You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

Rabon ba kuma inajin hakan a jikina tabbas akwai wannan ranar, ranar da za'ayi tankaɗe da rairaya da yardar Allah"

Jinjina kai yayi yace, "hakane Allah yasa mu dace Ayeeahah, amma da kin faɗamin bakyason sa tin farko ai da na ɗauke ki mun gudu ko??"

Yaƙarasa Maganar yana dariya.

Itama dariya tayi sosai kafin tace, "sai kace ba namiji ba??"

Yana dariya yace, "gaskiya da kuwa son zuciya da ɓatan hanya me kyau yayi yawa"


Lumshe ido kawai tayi ba tareda tace koma ba.

Zeyi magana Rookha ta shigo da sallama tace, "Mama na nemanki Aisha"

Gyaɗa kai tayi cikin sanyin jiki.

Kallonta yayi cike da kulawa yace, "Ayeeshah tashi kije"

gyaɗa kai kawai ta sakeyi Tana son tashin amma jikinta yayi nauyi gashi bata gaji da ganinsa ba, sai da yaƙara magana tareda miƙewa tsaye sannan itama ta tashi.


Tafiya take tana haɗa hanya saboda ɗan jiri da takeji gashi idanunta kamar an watsa yaji sun wani ƙeƙashe.

Hannunta Rookha taja tana cewa, "wallahi ba ruwan Mama mu muke nemanki ina cewa ina kika shiga ashe kina can kina kashe Love"

Bata iya cewa, ƙala ba sai murmushin da baya wuce kan leɓe"

Kallo ɗaya Nuriya tai mata tagane tana cikin matsanancin yanayi dan haka tace, " yakamata muje mu kwanta wallahi"

Rookha tace, "wallahi nima nagaji dama ga wadda muke nema nan kuma mun samu dan haka mu kama mu tafi"

....

Ita lokacin ma har tayi gaba,
Sai da tasha ruwa kaɗan saboda bushewar da maƙoshinta yayi sannan ta kwanta.

Har suka gama surutunsu kowa yayi bacci ita baccin ya gagareta tunane tunane sin addabeta, har gari ya waye batayi wani bacci me daɗi ba sai juye juye da take da ƴan ƙananun mafarkai, abun ya tsaye mata a rai ainun, ta kasa babbance tsakanin Jose da Khaalif abun tambayarma menene dalilinda yasa kowa yake sonta? shin dama ana samun mace irinta a duniya wadda da namiji ya ƙyalla ido akanta shikenan? anya ma kuwa son gaskiya suke mata ba na wani abu ba??, so da yawa takanyi wannan tunanin amma idan ta tuna kalaman Jose sai taƙara jin takaraya batajin ko da wasa akwai kalmar da ya faɗa mata wadda ba gaskiya ba ta lura da gasken gaske yake har yafi Khaalif Mohammad zurmawa dan ahi a lokaci ɗaya ya bayyana mata abunda bata taɓa zata ba amma ga wanda taso tin asali Khaalif shi kuma yakasa wani motsi har saida lokacin ya wuce.

Tin safe ta tashi tayi wanka ta haɗe cikin wani lesi kalar marun me ratsin bulu kwalliyar ta-ta ba wata bace daga hoda sai man baki ko kwalli ba son sakawa take ba, Amma duk da hakan be hana asalin kyawunta bayyana ba.
Duk wannan kwalliyar da tasha taƙi sakin jiki da kowa sai ƙasa ƙasa take da ido har yanzu jikinta a sanyaye yake ko abincin kirki bataci ba a hakan ma sai da suka haɗa ta da Mama sannan ta nutsu.

Safiyya ce ta kalleta cike da kulawa tace, "amaryar Yaya Khaalif ku zo ku rakani can mana"

Nuriya ce tafara tashi tana cewa, "muje idan kika biyewa ta Yaya Khaalif ɗinnan bazakiyi wani abun kirki ba munyi wanka munyi kwalliya me muke jira??"

Miƙewa Aysha tayi tana murmushi tace, "muje nima nagaji da zama gara naje nasha iska"


Sanye yake cikin ƙananun kaya riga fara tassss da wando baƙi sai gilashi baƙi wanda ya hana ganin ƙwayar idonsa, kansa a ƙasa yake tafiya, yayinda mahaifiyarsa take gaba yana take mata baya tafiya suke cikin nutsuwa Umma tanayi masa magana kaɗan kaɗan amma yayi banza ko ɗaya be ɗauka ba dan hankalinsa ba a kanta yake ba.

tin daga nesa ta hangosu taji gabanta ya faɗi har ƙasa rage saurin tafiyar tayi saboda fargabar isa inda suke sai dai ya zama dole dan kuwa tawowa suke suna nufo su, ganin ta zuba musu ido yasa Umma ta sakar mata tattausan murmushi tareda yimata alamar tayi kyau.

Ƙasa tayi da kai tana murmushi wata ƴar ƙaramar kunya ta kamata.

Kasa motsawa tayi har suka ƙaraso wajen Umma ta tsaya tana tambayarsu inda zasuje, sai da suka gama gaisawa da kowa sannan ta durƙusa har ƙasa ta gaisheta, ta amsa cikin fara'a da kulawa gami da sa musu albarka gaba ɗaya.

ganin sunyi gaba yasa tafara sauri dan ta cimmusu, caraf taji ya riƙo hannunta, tsayawa tayi cakk ba tareda ta juyo ba, cikin nutsuwa ya juyo inda take bayan ya zare tabarau ɗin nasa ya zuba mata ido, cikin wata kasalalliyar murya yace, "juyo na ganki mana Ashshahhh!!!"

juyowa tayi kamar yadda yace amma kanta a ƙasa takasa haɗa ido dashi.

Sassanyar ajiyar zuciya ya sauke gami da ƙara yin ƙasa da murya sannan yace, "Murmushin ki yakan sani cikin farin ciki rashin sa kuwa shi yake nasarar tarwatsa farin cikina ya rabani da nutsuwa ta, Kintashi lafiya??"

bata san lokacin da ta ɗago idanunta ta zuba masa ba takasa magana sai dai kallo, hakan ya bashi damar jefa ƙwayar idonsa cikin nata, lallausan murmushin sa me ƙara kashe mata jiki da jefa ta cikin wani yanayi yasaki sannan yace, "nakasa yin bacci me daɗi saboda fargaba da rashin sanin a wane hali kika kwana na saki damuwa ko??"

Ɗan riƙe kunnen sa yayi tareda cewa, "Afuwan bazan ƙara ba, na kasa sarrafa kaina ne babu yadda na iya sai na faɗa miki banida mafitar da ta wuce wannan dan idan baki sani ba ma zuciyata zata hukuntani yana da kyau na gwada miki koda kwatan-kwacin irin ƙaunar da nake miki Ashshah ko zan samu wannan damar?"

Wani dogon numfashi taja tareda sauke kallonta zuwa ƙasa a hankali tace, "......................................."





(😜🙄baza kuji ba to🤭)








*INDO CE..*
[7/5, 10:52 PM] INDO CE..: *💖💖💖RINTSIN SO💖💖💖*
(Wa nake SO???)



*Shafi na 10*



Aƙalamin
*INDO CE..*


ELEGANT ONLINE WRITER'S




*Bismillahirrahmanirrahim*







Tace, "Umma tana jiranka kaje ka rakata gida"

Gyara tsayuwarsa yayi yana murmushi yace, "tayi tafiyarta saboda itama tanason kasancewa ta tareda ke"

Ƙara yin ƙasa tayi da kai tana wasa da zoben azurfar dake hannunta idanunta sun kawo ruwa kamar wadda take jiran ƙiris ta fashe da kuka"

Cikin nutsuwa yace, "bazaki cemin komai ba Ashsha? shikenan zan wuce sai mun sake haɗuwa ko??"

Gyaɗa masa kai tayi alamar "eh"

Yace, "kije ƙawayen ki suna jiranki"

Batace ƙala ba tayi gaba yana tsaye har ta isa inda su Nuriya suka tsaya jiranta sai da ya tabbatar ta isa gurin sannan ya furzar da huci ya juya ya cigaba da tafiya.

Nannauyar ajiyar zuciya ta sauke tareda goge ƙwallar da tafara zubo mata dan gudun kar su ankara.

Rookha tace, "ke kuma daga gaisawa sai zama?? ko ance miki lokacin jiranki garemu??"

Murmushim ƙarfiin hali tayi tace, "na sani ko kuna dashi? kodan idan baku dashi ma taya zaku tsaya kuma??"

Safiyya tace, "wallahi kuwa ai Ya Jose ɗinne akwai mutunci akwai rashinsa amma ke naga taku tazo ɗaya ya fiye shan ƙamshi da yawa"

Gaba tayi tana cewa, "idan kun gama muhawarar nayi gaba, cikin ranta kuwa godewa Allah take da suka kasa gane asalin tsakaninta dashi.

Su Jose suna tafiya babu daɗewa Aisha ta dawo gurin Mama ta maƙale sai shagwaɓa a tashi a tafi gida daga baya ma fasa kuka tayi, Sosai Mama tayi mamakin faruwar hakan kuma tambayar duniya taƙi bata amsa, dan haka ta sauke alamar tambayarta akan Khaalif Mohammad dan tasan shine kaɗai wanda ze iya ɓata mata rai har tace a tafi gida.

Ba shiri Mama ta harhaɗa i nata i nata Sayid sai faɗa yake dan kuwa ba haka yaso ba kuma babu yadda ya Iya dolensa tafiya ta kamashi.

Aisha kuwa da ta tabbatar tafiyar za'ayi sai tayi murƙisisi ta dena kukan, tana shirin fita ne tayi karo da Khaalif da kallo ɗaya ta gane ba a wani nutsuwa yake ba dan haka ko kallon inda yake batayi ba, dan tasan ƙarshen zancen meyesa takeson tafiya"

Kamar yadda tayi tunani kuma hakanne tambayar da yafara jifanta da ita kenan, "meyesa zaki tafi yanzu??"

Ba tareda ta kalleshi ba tace, "inason komawa gida ne"

Yace, "na sani ai amma nan ma ai ba'a daji kike ba ko??? kodan saboda Jose ya tafi ne kema zaki tafi????"

Ido ta ware akansa tana masa kallon mamaki ya gyaɗa mata kai domin tabbatar mata da abunda ya faɗa"

Gaba tayi tana cewa, "duk daɗin gidan wasu kuwa be kai ya gidan ubana ba dan haka inason komawa can, sai ka tawo kawai"

Da ido ya rakata yana mamakin yadda ta juye lokaci ɗaya, kar dai Jose ya rushe duk wani tubalin ƙaunarsa a cikin zuciyarta"

Tunanin da yafara ɗarsuwa a zuciyarsa kenan lokaci ɗaya yaji ko sunan Jose baya so yaji an ambata wani masifaffen kishi yayi masa rumfa.

Har suka isa babu wanda ta saurara suna sauka ma ɗaki ta wuce ta kwanta.

sai bayan sati ɗaya da yin bikin sannan tafara dawowa hayyacinta shima ba warewa tayi fess ba duk ta rame tayi duhu saboda tunane tunanen da tasa wa ranta duk tambayar da Mama zatayi mata amsar ɗaya ce "ba komai"

Yau suna zaune daga ita sai Nuriya suna taɓa hira kaɗan kaɗan Nuriya tace, "nifa gaskiya yau sai kinyi min fashin baƙi, kuma kinsan akwai yarjejeniya a tsakanin mu to nabar wannan ma dan nasan yanzu kin gazgata ko kuma nace Yaya Jose ya gazgata miki yanzu abunda kawai nakeson ganewa tunanin da kike yake ƙarar dake a tsaye haka"

Tambayar tazo mata a bazata kuma tayi mata girma aka.
Shiru tayi tana wani tunanin lokaci ɗaya jikinta yayi sanyi idanunta suka ciko da ƙwallah.

Kamar baza tai magana ba sai kuma tace, "tunamin makoma ta nake Nuriya ni abun tausayi ce tabbas ina tausayin kaina kuma ina tausayin wanda suke so na ina shiga tashin hankali a duk lokacin da na tuna ƙalu balen dake gabana inaga ƙarshen rayuwata ne yayi wa'adi na yaƙare shiyasa wannan wahalar ta kunno min kai, banason Saifu Nuriya kuma shi zan aura, Jose ya riga ya haukace da sona ina tsoron rayuwarsa ta ɓalɓalce saboda ni alhakinsa baze barni na rayu cikin salama ba, Khaalif ya daɗe yana azabtuwa duk saboda ni, wane hali zasu faɗa shida ɗan uwansa??, jinake inama zan mutu da na raba gardama, Meyesa wai sai ni Nuriya?? ba ni kaɗaice mace ba meyesa suke min so me tsanani ni kaɗai?? na shiga RINTSIN SO Nuriya cikinsu nakasa gane WA NAKE SO kuma wa yakamata naso?? zuciyata takasa samun nutsuwa da ɓangare ɗaya meyesa nakejin babu wanda zan iya juyawa baya a cikinsu?? "

Nuriya da ta saki baki ido da hanci tana binta da kallon mamaki da al,ajabi sai a lokacin ta samu damar cewa, "ke Aisha?? bakyason Saif dama nufinki?? kin haukace ne da kike cewa kina son mutum uku a lokaci ɗaya?? kodai kin zauce ne Aisha??"

Wasu zafafan hawaye ne suka samu nasarar Wanke mata fuska ta girgiza kai cike da tausayin kanta tace, "Wallahil azim kinji nayi miki babbar rantsuwa gaskiya na gaya miki bance ina son su ba amma jinake kowa yanada babban matsayi a zuciyata bansan so ba Nuriya saboda ni mahaukaciya ce ni ba mutumce kamar kowa ba tabbas na zauce indai yadda nakejinsu har cikin raina shi ke nufin ina son su to tabbas nagama haukacewa, bansan ina zan sa kaina naji daɗi ba dole ne ciwon tunane tunane ya kamani nan gaba ma nasan zuciyata ce zatayi tsawa ta tarwatse na mutu, be zama lallai ni me tsawon kwana bace dan ruhi na baze iya ɗaukar wannan masifar ba, Saif beyi min adalci ba beyi nazari akaina ba kawai da son zuciyarsa yayi amfani ni ban taɓa sonsa ba koda sunan wasa ban kawo a raina ba, kawai na wayi gari naji duniya ta ɗauka Saif yana sona nima ina sonsa, meyesa ze min haka?? kuma hakan be wadatar dashi ba babu zato ya kai maganar gurin mahaifina shi kuma ya amince musu ya basu ni, kawai sai naji labarin ya sauya daga batun soyayya zuwa ga aure, tin a lokacin raina ya ɓaci na gaya masa bana son sa amma yaƙi ya amince haka ya haɗani da su Antin mu sukai min faɗa nikuma wacece da zan bi ZAƁIN IYAYE NA ba?? na ajiyeshi a wannan matsayin kuma nake binsa sahu da ƙafa a matsayinsa na wanda zan aura duk hakan be burgeshi ba sai ya banzatar dani tukunna, banajin ze iya kulawa dani koda ya aureni ko a waya ba dai Saif yace bari na tuna da waccan ba sai nayi magana yace I love u na tsani kalmar nan kamar yadda na tsani Saif dalilinsa yasa naji banason jinta kuma banason auren Saif ki faɗawa wanda ranki yake so bana son sa kuma bazan so shi ba hasalima na tsaneshi na tsani auren nasa, rashin sani ne yasa
Babana ya yarda cewa ina son Saif kuma xan aureshi ne kawai saboda Babana bayan haka kuwa da ya gane ni ba tsarar sa bace"

Sallallami Nuriya ta shigayi tana tafa hannuwa, jinjina kai tayi gami da cewa, "tabb lallai ma Saifu sai yanzu na yarda bashida tausayi da imani, tabbas ya shiga haƙƙin ki ya jefa ki cikin Tara ba Uku ba, ya haneki da wanda kike so sannan ya sallama ki sai kace ance masa ke ba mutum bace??? amma ba komai akwai Allah kuma zeyi miki sakayya ko ba daɗe ko bajima, wallahi raina ya ɓaci Aisha gaskiya an zalumce ki amma sai dai kiyi haƙuri shine mafita dan bazaki tayarwa iyayenki hankali ba, amma yakamata maza su dinga tunani kuma su dinga yimana adalci dan akwai irinsa da yawa a duniya wannan ba kyautawa bace zalunci ne kuma duk wanda ya zalunci wani Allah ze sakawa mutum ƙarshe kuma abun yaƙi yimusu kyau, rayuwar aure fa ba zaman ayi a tashi bane taya yake tunanin da haka ze iya rayuwa da mace ta har abada ko ba ke ba?? dan dai kina da haƙuri ne amma in wata ce da tuni anyi an gama"

Share ƙwalla tayi kafin tace, "badan ina haƙurin ba ai da tuni anyi walle walle komai yaƙare, mutumin da yake sa ran rayuwa ta har abada dani kuma yake banzatar dani kamar abu mara amfani banajin son gaskiya ne wannan,, hmm... indai nice akwai lokacin da gaskiya zatayi halinta bazan damu kaina ba yayi kawai lokacinsa ne wata rana da kuɗi akace yayi bazeyi ba"

Nuriya tace, "Allah ya kawo muku mafita amma kuna cikin yanayi wallahi bama dai kamar Khaalif ni shi nafi tausayawa"

Murmushin takaici kawai tayi batareda tace uffan ba.


Tana zaune tana tufka da warwara kiran ABU ya shigo bin wayar tayi da ido har wani lokaci sannan ta ɗauka tareda yin sallama, amsawa yayi sannan ya cigaba da cewa, "barka da wannan lokaci kina lafiya?"

Ɗan murmusawa tayi tana cewa, "lafiya lau"

Yace, "masha Allah jiya muna magana naga kin gudu a online ina fatan dai lafiya"

Tace, "wallahi lafiya kawai dai na sauka ne"

Yace, "kenan bakyaso kiji abunda zan faɗa miki ne yasa kika gudu?"

Shiru ta ɗanyi tana tunani tabbas zata iya cewa hakan ne duba da yadda ya ɗakko zancen tasan baze wuce hakan ba shiyasa ta gudu dan batada amsar da zata bashi, a zahiri kuwa cewa tayi, "aa ai zaka ganni idan anjima kawai lokacine ban samu ba"

Da sauri yace, "ahh ba sai kin wahalar da kanki ba ba wani abun dama zance miki ba dan magana ɗaya ce zuwa biyu, nazo da ƙoƙon barata ne kuma ina fatan zan samu karɓuwa"

Shiru tayi tana sauraren sa jin tayi tsitt ne yasa ya cigaba da cewa, "Eeeshu haƙiƙa Allah ya dasa min tsananin sonki a zuciyata tin kina ƴar ƙarama har zuwa yanzu babu abunda ya canja sai ma wanda yayi gaba, na kasa ɓoye miki saboda inaso nayi rayuwa ta har abada tareda ke dan Allah kiyi tunani kafin ki yanke min hukunci zanyi farin ciki idan ya kasance na sameki a matsayin matata Eeeshu zanji kaina tamkar wanda yafi kowa sa'a aduniya nasha gwagwarmayar rayuwa tin daga lokacin da mahaifiyata ta rabu da mahaifina narasa asalin farin ciki na narasa gata da kulawa yanzu rayuwata tana buƙatar ki Eeeshu domin kece sirrin farin cikina"

Tinda tayi ƙasa da kai ko cikall takasa furtawa sai wani kurman kuka da take mara sauti sai cin zuciya da azabtarwa, babu shakka taji labarin irin mugun halin da yafaɗa a baya yayi rashi a yanzu kuwa yanada kyau ace ya samu farin ciki ita kanta zata so ta zama silar wannan farin cikin nasa tinda dai ita ya zaɓa kuma ya damƙawa kyautar zuciyarsa tareda ɗora sa rai gareta.

Katse kiran tayi ta saki wayar ta rufe fuskarta da tafukan hannunta tana cigaba da kuka.

ABU.
da kallo yabi wayar yana mamakin yadda akayi ta tsinke ta baya son takura mata dan haka be ƙara kiranta ba ya cigaba da tsammanin warabbuka tareda saran watarana zata amince idan Allah yaso.









*INDO CE*
[7/5, 10:52 PM] INDO CE..: *💖💖💖RINTSIN SO💖💖💖*
(Wa nake SO???)



*Shafi na 12*



Aƙalamin
*INDO CE..*


ELEGANT ONLINE WRITER'S




*Bismillahirrahmanirrahim*







"Ban damu da damuwa ta ba Ashsha damuwarki kawai itace damuwa ta koda ni nayi farin ciki nasan ke bazakiyi ba dan haka nima babu amfanin nawa farin cikin"

Rausayar da kai tayi kafin tace, "ni kam banda wata damuwa"

Ɗan murmushi yayi yace, "idan nace ki rantse zaki iya rantsewa??"

Ƙasa tayi da kai tafara wasa da ƴan yatsun ta dan kuwa bata rantsuwa akan gaibu.

Ganin tayi shiru yasa ya rausayar da kai sannan yace, "nasan kina cikin damuwa kuma ina ɗaya daga cikin wanda suka haddasa miki damuwar shiyasa gaba ɗaya banida walwala, mutane da yawa sunce na canja kuma kece kika kawo wannan canjin da ana ƙorafin bana magana yanzu kuma kowa cewa yake Jose ya canja kamar ba shi ba to wai ya ake son ganina ne?? faɗawa soyayya dama yana sa mutum ya zama wani daban ne? kodan ni mahaukacin so nake shiyasa kowa yake iya gane na susuce"

Rasa abun cewa tayi sai dai ta kalleshi ta sunkuyar da kai.
Hakan yasa ya cigaba da cewa, "Ashshah dan Allah ki amsa min tambayar nan kina so sona ko bakya sona??, Na ƙagauta da son jin wannan amsar ki faɗa min gaskiya dan Allah karki ɓoye min"

Dogon numfashi taja kafin tace, "lokaci yana tafiya fa"

lumshe idanunsa yayi gami da haɗiye mugun yawu sannan yace, "hakan yana nufin bakya sona kenan?? idan na kira ki bakya ɗauka bakya sauraron duk wani abunda ya shafeni, idan na tuna hakan zuciya takan gaya min bakya sona amma nakasa yarda bakya sona har sai na samu tabbaci daga gareki, inada damuwa sosai Ashsha ba iya Khaalif Mohammad ne yake buƙatar kulawarki ba nima ina buƙatar samun farin ciki daga gareki amma matsayina be kai nan ba, da gaske rayuwata zata ƙare a gantale da gaske mafarkin samun ki a matsayin matata da nake baze tabbata ba kenan nida farin ciki mun bawa juna baya?? da gaske bakya sona haukana kawai nake??

"hasbunallahu'wani'imal'wakil" itace kalmar da ta shiga mai-maitawa a cikin zuciyarta sabida turnuƙun zafin da take mata, da kyar ta iya dannewa tace, "kenan?? idan nace bana sonka kaima zaka yarda?? bana fatan ranar da zata zo na iya gazgata maka bana sonka"

Ɗan gyara zama yayi sannan yace, "banga alamun kina so na bane amma fa kiyi haƙuri nayi miki shigar sauri bana iya sarrafa kaina ne akanki ko abunda ya shafeki, komai yanada mahaɗin rayuwarsa shukoki da tsirrai mafi yawanci ruwa ne abokin rayuwarsu ko ga mu mutane rayuwa tana tsanani idan ba'a samun ruwa sosai kiyi tunani idan ya kasance babu shi duka fa?? rayuwar zata yuwu kuwa?? misalin hakane nakejin zata faru dani kinada muhimmanci gareni na riga nayi zurfi nayi nisa banajin kira akan sonki, so yana buƙatar tausayi da kulawa Ashshah amma ni bana samun ko ɗaya daga gareki, kin kasa yarda da irin tsananin ƙaunar da nake miki me kike so nayi wanda ze sa ki gazgata cewa na mutu akan sonki?? ki faɗa min ko mene zanyi indai be kaucewa hanya me kyau ba na shiryawa fuskantar duniya saboda ke amma narasa duk wannan damar kin kasa yarda dani kin kasa yarda ina sonki"

Tinda yafara magana kanta yana ƙasa tunanin kalamansa take wanda suke mata kamance-ce-niya da na Khaalif Moh.. ɗinta, shima yakance bata son sa bata tausayin sa ina suke son ta tsoma ranta ne taji daɗi?? ya zatayi da soyayyar mutum uku da take ƙara ruruwa a cikin zuciyarta da kowane lokaci?? shin bazasu iya tausaya mata ba suyi mata uzuri?? sai da ya gama sannan ta dago ta zuba masa idanunta da suka fara canja kamanni cikin rawar murya tace, "banajin daɗin hakan da kake faɗa Jo kenan yanzu babu wanda zan faɗawa magana ya yarda?? bazance ina sonka ka yarda ba kenan Ya Jose??, bazan ɓoye maka ba ina son Ya Khaalif kuma kaima ina sonka

Murmushi yayi yace, " amma baki taɓa faɗamin ba ko so kike zuciyata ta tarwatse?, duk da nasan Khaalif ya fini matsayi Amma ke allurar cikin ruwa ce me rabo ka ɗauka idan ba rabonka bace ko ka

Please Login or Register in order to submit comment