You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

Ilyass. Wasu suka
tsaya yiwa Ango da Amarya fad'a. Yana rakasu
ta koma d'aki. A gaskiya iyaye sun mata ba zata,
sam bazakai t'sammanin ba y'ar masu dashi
bace,d'uk kamar wanchan karan karan nan ma
kawunsu na Zaria ne ya mata gado da
kujeru,shikam da zamani yake tafiya, shi yasa
koman su tsaf-tsaf. K'wance take tana kara
duben yanayin d'akin,sai ajiyar zuciya take na
wacce taci kuka, sosai ya mata k'yau, ga wasu
arnun labulaye, Allah sarki Abban ta da Ya
Suleiman, Yanzu ta yarda da wadatar zuci tafi ta
kud'i. Fatan ta Allah ya kaita lokacin da zata
rama musu itama. A haka har ya cimmata a
d'akin. Tsayawa yai yana k'allon ta, sai ta tashi
ta takure kanta tare da jingina a jikin allon
gadon. Sallama yai,sai ta duk'ar da kai ta amsa,
zama yai kusa da ita yana k'allon yadda d'uk ta
bata k'walliya da kuka,, shi a kullum yana da
tambaya ga mata,wai shin mey ke sasu kuka in
za'a kawo su gidan aure? A ganin shi farin ciki
yafi kamata suyi su kuma gode wa Allah. Hmm..
Bazaka gane ba AAA. Ya ya iyah,aikin lallashi ya
hau yi, sai d'ai dama bai ba,dan kuwa ya
jang'wa6o ta. Kuma fa ta manne mishi,amma
tana fad'in su Umma...Lol. Kamar wata yarinya
ya hau hura mata k'unne. Tuni k'wa sai ta nemi
kuka ta rasa,ya tafi garin su. Da dabara yai ta
janta har ta ware tana murmushi k'eta. A haka
har suka gabatar da da sallah kan ya d'akko
komai a "parlour" da "plate'. Haka ba dan dad'i
sai dan ya mat'sa mata taci kad'an. Ta tashi ta
k'washe kayan,a kitchen ta t'saya k'allo, lalle
duniya,wani abin ma bata san dashi ba. Ga nan
"gas cooker" da halamun mai gidan yasa. Dan
harda gidan ta. Ya shiga d'aki ta dawo parlourn,
shima ba laifi an mata bajinta d'ai-d'ai k'arfi,
kujerunta masu "Ledar" ne kalar 'Orange' da
"milky" labulan ma haka, ga dan "center carpet"
nata mai "grass" da "table" mai zanen "heart" a
jiki. Sai TVn ta "plasma" manne, sun had'a mata
"home theatre" dai,ga nan wata "flower" a tsaye
kamar g'wada da da ya'yanta "Orange''. Ajiyar
zuciya tai,jin an bud'e kofa. A hankali ta zauna a
kasa,yayinda shi kuma yai wajen TV, ashe har
sun had'a. Kujerar da take ya dawo da "remote"
a hannunshi, sai ya tasa kanshi a cinyarta yana
k'allon fuskarta da murmushi. Itama murmushin
take,amma cike da kunya, sai ya juya kan TV ya
d'anna "play". "Title" taga na "My heart will go
on... Wani page ya fito da ire-iren pic din da yake
d'aukan ta ta daga kai sama tana dariya har
hak'waran ta sun fito, Sai ya rubuta. To my
darling Furii.... Sai ga nan wakar "Celine Dion" na
"every night in my dream tana yi cikin "slow
motion" ta fara. Wani pic d'in ya shigo shima tai
k'yau, a kasa yasa.. "I have been in love with you
from the very moment I met you and every day I
continue to fall deeper in love with you".....
K'allonshi tai, tama kasa magana,dan sam wasu
ma bata san an d'auka ba,sukanyi dai fira
wataran taga kamar yana d'aukar ta hoto. Har ya
kare yana mai fallasa mata sirrin ranshi ne kawai
a gare ta,sosai ta gamsu da ganin abin, ya
kayatar ta.. K'allonshi kawai take tana tunanin da
gaske tun had'uwar su ta farko ya fara Sonta?
Ganin k'allon ba na karau bane yasa ya dawo
fad'i da bak'in shi, ina Fure bazata iya d'auka ba,
dan bataji ko ita tana mishi irin wannan son da
yake ta k'wadata da shi. Kan su farga har dare
ya ja sosai,tasan in zasu k'wana haka yana fad'a
mata irin kalaman nan toh bazata gaji da
sauraron shi ba. Ahmad kam karshe ne, ya kere
ta a komai, sai d'ai ya zame mata dole tai
ko'k'arin finshi iya kalami, a ganinta ita ya dace
ta haddace. By Feenat Ja'afar. 庐NWA.
9/29/16, 2:28 AM - Queen Safiyyert馃憫: "JUYA" 漏 Feenat Ja'afar. 23_K'allon yaje ya
kashe,dan jin TV na kukan a kashe ta ta kare,
sai ya ajiye "remote" d'in tare da juyo wa gare
ta, shi take k'allo, sai yai murmushi tare da zuwa
da t'sugunawa a gabanta kamar mai neman tuba.
Abin ba na magana bane a gare su, sai yasa
hannu ya ware g'yalen da ta nad'a, ya cire
d'ank'walin, sai ya ciro da ribbons d'in da ta
tufke kanta da ya sha "relaxer'' d'ai-d'ai fankar
"parlourn" ta k'ada gare su,tuni sai gashin ya
fara tashi, ina gogan baki ya saka,ganin yalasha,
tare da fad'in "SUBHANALLAH.... Hannu tasa ta
rufe fuska,dan sai ya bata kunya ma, cikin ranshi
kuwa,fad'i yake "Lalle t'sarki ya tabbata ga
Ubangijin Sammai.. Ubangijin d'aya k'era mishi
FURIIN shi mai saukin k'yau a baiyane, sannan
mai t'sananin k'yau a ciki.. Ashe Allah idan ya
hana k'yaun fuska,sai kaga ya baka k'yaun jiki...
Yanzu ya yarda kowacce mace mai k'yau ce, ina
ma Y'an uwan shi zasu d'aina zaban k'yalk'yal
banza, suje su lalumo irin wanda basa so da yai
imani su da auren mai k'yau sai d'ai-d'ai... Shidai
yace "ALHAMDULILLAH.. Ganin irin "postern'' da
yai yasa ta zamu itama tai yadda yai, sannan ta
hau fad'in cewar ita ce fa,ba wai sabuwa ba. Sai
yai murmushi kan ya tashi t'saye,sai ta bishi da
k'allo, hannunta ya riko tare da tasarta t'saye
suna fuskantar juna. Jin ba zaya jure ba yasa
bata nufa ba taji ta asama ya d'auke ta kamar
wata baby, sai ta sunne kai kamar marar lafiyar
da aka d'akko ta kasa tafiya. Gun fanka suka
je,sai ta mika hannu ta kashe, tare da sak'alo
wuyan shi. A gado ya zaunarta, sai shima ya
zauna tare da shafo kanta, halamun d'ai gashin
ya mishi, sai tai murmushi tare da sadda kai
kasa tana wasa da awarwaron ta. Sai shima ya
kama hannun, a hankali ya kai shi d'ai-d'ai fuska
yana k'allon filawar da ta fito da taimakon
hasken "bed lamp",cikin nutsuwa ya fara zame
su a hankali, babu magana sai d'ai murmushi.
Sannu a hankali har d'an k'unne ya tayata cire
wa,,kan ya cigaba da rera mata wakar dake
mantar ta kanta ma, sosai in da so,toh komai ya
kan tafi a sauki, sai d'ai fa Furii rakin nan daga
baya yasha shi, tushe k'unne kawai yai, kan daga
baya ya ji da lallashin. Asuba nayi ta bud'e ido,
yana rike da hannunta ya durkusa gabanta,kamar
mai neman ta inda zai fara tada yake, murmushi
ya sau mata,tare da kai hannu ya g'yara mata
gashin ta,sai ta k'au da fuska itama da
murmushin,sai dai hawaye na k'waranya. Ganin
har za'a tada sallah yaki tafiya yasa ta yunkura
zata mike, sai ya taso dan taimako, kai ta
girgiza, kan tace zata iya. Da k'yar ta lalla6a ya
tafi,kan tai dabarar tashi. Yau d'uk sujjada sai
Furii ta samu adu'a, har bazai ce ga adadi
ba,fatan shi Allah ya basu zuri'a da Fure daiyiba
masu t'sant'sar tarbiya irinta. Kan ya dawo ta
kimt'sa komai har ta kara k'wanciya. Haka ya
shigo da allura daga d'akin shi, macen dake
kunyar shi sai gata ta hau waro ido... Sai ya hau
lallashi,kan tai hakuri ba da zafi zai mata ba, kai
ta k'ada, kan a hankali ta tashi, tsinin allurar
kawai taga ta fara yarfe yat'sa. Hmm,tana kai
miki Fure. By Feenat Ja'afar.
Like 路 Reply 路 Report 路 Apr 24
Feenat Ja'afar Novel's
"JUYA" 漏 Feenat Ja'afar. 24_Soyayya suke kam
kamar babu gobe, a satin su Umma da Ya
Suleiman suka tare a sabon gida, amma fur
mutumin yace ya gano mata gida ita sai tai
wata,sai dai satin ta biyu taje,gida kam yayi,d'uk
da ba wani kato bane amma d'ai ya ninka nasu
na Zaria ma na da,katon parlour yasa aka zana
ma su Umman,ba wani kayan azo mu gani ba
ne,amma tsarin yayi, y'ar TVn su "standard" da
"dish" domin k'allo, kujerun su ma d'ai dai
k'arfi,sai t'sakiya "Chinese carpet",da "tiles" sai
"shining" yake,aciki yai musu "3 bedroom"
Kowanne da bandaki a ciki,da kitchen din Umma,
sai waje yai d'akin su Hassan guda biyu, da
"public toilet" t'sakar gidan y'ar madaidaiciya, ya
zuba musu "interlock". Sosai ajiya tai rana, filin
makotan su Abban Ya Suleiman ya siya,katanga
kawai ta had'a su,sai ya fidda kofar yadda zai
iya zuwa ma kowa. Randa suka tare murna
gunsu ba a cewa komai,dan kam ko yaya sabon
waje ak'wai k'yau. Da ta cika sati biyu ya batta
taje ganin sabon gida,d'uk da shi zuwanshi 2.
Ana haka azumi ya kama, sosai yana taimakon ta
ga kuma Maryam, dan "store" gare shi na delar
magani babba, d'uk da yakan je asibiti jefi-jefi,
amma zuwa shagon yafi,sannan yana da masu
kullar mishi,yanzu burin shi su Hassan su gama
secondary ya d'aura su kai, duk da ko ita FURIIN
bai sanarta ba. An gama azumi lafiya yau ta
kama sallah, t'saye yake gaban "mirror" ya daga
kai tana 6alle mishi ma6allin rigan shi, tana
gamawa ta wuyanshi da hannunta tana
murmushi, sai ya dago jin ta gama, "kai k'yau
sosai.. Ta karasa tana k'allon wuyan, juyarta yai
gaban mirrorn suna k'allon Kansu aciki da
murmushi, sai ta bashi sarka,cikin nutsuwa ya ke
6alla mata,sai ta shafo wuyan ta mudubi tace"
thanks. Murmushi kawai yai tare da d'auro kanshi
a kan kafadarta, fuskarshi ta shafo, "hala yau
azumin magana kake? Murmushi yai tare da kara
juyo ta, "kinyi k'yau ne shi yasa banson kat'se
k'allon ki da magana,ki gane ke d'ai, ya ruko
k'ugunta,sai tai kasa da kai tana murmushi,
idonta ya manna "lips" nashi,yana son yaga tai
d'an kasa da kannan tana murmushi, sai yaga
kamar "eye lashes" nata na karu wa. Hoto yai
musu,kan sukai shirin zuwa masallaci. Ana idar
da sallah ana huduba ta ciro waya tana mishi
"Happy Sallah" sai ga nan nashi, sai tai
murmushi, tare da goge nata tai mishi mai
sanyaya rai ta tura. Yau wanda bata ta6a gani
bama a abokanshi sunzo k'wasar gara, Furiin shi
abar alfaharin shi ce wajen girki,shi yasa ba
musu ya barta ta cigaba da makarantar ta. Tana
daga kitchen ita da Maryam,suna jiyo santin
su,sai kara fasa mishi kai suke, bak'in nan har
k'unne, Furii ta fitarshi kunyar Abincin sallah.
Washegari tai ma su Mama da Umma lafiyayye
su ma, "flask" daban tai wa Momy, Mama ma
haka. Lokacin suna parlour Abba yana ta fad'an
jiya basui abinci ba, yauma da yunwa zasu
barshi? Sam ya t'sani abincin y'ar aiki,yar aiki
mai girkin taje hutun sallah,ga Momyn ce da girki
tun jiya,nufin shi tashi yai bangaren Mama sai ga
nan flask daga Fure, shak'e da sinasir da wata
hadaddiyar miya, taji kaji,da murmushi Abban ya
k'alleshi, lokacin da yake gaida su, a gaban
Momy ya ajiye k'wandon. Da fara'a Abban yace
mishi "mey muka samu ne Abba na? Baki Momy
ta ta6e, sai yai murmushi, "Abba abincin sallah
akace na kawo muku.. Da fara'a ya k'alli Momy,
"Maryam bani,zuban naci anan ma,dan fita zanyi,
yai nufi kan "dining room'' d'inta. Ba dan ta so ba
ta d'au k'wandon tai kan "table'' d'in, tana bud'e
"flaks" kamshi ya doki hancin su,tuni Abba ya
fara tattare hannun rigar shi, Ahmad dake gefe
ya girgiza kai yana murmushi, sai yai "kitchen"
d'in Momyn ya tarowa Abba ruwan wankin
hannu. Zai fito sai ga nan momy,itama shi zata
d'ebo,harara ta sau mishi kan tai hanyar d'aki
dan jin haushin zag'wadin uba da d'an akan
abincin Fure. A kusa da Abban ya zauna,sai wani
lumshe ido Abban yake yana k'wararo santi.
Shikam gogan abin nema ya samu, yasan ko
waye in yaci abincin Fure sai yai santi. "Baba na,
da murmushi Ahmad d'in yace "Na'am Abba, sai
da ya kara yankar sinasir ya d'ang'wala a miya
kan yace, "amma makarantar koyan girki iyalin ka
take.... Haba wa,mai Ahmad zai in ba dariya ba,
Abban yace"Allah kuwa,, dake Abba cikin yaran
shi Aboki yake zamar musu. Kan ya farga yaci
tayi biyar, kira yake abarnan kamar an sa mata
madara. Shidai Ahmad baki yaki rufuwa. Tare
suka fito da Abban, shi yai mota,shi kuma ya nufi
bangaren su Mama. Yau ita kad'ai ce, Ummi d'uk
sun fita dasu Rukayya. Kok'arin tashi take ta
d'aura girki sai ga nan sallamar Ahmad d'in. Suna
gaisawa yace ga nan abincin inji pretty, cike da
jin dad'i ta bud'e tana godiya. Abinda sirikan
gidan basu ta6a ba kenan, wai kawo abinci ko
abincin sallah, su ganin su bata lokaci ne ma.
Sai ga Fure da bata ma fi wata da sati biyu ba ta
kawo sabon sauyi. Labarin santin Abba yake ba
Mama suna dariya. Tace "nima dama ko'k'arin
tashi nake na d'aura kan yaran nan su dawo.
Sosai Mama ta yaba da zabin d'anta, ganan
yaran nasu da suka taso cikin d'aular ba wacce
zata ma abinci mai dad'i, su d'ai barsu a mai aiki
sai ko dafa indomie. Ita kam Momy su Abba na
fita ta dawo parlourn, d'uk kamshin miyar Fure ta
karad'e mata "parlour", sai ta hau t'saki, da
mamakin ta Alhaji yaci da yawa da ta bud'e,
gashi fa itama ranta ya biya, amma sam taki koh
ta6a miyar. Tana nan a parlourn taji hayaniyar su
Rukayya, kana ganin su kaga sun k'waso gajiya
da yunwa. A kan abincin Rukayya ta
sauka,Huwaila ta zauna kusa da Momy, tana kai
loma d'aya ta hau lumshe ido, taji abinci ba irin
na Iyabo mai aiki ba. "Kai,"delicious".. Hannu
baka hannu k'warya ta fara ci,sai ta k'allo
Huwaila, "ka'r kiyi missing.. Da sauri itama tai
kan table d'in, daga t'saye ta d'an dana, a zaton
ta ko ba dad'i, ai tuni ta ja kujera.. Sai da sukai
nak, kamin Rukayya ta k'allo momy wace ta sau
baki tana k'allon su. "Momy yau kin mana mai
dad'i, kai,yaushe rabon da na ci irin wannan
abincin da yawa? T'saki Momyn tai,kan tace
"abincin kishiyar ki toh kika ci, kuma wai dan
iskanci suka hau k'ak'arin amai na gulma.
"Amma d'ai Momy da kin fad'a tun farko wallahi
bazan ci ba, cewar Huwaila, sai sukai kitchen
suna ta bala'i, wai y'ar neman gindin zama,sai
d'ai fa kan a wanke hannu har lashe wa akai
bama su sani ba..y'an Kot'ar nan. By Feenat
Ja'afar.
Like 路 Reply 路 Report 路 Apr 24
Feenat Ja'afar Novel's
"JUYA" 漏 Feenat Ja'afar. 25_Da ya je gida tai
mamakin yadda taji wai y'an gidan na santin
girkinta,sosai ya ji dad'i, dan murna sama yai da
ita suna hajijiya da tuntsura dariya. Shi yasa
yamma nayi tai wani abin,sannan tasa ya siyo
mata Aya da kayan had'i. Washegari ma
hadadden "meat pie'' da "doughnut" tai musu da
kunun Aya mai sanyi da k'ankara cikin kula,ya ji
K'wak'wa da kayan had'i da madara. Tun jiya da
yamma tai "doughnut", ta nika ayar ta,dake suna
da wuta "standard" ta samu k'ank'ara. Komai
Fure tai tana burgeshi matuka, ga nan kullum
cikin sabon t'sari take na girki. Fitowa tai daga
kitchen jin yana kiranta, da mamakin shi sai yaga
har ta gama shiri cikin "favorite" d'inshi wato
"Orange color". Wani dak'akken "swiss" ne mai
ruwan Orange da filawa fari, sai tai amfani da
wata "fashion" na kalar kayan,shi bai son
kit'so,sai ya had'u da mai son fakin,daga chan
kasan d'aurin tumin nad'in gashinta ya fito,sai ta
ja g'yale saman kan. Sosai tai mishi k'yau dan ta
lakanci abinda yafi so, karasa yai tare da k'ar6ar
abin hannun nata sai ya manne hannunta cikin
k'wanon da nashi, in ta ja sai shima ya ja,sosai
filawar tai k'yau ta hannun. Sai tai murmushi,
ganin hakan sai ya sassauta ta cire hannunta
tare da g'yara g'yalen, k'wanon ya ajiye sai ya
hau tayata g'yaran g'yalen. Ita d'ai nata
murmushi. Suna a mota hannunshi rike da lalle
yana dan dubawa tare da k'allon hanya,ita dariya
ma yake bata, dan tun safe da ya fita sauke
kayan "storen" shi da aka kawo bai dawo ba sai
dazun,shima yana wanka ya kara fita,sai waya da
ya mata gashi nan zuwa.. Sai zuwa yai yaga
lalle,mai yi har ta tafi, kuma ya kasa tambayar
yaushe akayi. Har suka je gidan suna a farin ciki,
sosai kamar wani rakumi,haka yake zama in yana
gaban Prettyn shi. "Part" d'in Mama suka sauka.
Ko jumawa batai ba tace taje wajen Momy,har
ga Allah tafi kaunar ganinta da Mama. Nata
"snacks" d'in ta ajiye Ummi ta d'au d'ayan sukai
"part" d'in Momy Gomnati. Kusan ilahirin gidan
da sirikansu a gidan ta same su,Aunty JIDDA ce
kawai bata a cikin su,harda amarya Hassana da
aka dawo daga "Honeymoon" ana ganinta aka
hau fikara. Har kasa ta gaida Momy,a ciki-ciki ta
amsa,daga nan kala bata kara ce mata ba tai
d'aki. Wajen y'an parlourn tai yo,bayan ta zauna
ta gaida su,d'uk sun amsa,amma biyu kam keya
ma suka juya mata. Aunty A'i ce tai mata
magana kan daga zuwa d'aya shiru, sai tai kasa
da kai tana murmushi,kan ta dago, "zamu zo
InshaAllah, Aunty Maryam ke harar su Sa'a,kan
su saita k'allon sun, sai suka d'an basar. Har
kusan azahar kan Momy ta dawo "parlourn''
samu tai suna alfari ma Fure, d'an t'sabar cin
fuska wai tarihin kanshi kowa zai bayar tunda an
hallara yau, kowa yasan juna, ita d'ai Aunty A'i ta
hakimce K'afa d'aya kan d'aya a kujera tana
d'anna waya,dan sam bata shiga haukar nan ta
k'annen mijinta. Amma jin Bayanin da Huwaila
take,kawai sai ta sau baki tana k'allon su da
mamaki. A ranta tana"Oh,thank God, Allah ya
gama su da sarakan dagawa da nuna su sune,
sai ta k'alli Momy,ko ajikinta, asalima murmushi
take musu ana k'wada arzikin gidan su. "Ni suna
na Sa'adatu.. (Huwaila) in bracket. "Ina da
aure,da yaro na d'aya, ta shafa ciki, "sannan ga
nan na biyu. Har wani k'ada ido take, "Abban mu
ya mallaki gida je har ba adadi,sannan kud'i a
"accounts" bamu san adadin shi ba,ga motoci sai
wanda ka kaga damar hawa, kowacce acikin mu
yakan mallaka mata mota in zatai aure,da gidan
ta na kanta,sannan mu fita kasar da muke so in
hutu ya t'saya, kai,kud'i yayi a rayuwa. Ta fad'i
tana k'allon Fure da ta sau baki. Sai ta k'allo
Hassana, " ke fa Matar yaya? Hassana ta g'yara
zama, tare da y'atsina, "ni baba na d'an Kasuwa
ne,sannan d'an siyasa ne ajahar nan da ma
Arewacin kasar nan,sannan yana aiki da
"Government'' nima ban san adadin kud'in da ya
tara ba,Abu d'aya na sani,shi sananne ne acikin
masu kud'in jahar nan. "Ga nan kuma t'sarabar
"Honeymoon" ta karasa magana tana wani k'ada
kai da shafa ciki kamar wacce tai abin kirki. Ita
d'ai Fure tai kasa da kai,abin har ya d'aina bata
mamaki, ya dawo bata dariya. Huwaila ce ta
k'allo ta, "Amarya ke fa? Dagowa tai tana k'allon
irin y'atsinar da mai tambayar take mata. Sai tai
murmushi, Ahmad da tun zuwanshi yai tsaye a
"corridorn" Momyn, har zai shigo,sai ya t'sinkayi
maganar Furen tana ce musu, "Ni? Sai suka daga
Kansu wasu harda murmushin keta. Su a dole
zasu tozarta ta. Sai tai murmushi kan ta k'alli
wani gefe. "Furera muh'd suna na. Baki suka
ta6e harda tafawa,wai "Furera"?? Sai tai
murmushi tace "Baba na makanike ne shi,mai
g'yaran mota ko babur.. "bai da kadara,sai
rumfar aikin shi guda biyu. Sannan ba fittacce
bane a garin nan balle ma akasar nan. "Tabbas!
ban tunanin yana ma da "account" ma,balle
kud'in shi har ya gaza kididdiga, sannan ko gidan
kanmu bammu dashi,a haya muke zaune,sai dai
Hamdala ga Rabba, abu d'aya na sani... "Baban
mu zaki ne,mai nema da k'arfin shi da Allah ya
bashi domin yaran shi, sannan ya bamu ilimi
wanda zai taimake mu anan duniya da kiyama, ya
bamu farin ciki, wanda har kullum in mun
k'alleshi mukan ce Alhamdulillah. "Sannan ya
bamu..... "Ke!!! ya ishe mu haka, kai ta dago,
Momy ce ta kat'se ta, sai sauran y'an parlourn
suka sa mata dariya,banda Aunty A'I da Aunty
Maryam, wanda tunda ta fara suka nutsu
sauraren ta jiki a sanyaye, tuni farad d'aya ta
k'wanta musu a rai,ita kam Ummi d'an karamin
t'saki tai ma su Rukaiyyan.. tana jin Rukayya
tace "Rubbish" cikin y'atsina. Sai ta k'ada kai,
tare da yin kasa da kai tana murmushi tare da
wasa da y'atsunta. Kai ya jingina a jikin
bango,t'sabar So da kaunar Furii ke kara shigar
shi, tabbas ya t'sani fari'a, sosai ta kara kima a
idon shi, d'an fed'e musu ainashin ita wacece...
Ji yai an dafa shi, da sauri ya bud'e ido ya k'alli
gun, Mama ce,har da d'an guntun hawayen ta
dan tun t'sayuwar shi ta t'sinkayi komai, sai ta
k'ada mishi kai, tare da ruko hannunshi suyi
"part" d'inta. Zama sukai,sai yai jugum, itama
d'ai shiru tai, chan ta kira shi ya dago,da
mamakinta sai taga idonshi ya k'ada kamar zai
kuka, sai ya marairaice mata, kafadarshi ta dafa,
"Ahmad, kai hakuri,ni ina ji a jikina matarka
alkairi ce gare mu a gidan nan, dole kaji ka toshe
k'unne ka, dan nasan zata iya bawa kowa
amasarshi d'ai d'ai shi tunda ta bada a wannan
karan, ,kar ka fara tunanin cire ta a y'an uwan
ka..kai hakuri, da sannu zasu gane nasan
wataran. Kai ya k'ada mata. By Feenat Ja'afar.
庐NWA. Feenat.mywapblog.com
9/29/16, 2:31 AM - Queen Safiyyert馃憫: Feenat Ja'afar Novel's
"JUYA" 漏 Feenat Ja'afar. 26_Ko minti biyar basui
da dawowa ba sai gasu ita da Ummi da Aunty
A'i. Fira suke cikin murmushi, sai Momyn ta dan
ji dad'in yadda Aunty A'in ta sau ma Fure jiki.
Aunty A'i tace, "dan d'aki ashe tare kuke da
amarya? Kai ya k'ada mata yana k'allon Furen da
murmushi. Sai mama tace Ummi ta zuba musu
doughnut dasu kunnun Ayar, sai tai ciki dan basu
gu,cikin murna tai kitchen da zamud'in zata kara
cin abincin Fure. K'allota Aunty tai tana taunar
"doughnut", "wai gaske ke ne ki kai ba aikatau
ba? Murmushi tai kan ta dan k'alli wajen
Ahmad,itama Aunty A'in sai ta k'alleshi. "Ok,kai
kayi kenan? Kai ya k'ada, "ya kika ji toh? Kai ta
k'ada tare da dauk'ar "meat pie", wannan ma ta
hau k'ada kai cikin santi, sai d'ai Ummi na zuba
mata kunun Aya ta hau g'yara zama, fad'i take
"kai,wannan kuma mey ne? Dariya suka hau
mata,ita kam ta dage da gaske take bata san
kunnun Aya ba,ita d'ai Fure kawai murmushi take
musu, dan tasan tsaf sai ta kasa sannin, dan
y'an gayu sai da lemon k'wali. Suma achan ba ko
kunya suna ganin Aunty Maryam ta fara ci suka
zira hannu, barin Hassana,kamar wacce bata
taba ganin filawa ba haka take narkar "snacks"
d'in. Rukayya ce bata ta6a ba,tabi Momy suka
zuba musu na mujiya kawai. Amma chan kasan
ranta bata manta daddadan abincin Fure ba.
Suna gamawa sukai bangaren mama,sai d'ai
yadda Aunty A'i ta had'e rai,shine yasa suka
gagara tankawa Fure. Sai da akazo sallah tukun
ta yaye g'yale da nufin zuwa alwala, baki Ummi
ta saka ita da sauran,ganin gashin Fure,ga nan
ilahirin shape nata ya baiyana cikin les din. Sai
tai murmushi, tana jiyo musun Huwaila da da
Hassana kan wai "attachment" tasa. Kawai sai ta
k'ada kai ta shige alwala. Har ta iddar ba wanda
ya motsa sai Ummi, Aunty A'i tace tana fashi,
Aunty Maryam kuma tana gun mama, kawai sai
ta zuba musu ido, da mamakin ta har uku suna
kan waya ana nuna kayan k'arya na d'aki wai
Huwaila zata sauya. Mama ce ta fito,sanyin hali
yasa ta tambaye su tukun sunyi sallah? Kansu na
waya suka girgiza halamar A'a, sai ta had'e rai,
''toh maza ku bar min nan, ace d'an musulmi har
uku bai sallah ba? Fure d'ai ikon Allah take
gani,ba musu suka bar parlourn sukai na
Momy,sai Hassana ce ke sinke kataje tai alwala.
Sam basu kaunar zama kusa da Mama,ita sam
bazata bar bawa ya wataya ba,ga nan Momy,suci
karan su ba babbaka ma ba ruwanta dasu.
Washegari kuma tai gidan su,sai dare ya d'akko
ta suka dawo. Sai dai koh a fuska har yau bata
nuna mishi abinda y'an uwanshi suka mata ba.
Sai d'ai a ranta tana fad'in ta d'aina tanka
musu,dan ta san rashin islamiya ke damun su.
Sai d'ai Hassana tafi bata dariya,mai tunkaho da
kud'in ubanta. Kud'in Tukudi, kud'in cizo,kusan
unguwar su d'aya da Y'an uwan su Adama, ta
bata sirrin komai ai, karya kuma ta kare. Tun
daga wannan ranar d'uk "weekend" d'in duniya
sai Fure ta aika ma Abba dasu Mama abinci,na
satin nan sai ya ninka na satin gaba dad'i. Sai ya
zama har Allah-Allah Abba yake ya ji ance
"weekend " tayi yana gida,dan ya k'washi garar
abincin sirikarshi mama na gefe tana mishi
murmushi. Dan sam Momy ta d'aina k'ar6a koh
an kawo mata. Ko ran girkin Momy ne kuwa indai
ya fad'a a ranar kawo abincin Fure Abba shi zai
ci. Bashi ba,hatta sauran mazan gidan irin su
mijin Hassana nasan girkin Fure. Dan ak'wai
lokacin da yazo ya samu Fure ta gama girki tana
"serving" yayan shi shima ta zuba mishi, da
hadd'en lemonta na kullum,tuni ya soma wa
Ahmad santi, nan tana daga d'aki taji yana
t'surkutawa Ahmad d'in wallahi ba abinda
Hassana ta iya sai dafa indomie da k'wai,kai
ranar Fure taci dariya ta gode Allah. Sosai zata
gode ma Allah a bisa yadda ya sauya rayuwarta
farad d'aya.. Babban farin cikin kuwa shine
yadda ta zama fitilar haskawa ga mijinta, ta
zama abar alfarin shi, ya zama abin nuna ma
sa'a, domin ya bata d'ukkan farin cikin dake a
gidan aure,ance zo mu zauna zo mu sa6a.. Toh
a gaskiya Fure sai anyi kure,kan taga sun sa6a
d'in, albarkacin mijinta ta leka garin manzo, ta
leka kasar da ko a mafarki batai tunanin zuwa
ba. Sai d'ai dake Allah ya kan jarrabi bawanshi a
d'uk farin ciki toh dole ak'wai bak'in ciki, ba
komai zaya had'a maka 100% ba a
rayuwa,matuka yanzu burinta haihuwa. Ko dan
ganin yadda har ta fara taka matakin gori daga
y'in shekara agun dangin Ahmad. Yanzun kam ta
kara samun matsayi, daga y'ar MATSIYATa ta
koma JUYA. Bata jin da taron da za ai a watse
lafiya ba tare da an wat'sa mata magana ba.
Hakan yasa ta halarci ganin likita,ko d'an ganin
mey matsalar. Duk da shi ta gun Ahmad d'in d'uk
kaunar shi da yara bata ga chanji ba, asalima
cewa yai yaushe ma akai auren? Kar ta tada
hankalinta, "soon'' zasu samu baby. Tanan kawai
takanji sanyi,har ta manta bakin cikin su
Huwaila. Ranar sun fito ziyara sukai har gidan
k'aninshi mijin Hassana, dak'yar ya yarda,shima
sai da tace bai fa je ganin baby ba. Suna a
"parlour" yana cin abinci, da murna ya tari d'an
uwanshi, itama Hassana ba laifi, ganin Ahmad ta
sau mutunci,dan sam bai bata fuska koh a gida
suka had'u. Sai dai motsi kad'an ta ambaci
sunan y'arta, ita a dole zata bawa mara D'a
haushi. Murmushi kawai Furen ke mata,shikam
Ahmad kamar an tsikare shi yace ta tashi su tafi.
Direct gidan Aunty Jidda suka sauka, hakima
isassa, Allah ya gani d'uk Familyn su Ahmad tafi
ganin tsanarta karara akan Fuskar Aunty Jidda.
Ba abinda ta bari na Momy,sosai in ka ganta sai
ka d'auka K'anwar Momyn ce ma,dan sosai tafi
Momyn tsufa. A kofa ya batta kan zai shigo Abba
na neman shi. Kai ta k'ada mishi, sai d'ai tana jin
jina

Please Login or Register in order to submit comment