You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

aka tsayarda lokacin auren Khaalif Mohammad da Nuriya.

yau Aisha ta tashi ba lafiya har ta kaiga asibiti bayan wani lokaci ma'aikatan asibitin suka sanarwa Yusuf cewar an samu ƴan tagwaye mace da namiji amma sun koma dukansu macen bata zo da rai ba namijin kuma daga baya ya koma.

Sosai jikinsa yayi sanyi liƙiss
Allah kenan me yadda yaso gashi dai ya basu ƴan biyun da suke ta muradi kuma ya karɓi abunsa.

Bayan wasu lokuta aka sallemata daga asibitin ta samu lafiya sosai tayi tangargar.


Haka suka koma rayuwarsu cikin farin ciki da walwala bayan wasu watanni taƙara samun wani cikin, sai fatan Allah ya raba lafiya.


Rookha ma ta samu ƴarta mace santaleliya taci sunan Aisha ana kiranta Humaira.



Tana zaune ta miƙe ƙafa sai ciye ciye da gwaguye gwaguye take itace goruba itace gyaɗa itace aya.
Yusuf ne yayi sallama ta amsa tana murmushi tace, "barka da dawowa"


Yace, "yauwa, kina nan kina cin ko?"
Tayi dariya gami da cewa, "kyautar da Allah ya baka ce ta kawo hakan"

Dariya yayi yace, "to Allah ya raba lafiya kuma ya bamu masu albarka"

Ta amsa da "amin"


Bayan wani ɗan lokaci ta haihu lafiya ƙalau ta samu namiji shi kuma yaci sunan ABU Abubakar.

Ansha murna da farin ciki ta ko ina ALHAMDULILLAH .








*Alhamdulillah. anan na kawo ƙarshen littafi na me suna RINTSIN SO na godewa Allah da yabani ikon farashi lafiya kuma na gamashi lafiya kuma ina roƙon yafiyarsa a dukkan kuskure na a ciki.*


*ina godiya sosai masoyana ina fatan ganin so da ƙaunar ku a littafina na gaba da nayi waja waja da basirata wajen tsara muku shi wato DOGON YARO* inkiya *(JANCY)* *Naira 300 Ne Kacal Ba Yawa, Sai Na Jiku.*


*KU BIYO NI A CIKIN LITTAFIN (SIHIRIN ƘAUNA) DOMIN JIN MEKE ƘUNSHE A CIKIN WANNAN SALON SHI KUMA KYAUTA NE BA KO SISI KAWAI ƘAUNA CE TASA NA TSARA KUMA NA RUBUTA MUKU SHI*


Sunayen littafai na. Sirrin Ƙeta A Jini Ɗaya Tajmahaal paid book Ib Ɗan Wanka Rintsin So tareda Sihirin Ƙauna da nake kan rubutawa sai Dogon Yaro.





*Jinjina gareki Ummu Sulaim ina godiya da yabawa da irin ƙoƙarin ki Allah ya saka da Alkairi*

*Waziriya ta wato Salmaaji kema taki dabance Allah yabar kyakkyawar ƙauna*


*sauran masoyana musamman Group 1 abun alfaharina Allah ya ƙara zumunci, bazan iya zayyana sunayen ku ba amma tabbas kuna raina*














*INDO CE..*


Downloaded From https://tknovels.com.ng


Please Login or Register in order to submit comment