tana fatan cimma nasara in sha Allah. Bata jira Dada
ba ta fara narkar abincin son ranta, shi yasa take k’iba kamar me, don bata saurarawa abinci. Dahda da ya
fito ya zauna yana kallon table d’in Imaan ce kawai ba Amaa. “Ina Amaa?” Ya furta yana kallon Imaan.
Imaan ta mik’e tana furta “Bari na kira ta, bata jin da’di ne.” “Zauna.” Moddi ya ce yana mik’ewa ya nufi
hanyar da zata kai shi d’akinsu. Imaan ta runtse ido tana jin gabanta na fa’duwa sam bata son keb’ewar
Dada da Amaa Amma bata isa ta nuna ba. Yarda yake taku kamar yana taku ne da bugun zuciyar ta. Bai yi
making any sound ba ya tura k’ofar a hankali ya shiga bedroom d’in. Idanunta a lumshe suke kamar mai
barci sanye cikin wando da rigar jeans a hankali Dahda ya lumshe idonsa yana jin abu yana dukan
zuciyarsa har ya k’arasa bakin gadon idanunsa zube a kan surarta. Komai yana sake ta’azzara a ransa.
Hannu ya saka ya zare wayarta da ta rungume a k’irji. Idanunsa ya sauka a kan rubutun da take yi cikin
diary d’in wayarta wasu irin words zafafa a k’asan hotonsa kamar dai saurayinta ko mijinta. Words d’in shi
kansa sun masa girma bai San kuma a inda ta samo su ba. Idonta a lumshen bata bu’de ba duk da tana
shak’ar k’amshin sa sai dai a zatonta imagination d’in da ta Saba ne ta San ba abinda zai kawo Dada
d’akinsu a wannna lokacin. A zafafe ta ce “Imaan ajiye min wayata kada ki ga abinda zai hana ki barci. Kin
kasa yarda da abinda nake gaya Miki wallahi da gaske ina jin son Mahaifina shi zai yi ajali na…..”
“Amaaa…!” Ya fa’da cikin dakakkiyar muryar da ta saka Amani saurin bu’de ido hankalinta a tashe ta ce
“Dah….” Kallon da yake mata ne yasa ta San tabbas ya karanta abinda ta rubuta a cikin wayar. Hankalinta
ya tashi ta dinga jin bugun zuciyarta yana sake ninkuwa jikinta ya fara rawa. Wata irin fusga Dahda ya
mata ta dawo daf da shi. Sunkuyar da kanta ta yi jikinta na shaking. Dahda kallon ta shima yake nasa
hankalin yafi nata tashi. Me yasa? Ashe itama tana jin abinda yake ji? Me ye hakan? Zagayeta kawai yake
da idonsa kafin cikin wata irin murya ya ce “Kin haukace ko?” Ta yi saurin d’aga kai a hankali ta furta
“Wallahi ni kaina na San na haukace Dahda pls ka yi min afuwa wallahi Ban san me ya same ni ba…”
kallonta yake a zuciyarsa shima yana furta “Ni kaina na haukace Amaaa…. Alwan ya haukatamu me ya
shiga kai na wace irin matsala na jefa kai na son y’ar cikina?” Jira take ta ji ya mata magana sai ta ji ya yi
shiru ta San ba mamaki tashin hankali ne ya hana shi magana. A hankali ta ji kamar an rufe k’ofa da sauri
ta bu’de idonta ganin Imaan a tsaye Dahda ya ajiye wayar ya fice daga d’akin. Imaan ta bi shi da kallo
kafin hankali tashe ta isa wajen Amani ta kama kafa’darta ta girgiza tana furta “Amaaaa menene?” Amaa
da shock d’in da ta shiga har lokacin bai saketa ba ta fa’da jikin Imani tana sakin kuka ta furta “Daaa,
Knows everything Imani ya zan yi? Ban san hukuncin da zai d’auka a kai na ba.” Imani ta Ware ido ta ce
“How comes? Ta Yaya ya sani?” Amani lumshe ido ta yi tana nuna mata wayarta. Jikinta na rawa ta d’au
wayar karatun take ita kanta tana jin hankalinta na sake hauhawa bata tab’a sanin akwai wannan a wayar
Amaan ba da bata barta ta ajiye ba ko don gujewa zuwan irin wannan ranar… Amani kifewa ta yi a
saman gado tana sakin kuka mai tsuma zuciya tabbas da wannan abin gwara a ce bata raye ta bi Mammy
itama ta huta da wannan masifar. Eeh masifa mana abu sai ka ce almara. Tunda take bata tab’a jin me irin
matsala kwatankwacin irin tata ba. Imani ficewa ta yi jikinta a sanyaye ta zaga can baya. Wayarta ta ciro
ta kira Umma teey. Ta fashe da kuka tana cewa Umma teey ki yi waya ki cewa Daaa a kawo mu zamu raka
ki unguwa ina son gaya Miki wani abu ne, amma don Allah kada ki ce ni na kira ki.” Umma teey da ta ji
gabanta ya tsinke ya fa’di ta ce “Okay” muryar ta na rawa ko minti guda bata k’ara ba ta danna kiran
Kiddo. Wayar ya bi da kallo yana jin zuciyarsa na sake masa bugu, ga nauyi da ta masa. Sai da wayar ta
katse ta sake kira sannan ya d’aga wayar a kasalance idonsa a lumshe ya furta “Teey.” Fatima ya saki
ajiyar zuciya ta ce “Kuna lafiya Kiddo?” Ya d’aga kai kamar tana ganinsa sai kuma ya tuna bata ganinsa
don haka ya ce “Lafiya.” “Alhamdulillah ta furta a hankali. “Saka Driver ya kawo min su Amaa, anjima za
su raka ni biki.” “Okay.”

Kawai ya ce yana cutting kiran bai kawo komai a ransa ba ya kira layin Imani ya ce “Su shirya Driver zai kai
su gidan Umma teey.” Imaan ta kalli Amaa ta ce “Ki shirya Daaa ya ce a kai mu gidan Umma teey.” Amaa
bata ji komai a ranta ba, Allah yasa ma gidan Umma teey d’in zasu koma ko ta daina ganin Daaa ta daina
jin abinda take ji game da shi.” Tsaf suka shirya dukkansu ba walwala. Imani ta ha’da musu kaya kala biyu
a akwati don ta San

Please Login or Register in order to submit comment