You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

sai d'ai yana tafiya ta k'ar6i
"pass" tai ''Hostel". Kuka take wanda da
biyu,itama d'ai ta zurma d yawa, amma irin su
Uncle Ahmad tasan ba ajin su bane,wai k'warya
tabi k'warya, yadda yake da aji da k'yau tasan
yafi k'arfin ta, zuciya kawai ke yaudarar ta. Tun
tana damuwa da son Uncle Ahmad har ta jingine
shi ta hau karatun ta. In har da rabon zasu gana
kila ta ganshi. Sun gama "exams" kowa ya tafi
gida da k'ewar juna da dunbin k'yaututtukan
ta,sa6anin Adama da suke kusan unguwa d'aya
da Pretty. K'allon Fure Umman su take,d'uk ta
rame kibar nan ta dawo y'ar chas da ita,"har yau
ina mamakin ramar nan taki Furera,ko A'i batai
rabin ramarki ba data gama makaranta.
Murmushi tai,kan tace"Umma karatu ne, zai
maida kiba ta har da k'ari, kai ta k'ada, sai dai
har yau tana mamakin yadda Fure ta nutsu gaba
d'aya, ta zama wata irin sassanya,a zaton ta d'uk
makarantar ne, sai d'ai gashi har sun shafe wata
1 da gama makaranta Fure na yadda take,kawai
sai ta bada girma ne ya shigi Fure. Abu d'aya ke
ci mata tuwo a k'warya yadda shiru ba labarin
Uncle Ahmad, ga yadda tsabar tunanin shi ke
hanata sukuni,takanji zuciyarta na wani iri in ta
tuno shi, gashi ko numbern shi bata rike ba,
dabara ce ta fad'o mata,fatan ta Allah sa Abban
su yai saving numbern, dan tana yawaita kiran
shi da ita. By Feenat Ja'afar.
Like 路 2 路 Reply 路 Report 路 Apr 14
Feenat Ja'afar Novel's
"JUYA" 漏 Feenat Ja'afar. 7_Da dare Abba ya
dawo a wajen aiki ta d'au wayan da nufin zata
kira k'awaye, d'akinsu ta kule,kan ta hau duba
"contact" "Fure schl" taga sunan wani contact,
tasan kenan numbern da take kiran Abba dashi
ne a makaranta, gabanta na fad'uwa tasa
numbern a "private" kan tai "dailing'' g'yara
k'wanciya tai,tana sauraron yadda wayan ke
"ringing" bugun zuciyarta na k'aruwa, sai da ta
kusa yankewa har ta sadddak'ar ta sinkayi
sallamar shi da muryar da ke sata cikin nutsuwa.
Ido ta lumshe tana sauke numfashi da sauri,
hannu tasa a d'ai-d'ai zuciyarta dake mata
barazanar fitowa fili. "Da wa nake magana pls?
Sai a sannan ta bud'e ido,tama manta da ya
d'auka,sai da ya kara sallama kamin a hankali ta
zare wayan a k'unnenta tana hawaye ta kashe.
"Ashe ita kad'ai ma ta damu dashi? Kila ma shi
ya manta kashin wata Fure a wani gu, zatan ta
baya ma kasar, dan yasha sanarta "England" zai
je masters, ashe yana kasar a garin amma bai ko
neme ta ba har tsawan wannan lokacin... "Fure
lafiya? Umma ce ta katse ta,da sauri ta goge
hawayen tare da k'ak'alo murmushi, "ba komai
Umma,, da mamaki Umman tace "ba komai ki ke
kuka? Jin dad'i komai? Kai ta k'ada,tare da
kawar da zancen da cewa "yaushe Aisha zata
dawo Umma? Zama Umman tai,kan tace" a satin
nan zaki ganta, ai tasha hutu kusan wata biyu
kenan,amma Furera tun dawowar ki na fuskanci
kin sauya, kin zama shiru-shiru, kodai ba ki lafiya
ne? Kai ta k'ada kan a hankali ta zame ta
k'wanta cinyar Umman, "Umma ba komai,
makaranta make ma son shiga Umma. Kai ta
k'ada mata," yana da k'yau, Allah shige
gaba,amma sai kin tsaida tunaninki waje d'aya,
gashi har yau kin kasa maida jikin ki,sai ma wata
ramar da naga kina yi. Kai ta k'ada mata,kan tai
ko'k'arin had'iye kukan ta. Gaba d'aya ta tattara
Uncle Ahmad ta jingine shi gefe,har numbern shi
ta ma goge,dan in d'ai ta motso mata in ba
muryar shi taji ba bata samun sa'ida, yanzu kam
Alhamdulillah, ta samu ta fara manta so,sai d'ai
"memoryn' baya yana a K'wak'walwar ta. Yanzu
karatun ta kawai tasa a gaba,a bangaren
''catering''. Yaya Suleiman ya kamalla karatun shi
har an bashi aiki,yanzu burin shi aure,sai dai har
yau bama budurwar,babban burinshi kamin na
yanzu bai wuce ya tara kud'i ya tada ginin Abban
shi ba,dan sosai yake da murad'in iyayenshi suyi
nasu su huta da haya. InshaAllahu zaya hutar da
Abba aikin makanikanci bada jimawa ba,yai
alkawarin ji da iyayen su da y'an uwanshi dad'i
na duniya in har Allah ya bud'a. Albashin shi na
farko Abba da Umma ya direwa,a ganinshi su yafi
kamata su fara ci kamin kanshi, musamman
Abban su mai arzikin zuci,ya sani da Abban su
mai jajircewa ne mai kuma nema da guminsa,shi
yasa yake kara alfari dashi yake kuma neman
koyi da dabi'un shi. Zaune suke da
yamma,dawowar shi a aiki kenan suna zaune a
katuwar darduma a tsakar gida shida Umma da
sauran k'annen shi,yakan yi nishadi in ya ji shi
cikin gida haka da d'uk Familyn shi,Abba kawai
ya rage baya a cikin su,tad'in bikin Aisha suke da
Umma, yayinda Fure ke zaune tana taya su
Hassan da Hussaini "Assignment",sai d'ai jefi-jefi
yayan nasu na sako ta cikin zancen. Ka gansu
g'wanin ban sha'awa, gidan su ba k'yara bare
hancini, kowa yana nan-nan da juna. Adama tai
sallama, cike da murnar ganin K'awarta ta shigo
gidan. Wani ihu da suka zuba kan Furen ta tashi
suka ruk'unk'umo juna, daga Umma har yayan
baki suka saka suna k'allon su,toh g'wara Umma
dama tasan halin Adama da Fure,amma shi da
mamaki kawai yake k'allon su musamman
Adama, sai da suka gama rawar kansu tukun
cikin kunya ta gaida Umma,kan ta sauke
k'allonta akan Ya Suleiman,da halamun kowa d'ai
yai katari da " soul mate " d'in shi, dan kasa tai
da kai,lokacin da ta gano waye shi,shikam
k'allonta kawai yake da murmushi,kai duk'e tace
"ina yini Ya Suleiman, Fure ce ta katse shi,"
Adama ce fa Yaya,ta girma koh? Murmushi yai
kan ya amsa,"ai sam ban gane Adama
ba,"2years" d'uk sun kara girma,koh Umma?
Murmushi ita d'ai Umma tai,da halamun ta gano
bak'in zaren. By Feenat Ja'afar.
Like 路 1 路 Reply 路 Report 路 Apr 14
Feenat Ja'afar Novel's
"JUYA" 漏 Feenat Ja'afar. 8_D'aki suka shige,
suna firar yaushe gamo, "kawai ki kaje kikai
zamanki a Abuja abinki? Murmushi tai, kan ta
ware "pashminan" kanta, "k'awata Abuja tayi a
rayuwa, ke! Bari kawai, Allah kamar kar na dawo,
naci fa na k'wanta, hatta kayana wanken ake.
Hannu ta bata suka tafa tana "shege Ada,kinyi
k'yau ke kin ganki? " ke d'ai bari, zama ta g'yara,
"kai k'awata yayan kun nan fa Allah sai had'uwa
yake kara yi, d'uk yafi y'an gidan nan k'yau fa..
Dariya ta tuntsire mata dashi, kan ta bata suka
tafa, " dad'ina da k'awata ba fulako,ki ce munyi
kasuwa? Hannu ta kai bak'inta halamar tai a
hankali,"Allah dama ranar yace nai mishi
budurwa a unguwar nan,sai kuma naga shima
kamar ya zurma. Wasa-wasa d'ai zance ya
tabbata tsakanin Adama da Ya Suleiman, har
magana taje gidan su Ada, sosai ba wanda yakai
Fure son wannan had'i, sai kuma su da suka
k'ulla abunsu. Biki kam ya karato, d'uk da yazo a
lokacin da Fure ke shirin y'in Exams a school.
Tafe suke ita da Aisha da k'awayenta su biyu
daga saloon,ganan g'wagg'waran su a leda da
aka nad'a musu, k'awayen suka tsaida 'Taxi"
suna sanar da Aisha sai goben, sauri suke, ganan
magriba ta wuce amma hanya d'uk "go slow", sai
sunyi kamar zasu t'sallaka sai Fure ta
r'unkumota har wata motar ta taho, t'saki Aisha
tai," wallahi kamar tashin k'auye kekam, da tuni
mun wuce sai wani rirrike ni kike. "A ke,rai d'aya
ne, a yadda kowa yake saurin nan muje wucewa
da garaje kawai sui ciki damu? Kai Aisha Amarya
ta k'ada," toh ni kam zan t'sallaka, dan kinsan
Abba in ya dawo ya tarar bamu dawo ba fad'a
zai,in yaso randa mutane suka d'auke K'afa sai
kizo. Hijab d'inta ta rike,"wallahi baki isa ba.
Yanzun kam mota suna d'an nesa, hannun Furen
ta kama"ki biyo ni toh yanzun. Da d'an gudunta
Aisha tai gaba,sai jin Fure ta zame hannunta tai,
"tsaya ledar mu, ina, A'i har ta wuce,da sauri ta
ju ya da nifin ta t'sallaka t'saut'sayi, ashe wata
jar CRV ta kuts'o,da gani kuma sauri su ma suke,
gashi tazo t'sakiyar k'walta,ga ihun Aisha na tai
gudu ta karaso. Ga ihun "horn" din motar,d'uk sai
ta kasa gaba ta kasa baya,suka had'u da tsoron
k'walta suka rikita Fure,ido ta rintse,tare da
sakar ledar kayan a kasa ta rufe k'unnenta da
hannunta d'uk biyu, tasan ba makawa sai motar
nan tai ciki da ita. Jin shiru ba ai ciki da ita ba
saima hasken motar da ya dalle mata ido da dan
jin hayaniya yasa a hankali ta bud'e ido jiki na
ka'r-ka'rwa. "Da ke! ke da asara wallahi bamu
ba, so nai a yabimin ta kanki tunda kin gaji da
duniyar shi kuma ya tsaya.. Babbar mace ce,sai
d'ai da ka ganta zaka san isassiya ce mai ji da
kanta, k'allo d'aya zaka mata kasan naira na inda
take, fara ce mai kiba ba chan ba. Sam ita bama
ta lafiyar Furen take ba. Masifa take ma Fure
kamar ta rufeta da duka,gashi ita Furen ta tsaya
kem! Kamar an dasata a gun,har yanzu jikinta na
ka'r karwa, Aisha data karaso ita kad'ai ke bawa
Hajiyan hakuri,tare da ko'k'arin janye Fure. Wasu
da suka gaji suka zame bi ta gefe. Haka take ga
wanda yake " driving ",tunda ya taka birki yake
k'allon wacce yaso ya bige, kamar wani wawa ya
sau baki yana k'allon Fure ba ko kiftawa, ganin
suna neman tafiya yasa da sauri ya 6alle murfin
mota yai gunsu, Hajiyan ta zata k'addamar musu
zai yi sai taja baya,yace"Momy shiga mota in zo
yanzu. Sai da yaga ta shiga mota yai gunsu
Furen," Aisha. Da sauri Aisha ta dago,wanda
Fure itama tai saurin dagowa lokacin da zata
d'au ledar, "a pharmacy? Ba d'ai kai ne a motar
ba? Idon shi akan Fure yake yana murmushi,
yayin da itama Furen ta zuba mai ido ba koh
kiftawa. Tabbas itace,ya fad'a a zuciyar shi,sai
da Aisha ta kara magana kan ya juyo gare ta,
"kuyi hakuri amaryar mu,sam ban zata ku bane,
kan Fure ya dawo, " Furera da fatan bakiji ciwo
ba?....Momy ce ta katse shi da cewa "Kai dare
fa na kara mana a titi, kabar wannan yaran dama
y'an titin ne daga gani mu tafi. Wai waya wa
yai," toh Mom,coming. "Ku kara hakuri pls
Amarya, ya dubi Fure,da itama shi take k'allo ba
ko kiftawa, Aisha ma da mamakin ina yasan Fure
take, sai kuma mamakin uwar shi bala'e'iya,
Tana nan a haka har sukai sallama amma ita ta
kasa furta komai. Har ya shiga mota shima yana
waiwayen ta. Ko da suka je gida su Umma suna
ta tambayar su ina suka tsaya har haka? Furen
Aishan ta k'alla, "Umma amare ne sukai yawa a
garin,ga gidan mai kunshi ma acike. ''Toh ita
Furen mey ya same ta? Koh yunwar ce? Da sauri
Aisha ta k'ada kai, dan tasan in d'ai ta sanar da
Umma abinda ya faru yanzu zata rikice. Juyi
kawai take a katifa, har yanzun ta kasa
t'ant'ance murna take ko akasin haka? Ga Aisha
ta dameta da tambayar ina Ahmad yasan ta? Kai
kawai ta k'ada mata, kan tace itama bata sani
ba. Juyi ta kara yi,sai ga hawayen da tun dazu
take bidar su zubo sunki sai yanzun. "Dama
uncle Ahmad na garin nan har yanzu? Lalle
yanzu ta kara tabbatar da ihu kawai take bayan
hari, tunda har address ta bashi in yaso zai neme
ta. Haka ta lulluba tai mai isarta kan ta sa a
ranta indai tana da zuciya toh tabar tuna uncle
Ahmad. Suma chan su Momy tun a mota take ta
kara zagin su Fure,shi d'ai yai shiru,tunani ne fal
ranshi har suka zo gida. K'wance yake yana
k'allon" A.Cn d'akin nashi, kawai yanayin Fure
yake tuno wa, ashe Allah zai sa yaga Fure a
fad'in garin nan bayan rasa address d'inta da
wayar shi? Murmushi yai,a hankali ya
furta"Pretty" sai kuma ya gintse. Tabbas Fure na
matukar kama da Aisha,sannan sosai yasan
yayan Aishan a A.B.U,toh meye had'in su da
Fure? Dan tun dawowar Suleiman a dalilin auren
Aisha sau biyu yana zuwa gidan su,amma bai
ta6a ganin Fure ba... Gaban shi ne ya fad'i
sakamakon tunawa da zanchan su na jiya da
Suleiman d'in, kan wacce zai aura makarantar da
yai service tayi,kuma shekarun d'aya.. Kar fa ace
Furera ce wacca Suleiman zai aura? Kila koh
y'an uwa ne shi yasa suke kama... Cewar wata
zuciyar. Tashi yai zaune,dan tuno da g'yaran
amaren da suka sha ga uban lalle da kayan
g'wag'gwaro da suka fad'i kasa. By Feenat
Ja'afar. 庐NWA. Feenat.mywapblog.com
9/29/16, 2:17 AM - Queen Safiyyert馃憫: [4/16, 12:30 PM] Feenat Ja'afar: "JUYA"
漏 Feenat Ja'afar.
9_Washegari "10am" a kofar gidan su Aisha ta
mai,a kofa ya same su, da halamun daga wani
waje suka dawo,tsaye suke da Ya Suleiman suna
ta nishadin su da dariya,tun a nesa kawai ya
bada hasashen shi ya zama gaskiya,toh amma
ita Furen wace tasu? Ina ne gidan su?
Tun tsayuwar shi Fure ta tsagaita dariyarta tana
dub'en motar,tabbas ta jiya ce, k'allonta Yayan
nasu yai,kan ya k'alli inda take k'allo, tuni fara'ar
shi ta karu tare da furta"A'a, AAA.. Kan yai
wajen shi,Aisha ma ta fara fara'a, ita kam kasa
tai da kai,dan ganin suna yin wajen su da Uncle
Ahmad d'in.
Idon shi na kanta,ganin yadda Yayan nasu ya
shiga t'sakiyar su ita da Aisha,da fara'a suka
gaisa da Aishan,kan itama tace"Uncle ina
k'wana.. Damm! Ya ji zuciyar shi ta buga,a
hankali ya amsa,tare da d'auke kai a kanta,
shikenan Pretty ta fita a rabon shi? Ido ya dan
rintse,"kai zurfin ciki bai ba a rayuwa, gashi yana
k'allo k'wado zai mishi K'afa.
Ya Suleiman ya k'allo shi, "nasan dama zaka
sansu, sai ya k'allo Fure da murmushi, itama ta
k'akalo murmushin dole. "she's my.. Da sauri ya
tare mashi numfashi da fad'in" I know, sai yai
murmushi a takaice, kan ya k'allo Furen, Ya
Suleiman yace"ok,kun ta6a had'uwa a gidan ne
hala? Kai ya k'ada, duk sai ya ji tsayuwar ta
gundure shi,Aisha ce ta katse shi da fad'in
"Ina Angon ka barmin shi? sai kuma ta rufe fuska
ganin yadda Yayan su ya kafa mata ido, " iyee!
Lalle fitsaru. Shikam murmushi yai kan
yace"yana a masaukin shi,zai zo bada jumawa
ba.
"Zan wuce, dama Ilyass ne yace na tabbatar da
lafiyar Madam d'in shi,sai mun had'u a " Dinner ".
K'allo su Fure yai,"toh amare zan wuce,sai mun
had'u anjima, kai Fure ta k'ada mishi, kan ta d'au
ledar su ta shige gida,da tsabar takaici,ashe ma
ba dan ita yazo ba? Ajiye dilkar tai da suka
k'ar6o, tai ciki ta bar y'an biki a t'sakar gida.
Shikam a mota d'uk ya rasa sukuni, Fure ita ce
mace ta farko da ya fara jin " feeling'' akanta,
hatta Maman shi tasan da zancen Furera,yau da
ya sanarta yaga Furera k'warai ta tayashi
murna,har yaje gida sukuku yake jin kanshi. Sam
baida kuzari.
D'akin Maman shi ya zu6e, wanda indai maganar
mace ne toh dole sai wajen ta,amma sauran
lamari Momy ce ja gaba sama da Maman tashi.
Mata biyu ne ga Baban shi, Momy itace Uwar
gida,yayinda Mama ke amarya, d'uk a zankuwa
aka haife su, sai d'ai lokacin su Ahmad na yara,
kamin suka dawo Kaduna da zama gaba d'aya.
Baban su Alhaji Abba Ahmad "costom" ne kan
yai "resining" ya zama d'an k'wangila.
Sosai yana da kud'i, sannan da dattako, Momy
nada fad'a, sam taki jinin talaka,dan baban ta
babban "costom" ne lokacin da Alhaji Abba ya
aure ta.
Ga matukar dagawa da raina mutum,ga son fasa
taro,komai ita ke ju ya shi son ranta a
gidan,yaranta 3,Hauwa(Aunty Jidda), itace babba
a gidan,sai Nasir,da Huwaila, sai y'ar K'anwar ta
da take ruko Rukayya.
Kan aka auro Mama, d'uk itama gidan su ba
laifi,gata mace ce har mace,mai hakuri da
t'sabar sanin ya kamata,tana da kawaici, kullum
zaka samu fara'a k'wance kan fuskarta, da fari
Momy ba taso zama da kishiya ba sam ita,
sai d'ai kuma wani had'in Allah, kawai sai tasu
tazo d'aya, dan komai ta sakar mata ta
mallake,hatta yara in ta haifa toh sun koma
zaman d'akin Momy,ita kam dake mai hakuri
ce,d'uk sai ta sallama mata su, yaranta
shida,Usman, wanda shine mijin Aunty A'i, sai
Aunty Maryam,Ahmad,da Ummi autar ta rasu.
Amma d'aya kawai ta rike wato Ummi.
T'sakaninta da sauran sai gaisuwa koh in taje
bangaren Momyn,sai ko randa ta motso musu
suzo bangaren ta,dan ita k'wa6arsu take matuka,
amma a d'akin Momy sunan ka"kai komai ba
komai na".
D'uk da mugun hali irin na Momy sam batai ma
yaran Mama mugunta,batta da mitar ta,hakan ne
yasa ita maman sam bata damuwa,sai d'ai abu
d'aya, duk yaran kad'an ne basu kin talaka da
raini,wannan dabi'ar ita kad'ai ke ciwa Mama
tuwo a k'warya.
Dan tamkar fad'an Allah d'uk yaran gidan sai mai
kud'i, in maza ne sai ya'yan manya masu k'yau.
Hudubar Momy kam tai aiki,Ahmad shine ya fita
daban,wanda sam baiya burin auran y'ar masu
dashi,sannan kuma k'yak'yawa.
Asali ma tun tashin Rukayya Momy tace itace
Matarshi, shikam fur yaki, dan ka'f ba abinda ta
bari a halin Momy,tamkar ita ta haifo ta.
Gadai k'yau har k'yau, amma sam ba hali. Shi
yasa ko dariya Ahmad bayayi a gaban ta,
asalima ita d'uk gidan shi tafi tsoro.
Takanyi ma Momy kukan sam Ahmad bai kula
ta,sannan ga hancinin tsiya. Momyn takance ta
k'wantar da hankalinta,Ahmad kamar ya zama
nata an gama.
Haka kowa yana da burin fita kasar waje yai
karatu a gidan amma banda Ahmad.
Rayuwa mai sauki shi ya za6arwa kanshi, kuma
a zahiri kowa a gidan naji da Ahmad, har sukan
kira shi da mai "ra'ayin kanshi".
Anan ya had'u da Ilyasa,yayinda shi Ilyass yake
abokin Ya Suleiman. Nan suka k'ulla abota, duk
da kowa bangaren shi daban,sannan ba yadda za
ai ya nuna maka shi d'an wani ne,dan ko mota
bai ya zuwa da ita cikin A.B.U.
Ko Abban ne a yanzu d'ai da Ahmad yake yawo
ko ina zashi,tunda sauran manyan yaran kowa ya
kafu da K'afarshi.
Sosai Abban su yake son yaran shi,haka bai son
takura musu,yai musu sa6o da jin dadi,d'uk da
shi d'ai bai kin talaka,sannan baida wulakanci.
Mama ce ta k'allo Ahmad," ya d'ai? Har ka dawo
a gun Fureran? Kawai sai ya k'wanto cinyarta
"Mama aure zatai go6e.." Ya Salam! Shine
kalmar da maman ta fad'a.
Kamar ya k'urma ihu haka yake ji.
"Ita ta fad'a maka? Kai ya girgiza, " A'a, Aboki na
d'ai zata aura.
Kanshi ta shafa cikin sigar lallashi, "kai hakuri
toh,Allah yasa hakan shi yafi zama alkairi, Amma
sosai nima d'uk da banga Furan nan ba ta shiga
raina. Nan tai ta bashi baki,kan matar mutum
kabarin shi.
By
Feenat Ja'afar.
[4/16, 1:44 PM] Feenat Ja'afar: "JUYA"
漏 Feenat Ja'afar.
10_Da k'yar ya iya shirya wa zuwa wajen
"Dinner". Sosai yai k'yau cikin manyan kaya yau
da ya shige su,dan shi ma'abocin kanana ne.
Farar shaddar ta matukar k'ar6ar shi, ga hular
nan ta kama,sai kamshi yake kamar Angon ba
wai abokin Angon ba.
Parlourn Momy ya shiga,don sanarta ya fita.
Rukayya ce kawai a parlourn tai d'ai-d'ai a kujera
tana " 2go". Tana ganin shi ta mike da rawar kai
harda ce mishi yai k'yau, baki ya d'an ta6e kan
ya had'e rai''ina Momy? Da dan harara ta nuna
mishi d'aki ta koma ta k'wanta a ranta tana"ka'r-
ka'ra a d'aura mana aure ne,zaka shigo hannu.
Sukuku ta gama shiri tun jiya batta kuzari,
hakanne ma yasa Y'an uwan suke d'an sata
nishadi,amma da anjima zata dawo gidan jiya,su
sun d'auka koh rabuwa da Aisha ke sata haka.
Tsaye suke a gaban madubin su na katako a
d'akin su,kanta kawai take k'allo, matuka tai
k'yau tamkar wata k'yak'yawar. Tabbas in kana
da k'yau ance ka kara da wanka.
A d'uk k'walliyar k'ewayen idonta yafi ko'ina
d'aukar hankali.
Ma'abociyar ita gashin ido ce dana gira sune
tushen k'yanta. Yau sunsha" Mascara'' da "eye
liner''. G'yaran jikin da fatarta ta samu ita ta
fidda ta zama " Black Beauty",
net ne "gown" "combination" d'in fari da "pink" a
jikin ta.
Daga sama aka sa farin zuwa chan g'wiwa,
kasan aka mishi tattara da "pink" d'in, da "head'
na "pink" da k'yali-k'yallin "silver''.
sosai tai k'yau ainun kamar itace amaryar.
d'uk da su masu karamin k'arfi ne amma ak'wai
zuciyar yi,dan sosai sun fitar da kansu
kunya,d'ai-d'ai g'warg'wadon hali Abba da Ya
Suleiman sun fitar su kunya.
Kawun su na Zaria shi ya d'au nauyin gado da
kujerun Aisha y'an zamani,sosai y'an uwa ma
sun musu kara abin sai son barka.
Adama ma tasha lefe Ya Suleiman kamar ba
go6e,ranar albashi yai rana da taimakon
makanikancin.
Aisha ce ta shigo ita ma sanye da" net"
"brown".. Sosai tafi Fure k'yau,amma a yau d'uk
sun had'u sunyi k'yau sosai.
Gaban madubin taje tana murmushi, kanta ta
d'aura akan kafad'un Furen, " y'ar uwa tamkar
kece amaryar kinyi k'yau ainun,, murmushi Fure
tai d'uk tai laushi, "ku nake tayawa k'yau tunda
kunyi k'yau kuma. Tai murmushi, "dan Allah
Furare mey ke damun ki? Tun randa abin nan ya
faru d'uk kin dawo wata iri, kinyi sanyi sosai,
"dazun naji kince ma "pharmacy" Uncle, amma
kince min baki sanshi ba,bayan Ya Suleiman yace
anan yai "service'' a school d'inku,mey kike 6oye
min ne? Murmushi tai kad'an kan ta juyo, gaskiya
ta fad'a mata kan ta sanshi sosai.
Ido kawai ya zubawa kofar " Hall" d'in dan jin
ana sowar ga Amare nan, Asha da Angonta ne a
gaba,sai gata ita da Ya Suleiman, sai dai shi ya
ju ya waje lokacin da ya gane Adama ta tsaya.
Ido ya rintse dan ganin lokacin da Ya Suleiman
ya rad'a ma Furen wani abu tana d'an tushe baki
da dariya. Tsayawa su Aishan sukai,har ta
karaso bai daga kanshi ba.
Tana daga kanta tai ar'ba dashi ido rufe,da sauri
ta d'auke kanta jin wani abu na taso mata a
zuciya wanda tuni ta rufe bab'in shi.
Sowar daya kara ji ne yasa ya bud'e ido,sai ga
Adama sun shigo da Ya Suleiman, da sauri ya
k'alli wajen su Aisha yaga Furen na tsaye tana
d'an murmushi tare da d'an had'a hannu tana
musu tafi a hankali.
Wata ajiyar zuciya ya saki tare da sakar
murmushin farin ciki.
"Dama Adama ce matar Eng.Suleiman? Kai
amma ansha dashi k'warai. Tashi yai Shima yana
d'an tafa musu da murmushi a fuska,kan a
hankali ya ju ya ga Fure, wacce itama da sa'a ta
k'allo shi,murmushi ta sakar mishi wanda kamar
dak'yar ya fito,kan ta d'auke kai a hankali.
Sosai ya famo mata wani ciwo,ga wani uban
k'yau da ya mata cikin manyan kaya yau d'aya,
dak'yar ta saita kanta.
Chan inda aka warewa abokan Ango da na Amare
ta nufa kai d'uke, kujerar da ke k'allon shi kawai
ta rage" empty " shikam har yanzun k'allonta
yake har ta zauna.
Ana gabatar da abubuwa shikam Fure kawai ya
zubawa na mujiya,sosai tai mishi k'yaun ban
mamaki, ga wata nutsuwa da yaga tai bala'in
mishi, kamar ba Fureran da ya sani ba. Kowa ya
tashi,na taka rawa suna yi,na yawo nayi, sai ya
rage daga Fure sai Uncle Ahmad.
Kai duk'e ta gaida shi da sanyin murya,jin bai
amsa ba yasa ta dago,murmushi yake yayin da
idon shi ke k'anta. Sai ta samu kanta da kunyar
shi.
Da k'yar ta samu ta zame da wayyon Adama na
kiranta.
Binta yai da k'allo, yau d'aya Fure ta kara
mamaye zuciyarshi, bazai kuma kara sakacin ta
ku6uce mishi ba. Wa yaga "real Love'.
Daga ita har shi har aka tashi fara'a suke, ita
kam batasan tata ta meye ba.
Maimakon yadda suka zo su koma tare ita da
Amare,kawai sai mazajen su suka d'auke su,Ya
Suleiman yace ya had'a mishi da y'ar K'anwar
shi da wata cousin nasu.
Ba dan taso ba suka shiga motar,wata "civic"
baka mai k'yau.
Baya Sadiya tai saurin shiga,wai ita ta shiga
gaban. Haka tai sakare,kan ta bud'e ta shiga,ya
ja su.
A hankali yake tuki cikin nishad'i,ya kan d'an
k'allota kad'an kan yai murmushi, itama takan
d'an satar k'allon shi ta gefen ido, fuskarta
sake,sai d'ai ba walwala,kowa y kasa ce wa
kowa uffan.
"A.C ya kara,kan ya hankali ya kai hannu ya
k'unna wakar da in d'ai zai ji ta toh Fure ke fad'o
mishi, sai d'ai yau gata gare shi, a hankali ya d'au
"remote" ya d'anna "play" sai ga nan wakar
"Nothing gonna change my love you ta shigo.
Tsam ta nutsu, tare da sauraran b'aitin cikin
wakar,sai ta samu kanta da lumshe ido kamar
mai bacci,tare da jingina kai a kujerar motar.
k'allo ta yai,kan shima ya jingina a kujerar yana
tukin shi cikin nishad'i,tamkar ance an bashi
Fure.
By
Feenat Ja'afar.
9/29/16, 2:18 AM - Queen Safiyyert馃憫: "JUYA" 漏 Feenat Ja'afar. 11_Ido rufe kamar mai
bacci taji sun tsaya,maganar sadiya ta tsinkaya
tana mishi godiya,kan ta fita,k'allo shi tai,kan
cikin sanyin murya tace"mun gode Uncle, ba ta
jira mey zai ce ba ta fara ko'k'arin fita,sai dai
gam, kofar a kule,tsam tai,kan a hankali ta juyo
ta k'alleshi da halamar tambaya. Shima idon ya
zuba ma ta,sai ita ta k'au da nata,kusan minti
uku ya ki magana, ita kuma tsabar haushin shi
ma take ji,wanda ita kanta bazata ce ga dalili ba.
Chan yai ajiyar zuciya, kan cikin nutsuwa
yace"Furera... Kanta na gefe ta amsa,sai kuma
ya kasa ce mata komai,mota ce ta hasko su,su
Aisha ne, gaba d'aya suka bisu da k'allo ganin
yadda suke a nishad'i, kawai sai ya d'anna
"unlock" kan yace"ki tsimaye ni gobe..dan
K'allonshi tai kan ta k'ada kai tai waje,da k'allo
ya bi ta, kan shima ya fito. Gun su Aisha tai,duk
jikinta yai lak'was,ganin ba Adama tasan sun
kaita gida. T'sakiyar su Ya Suleiman ta shiga da
Aisha, yayansu mai saukin kai ne,ba ruwan shi
da hantarar su ko k'yara, shi yasa k'warai ya
zama abokinsu. Murmushi kawai Ilyas yake
musu,ganin yadda Fure ke shag'wabe fuskarta.
Uncle Ahmad ya karaso yaga Ya Suleiman ya
kama hannun Fure,sai ya t'sinkayi maganar shi
cikin lallami,"wai Aisha mey ya samu Furii ne tun
jiya bata da walwala? Murmushi tai,kan ta k'alli
Uncle Ahmad wanda idonshi ke kan Ya Suleiman
a na Fure. "Na tambaye ta tace ba komai. Ilyas
yai murmushi," hala bata son ku tafi ku batta ne?
Gida su Aishan suka shiga,kan su kuma suka hau
fira a kofar gidan. Kasa d'aurewa Ahmad yai,"wai
ni Engnr. Meye had'in ku da Furera pls? Na kasa
gane wa fa.. Dariya sosai Ya Suleiman shida
Ilyass suka,kawai sai ya sa musu ido,shi d'ai
amsa yake nema. "Amma tambayar ta ban
mamaki "pharmacy", cos jiya ka ce min" you
know'' I thought ko a makarantar su kasan ta ai.
Kai ya k'ada, "Eh,amma bansan nan ne gidan sun
ba. Ilyass ne ya dafa shi da d'an dariyar shi,
"kana da abun dariya Aboki,hala neman iri ka ke
ka fara bamu girma tun yanzun? Murmushi yai,
tare da k'ada mishi kai, " toh abinda yai Aisha
shi yai Fure yai kuma Engineer.." Same Ma,
same Baba.. "Ko in ma ta d'an g'wari-g'wari? Kai
ya k'ada murna fal cikin shi,kan ya k'allo
Suleiman, wanda har yanzu yake dariya kasa-
kasa. " a gaskiya na wahala a neman K'anwar ka
Engr. Ashe tana a kusa ma ban sani ba?
Murmushi yai, kan ya k'ada kai. "Pretty".....
"Furera''.... Kai, yanzu na gane, ashe ita ce
wacce ake neman nan ido bud'e. Cewar Ilyass
cikin shakiyanci. "Shegen kaya, kai yanzu ko
kamar ai zaka d'akko hanya. Kai ya k'ada

Please Login or Register in order to submit comment