You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

haka tasake d'aukar k'afa taje gidanshi yace tayi hak'uri ana ta k'ok'ari anaso ahad'a dukiyar Alhaji Muhammad sannan araba masu gado.
Duk atunaninta dagaske ne dan haka takoma gida ammah har sati biyu bataji wata maganaba dan haka tabarshi tasake zuwa wajen wani abokin Abbu me suna Alhaji Surajo shima dai ba bayani, saida taje wajen aminnan Abbu hud'u ammah da sun shiga maganar ana kwana biyu zata watse.

Nan hankalin Ammi yatashi sosai taje tasamu lauya d'in Abbu watau Barr Muhsin tafad'a mashi.
Abinda yabata mamaki shima baiyi wani yunk'urin taimakonta ba dan ganin gadonta ya fito, dan haka tafitar da kayan d'akinta tasiyar taje tashigar da k'ara kotu, duk wannan abun fa Ammi tana yine dan kawai nawa hak'k'in ba ma nataba saidai abinda ita bata saniba shine wannan k'arar da tashigar zata zame mata matsala a rayuwa.




_*Remain 1 page mugama free Page's😍*_







_Sis Nerja'art✍🏻_
[3/14, 21:42] Sis Nerja'art👰🏻: *......FANSAN RAI.......*



_*STORY AND WRITTEN BY SIS NERJA'ART✍🏻*_



*INTELLIGENT WRITERS ASSO....®*
[On Ward Together]


*DEDICATED TO ZM CHUBA'DO*

_Wannan littafin na kud'i ne ga duk me buk'ata zai biya d'ari biyu N200 Kacal zai turo MTN card ta wannan number d'in 09035938246 ko katuro 200 ta account number d'innan 5330055604, *NANA HALLIRU* FIDELITY BANK, idan katura ka aiko da screen shot na transaction ta wannan number 09035938246_

_Ga mutanen Niger zasu tura 300f ta wannan number d'in +22794775574_
_Gareku masoyan gaskiya_


_*GARA B'ASA! GARA B'ASA!! GARA B'ASA!!!* wannan gara'basa anyi tane kad'ai ga duk wanda keson karanta littafin *FANSAR RAI* da *RESHE YA JUYE DA MUJIYA* na shaharariyar marubuciyar nan watau *AMINA ABBA UMAR* ga duk mai bukatar karanta duka novel's d'in biyu zai biya *N300* kadai domin samun damar karantasu cikin aminci, gareku masoyan gaskiya muna jiran ku nuna mana k'aunarku ta hanyar biyan *N300* kad'ai, idan duka biyun kakeso zaka turo kud'i ta wannan account number d'in 3092292135 FIRST BANK, ko kuma katin waya Mtn na d'aya daga cikin Numbers d'in nan 09035938246 ko kuma 07030792790, ko 07036073670, sai ka aiko da shedar biya ta d'aya daga cikin numbers d'in, sai munji daga gareku masoyanmu_


_Last Free Page_

*PAGE TWELVE*

Wasu siraran hawaye ne suka gangaro ma Jawahir masu d'umi saurin runtse idanunta tayi tacigaba da cewa Ammi tana shigar da k'ara a Shara'a Court suka aiko ma Abba da takardar shammaci na ana gaiyatarshi a court akan k'arar da Ammi tashigar nashi dan wani tsohon alkali Makobcinmu yasama mata lauyan da zai tsaya mata, Abbu na jin haka hankalinshi yatashi yaje yasamu Barr Muhsin yafad'a mashi nan sukazo suna lallab'ata akan taje tajanye k'arar ammah tak'i dan haka Barr Muhsin yace zai tsaya yakare wanda ake k'ara, ana saura sati d'aya azauna kotu Abba Mu'azu yazo yasamu Ammi a d'akinta yace shi ya yarda zai bada duk wata dukiyar Abbu araba idan ta amince takawo duk wasu takardu nashi da suke hannunta shima zaisa atattaro sauran, Ammi tace bata yadda ba bazata bayarba abin ya 'bata ma Abba Mu'azu rai sosai da yaje yana fad'a ma matarshi ne Yaya Aliyu yaji nan ranshi ya'baci yace yanzu Abba wacchan matar har ta isa takaika k'ara akan kud'in dan uwanka? Wallahi bata isaba sai na nuna mata batada wayau, wacece ita,,,cike da jin dad'in kalamanshi Abba yace kabarta kawai Aliyu nasan ta inda zan biyo mata dan bata isa tatozarta ni a Idanun jama'a ba.
Wallahi Abba batada amfani acikin gidan nan kawai akorata takoma garinsu tunda wanda ya aurota ya mutu ya bar duniyar.
Murmushin mugunta Abba yayi yace Son kai ma kake fad'a ana ji, katayani tunanin hanyar da zamubi mukoreta tatafi tabar mana garin.
Uhm shikenan Abba zan samo mana mafita.

Bayan kwana ukku da yin abun Ammi tana kwance tana bacci da rana nikuma ina gefenta inayin homework d'ina dan a lokacin na cigaba da zuwa school ina SS 2 kamar an mintsireta sai ganin Ammi nayi ta tashi a firgice da mamaki nake kallonta nace Ammi Lafiya?
Bin d'akin tashiga yi da kallo sai chan tace Jawahir kebbi nakeson zuwa hankalina ya yi gida.
Zaro ido jawahir tayi tace Ammi kebbi kuma?
Murmushi tayi tace Eh jawahir inason zuwa dan ina ji a raina bazan kai wani lokaci ba,,hawaye ne suka gangaro mata tace ganinsu shine kwanciyar hankalina zanje kawai.

Fashewa jawahir tayi da kuka tace nima zan biki Ammi.

A'a Jawahir bazanje dakeba kizauna kawai insha Allahu zuwa jibi zan dawo,,,Ammi na fad'in haka tafara had'a kayanta cikin wata yar k'aramar jakka tazuba kaya kala ukku da takardun gidanta da Abbu yabata take ta faman boyesu tana gama had'awa tasaka hijab tajuyo takalli jawahir da ke tafaman kuka tace kiyi hak'uri jawahir idan da rabo zan dawo gareki.
Rik'ota jawahir tayi tace dan Allah Ammina kar kitafi kibarni.
Cikin sanyin jiki Ammi tak'wace jikinta tace jawahir kikula da kanki,,,tana fad'in haka tajuya cikin sauri tafita daidai zata fita Aliyu yashigo gidan tsayawa yayi yana kallonta a wulak'ance saida taganshi tatuna batayi sallama da su Ummah ba dan gabad'aya jin jikinta take wani iri,,tsayawa tayi tace Aliyu kafad'a ma ummanku na tafi kebbi.
Yatsina fuska yayi yace toh menene namu a ciki kiyi ta tafiya mana.
Ammi batace komai ba tajuya tafita dan indasabo ta saba da rashin kunyar Aliyu, malam Idi driver tagani wajen megadi suna hira nan ta isa wajensu suka gaisa sannan tace mashi kebbi takeso yakaita.
Da mamaki suke kallonta sukace Hajiya Lafiya zakije kebbi a wannan lokacin?
Murmushi tayi tace buk'atar hakan ne yataso min.
Malam idi yace toh Hajiya muje,,,megadi ne yataso yabud'e mata mota tare da yi mata Allah yakiyaye tana shiga motar idi na shirin tadawa sai ga Alhaji Mu'azu ya shigo gidan kallon malam idi yayi yace ina zakaje da ita?
Jikin malam idi yana b'ari yace daman kebbi tace inkaita.
Abba Mu'azu kallon Ammi yayi sannan yawuce yashige gida, Ammi runtse idanunta tayi wasu hawaye masu zafi suka gangaro mata ahaka suka kama hanya.

Tunda suka Kama hanya Ammi sharar hawaye kawai take ahaka sukayi tafiyar kusan awa biyu suna shiga wani d'an kauye dake mararrabar katsina nan suka fara ganin wasu motoci biyu suna bin bayansu ammah basu kawo komai a ransuba sai malam idi da yaga sunk'i wucewa sai yarage speed dan suzo suwuce su ammah da mamakinshi sai yaga su ma sunrage yace Hajiya wad'an chan motocin sai bin bayanmu sukeyi, Ammi ta cikin mirror takallesu tace k'ila su ma hanyarmu sukayi ko gari d'aya zamuje.
Malam idi yace hakane dan haka yacigaba da tafiyarshi normal ta wata boyayyar hanya suka ratsa sukabi dan suyi saurin isa kebbi da mamaki sai ganin motocin sukayi sun biyo bayansu lokaci guda d'aya daga cikin motar tak'ara gudu tazo ta wucesu tana wucewa tasha gabansu cikin sauri malam idi yaja wani irin burki dan kar yafad'a ma motar nan motar bayansu itama tatsaya, motar da take gabansu ce aka bud'e wasu karti biyar suka fito k'osassu rikicewa Malam idi yayi yafara salati tare da k'ok'arin so yatada motar ammah kafin yayi wani yunk'uri har mutanen sun iso ta window suka Fisge key d'in motar tare da bud'e k'ofar suka fiddoshi yafad'o k'asa, Ammi fasa k'ara tayi tare da furta innalillahi wa'inna ilaihiraji'un nashiga ukku.
Zagayawa sukayi suka bud'e mata sukace tafito, jikinta yana rawa tafito tace dan Allah kuyi hak'uri kufad'a min abinda kukeso.
Dariya suka kwashe da ita gabad'ayansu sun dad'e suna yi kafin daga bisani sukayi shuru d'aya daga cikinsu ne yace bamu buk'atar komai a wajenki face ranki kawai da mukeso.
Ammi na jin haka ta ida rikicewa malam idi yace dan Allah kuyi hak'uri kar kukashemu.
Tsawa suka kwatsa mashi sukace yayi masu shuru nan wani k'ato bak'i k'irin yayo wajen Ammi da shar'be'biyar wuk'a baya tafara ja a tsorace tana cewa dan Allah kar kakasheni mi nayi maku da kukeson rabani da raina? Waige waige tadinga yi tahango wata yar hanya aiko nan tabaza aguje nan suka bita dukansu, gudu take iya k'arfinta duk k'ayoyin da suke cikin dajin ta taka ammah bata ma san tana takawaba saboda bala'in da take gani, ka san ba'a had'a gudun mace da namiji ganin sun kusa taddota yasa tak'ara gudu tana ambaton sunan Allah bata ankaraba sai ji tayi wani ya tad'e mata k'afa ta fad'i daidai wajen wani suri, ja tadinga yi da baya tana kuka tana cewa dan Allah kuyi min hak'uri, wani ne yazo yazare mata hijab tare da damk'ar gashin kanta yajuya yakalli sauran yace gaskiya tana da kyau da son samune ace yanzu na d'an huta da ita kafin akasheta.
Nan sukasa dariya sukace ai kana hutawa da ita muma sai mun huta da ita.
Ammi Khausar tana jin haka tabud'e baki dakyar tace babu wanda ya isa yata'ba min jiki saidai kukashe ni.
Daidai lokacin Malam idi ya iso wajen cikin sauri yaduk'a gaban wanda yake rik'e da Ammi yana rok'onshi kar yakasheta.
Shuru yayi yana kallonshi nan wani yatafo daga bayanshi batare da sanin malam idi ba saidai yaji anda'ba mashi wuk'a dakyar ya iya yin salati nan yafad'i k'asa yana shure shure jini yana ta malala har yamace.
Wata irin k'ara Ammi Khausar tasaki cike da tashin hankali nan wanda yake rik'e da ita yabuga mata kanta ajikin icce,dinga buga mata kan yayi a iccen da dukkan k'arfinshi jini yadinga fita ta kan, kumbura yayi sosai tun tana motsi har tamace saida yatabbatar da mutuwarta sannan yasaketa tafad'i k'asa ya amshi wuk'a yaluma mata sannan suka wuce cikin sauri suka bar wajen.
'Daid'aikun mutanen da suke wucewane a saman abin hawa suka ga motar a gefen titin a bud'e suka kira police sukazo sukayi bincike har aka gano gawarwakin aka bincika motar aka d'auko jakkar Ammi Khausar aciki aka samu duk wani address d'inta.
Aka d'auki gawarwakinsu aka kai gida.

Jawahir wani irin kuka tadinga yi mai shiga rai tana jin kamar yanzu ne abun yafaru kasa cigaba da labarin tayi saboda kukan da takeyi Barr Faruk jikinshi sanyi yayi sosai d'ago kai yayi yakalleta yace jawahir kiyi hak'uri Allah ubangiji yajik'an su Abbu da Ammi.
Goge hawayenta tayi tace Ameen sannan tacigaba da cewa....

A ranar naga tashin hankali sosai a lokacin da nacikaro da gawar Ammina a tsakar gidanmu an kawo kanta ya yi suntum kamar zai fashe bansan lokacin da nasulale nasuma ba saidai gani na nayi a gadon asibiti wata mata tana jiyyata ashe har nayi sati bansan lokacin da aka kai Ammi gidanta nagaskiya ba saida na'kara kwana d'aya nan namatsa saida aka sallameni nakoma gida lokacin har anyi sadakar sati d'aya, kuka nadinga yi sosai saida wani malamin mu da yazo min gaisuwa yayi min wa'azi sannan nadaina, damuwa nad'auka nasa ma raina duk na fita hayyacina saida nayi wata d'aya nadawo daidai, na d'auka mutuwar Ammi zaisa su Abba Mu'azu sucanza ashe abun ba haka bane Ammi tana wata d'aya da rasuwa nan aka tasoni a gaba duk wani aikin gida yadawo kaina, nakoma kamar wata baiwa tun ba'aje ko'ina ba na ida fita hayyacina abinci sai anso ake bani inci, dakyar nasamu nagama SS2 rashin kud'in da zasusa incigaba da karatuna yasa karatun yatsaya dan Abba Mu'azu cewa yayi bazai biya min ba.......

Tana kawowa nan Barr Faruk yaji ta yi shuru d'ago kai yayi yakalleta da mamakinshi sai yaga tana bacci.
Saurin mik'ewa yayi ya isa bakin gadon yaga dagaske ko baccinta takeyi cikin ranshi yace ikon Allah tunda nake ban ta'ba ganin mutum irin wannan ba, d'aukar laptop d'inshi da wayoyinshi yayi yakoma parlor yazauna yana cigaba da aikinshi.



Tayi awa d'aya tana bacci ahankali tafara juya kanta tana girgizawa tanaso tabud'e idanunta ammah ta kasa wata irin k'ara tasaki tare da bud'e idanunta a firgice ta tashi zaune lokacin da taga jini duk a hannuwanta bin hannuwan tayi da kallo tare da girgiza kai tace a'a meyasa hakan tafaru? Hoton da yake kusa da ita tayi saurin d'aukowa taduba hoton Alhaji Sa'idu tagani tabbas shine wanda tayi mafarki dashi d'aukar hoton tayi tayaga gutsin gutsin tasaka cikin dosbin dakyar take tafiya tana jan k'afa har tashiga toilet wanke hannuwanta tayi cikin sauri tacire jallabiyar tasaka kayanta da tazo da su dasauri tafito daga bedroom d'in, barr Faruk d'agowa yayi yakalleta yace lafiya jawahir me yake faruwa? Muryarta tana rawa tace Barrister tashi muje kamaidani zama na a nan akwai had'ari, daman ba na fad'a makaba cigaba da rayuwata a doron k'asa hadarine, muje kamaidani kafin tazo inba hakaba kaima rayuwarka zata iya salwanta.
Mik'ewa yayi cikin rashin fahimtar maganarta yace jawahir wacece zatazo?
Lokaci guda jawahir tarikid'e Idanuwan nan sukayi jajir cikin d'aga murya tace na ce muje kamaida ni!
Barr Faruk bai musaba yad'auki system da wayoyinshi yawuce gaba jawahir tana dafe da kanta ahaka take binshi har suka fito yarufe d'akin yaje yabasu key d'insu sannan suka wuce wajen motarshi.
Suna shiga tura kanta tayi tsakanin cinyiyonta wani irin sautin kuka takeyi, gabad'aya kan Barr Faruk ya d'aure yarasa dalilin damuwarta a lokaci guda ahaka har suka isa gidan yarin suna isa tana shirin bud'e mota tafita yakira sunanta juyowa tayi takalleshi yace sai yaushe zaki ida min labarin?
Girgiza kai tayi tace bazan iyaba Barrister akwai had'ari sosai acikin rayuwata, Barr Faruk yace duk da haka jawahir ya kamata kidaure.
Bud'e motar tayi tafita shima nan yabud'e yafito nan yawuce gaba wasu 'yan sanda sukazo suka rik'eta wata irin tafiya takeyi tana rangaji har office d'in shugabansu.
Da mamaki yake kallonsu yace Barrister lafiya?
Murmushi Barr Faruk yayi yace lafiya lau na maidota kamar yadda nayi Alk'awali.
Murmushi yayi yace aiko ka kyauta dan ina nan hankalina a tashe na kasa zaune da tsaye saboda gangancin barinka da nayi kuka fita da ita dan na karya dokat aikina, ammah kamar ta yi kuka ko?
Kallonta Barr Faruk yayi yaga yadda idanunta sukayi jajir.
Alhaji Mahadi sawa yayi 'yan sanda sumaidata d'akinta dakyar take tafiya tana yin baya kamar zata fad'i.

Bayan tafiyarsu Barr Faruk yace kasan duk wanda yake cikin gidan nan yatuna rayuwarshi tabaya dole yaji wani iri.
Hakane ammah in kayi rayuwa mekyau ba.
Murmushi yayi yana shirin yin magana wayarshi tafara ringing d'aukowa yayi yai picking tare da yin sallama yace Daddy.
Daga chan 'bangaren dady yace Faruk kazo gida yanzu zakaje Daura.
Daura kuma Daddy? A wannan lokacin?
Daddy tsinke wayarshi yayi Barr Faruk yayi murmushi yace Alhaji Mahadi bari intashi intafi ana nemana a gida ammah kafin intafi zan d'anyi magana da jawahir.
Alhaji Mahadi shuru yayi sai chan yace shikenan Barrister babu damuwa bari insa arakaka.
'Daya daga cikin ma'aikatan gidan yakira nan Barr Faruk yamike suka tafi suna zuwa yasamu jawahir kwance a k'asa idanuwanta a rufe daga gefenta yatsugunna yace jawahir.
Zumbur tatashi zaune hawaye na fita daga idanunta bakinta yana rawa tace Faruk kabar wajen nan kawuce katafi kar taganka.
Da mamaki yace wai jawahir wacece zata ganni? Kukan me kike haka? Wai me yake faruwa da rayuwarki?
Cikin kuka tace Faruk kaje kawai,
Faruk yace babu inda zanje jawahir sai kin fad'a min abinda yake faruwa.
Juyawa tayi cikin sauri tafara waige waige sai kuma chan tamik'e tsaye dakyar tana kyangasa k'afa tanufi wajen da dutsin nan yake ajiye tana zuwa tad'agashi dakyar tajawo d'an k'aramin littafinta jinginewa tayi jikin bango cikin sauri Barr Faruk yataso yazo inda take a tsaye yace lafiya jawahir?
Kallonshi tayi da idanuwanta da suka fara lunshewa cikin jigata tace Barrister ga wannan duk wani bayani da kake nema zaka samu a ciki, katafi.
Amsa yayi yarik'e, yace jawahir yakamata akaiki asibiti ko bakida lafiya.
Girgiza kai tayi tace kaidai katafi.
Barr Faruk har ya bud'e baki zaiyi magana tace dan Allah kar kace komai katafi kawai.
Juyawa yayi cikin sanyin jiki yafita.
Yana fita jawahir tafad'i k'asa a sume.

Tausayinta duk yacika Barr Faruk haka yawuce yatafi cikin sauri dan amsa kiran Dadynshi.

Yana isa a parlour yasamu Daddy yana jiranshi ko zama baiyiba Daddy yace Faruk d'azu Malam ya kirani ya ce yana ta Kiran wayarka bai samuba lafiya dai ko?
Zama yayi sannan yace Daddy ina tunanin network ne.
Toh shikenan yanzu kaje kashirya kaje Daura ya ce yau yau d'innan yana son ganinka.
Yau kuma Daddy me yake faruwa?
Nima ban saniba Faruk kaidai kaje kashirya inkaje sai kaji dan tun d'azu yake kirana a waya yana tambayata ka tafo.
Mik'ewa Barr Faruk yayi yace shikenan Daddy bari inje inyi wanka inyi sallar la'asar sai intafi.
Daddy yace toh shikenan haka yakamata.

Har yagama shiri yana tunanin dalilin kiran gaugawa da kakan nashi yakeyi mashi koda zai tafi Daddy tsaraba yabashi sosai yace yakaima Mahaifin nashi, bayan ya yi sallama da iyayenshi yakama hanyar Daura gudu yake sosai.



Bayan tafiyar Barr Faruk da minti talatin aka kira Alhaji Mahadi shugaban prison a waya yana yin picking daga chan 'bangaren akace masu kula da bincike ne.
Alhaji Mahadi yace toh Lafiya dai ko?
"Eh toh kana da labarin mutuwar babban d'an kasuwar nan Alhaji Saidu Nepa?
Da mamaki Alhaji Mahadi yace banda labari yaushe yarasu?
Daga chan 6angaren akace baifi awa d'aya da rasuwa ba shine muke bincike akan mutuwarshi mun tsinci hoto irin Wanda aka kashe su Alhaji Saminu shine mukeso muji shin wannan yarinyar jawahir tana prison d'innan?
Eh Eh tana nan a rufe,,,,cewar Alhaji Mahadi.
Daga chan 'bangaren akace babu inda taje yau? Ba aje da ita ko kotu ko asibiti ba?
Shuru yayi sai chan yace am a'a d'azu Barr Faruk ya fita da ita ya yi bincike akan aikinshi.
Wanene kuma Barr Faruk?
Lauyanta da yake kareta ammah sun dawo tun d'azu.
Shikenan zamu nemeshi.



Cikin 50 minutes Barr Faruk ya isa daura saboda gudun da yake da motar yana isa a k'ofar gidan kakannin nashi yaga malam zaune yana ba wasu darasi dan haka yatsugunna yagaishesu bayan sun gaisa yashiga cikin gida yasamu yar tsohuwar tashi suka gaisa nan takawo mashi hura damamma yana sha suna hira yana janta ahaka har yagama yace bari yaje yaga ko malam ya gama dan lokacin biyar da rabi tayi tace Eh gaskiya zuwa yanzu ya gama.
Yana fita yasameshi zaune yana jan carbi daga gefen d'an buzunshi yazauna suka sake gaisawa yatambayeshi mutanen gida yace kowa yana lafiya,
Malam yace ai mahaifinka ya kirani d'azu ya ce wai iyayen yarinyar da zaka aura sunce ad'aga sa ranar sai zuwa jibi ayi baikon.
Faruk yana shirin yin magana nan wayarshi tafara ringing fiddowa yayi yai picking tare da yin sallama.
Daga chan 6angaren akace Barr Faruk muna buk'atar ganinka a yanzu dan samun cikakkun bayanai daga wajenka saboda munsan kana da labari awa biyu da suka wuce ankashe babban dan kasuwa Alhaji Saidu nepa, da mamaki yake saurarenshi yace ankashe shi kuma?
Eh saisa mukeso muji daga gareka dan antabbatar mana ka fita da jawahir daga prison yau.
Cikin sanyin jiki yace ammah koda nafita da ita ai babu inda taje hotel kawai muka safka.
Barrister koma menene inkazo sai muyi magana dan yanzu haka muna a cikin bincike.
Barr Faruk yace shikenan sai na shigo, yana gama wayar kallon malam yayi da yatsareshi da idanu yace wacece jawahir kuma?
Barr Faruk yace wata baiwar Allah ce da nake tsaya mawa a shara'arta shine wai suke zarginta da kisa.
Jinjina kai Malam yayi yace kusan abinda yasa nace kazo kenan akan yawan mugun mafarkin da nake akanka.
Mafarkina kuma? Yafad'a cike da mamaki.
Eh mafarkinka kuma duk akan wannan aikin naka ne, Faruk ya kamata ka ajiyeshi dan ina tsoron wani abu yafaru da rayuwarka.
Gabanshi wani irin mummunan fad'uwa yayi yace ajiye aiki kuma malam? Kar kayi duba da abinda kagani acikin mafarki dan duk wannan sharrin mafarki ne.
Eh Faruk zai iya zama haka ammah ni ina tsoron abinda zai faru da rayuwarka ko ga wani naka......



_Shin wane irin mafarkine Malam yayi da har yakeso Barr Faruk ya ajiye aikinshi?_

_Shin Barr Faruk yana da yadda zaiyi yakare jawahir akan zargin kisa da akeyi mata?_
_Anya kuwa ba jawahir bace take kisan nan ba? inko ba ita bace toh wanene?_
_Wane dalili ne yasa aka d'aga baikon Barr Faruk kodai akwai wata k'ullaliya a k'asa da akeson yi?_
_Shin minene cikin wannan littafin (diary) da jawahir taba Barr Faruk?_


_Tofa laifin dad'i k'arewa, wad'annan amsoshin naku duk suna acikin cigaban *FANSAR RAI* kar kumance har yanzu bamuyi komai ba acikin labarin d'and'ana labarin kawai mukayi_
_Ga duk me buk'atar cigaba da karantawa cikin aminci zai biya d'ari biyu (200) dan kasancewa da SIS NERJA'ART_
_Akowane lokaci muna maraba da masoya nagaskiya Sis Nerja'art takuce_







_Sis Nerja'art✍🏻_


[7/24, 11:09 PM] Sis Nerja'art 2: *......FANSAR RAI......*



*INTELLIGENT WRITER'S ASSO....®*
[On Award Together]


_Follow me on Wattpad: *Sis-Nerja*_


_Wannan Littafin na kud'i ne domin karantawa cikin aminci da yarda ga duk me buk'ata zai turo katin Mtn na d'ari biyu N200 kacal ta wannan number d'in 09035938246, ko ta account number 5330055604, Idan katura ka aiko da screen shot na transaction a wannan number d'in 09035938246_


_Akwai gara'basar *RESHE YA JUYE DA MUJIYA* na shahararriyar marubuciyar nan *AMEENA ABBA UMAR* tare da novel d'in *FANSAR RAI* akan farashin N300 kacal, ko da kud'in ka sai da rabonka_



PART TWO

_~GORON SALLAH~_

*PAGE 1*


Kwance yake saman makeken gadonshi yad'age kanshi sama yana kallon Ceiling tare da lumshe idanunshi kamar me bacci ammah azahiri tunani yake rayuwar jawahir kawai yake tunani akan irin gwagwarmayar da tasha, tambayar kanshi yafara yi daman ashe tana da aure? Toh ina mijin nata? Meyasa bai ta'ba ganinshi ya je wajenta ba??tambayoyin da suka dinga mashi yawo kenan a k'walwa saidai me a gefe d'aya Allah Allah yake yi gari ya ida wayewa yayi wanka yatafi gidan kaso na mata dan yagana da ita dan ya fi so ya ida samun full details kafin yafara aikinshi,,,, yana cikin wannan tunani bacci 'barawo yasace shi.


Wajen k'arfe bakwai kiran da yashigo wayarshi ne yatashe shi dakyar yabud'e idanunshi da sukayi mashi nauyi saboda rashin samun isashen bacci, d'auko wayar yayi yaduba yana ganin me kiranshi sai ma yamaida ta silent sannan yamik'e yashiga wanka.

Bayan ya fito ya shirya cikin shirinshi na tafiya aiki jikkar laptop d'inshi da wayoyinshi yad'auko yafito parlor daidai da Momcy ta shigo parlorn d'auke da plask tsayawa tayi tana kallonshi.
Murmishi Faruk yasakar mata tare da gaisheta.
Amsawa tayi sannan tace Son ka dai san babu inda zakaje sai ka yi breakfast ko?
'Bata fuska yayi yace Momcy bana jin yunwa.
Batace mashi komai ba tawuce dining area.
Ajiye kayan da suke hannunshi yayi yabi bayanta yana zuwa yaja kujera yazauna, fara serving d'inshi tayi sannan tace d'azu Nasiba ta kirani a waya ta ce tana ta kiran wayarka baka d'auka ba.
Yi yayi kamar baiji ba yafara breakfast d'inshi.
Kallonshi Momcy tayi tace Faruk magana fa nake maka ka min shuru.
'Dagowa yayi yakalleta yasakar mata murmushi sannan yace momcy time d'in bacci nake kuma ko da natashi ban bi ta kan wayarba saboda naga zanyi late ban tafi aiki ba.
Momcy kallonshi kawai tayi tawuce tatafi cikin ranta tana mamakin halin d'an nata.

Sama sama yayi breakfast d'in yamik'e yad'auki kayanshi yaficce yabar gidan.

Yana cikin mota yana tuk'inshi a nutse nan wayarshi tafara ringing kallon wayar yayi ganin sunan da yabayyana a jikin screen d'in wayar yasa yai saurin yin picking tare da yin sallama,,, yanayin yadda yake maganar kawai zaka gani kagane cewa akan wajen aiki ne suke tattaunawa sun dad'e suna wayar kafin daga bisani suyi sallama.

Suna gama wayar d'an guntun tsaki yaja tare da canza hanya yanufi wajen aikinsu.

Yana isa yai parking a daidai inda yasaba yin parking yad'auko bakin space d'inshi yadad'e fuskarshi sannan yafito daga cikin motar yazagaya yabud'e mazaunin me zaman banza yad'auko jakkar laptop d'inshi.

Tafiya yake cikin takunshi me burgewa duk inda yagifta sai mutane sun mashi barka da safiya saidai kawai yad'aga masu hannu, wad'anda suka yi mashi farin sani ne kawai zasuce daman haka yake dan Barr Faruk ba mutum bane me yawan son hayani.


Yana zaune a office d'inshi akayi mashi knocking izini yabada ashigo nan aka turo k'ofa.
'Daga kai yayi yakalli me shigowa sai kuma yamaida kallonshi ga system d'in shi.
Sacratery takowa yayi ya iso wajen Barr Faruk daga gaban table d'inshi yatsaya yace Barrister barka da aiki.
Batare da ya d'agoba yace yauwa barka.
File d'in da yake hannunshi yamik'a mashi yace gashi oga yace akawo maka.
Ohk ajiye nan.
Ajiyewa yayi saman table d'in yace atashi lafiya sannan yajuya yafita.
Barr Faruk d'auko file d'in yayi yabud'e yafara dubawa chan sai yamik'e tare da d'aukar file d'in da key d'in motarshi yafita.
Saida yafara biyawa a office d'in ogansu suka tattauna sannan yatafi.


Yana barin nan direct gidan yari yawuce yana isa kamar yadda yasaba office d'in abokin nashi yafara safka bayan sun gaisa ne yanuna yanaso yaje yagana da jawahir.
Alhaji Nasibi yanuna ba matsala nan yakira wani ma'aikacin gidan kamar yadda

Please Login or Register in order to submit comment