You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

tayi mamaki sosai Har sai da ta kasa ɓoyewa.

Khaalif ma ba ƙaramin mamaki yayi ba dan be sanar masa ze zo ba zuwan bazata yayi masa, koda ya tambayi dalili yace masa gaisuwar azumi yazowa Mama.

Mama kam tayi farin ciki sosai da sosai.
Sunyi hira sosai daga baya Maman ta fita Shahid yana shirin bin bayanta ABU ya dakatar dashi da cewa, "ƙanin ƙanwata kiramin Eeeshu kaji?"

Shahid yace, "to"

Da tsallen sa yaje ya gaya mata, ido a waje take kallonsa zuciyarta na tsalle, kardai mugun mafarkin da ta daɗe tanayi ya tabbata, taɓe baki tayi tace, "to me zanyi masa kuma?"

Shahid yace, "sai kinje zakiji"

Badan taso ba ta nufi ɗakin sai murguɗe murguɗe take, daga hanyar ƙofa ta zauna tace, " gani Ya ABU"

Fuskarsa ɗauke da murmushi yace, "Eeeshu badai har kin gaji dani ba daga zuwa biyu har anfara gajiya da gani na?"

Tana dariya tace, "aa"

Ya sauke ɓoyayyar ajiyar zuciya kafin yace, "naga daga gaisuwa ko takaina baki ƙara bi ba kodai nima na zama Jose ne??"

Tace, "wallahi aa ai naga kuna hira ne da Mama kuma kaga bazanzo na saku gaba ba dan hirar yaushe gamo kukeyi"


jinjina kai yayi yace, "lallai ƙanwata akwai hankali, nima yanzu tafiya zanyi ai"

Tace, "wai tin yanzu ka bari sai anjima"

Yace, "ƙauyen mu da nisa Eeeshu kuma dare yayi"

Tace, "to Allah ya tsare"

yace, "amin"


Shiru ce ta biyo baya har wani lokaci sannan ya ɗan saci kallonta ya murmusa sannan yace, "Eeeshu?"

Kallonsa tayi alamun ta amsa.
Ya cigaba da cewa, "Eeeshu yaushe ne zaki cika min alƙawarin da kika ɗaukar min??"

Zaro ido tayi tareda cewa, "wane alƙawari kuma ni ƴarnan??"

Ƴar dariya yayi yace, "ba wani abun tashin hankali bane fa, alƙawarin da kikayi na zama dani idan zanyi aure"

Ido ta ƙara gwalala masa arazane bakinta har motsi yake saboda son tayi magana amma kallonda ya yake mata yasa takasa furta komai, girgiza kai ta shigayi dan kuwa kwata kwata bata fahimci inda jirginsa ya sauka ba.....



(🙄😏🙄 na rasa ma kalar hararar da zan muku😂😂 wallahi nasha wuya gurin rubuta fejin nan sau uku inayi yana gogewa😥 ga murar da nakeyi😿 kuma ƙarshe ma ko sannu bazaku iya yimin ba bare comment dan naji daɗi😒, wallahi in kunga typing error ma sai dai kuyi haƙuri🤷🏻‍♀️🤷🏻‍♀️🤷🏻‍♀️🤷🏻‍♀️)





*INDO CE..*
[7/5, 10:51 PM] INDO CE..: *💖💖💖RINTSIN SO💖💖💖*
(Wa nake SO???)



*Shafi na 4*



Aƙalamin
*INDO CE..*


ELEGANT ONLINE WRITER'S




*Bismillahirrahmanirrahim*




murmushi ya sakar mata kafin yace, "ina nufin lokacin da kina yarinya kinyi min alƙawarin zama a gidana idan nayi aure"

Ƙasa tayi da kai tace, "Laah ya ABU ai kuma yanzu na girma"

Yace, "hakan ne ma yasa nayi ƙoƙarin tuna miki, nasan baki manta ba ai ko?"

Tace, "ai kuwa na manta"

Murmushi yayi ya tashi yana cewa, "zan wuce Eeeshu sai wani lokaci ko??"

Kai kawai ta gyaɗa masa dan kuwa ya barta cikin ruɗani, a inda yatafi yabarta anan ta zauna tai ta tufka da warwara.

Koda ya koma gida shirin kwanciya yayi amma baccin ya gagara, tunani ne fall cikin zuciyarsa a duniyar nan wa yake dashi wanda ze fara sanin sirrin zuciyarsa?, bashida mahaifiya mahaifinsa be damu dashi ba, waye ze jiɓanci lamarinsa? tabbas yanason zayyana abunda yake zuciyarsa ga mutum mafi kusanci dashi sai dai ya rasa wa ze tinkara, a duniya ɗan uwa ɗaya gareshi Khaalif sai dai bayajin ze iya furta masa wannan babbar maganar yana matuƙar tsoron abunda da Khaalif ze faɗa a lokacin da ya sanar masa haka kawai yakeji kamar ɗan uwansa ma ya faɗa RINTSIN SO kamar yadda shima ya kasance, sai yanzu yake ƙara tabbatarwa kansa shi maraya ne wanda yayi rashin wani babban jigo na rayuwarsa, ya rasa mahaifiya wadda itace wadda ko be faɗa ba zata gane halin da ya faɗa, a yanzu waye zeyi Alƙalanci tsakaninsa da ɗan uwansa? mahaifiyarsu ta rasu gashi ba mahaifinsu ɗaya ba babu wani wanda ze iya tausasa ɗayansu idan hakane kuwa tabbas sun faɗa garari dashi da Khaalif ɗinsa, ya tabbata da mahaifiyarsu tana na wani abun ze zo musu da sauƙi.

kuka me tsanani ne ya ƙwace masa ya shiga mazgar abunsa kamar ƙaramin yaro lallai rayuwa duniya me yayi bayan irin wahalar da yasha ta rayuwa har ya girma ga wata baƙar ƙaddarar ta ƙara riskarsa.

Haka yai ta kuka babu me rarrashinsa babu wanda yasan ma yanayi bare ya kawo masa ɗauki.

tana zaune tana karatun Alƙur'ani wayarta tafara ƙara ɗauka tayi ta zuba mata ido ganin ko wace yasa tafara murmushi ta kara a kunne gami da cewa, "Hello Rookha!"

A ɗaya ɓangaren Rookha tace, "yagarin ne Ayeeshan Yaya Khaalif"

Murmushi Aisha tayi tace, "lafiya wallahi"

Rookha tace, "ke shegiya saura kaɗan bikin Anti laila na kusa zuwa kano, wayyo Allah idan na tuna jinake kamar na mutu dan daɗi"

Aisha dai dariya ta shigayi sannan tace, "to ƙafar yawo asha biki dai"

Rookha ta ɗanyi sanyi da murnar da take sannan tace, "ba wasa fa Ayeeshah wallahi farin ciki nakeji kuma karki zata fa dan bikin nake murna, kawai dan zan haɗu da Ya ABU shine kawai farin ciki na, ina son nuna masa soyayyar da babu wata ɗiyar da zata iya yimasa ita a duniyar nan"

Laƙwas Aisha tayi jikinta yayi sanyi sosai, tausayin Rookha ya danne duk wani karsashin ta.

Jin shiru yasa Rookha tace, "lafiya kike kuwa??"

Cikin ƙarfin hali tayi murmushi me sauti tareda cewa, "lafiya mana Rookha kibari kawai ai nasan bikin zeyi daɗi Allah dai ya kaimu lokacin"

Tace, "amin ƴar uwa sai munyi waya"

Da haka sukayi sallama, Aisha tabi wayar da kallo cikin sanyin jiki.

itama Rookha mamakin sanyin da taji Aisha tayi take dan kuwa ta saba ƙwarara mata guiwa akan ABU amma yau duk ba wannan.


Khaalif Mohammad.
yana zaune ya haɗa kai da guiwa zuciyarsa tana masa wani irin tuƙuƙi da ɗaci, ya ɗan kwashi lokaci a haka kafin ya ɗago idanunsa da suka canja kala suka koma jaa ya zuba a guri ɗaya da alamu tunanin wani abu yake, ko motsawa bayayi sosai sai dai jefi jefi yakan haɗiyi wani mugun yawu, girgiza kai ya shigayi tareda cewa, "Ayeeshah ina cikin ƙuncin rayuwa ta dalilin ki meyesa kika dena SO na a lokacin da Sonki yayi min mugun harbi?, meyesa zaki nesanta dani a lokacin da nakejin kece bugun numfashi na?, Ayeeshah baki san ina sonki ba amma ni nasan ina sonki so na haƙiƙa son da ze iya tarwatsa rayuwata, zuciyata a ƙuntace take takasa bayyanar miki da abunda ke cikinta Ayeeshah nakasa faɗa miki ina sonki gashi har lokaci na yaƙare inama zan iya gaya miki ko zanji sanyi sanyi, watan wata rana zaki auri wani ba ni ba Ayeeshah ta bazan iya jura ba ya zamo wajibi gareni na nesanta gani na dake bazan iya jurar ganin ranar da zaki auri wani ba Ayeeshah.

Kasa ƙarasa maganar yayi saboda zazzafar ƙwallar da ta shiga zubo masa, Allah sarki Ummi na na rasaki narasa mahaifina yau gashi Ayeeshah zata gagareni na zama banida wani amfani dan babu wani jigo a gareni, nasan da kinanan rayuwar zatayi min sauƙi koda yaushe cikin tsanani nake Ummi nakasa sanin yaushe zan dena kukan rashi"

Wannan shine abunda zuciyarsa take gaya masa yayinda yake ƙoƙarin tsaida ƙwallarsa amma taƙi tsayawa.


Jose.
jin motsin Umma ne yasa yayi saurin soke wayar a Aljihunsa yafara zare ido da kallo ɗaya zaka gane bashi da wata cikakkiyar gaskiya.

Murmushi tayi irin na manyance sannan tace, "wayata dama na shigo ɗauka ko ka ganta??"

Shafa kai zuwa ƙeya ya shigayi yafara inda inda.

hannu ta miƙa Masa tareda cewa, "bani idan ka ganta"

Cikin in-ina yace, "ai tanaaa, gata ma a aljihu na ai"

ya faɗa tareda saurim zarowa ya miƙa mata.

Ta kalli wayar ta kalleshi kafin tace, "me kake min da waya??"

Yace, "Umma hotuna nake kalla"

Ta murmusa tareda cewa, "hotuna kake kalla ko kuma hoto??, ba yau ne farko ba fa, hala babu hotuna a wayarka?"

Ƙasa yayi da kai yana mui mui da baki da alamu magana ce me ƙarfi a bakin nasa wadda besan tayaya ze furta ba.

Zama tayi a gefen gadonta sannan tace, "Aisha ƴar ƙanwata!! yanayin tsayuwar hoton ne ya burgeka??"

Zaram yayi ya kalleta dan kuwa ta sosa masa inda ke masa ƙaiƙayi, da sauri ya zauna gefenta sannan yace, "Umma ta maganar gaskiya bana iya ɓoye miki sirrin zuciyata wallahi na daɗe ina son ƴar nan taki sai dai banajin zata So ni dan naga kamar ta fiye girman kai, wallahi Umma Mahaukacin so nake mata tabbas zan susuce idan Ashsha bata sona"

Da ido Umma ta bishi har wani lokaci sannan ta sauke ajiyar zuciya tareda ambaton sunan Allah buwayi, sai da ta lumshe ido ta buɗe sannan tace, "Jose Aisha bata da girman kai miskilanci ne ya gamu da miskilanci shiyasa karon yaƙi yin kyau, amma bata da girman kai sai dai tana da nauyin baki, baka taɓa janta da magana ba baka bata fuskar da zakaga rashin girman kanta ba shine zaka yanke hukunci? abunda zuciyarka take gaya maka ba gaskiya bane banyarda ba"

Kafin taƙarasa abunda take son faɗa ya katse ta,
Da sauri ya riƙo hannunta gami da ɗorashi kan ƙirjinsa daidai ƙahon zuciyarsa cikin wata sabautacciyar murya yace, "Umma ke mahaifiyata ce bazan taɓa yafewa kaina ba idan na faɗi maganar da kece wadda zaki fara ƙaryatawa, Umma na rantse da Ubangijin da ya dasa zuciyar da take bugawa a ƙirjina ina son Ashsha fiye da kaina, Umma idan kin ƙaryata zance na ta yaya Aisha zata yarda cewa ina sonta?? ki yarda dani ki gazgata gaskiyata dama kawai nakeso wadda zan gwadawa duniya irin son da nakewa Aisha"

Rungumeshi tayi ta shiga bubbugar bayansa ganin yadda ya burkice lokaci ɗaya, sai da yayi sanyi sannan tace, "Jose bazan taɓa ƙaryata ƙaunar ka ga Aisha ba domin nima sheda ce, ba wannan ne naƙi yarda ba ban yarda tana da girman kai ba amma tabbas na gazgata Kana sonta kuma koda yaushe ina maka add'ar samun farin ciki a rayuwar ka tareda Alkairi akan komai, ka dawo nutsuwarka Jose, Aisha bata shiga sabgar wanda be shiga tata ba haka tana jan mutuncinta dan gudun wulaƙanci, amma tana da mutunci ga duk wanda yake mutunci da ita, kaima ka jaraba ka gani kuma zakace mahaifiyarka ta gaya maka wannan, kuma hakan sirri ne wanda ba kowane yake samu ba"


(Allah sarki me uwa ɗan gata.. Allah ka rabamu da iyayen mu lafiya ka sakanya musu da mafificin alkairi ka kare su daga dukkan wani sharri ka sanya su cikin entattun bayinka, ba dan mu ba badan wayon mu ko iyawarmu ba dan Albarkacin shugaban mu Annabi Muhammad (SAW) ya Allah kayi musu jagora ka wanzar da haske a tattare dasu a duk inda suke, wanda muka rasa Allah ka jiƙansu ka wadata su da rahmarka ya Allah, (Ameen) wannan addu'a ba ni kaɗai ba har ku masoyana dan Allah kuce AMIN. ALLAH YABAMU IKON KYAUTATA MUSU)


Nannauyar ajiyar zuciya ya sauke sannan yace, "nagode sosai Umma Allah ya jiƙan mahaifanki"

Ta amsa da amin tareda ture shi daga jikin ta tana cewa, "do Allah ɗaga ni kana neman karya min kafaɗa, wai Jose duk ina wannan kunyar taka??"

Da sauri ya ƙara rungumeta yana cewa, "Umma dan Allah kiyi shiru"...

Ta murmusa gami da cewa, "fatan nasara YUSUFU Allah yai mana jagora"

Sosai Jose yaji daɗin ƙwarin guiwar da ya samu daga mahaifiyarsa dan haka yasha ɗamba ya gyara ɗamarar tinkarar guguwar dake gabansa.


ABU.
Yanzu bashida ishashshen lokacin da ze ware yaje gidansu Aisha gashi da ko wace Sa'a tunaninta da kewarta ƙara yawa suke gareshi dan haka ya yanke shawarar neman lambarta.

a yanzu tunaninsa ɗaya waye ze bashi lambar??

a gurin wa ze same ta???

ko dai ya nemi Rookha ta bashi??

anya kuwa idan yayi haka yayi adalci??

shin idan ya tambayi Khaalif Mohammad ta wace fuskar ze fahimce shi???.




(KU BASHI SHAWARA FANS ƊINSA😂)






*INDO CE..*
[7/5, 10:51 PM] INDO CE..: *💖💖💖RINTSIN SO💖💖💖*
(Wa nake SO???)



*Shafi na 5*



Aƙalamin
*INDO CE..*


ELEGANT ONLINE WRITER'S




*Bismillahirrahmanirrahim*






Ya daɗe yana neman lambar amma be samu ba duk wanda yake tunanin ze samu a gurinsa sai yaji babu har ƴar rama sai da yayi, sai daga baya ya sallama, wayarsa ya ɗauka ya turawa Khaalif Mohammad kira sai da ta kusa tsinkewa sannan ya ɗauka, a tare sukayi sallama kafin Khaalif Mohammad ya amsa, ABU yace, "yagida?"

murya a cunkushe yace, "lafiya lau Bro"

Shiru ce ta biyo baya, ya shiga tunanin ta yadda ze shawo kansa cikin sauƙi haka kawai ya tsinci kansa da lafta masa ƙarya yace, "Hajja ce dama takeson yin magana da Mama kuma na nemeta ban samu ba ka turo min lambar Eeeshu"

Shiru Khaalif Mohammad ya ɗanyi sannan yace, "ok bari kawai idan na koma gida zan kira ka"

Cikin ƙarfin hali ABU yace, "idan kuma sauri ake kenan sai an jira ka??, ka turo min kawai ai nasan da hakan nace ka turo min ko??"

Badan ransa yaso ba yace, "to shikenan zan turo maka bata son a dinga rabawa mutane lambarta ne shiyasa, naji kamar ranka ya ɓaci kayi haƙuri"

Ɓoyayyar ajiyar zuciya ABU ya sauke tareda rintse idonsa har ga Allah yana tausayin ɗan uwansa sai dai shima abun a tausaya masa ne, "ina jira" kawai ya iya cewa ya kashe wayar.

Khaalif mohammad ya raka wayar da ido yana mamakin abunda ya faru haka kawai yakejin kamar be gamsu da maganar ABU ba amma yasa a ransa koma menene Allah ya fishi sani dan haka ya fauwalawa Allah..

Ba wani ɓata lokaci lambar ta shigo murmushin farin ciki ne ya ziyarce shi, har ya tura kira ya fasa saboda idan ya kira ta a yanzu ma bashi da abun cewa.

koda Khaalif ya dawo gida suna Hira da Mama yace, "kunyi waya da Hajja ɗazu ko??"

Da ɗan mamaki tace, "Hajja kuma yaushe kenan?"

Cikin sauri yace, "Mama Hajja fa ɗazu ABU yace na bashi lambar Ayeeshah zakuyi magana da Hajja"

Mama tana shirin tayi magana Aisha ta fito ciki hanzari tace, "ya kira ni kuma lokacin bacci nake nace ni bazan tashi ba kuma kowa ma yasan ba son bada wayata nake ba ato"

Taƙarasa maganar cikin sigar ko in kula.

Ba Khaalif kaɗai ba Mama kanta sai da tayi mamakin hakan da Aisha tayi kuma tana gama maganar ta shige ɗaki duk suka rakata da ido.

Tana shiga ɗakin ta jingina da bango tana rintse idanunta da ƙarfin gaske, wayyo Allah na wai ni kaɗaice mace a duniya da kowane namiji yake ƙoƙarin fakewa dani??, shi yazo ya tirke ni da maganar aurensa, kai kuma ka damu dani a lokacin da na cire sa rai na da kai, ga ɗan uwanka yana neman jefa kansa cikin wani ƙangin duk a dalilina, ina tsoron Yaya ABU ya zama silar tarwatsewar ZUMUNCI DA AMINTAR dake tsakani na da Rookha, ina cikin firgici ina cikin wata rayuwa Allah ka kawo min mafita"

Zamewa tayi tai zaman daɓaro a wajen tareda fashewa da kuka.

Sayid tareda Khaalif har gware suke wajen shigowa ɗakin yayin da Mama take bayansu.

A matuƙar gigice Khaalif mohammad yake tambayarta abunda ya faru.

Ganin sun shiga ruɗani yasa ta dena kukan ta share ƙwallar tareda danne duk wani ƙuncin da takeji tafara ƴar dariya.

Sororo suka tsaya suna binta da ido, a marai-rai-ce Khaalif mohammad yace, "Ayeeshah meke faruwa??"

A shagwaɓe tace, "wallahi Mama tiles ɗin ɗakin nan mugu ne kawai daga shigowata ɗaki ya zameni na faɗi kuma sai da na buge kaina a bango"

Ɗan murmushi khaalif mohammad yayi tareda cewa, "Ayyaa Allah sarki ƙanwata sannu banji daɗi ba gaskiya be kyauta ba, dama ni ya kayar ba ke ba amma karki damu ki dena yi masa kuka kar ya raina ki"

Mama kuwa tsaki ta ja ta taɓe baki sannan tace, "to kuwa Allah ya shirya ku dukan ku kaima da taya ɓera ɓari, bata bugun bane da har ta samu bakin yiwa mutane ihu kamar wata yarinya ko mahaukaciya"

Da sauri tace, "Mama ina ganin fa kin faɗi gaskiya dan wani lokacin ji naje kamar na haukace ya kamata ku kaini asibiti naga likitan ƙwaƙwalwa tunani sun sa na fara zaucewa Mama"

Zuwa yanzu Mama riƙe haɓa tayi saboda abun yafara girman kanta.

Khaalif kuwa da yake akwai ƙarfin hali da juriya sai da ya dara sannan yace, "shikenan tashi muje dama na daɗe ina tunanin hakan ashe da gaske ne kina buƙatar likitan hankali"

Yayi maganar cikin sigar zolaya.

Harara ta buga masa taja tsaki kafin tace, "kaga wa kake da suna? Khaalif ko? idan kana neman mahaukaci kaje can ka duba amma ba'a gidan nan ba, bana son dattin ƙwaƙwalwa"

Harara Mama ta zuba mata hakan yasa tayi gim da bakinta ta miƙe tana karkaɗe karkaɗe ta koma gado ta kwanta.

Khaalif ya murmusa tareda cewa, "haka dai aci a ƙoshi a kwanta ba aikin fari ba na baƙi"

Ta murguɗe baki tace, "daɗin ta dai ba wani ne yake yin abincin da kuke ci ba, kuma lokacin da zanyi aikin ba gayyato ka zanyi ko nace dole sai ka sani ba dan haka karka samin ciwon kai ka fitarwa mutane daga ɗaki ko kuma ni na tashi na fita"

sim simm yayi ya fita dan baya son abun yayi tsauri yanzu sai ta ƙare masa rashin mutunci tinda tsakiyar kai har tafin ƙafa.

ABU yana zaune sai saƙi da warwara yake har wani ɗan lokaci sannan ya ciri waya ya tura mata kira.

Tana cikin jin waƙa ta saka iyafis kiran ya shigo bata tsaya dubawa ta ɗauka tareda yin fakare dan taji waye me nemanta.

sassanyar muryarsa ce tayi tafiyar mashi da ita lokacin da ya rangaɗa mata sallama, sai da numfashinta ya ɗan tsaya kafin ta sauke ajiyar zuciya ƙirjinta na bugawa, sai da ya kuma yin sallamar sannan ta amsa a sanyaye.

Ajiyar zuciya ya sauke sannan yace, "ina gaisuwa Queen Eeeshu barka da wannan lokaci"

A daburce tace, "barka dai yagida?"

Yace, "gida lafiya lau sai godiyar Allah ya Mama? ya jiki jikin nata??"

Tace, "taji sauƙi sosai bari na kai mata wayar"

Da sauri ya dakatar da ita da cewa, "Eeeshu ke nake nema dama kice ina gaisheta cewa nayi tinda bakya nema na ni bari na nemeki"

tattausan Murmushi me sauti ta saki sannan tace, "Ya ABU!! to amma dai bazance komai ba dan kuwa ka fini gaskiya nagode da tunawa dani"

jin tana ƙoƙarin kashewa yasa yayi saurin dakatar da ita,
yace, "idan na manta dake tamkar fa na manta kaina ne kinga kuwa daga lokacin na fita daga sahun masu hankali, Eeeshu har yanzu kin kasa sakin jiki dani kamar baki sanni ba? amma nasan ba haka kikewa Khaalif mohammad ba ai"

ƴar dariya tayi tace, "to ai nafi sanin Khaalif ɗin ne shiyasa kaifa sai yanzu nasanka amma daa labarin ka kawai nakeji"...

murmusawa yayi har sai da haƙoransa suka bayyana sannan yace, "tab gaskiya ba haka yakamata ayi ba, ni na riga khaalif Mohammad zuwa duniya dan haka ni yakamata kifara sani kafin shi"

Dariya tayi tareda cewa, "gaskiya kana da abun dariya, ga wanda nafara buɗar ido na gani ga kuma wanda zan fara sani, beyi maka kama da tatsuniya ba kuwa???"

yanayin yadda take maganar yafi komai ɗaukar hankalinsa ba shiri shima yafara dariya kamar yadda takeyi, jin tayi shiru yasa ya sauke numfashi sannan yace, "ko ɗaya yafi min kama da wasa amma, ni nasan Khaalif ya riga ya mamaye duk inda nake tunanin za'a tsakura ni nasan kinfi shaƙuwa dashi har cikin rai"
..

da sauri tace, "a'a a'a rufamin asiri Khaalif ɗin da baya son ganin farin ciki na??""

Ido huɗun da sukayi dashi ne yasa tayi saurin haɗiye sauran maganar tana ƙwalala masa ido.

kallon mage da ɓera suka shiga yiwa juna kafin ya matso tareda miƙo mata hannu yace, "mugani keda waye???"

Kallon wayar tayi taga har zuwa lokacin ABU be katse ba da sauri ta katse ta bankaɗa cinyarta ta jefa wayar sannan tasauke ɓoyayyar ajiyar zuciya a dake tace, "ai ba taka bace tawa ce"


Yace, "na sani kawai gani zanyi naji ana ambaton sunan marayan Allah bansan laifin da na aikata ba"

Murmushin gefen baki tayi tace, "cewa tayi Ayeeshan yaya Khaalif shine na faɗa mata gaskiya ko ƙarya nayi??? gaskiya ce ba son ganin farin cikina kake ba idan kuma kanada hujjar kare kanka to??"

Durƙusawa yayi kan guiwarsa yana fuskantar ta, kamar ze fashe da kuka yace, "Ayeeshah wallahi ban taɓa yin wani abu da gayya dan ɓata miki rai ba kuma bana fatan nayi wannan daga yanzu har zuwa lokacin da raina ze bar gangar jikina, ina son farin cikin ki sai dai bansan meyesa kika zaɓa mana irin wannan rayuwa ba, ina amfanin na ƙuntata miki kin ƙuntata min kenan rayuwata batada wani amfani Ayeeshah ko meye nayi banayi miki dai-dai abunda nake sa ran ya saki farin cikin sai naga ya saki ɓacin rai ƙanwata wai shin ni kaɗai ne mutum mara sa'a da ya kasance haka a duniya?? bana iya yiwa mutum abunda ze faranta masa kenan?? shiyasa wani lokacin nakanji inama ni ba rayayyen mutum me tsawon rai bane inama na mutu tin kafin na sanki Ayeesha, bana jin daɗin ɓata miki rai da nakeyi sai naji bazan iya yafewa kaina ba"


Ido ta zuba masa jikinta yayi matuƙar sanyi takasa furta masa ko uffan sai hawaye da suka cika idanunta.

Jin shirun nata yayi yawa yasa yace, "Ayeesha hakan ma ya ɓata miki rai ko?? kice wani abu dan Allah"

Murmushi me ɗauke da wani Sirri ne ya wanzu akan fuskarta ta kauda kai tareda cije gefen leɓenta ta girgiza kai tareda cewa, "a'ah banida abun cewa ne indai kaji nayi shiru kasan dai baki na sai kace Reza haka yake idan kaji be furta ba to be samu abunda ze faɗa bane, karka wani damu kanka idan natashi magana wata ma ko ni kaina sai na faɗa nake ganewa" Murmushi ta sakeyi kafin tace, "ya akai yau ka dawo da wuri??"

ƙululun da ya tsaye masa a maƙoshi ya haɗiye da kyar sannan yace, "nima kaina ban zata haka ba kawai canjin yanayi ne, ni bari naje waje dama Mama ce tace na tambaye ki ina kika ajiye mana mukullin ɗakin mu"

Tace, "uhm

Please Login or Register in order to submit comment