You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

kaina"

Wani shu'umin murmushi ne ya buwayi fuskarsa har cikin ransa maganar ta ratsa shi be taɓa tsammanin akwai ranar da zata zo Aisha taƙara kiransa da Yaya ba shiyasa yaji abun kamar a mafarki, gefe guda kuwa yana mamakin yadda har take iya yimasa murmushi yau bayan idan ta ganshi kamar taga shaiɗan amma yau gashi ta saki jiki dashi, beyi tunanin komai ba dan kuwa idonsa ya rufe haka kawai tinda ya ɗakko ta yakejin wani irin shauki har ma ya kasa yi mata kashedi ta hanyar azabtarwar da yace ze bi mata da farko.

Muryarta wadda take ƙara bauɗar da tunaninsa ce ta sarƙaƙa cikin kunnen sa, da yake lallaɓa shi take cikin sigar rarrashi tace, "dan Allah ka fita zanyi wankan karka ƙara shigowa kuma"

yace, "na yarda kuma kiyi sauri dan nasan kina tareda ni bazan juri zama ni kaɗai ba"

Kai ta gyaɗa masa tana murmushi, yana juya baya ta doka masa harara me taken ZALLAR ƘIYAYYA.
Sai da ta tabbatar ta garƙame ƙofa sannan tafara wankan tanayi tana kuka sauƙin ta ma dai da ruwan ɗumi yadda take shan jiki da ruwan sanyi ne da ta ɗanɗana ta"

Yana nan zaune ta fito sai raɓe raɓe take cikin sanyi tace, "na fito"

Kallonta yayi sama da ƙasa kafin yace, "kuma shine kika ɗauki kayan da kika cire kika mayar dan shirme??"


Tace, "kaga malam bana son iskanci nan fa ba gidan ubana bane ina naga wasu kayan"

Yana dariya yace, "A'isha nine ɗan iskan ko?? kodan yau banyi miki iskancin bane yasa kika samu bakin magana?"

sai a lokacin ta tuno da irin halinsa na rashin imani gudun kar a kuma yasa tace "kayi haƙuri" sannan taja baki ta tsuke.

bata ankara ba sai ganinsa tayi a gabanta yana binta da kallo yana murmushi yace, "A'isha makullin sirrina gaskiya naga ƙoƙarin ki da kika kasa gayawa kowa, to amma yanzu kinga Saif ya jawo mana dama abunda naso gaya miki tin farko shine bana son sunana ya fito duk gumurzun da za'ayi idan kikace nine kinsani ke zaki kwana a ciki dan idan nace banyi ba babu me cewa dole nayi"

Ƙasa tayi da kai tana murmushi tace, "Dawood Yayan Saif gaskiya kun more wajen tarwatsa farin cikina da kai da ƙanin ka, to amma ba komai indai akan wannan ne karka wani tashi kanka tsaye, duk tsawon shekarun da aka ɗauka ko mahaifiyata bata san anyi ba bare wani kaga kuwa babu dalilin da ze sa yanzu na faɗa"

Yace, "wow A'isha gaskiya kin iya riƙon amana irin ku wahala kuke a zamanin nan"












*INDO CE..*
[7/5, 10:53 PM] INDO CE..: *💖💖💖RINTSIN SO💖💖💖*
(Wa nake SO???)



*Shafi na 24*



Aƙalamin
*INDO CE..*


ELEGANT ONLINE WRITER'S




*Bismillahirrahmanirrahim*








yaƙara da cewa, "har yanzu ƙara kyau kike amma kin ɗanyi baƙi ba kamar lokacin da kina yarinya ba da fa kamar a taɓa jini ya fito haka kike"

Zamewa tayi zuwa gefe tana cewa, "zafin duniya ma kaɗai ya isheni bare kuma kasan wani idan yana girma kamannin sa suna ƙara fitowa sai kaga ya canja launi"

Yace, "hakane kuma"

Wasu kaya ya miƙo mata yana cewa, "maza ki canja kaya"

Karɓa tayi tareda nufar hanyar ɗakin wanka, da ido ya rakata har ta ɓacewa ganinsa sannan ya saki murmushi tareda cewa, "A'isha manyan gari"

yana nan zaune ta fito ta tsaya akansa ba tareda ta kalleshi ba tace, "gida zan tafi"

Yayi kamar be ji ba sai da taƙara cewa, "nace ka kaini gida ko?"

Ido ya zuba mata har tsawon wani lokaci kafin yace, "anan zaki kwana"

A zabure tace, "me????"

Sarawar da kanta yayi ne yasa tayi saurin sakin maganar ta rintse ido gami da cije leɓenta, sai da ya sassauta sannan tace, "Dan Allah Dawood karka ƙara cutar dani ka maidani gidan mu, ka fita daga rayuwata ko na samu sassauci, nayi maka alƙawarin bazan faɗawa kowa abunda yafaru ba ko a wane matsayi aka ɗaukeni zan yarda amma dan Allah karka ƙara cutar dani"

wata ƴar dariya yayi sannan yace, "na yarda bazaki faɗawa kowa ba yakamata kema ki yarda bazanyi miki komai ba indai ba ke kika amince ba, amma fa anan zaki kwana bazan kaiki gida da daren ba"

Sanin ba kaitan zeyi ba yasa ta koma ta zauna ta buga tagumi.

sai da ya gama abunda zeyi sannan ya kalleta tace, "tashi muje ki kwanta"

Bata tsaya yimasa gardama ba ta bi bayansa wani ɗan madai-daicin ɗaki me ɗauke da matsakaicin gado ya kaita sannan yace, "duk abunda zaki iya buƙata akwaishi a ɗakin, sai da safe ko??"

Gyaɗa kai tayi idonta a ƙasa. yace, " bazaki ce min komai ba??"

Shirun taƙarayi dan kuwa bata san abunda zatace masa ba hasalima ta ƙagu ya tafi yabata guri dan ba ƙaunar ganinsa take ba.

Ɗan murmushi yayi kafin yace, "shikenan sai da safe naga kamar kina jin bacci sosai"

be jira me zatace ba ya fice, sai da ta sauke ƴar ajiyar zuciya sannan taƙarasa kan gadon ta zauna a gefen sa ta shiga ƙarewa ɗakin kallo har wani lokaci kafin taja tsaki, tareda zullumi da adda'a a bakinta ta haura kan gadon ta kwanta gami da lumshe idonta tana jiran zuwan bacci, tin tana sa ran ze ɗauke ta har ra dena saboda tunane tunane da suka durfafeta ga idonta sun ƙeƙashe babu alamun bacci a tattare dasu sai zafi da zugi kawai suke, fargaba da tsoron abunda ze faru kuwa sunyi cunkuss a zuciyarta hakan ya haifar mata da buguwar zuciya akai akai wanda yasa jikinta ya ɗauko tsuma, ta daɗe cikin wannan yanayin tana shan azaba kafin zuciyarta tayi rauni har kuka ya samu damar kufce mata hawayenta suka zuba, sai a lokacin ta ɗanji damar zugin da takeji sai dai kanta da ya cigaba da tsala ciwo, ta daɗe tana kukan sannan bacci me cike da mafarkai munana yayi ɗaukar shaho da ita, batafi minti ashirin ba tafarka bayan wani lokaci taƙara komawa, haka tayi baccin guntu guntu sai ƴan mafarkai da tunani da take faman yi, sai gab da Assubhu sannan bacci me nauyi ya ɗauketa.

lokacin Sallah yanayi kuwa Dawood yazo ya tashe ta a cewar sa tayi Sallah ko takansa bata bi ba ta nufi inda take tunanin ɗakin wanka ne ta ɗauro alwala ta fito lokacin shi kuma ya fita hakan kuwa ba ƙaramin daɗi yayi mata ba, tayi sallarta cikin nutsuwa tareda roƙon Allah sassauci.

Sai da tayi addu'o'i sosai sannan ta koma bacci, ba ita ta farka ba sai tara da minti arba'in da biyu 09:42 sannan ta tashi a razane tana wuri wuri da ido ai kuwa idonta ya sauka akan Dawood da yake zaune a gefenta yana ƙare mata kallo kamar wanda yaga baƙuwar halitta, ashe dai mafarkin da tayi gaskiya ne banbancin kawai a iya kallonta ya tsaya be taɓa ta ba.

Yadda ta zazzaro masa ido ya tabbatar masa a firgice ta tashi ya sakar mata murmushi sannsn yace, "Barka da safiya ƙanwata A'isha ina fatan lafiya kika tashi"

da kai ta amsa masa da "e" cikin ranta kuwa cewa take azzalumi ko meye damuwarsa da lafiyata bayan ya rabani da ita?"

Katse ta yayi da cewa, "na haɗa miki ruwan wanka kiyi ki fito kiyi kari"

Bata tanka masa ba ta zame tayi ƙasa har ta fito daga wankan yana nan zaune, zama tayi a gefen gado tayi zugummm ba um ba um um,.

Abincin karin ya ya dire mata sannan ya koma ya harɗe, da taƙi ci sai da taga yayi da gaske sannan ta ci saboda tsoron abunda ze biyo baya.

Sai kusan Azhar sannan ya ɗakko mota yace ta shiga ya maida ita gida tayi kukan tayi magiyar har tagaji ta dena ta zuba masa ido.

Da har ƙofar gida ze kaita sai da ta dage bata so sannan ya haƙura ya direta a bakin layinsu bayan ya ƙara jaddada mata kar yaji ta ambaci sunan sa a cikin labarinta, hakanan ta amsa masa sannan ya barta ta tafi, bugun zuciyarta ƙara gudu yake a duk takun da tayi da sunan ta nufi gidan.

tana yin sallama sukayi ido huɗu da Mama ta bi ta da kallon mamaki da tambaya.

Ƙasa tayi da kai a ciki ciki tace, "sannun ku" daga haka ta wuce ta nufi ɗakinta.
Mama da ta daskare a zaune tace, "Aisha????? kina cikin hayyacin ki kuwa???"

Aunty Maimuna ta jinjina kai tareda cewa, "tabɗi jam Aisha ya zamu ganki anan yanzu kuwa bayan kamata yayi ace kina gidan mijinki"

Duk da ba kallonsu take ba amma tasan duk idanun su suna kanta kuma jiran amsarta suke, Rintse ido tayi da ƙarfi a ƙagauce tace, "ya sakeni saki uku".

Mama kasa magana tayi sai sauran mutanen da suke gurin me salati tanayi me ƙara jefo wata tambayar tanayi.

Aunty Zuhailat tace, "iskanci ne ko ƙuruciya yake damunki Aisha?? akan wane dalili zaki zo mana da irin wannan banzan zancen??"

Tace, "Aunty Zulaihat wallahi Saifu ya sakeni ga takardar ma a hannu na"

Inna lillahi wa inna ilaihirraji un shine kalmar da Anti Zulaihat ta faɗa cikin rawar jiki da firgici,
Aisha kuwa wuce tayi ta nufi ɗaki har taje ƙofa Mama ta dawo da ita da cewa, "zo nan dan ubanki Aisha"


Dawowa tayi idonta a ƙasa tayi tsaye tana sauraren su, Cikin kuka Mama tace, "yanzu Allah ya rufa miki asiri ya rufamin shine zaki kashe aurenki?? Saif dai nasan bashi da wata matsala ko meye yafaru daga ke ne, maza ki gaya min wace tsiyar kika shuka"

Gyara tsayuwa tayi gami da cewa, "ku tambaye shi mana shi da yai sakin"

Mama takasa cewa komai sai sharar Ƙwallah, Cikin ɓacin rai Anti Maimuna tace, "bazamu tambaye shi ba ke zamu tambaya"

Tace, "aikuwa zaku mutu bakuji ba"

Tana rufe baki Anti Zulaihart tayi kanta da duka sai da ƙyar mutane suka dakatar da ita aka bata baki sai kuma ta fashe da kuka.

Aisha kuwa gefe ta koma ta cigaba da ƙasa ƙasa da ido yanzu kukan ma har ta kai matakin da takejin baza ta iyayinsa ba zuciyarta ta bushe.

Mama tace, "ku ƙyaleta idan ubanta yazo sai ta gaya masa tinda shine maɗaurin auren nata"

Bata tanka ba kawai ta wuce ta shige ɗaki, wata ƙanwar Abban su wadda suke Ɗan wa da ɗan ƙani ta tashi ta bi bayanta, da yake akwai tsugul da son nuna iyawa ta raɓa kusa da ita cikin sigar lallami tace, "Aisha kinga ran mahaifiyar ki ya ɓaci kije ki bata haƙuri koda bazaki gaya mata abunda yafaru ba, amma kinyi ƙememe da ido ko hawaye bakyayi ai dole ace kece da laifin kije ki bata haƙuri kinji ko?? kar ta gayawa Abban ku ya ɗauki tsatstsauran mataki fa"

A faɗace Aisha tace, "yaaa isa hakaa!! har shekara nawa zan ɗiba inayiwa ɗa namiji kuka??? bazanyi ba ɗin haƙurin ma bazan bayar ba tinda idan na faɗa ma ba abunda ze ragu ko ya ƙaru dan haka kar a ƙara yimin zancen banza na ɗebi tsawon lokaci ina kokawa saboda namiji yau ɗaya dan na samu hutu shine za'a takura min?? ki fita tin ina ganin mutuncin ki ki bani guri"


Kamar munafukar kaza haka ta summ summ jikinta har rawa yake ta bi iska ta fice daga ɗakin...

Waya Mama tasa aka kira Abba aka sanar dashi ai kuwa sai gashi ya dawo shima tin kafin ya dawo ya zabaro Saifu bayan dawowarsa kaɗan sai ga Saif ɗin.

Aisha kuwa tanajin su tayi kamar bataji ba, Abba ne ya fara yambayar Saif ba,asi ai kuwa ya zayyana masa abunda yafaru tin jiya"

Shiru yayi yana nazari sannan yasa a nemo masa ita a gefe ta tsakure tana jiran abunda ze ce, sai da ya ɗanyi gyaran murya sannan yace, "kinji abunda ta faɗa ko??" ta gyaɗa kai, yace, "to hakane" tace, "eh amma fa karya ƙara cewa ina neman maza dan ba aikina kenan ba"

Cikin fushi Abba yace, "bayan tin jiya ya sakeke kuma ina kika kwana?? wannan ma kaɗai ya isa shedar abunda yafaɗa, Subhanallahi Aisha wannan rayuwar kika zaɓawa kanki?? A uzu billah"

Saif yace, "gata nan dai ana ganin kamar su kaɗai ne masu tarbiya duk dangi ashe kura ce a lulluɓe da fatar akuya, ku tambaye ta waye wanda take zuwa gurinsa dan ni an daɗe ana sanar dani akwai wani namiji da take zuwa gurinsa, kuma ko waye sai munyi shari'a dashi"


Cikin ƙunar rai Mama tace, "ka tambaye ta Alhaji ni ta ɓatawa suna ta zibarwa da mutunci dan nice uwa mace, ko meye yafaru ni za"a fara hari dan haka ta gaya mana da yaushe ta zama haka da yaushe ta watsar da tarbiyar da muka bata?? ta gaya min waye wanda ya lalata ta wallahi sai dai duniya tarabani dashi dan ni ƴa ta nasan ba karuwa bace sai dai in wanine yaja ra'ayin ta"

Cikin tsawa Abba yace, "zaki goyi bayan ta ko??? gashi ƙiri ƙiri kina ji kina gani zaki ce ba haka ba?? ta gaya min ma jiya gidan ubanwa ta kwana"

Shiru tayi dan kuwa tana matuƙar tsoron Dawood babu yadda za"ayi tace a gidansa ta kwana.

Abba yace, "zakiyi magana ko kuwa sai na fara dukanki??"

Tace, "Abba wallahi kawai zargina ake amma ni bana haka wallahi kunji na rantse"

Saif yace, "ƙarya fa take munafuka ai na firgita da lamarin yarinyar nan azzaluma ni ai ta gama cutata kuma bazan yafe ba duk ma abunda na kashe dan aurenta sai an biyani"

Abba ya jinjina kai kafin yace, "daga nan zuwa gobe ki gaya min waye idan ba haka ba ranki ze ɓaci, ku kuma ku sa ido akanta karta ƙarayin wani gurin"

Mama ta share ƙwallah gami da cewa, "to"


Komawa tayi ɗaki ta zauna sai fici fici take da idanu.


Nuriya da take ta kuka ta kalleta cike da damuwa tace, "Aisha wannan wane irin baƙin labari ne?? neman maza kike???"

Murmusawa tayi kafin tace, "ba nice na nemeshi ba shine ya nemeni Nuriya, kasancewar ki amintacciya a gurina ke kaɗai zan iya gayawa, amma ki tashi mu zagaya inda babu mutane"

Tashi Nuriya tayi suka zagaya gurin ba kowa duk suna ɗayan sashin suka nemi guri suka zauna, Aisha tace, "lokacin ina yarinya Mama ta taɓa yin wata rashin lafiya me tsananin da sai da aka kwantar da ita a asibiti tayi kwanaki, to a wannan datsin ne wata rana, su Sayid suna makaranta Anti Zulaihart ita aka bar mana a gida domin kulawa damu, a ranar tace min zataje asibiti gurin Mama ni kuma na zauna a gida sai na kulle kar nabar kowa ya shigo, nayi nacin duniya da magiya akan tabarni muje tare amma taƙi, haka tasa ƙafa tabar gidan nan tabarni duk da ƙananun shekaru na, ina zauna zaune sai naji ana ta bugun ƙofa............."







(Littafai na, SIRRIN ƘETA A JINI ƊAYA TAJMAHAAL Paid BOOK IB ƊAN WANKA Tareda RINTSIN SO"








*INDO CE*
[7/5, 10:53 PM] INDO CE..: *💖💖💖RINTSIN SO💖💖💖*
(Wa nake SO???)



*Shafi na 25*



Aƙalamin
*INDO CE..*


ELEGANT ONLINE WRITER'S




*Bismillahirrahmanirrahim*





"....da nace bazan buɗe ba sai naji ba'a dena bugun ba dan haka nayi tambayar waye, nan yake ce min Dawood ne, nace Mama bata nan ya tafi idan ta dawo sai shima ya dawo, amma sai yaƙi sai ma cewa da yayi aiko shi akai ze ɗauki wani abu, ni kuma jin hakan yasa na buɗe masa da tunanin gaskyar abunda ya faɗa, sai bayan nan nagane ashe labarin ba haka yake ba, to a wannan lokacin ne ya samu dama dan kowa baya nan, da yake inada gardama da na bujire masa ma haka yasamin ƙarfi, bayan nan kuma ya bani kyakkyawan kashedi akan kar na faɗawa kowa yace idan na faɗawa wani to zeyi min abunda yafi wannan, to ni kuma ina tsoron hakan, mutumin da ya iya danne ƙaramar yarinya yayi mata fyaɗe menene baze iya aikawata ba? ko akaina ko akan wani nawa nasan ze iya cutar damu, ga yara nan su Aunty sun haifa banaso ta dalilina ya cutar da wani dan haka yanzu ma bazan faɗa ba zan cigaba da riƙe maganar har zuwa lokacin da Allah ze tona masa asiri"

"Haka nasha wahala a lokacin nan kafin kowa yazo na kwanta ga zazzabi ya tara ni, shi dama Dawood babu wata alama da yabari wadda zata nuna wani abu yafaru sai dai azabar da nakesha kawai koda Anti Zulaihat ta dawo ta tarar ina zazzaɓi sai tace nasha magani bayan nasha taga abun ba sauƙi sai ta tsiri cewa aje asibiti ni kuma ina tsoron su gane wani abun dan haka na daure na dena nuna damuwata kuma na kafe akan bazanje ba, haka sukai ta yimin tambayoyi amma naƙi basu amsa me kyau, Anty Maimuna a lokacin taso gane kamar wani abun yafaru saboda yadda taga ina tafiya da kyar kawai sai nace musu ciwon ƙafa nake kuma na tubure ahakan har sai da nayi abunda ya ɓata musu rai sukai fushi suka ƙyaleni, dama idan Abban mu ya dawo gidan su suke tafiya yana dawowa kuwa sukai gaba shi kuma dama Abba yana ɗakinsa muna namu, ...
Haka nayi ta haƙuri na danne duk wani raɗaɗin da nakeji na kwana cikin wannan baƙin ƙadamin, washe gari ma na ƙoƙarta ina ɗan zagayawa kar su ganni a kwance su kinkime ni sukaiwa likita kowa yayi maganar tafiyata sai nace ciwon ƙafa nake idan ka matsa kuwa duk zafin da nakeji akanka zan juyeshi dan kuwa DA INA YARINYA inada faɗa sosai"
.....

Nuriya ta numfasa kafin tace, "lallai wannan ya cika mara mutunci kuma maci amana in Allah ya yarda sai ya gamu da abunda hankalinsa baze ɗauka ba sai ya gamu da ƙuncin duniya da na lahira baze taba ganin ƙarshe me kyau ba mugu, shine kuma dan rashin kunya har Saif ne za'a kaiki gidan sa ya koro ki saboda wannan dalilin? lallai bashi da ma hankali"

tayi Murmushin takaici tace, "Nuriya Saif be san hakan ce tafaru ba amma ko ya sani ma hakan zeyi min dan kuwa suna da mummunar aƙida ta son zuciya, a koda yaushe neman tsari nake dasu da irin su"

Haka sukaita jajantawa juna sannan suka koma ɗaki.

Washe gari kamar yadda Abba yace ta sanar masa hakan yaƙara tambayarta amma ko alu bata ce musu ba haka akaita gumurzu da ita amma taƙi faɗe har dukanta sukai dik ta shanye, hakan ya tabbatar musu da gaskiyar Saif tin daga lokacin suka hau dokin zuciya suka dena saurarar ta ko abunda ya shafeta kowa fushi yake da ita daga kan Abba Mama Anti Zulaihat Anti Maimuna kowa fushi yake da ita gaba ɗaya rayuwar tayi mata ƙunci bata da aboki sai kuka duk mutanen gidan ƴan biki sun tafi Nuriya ma ta tafi sai Sayid ne kawai yake ɗan kulata shima Mama hanashi takeyi.

yau tana zaune Sayid yazo ya miƙo mata wata takarda karɓa tayi ta warware kafin ta tashi da sauri cikin rawar jiki ta yafa mayafinta sannan ta nufi ɗaya sashin yana tsaye ya riƙe ƙugu idonsa yana kan guri ɗaya da alamun wani tunanin yake.

Cikin sauri taƙarasa inda yake cikin fara'a tareda farin cikin ganinsa, ido ya zuba mata da yake itama shi take kallo yanayin kallon da yake mata sai taji ya sare mata guiwa, cikin daurewa tace, "Khaalif Moh.. meke faruwa ne?"

Yace, "ba komai"

Shiru ce ta biyo baya kowa da nasa tunanin tasan dai da kyar ace babu komai ɗinnan dan ko a yanzu taga canji, katse mata tunanin yayi da cewa, "Ayeesha kinsan abun hakane meyesa baki sanar dani tin wuri ba?"

Cikin mamaki tace, "me kenan??"

yace, "au baki gane ba??"

Tace, "Khaalif wata magana kayi min wadda ban fahimta ba"

Hannunta ya kama ya janyota jikinsa yana cewa, "to bari na ganar dake"

Ido taƙara waro masa cikin alamar tsoro dan kuwa ta lura yau babu alamun soyayayya sai dai wani abun.

Sake rungumeta yayi tsam sannan ya jefa idanunsa cikin nata, cikin wata kalar muryar da bata saba ji daga gareshi ba yace, "kinsan haka abun yake da arha amma kika hanani, ko ni ba namiji bane?? faɗa min mana?? da nufinki na aureki a haka?? to maganar gaskiya bazan iyaba na auri budurwa amma babu lasisin budurci kinga ya tashi abanza"

Tsananin mamakin irin kalaman da suke fitowa daga bakinsa yasa ta kasa magana sai kallonsa da takeyi, murmushi ya sakar mata kafin yace, "wannan kallon na meye ne?? ya isa haka mana abunda bakiyi tunani ba kafinki faɗa sona shine yake faruwa baki taɓa tambayar kanki meyesa duk matan duniya ke kaɗai na maƙalewa ba duk da irin rashin mutuncin da kika shuka min a baya?? nifa dama ba komai nake yiwa ba, ba wai zuciyarki nake buƙata ba iya jikinki ma kaɗai ya isheni more rayuwa amma yanzu labarin ya sauya ni nafasa kije ki auri wanda ze iya aurenki a haka, amma fa raina ya ɓaci sosai da sosai nayi takaicin rasa abunda na daɗe ina muradi, Ayeesha ni ba namiji bane da bazaki yarda dani ba??"

A'uzu billahi itace kalmar da take mai-mai-tawa akan leɓen ta jikinta har kakkarwa yake saboda razani da kiɗima,

Yace, "Ayeesha yanzu nasan ai kin gane me nake nufi ko??"

Jin yana neman wuce iyakarsa ta haryar taɓa inda be dace ba yasa ta shammace shi ta zame tayi gefe tana so tayi magana amma takasa saboda zuciyarta da take bugawa cikin sauri, wasu zafafan hawaye ne suka wanke mata fuska da kyar tace, "Khaalif wallahi ni ba mutuniyar banza bace ni ba ƴar iska bace fin ƙarfina akai duk yadda kake zato na ba haka nake ba wallahi ni bantaɓa iskanci da wani ba, kai ma Allah yayi min tsari da kai shaiɗani ashe dama duk soyayyar taka ta ƙarya da yaudara ce Khaalif?? meye ribarka dan ka cutar dani?? amma Allah yana kallon komai kuma ze saka min wallahi Alhakina baze barku ba Khaalif kun cutar dani kun zalumce ni"

Gyara tsayuwar sa yayi kafin yace, "ban cutar dake ba

Please Login or Register in order to submit comment