You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

tace shikenan Faruk ina nan ina jiranka dan Allah kar kabarni.
Murmushi yayi yace kar kidamu da sannu zan baki mamaki dan banaso aja lokacin bikkin mu, nidai fatana kidaure kicire duk wata damuwa a ranki kikwantar da hankalinki sannan kidaina kirana a waya kar parents d'inki sugane har yanzu muna tare ransu ya'bace kibari mubi komai a sannu Nasiba.

Cikin jin dad'in kalamanshi tace toh shikenan Hearty duk yadda kakeso haka za'ayi.
Lumshe idanunshi yayi tare da sakin murmushi sannan chan k'asan mak'oshinshi yace kece rayuwata zan kasance da ke akowane lokaci acikin zuciyata, kikwanta kiyi bacci.
Ita kanta lumshe idanunta tayi tana fitar da murmushi me sauti "Nagode sosai Hearty hak'ik'a nayi farin ciki da jin kalmar nan a yau zanyi baccin da rabon da inyi irinshi tun muna tare shikenan sai dasafe.
Sallama sukayi suka kashe wayar kusan a tare suka manna wayoyinsu a bisa k'irjinsu suna murmushin farin ciki, kowa na jin soyayyar d'an uwanshi tana fizgarshi.


Chan Faruk yaji shigowar text yad'aga wayar yana dubawa sai ganin number d'in Alhaji Mansur yayi ta turo mashi.

Murmushin jin dad'i yayi cikin ranshi yace kin gama min komai My Life, nan yatura mata " Thanks my wife to be insha Allah, Good Nyt, kiyi bacci me dad'i.

A karo na biyu tasake lumshe idanunta cikin jin dad'i tace Night too My Everlasting,,, tana manne da wayar a k'irjinta a haka tayi bacci.


Achan 'bangaren Faruk tashi yayi yagama duk abinda zaiyi sannan yakoma yakwanta.


Washe gari yana zaune a parlorn d'akinshi yana kallon kwallo inda a saman d'an teburin da yake gaban kujerar da yake zaune fruit salad ne yana sha, sai wajen k'arfe sha d'aya yagama kallon yamik'e yad'auko wayarshi da yajona charge yakoma inda yake zaune kasancewar ranar bazaije wajen aiki ba, Number d'in Alhaji Mansur yalalubo yakira, har saida takusan tsinkewa sannan akayi picking, sallama yayi daga chan 'bangaren Alhaji mansur ya amsa a dak'ile tare da tambayar wanene.
Faruk bai damu da yanayin da ya amsa shi ba yace am Barr Faruk ne daman na kira ne intambayeka dan Allah in ba damuwa ina zan sameka dan akwai magana me muhimmanci da zamuyi.
Tun kan yarufe baki yaji muryar Alhaji Mansur cikin fad'a yana cewa babu wata magana me muhimmanci indai ba janyewa kayiba kabari aka kashe yarinyar chan kamar yadda takashe wasu.
Murmushi Faruk yayi dan yanayin yadda yayi maganar ta so tabashi dariya ammah yadanne sannan yace koma menene kaban dama muhad'u sai mutattauna.

Toh shikenan zan turo maka adress d'in Guest House d'ina sai kazo kasameni.
Cikin jin dad'i Barr Faruk yace toh shikenan sai na jika,,, bai jira jin abinda zai ce ba yakashe wayar tare da saving d'in recording d'in da yayi,
gudar wayarshi yad'auko yakunna muryar da yake tunani ta Alhaji Mansur ce yasake saurare tabbas ya ida gasgatarwa da tashin ce, yana nan zaune sai ga message ya shigo wayarshi yana dubawa yaga Alhaji Mansur ne, murmushi yayi yace dakyau haka nakeso nan yamik'e yashige bedroom d'inshi bai dad'eba yafito hannunshi rik'e da key d'in motarshi fuskarnan ya dad'eta da bak'in glass d'aukar wayoyinshi yayi yafita yabar gidan.



Yana isa k'ofar gate d'in gidan duk security's suka taso suka nufo wajen motarshi ganin haka yasa yagane bazasu barshi yashiga ba nan suka fara tambayarshi me yazo yi? batare da ya basu amsaba yad'auko wayarshi yakira Alhaji Mansur yana yin picking yace gani a k'ofar gidanka wad'annan k'attin da katara sun hanani shigowa.
Ba su da akace ma k'atti ba hatta shi kanshi Alhaji Mansur ya ji ciwon abun dan de kawai yana so yasan abinda yakawoshi saisa yadanne fushinshi yace basu waya muyi magana.
Mik'ama d'aya daga cikinsu wayar yayi yace oganku yana son magana da ku.
Amsa yayi yakanga a kunne nan sukaji yana cewa ohk sir angama, mik'a ma Barr Faruk wayar yayi sannan yabada umurni aka hangame mashi tank'amemen gate d'in yashigar da motarshi parking yayi yafito nan d'aya daga cikinsu yayi mashi jagora zuwa cikin gidan, Faruk ko kanshi d'aurewa yayi ganin makeken Guest House d'in Alhaji Mansur ahaka har suka isa wani tank'amemen parlor inda Alhaji Mansur d'in yake zaune ya kame sai hura hanci yake.
Sucurity d'in komawa yayi inda Barr Faruk yayi sallama yashiga, amsawar ma cikin tak'ama aka yi mashi, murmushi kawai Faruk yayi yaje yazauna saman kujerar da take opp d'in wadda Alhaji Mansur yake zaune cikin tak'ama yazauna tare da d'aura k'afa d'aya saman d'aya, koda Alhaji Mansur yakalleshi saida yaga ya yi mashi k'warjini, zare glass d'in da yake fuskarshi yayi sannan yace sannu Alhaji.
Cikin isa ya amsa da yauwa ka ce kana son ganina ko?

Murmushi yayi yace Eh saboda inaso ka amsa min wasu tarin tambayoyi da ke gareni.
Da mamaki yake kallonshi yace wane irin tambayoyine haka?
Ta'be baki yayi yace ba wasu tambaboyi bane masu wuya kawai dai akan case d'in mutuwar su Alhaji Muhammad Mai kud'i ne.

Gaban Alhaji Mansur wani irin mummunan fad'uwa yayi yai saurin gyara zaman shi tare da kallon Faruk yace ban fahimceka ba me kake nufi?
Murmushi yayi yace daman bazaka fahimceni ba saidai yanayin yadda kafirgita ya sa na gane ka d'an fahimci wani abu, ammah dai kar kadamu da wannan na san dai Alhaji Muhammad abokinka ne kai da su Alhaji Tanimu toh abin mamakin bayan mutuwarshi kuka koma kuka k'ulla abota da yayanshi Alhaji Mu'azu, saidai hakan baisa kuyi tunanin ko za'a iya zarginku da wani abu ba? Ko ma ace akwai wani abu da kuka shirya ku d'in?

Zumbur Alhaji Mansur yamik'e tsaye cikin fushi yace ban ganeba me kake nufi, wannan ai zancen banza ne ka zo ne daman dan karaina min hankali?

Murmushi yayi a karo na biyu sannan yace kaga Alhaji da ka zauna munyi magana cikin kwanciyar hankali ba sai an jiyo abinda muke tattaunawa ba.

'Daga murya yayi yace kowa yajiyo man ina ruwana, watau ni kake zargi ko kenan?

Shima mik'ewar yayi yace ni ba zarginka nakeba tambayoyi suka kawoni wajenka kuma ya kamata ka amsa min su, shin ya labarin kud'ad'e, gidaje, filayen marigayi Alhaji Muhammad da suke hannunku ko kun ajiyesu ne sai d'iyarshi ta fito daga gidan kaso sannan kumallaka su a wajenta tunda kawunta wanda kuke tayawa ajiyewa ya rasu?


Alhaji Mansur mutuwar tsaye yayi yana kallon Faruk da tsantsan mamaki jin kalaman da suka fito bakinshi bayan babu wanda yasan wannan sirrin sai su kad'ai toh ina yaji hakan?

Yana cikin tunanin yaji muryar Faruk ya cigaba da cewa sannan takardun kamfanin yarinyar chan ya kamata ace kun damk'a mata abunta, filayen da gomnati tasiya ma a wajenku ko tana da alak'a da su?

A fusace cikin d'aga murya yace ya isheka haka Barrister! ya isa!!! Watau ni zakazo kaci ma mutunci dan kawai mahaifin Nasiba ya hanaka auren d'iyarshi ni zaka ja ma sharri? Toh wallahi ya zama dole indamk'a ka a hannun hukuma dan bazan lamunci hakan ba da girmana a gari kanemi kazubar min da shi, duka dukiyar muhammad nawa take da har zamu so mucita kaduba girman Guest house d'ina wanda ko rabin girman gidana bai kai ba shin wannan bai isa yazama shaidaba akan cewa na fishi dukiya? Bazan barkaba dole kotu tashiga ciki,,, wayarshi yad'auko yana shirin lalubo number.

Murmushi Barr Faruk yayi yace kiran wayar da zakayi daidai yake da tona ma kanka asiri, shin zaka iya tuna wata mota sabuwa fil da Alhaji Muhammad yasiya wadda kaci burin kamallaketa Wadda cikin motocinka babu kamar ta? Ko zaka iya tuna wayar da kukayi da Alhaji Mu'azu akan son mallakar dukiyar jawahir da take cikin account d'in mahaifinta?..

Wayar da take hannunshi ce tasu'buce tafad'i nan yafara zufa 'yan cikinshi saida suka kad'a, wuta tad'auke mashi d'if saida yayi kusan minti biyar suna kallon kallo da Barr Faruk sannan yayi k'ok'arin saita kanshi sannan cikin inda-inda yace ina kaji wannan? wanene yafad'a maka hakan?

Tsayawa Barr Faruk yayi yana kallonshi ganin haka yasa Alhaji Mansur yanufoshi a harzuk'e yana cewa tambayarka nake kabani amsa!

Ja yayi da baya yace ka ga kar kamatso min nan ni tambayarka nayi kuma amsa nakeso.

Idanuwan Alhaji Mansur jajir sukayi saboda 'bacin rai cikin fushi yanuna mashi hanya yace fitar min daga gida tun kan insa afitar da kai ta k'arfi, wannan cin fuska ya yi yawa ace katako har cikin gidana kaci min fuska, kai wanene a garin nan da har zakayi min haka?

Ta'be baki yayi cikin nuna rashin damuwa yace na ji zan fita kuma ni ba kowa bane saidai inaso kasani na san abubuwa da dama agame da duk abinda kuka aikata, sannan kashirya zan k'ara dawowa gareka dan neman amsar wad'annan tambayoyin kai har ma da wasu na daban, murmushin gefen baki yayi sannan yace na barka lafiya,,, yana fad'in haka yajuya yafita.


Alhaji Mansur tsaye yayi yakasa ta'buka komai mamaki duk ya gama cikashi nan kuma yafara zagaye d'akin yaje yadawo haka yaitayi cikin ranshi yana tunanin wanene yasanar da Barrister duk wannan to kodai yarinyar chan ce? Toh ammah ita kanta batasan abinda duk muka shiryaba, saidai ya kamata inyi wani abu a nan, komawa yayi yazauna yad'auko wayarshi yalalubo wata number bata dad'e tana ringing ba akayi picking ko sallama bai tsaya yi ba yace Alhaji da matsala.

Daga chan 'bangaren akace matsala kuma? Wace iri kenan?

"Lauyan wannan yarinyar ya zo ya sameni ya tisani a gaba yana min wasu tambayoyin da suka nemi surikita min k'walwa wanda bansan amsoshinsu ba ammah ba ma wannan ba tambayar a nan itace duk ina yasan wad'annan abubuwan?

Daga chan 'bangaren dariya aka fara kyalkyatawa har saida Alhaji Mansur yafusata ganin dariyar batada niyar k'arewa yasa yace watau kai dariya ma kakeyi ko?

Dole inyi dariya Alhaji Mansur wannan abun bai kamata yad'aga maka hankaliba.

Ajiyar zuciya yasafke yace hakane ammah ya zama dole inyi wani abu akan yaron nan kafin yanemi tozartani koda na san hakan ba zai ta'ba yuwuwa ba ammah dole inga bayanshi, ya kamata muhad'u da kai zuwa anjima domin musan ta inda zamu 'bullo mashi.
Toh shikenan babu damuwa zan shigo.

Kashe wayar yayi tare da mik'ewa yana cigaba da zagaye d'akin still dai wayarshi tana a hannunshi, ya dad'e a tsaye yana kaiwa da kawowa daga k'arshe yatsaya waje guda tare da duba wayarshi yakira wata number ana yin picking batare da ya yi sallama ba yace Barrister ina son muhad'u da kai yanzun nan kazo gidana kasameni.
Ohk ba damuwa sai ka zo ina nan ina jiranka.

Yana gama wayar komawa yayi yazauna tare da cije le'be yana jinjina kai yace tabbas ya zama dole inyi maganinka Barrister ba ma kai ba duk wanda yace zai shiga rayuwata sai naga bayanshi dan haka muje zuwa.




Bayan ya bar gidan Alhaji Mansur direct gidan kaso yawuce yana isa yasamu jawahir zaune jingine da bango ta d'age kanta sama tana kallon rufin d'akin inda hawaye suka fara wanke mata fuska, daga gefenta yatsaya yana mata kallon mamaki.
Ahankali tajuyo takalleshi tare da goge hawayen fuskarta sannan tasadda kanta k'asa tace Barrister ina jin tsoro dan Allah kazare hannunka daga cikin wannan case d'in kar wani abu yasamu rayuwarka.
Jikinshi sanyi yayi nan yatsugunna gabanta yace jawahir meyasa kikace haka? Kikwantar da hankalinki babu abinda zai faru zanyi k'ok'ari sosai wajen ganin na fitar da ke a cikin gidan kason nan ke yakamata kibani k'warin gwiwa domin wannan shine zama na k'arshe da za'ayi ya kamata mucigaba da addu'a insha Allahu mune da nasara.
Girgiza kai tayi tace baka fahimceni ba Barrister.
Na fahimceki man indai akan su Alhaji Mansur ne kicire duk wata damuwa a ranki daidai nake da su sannan basu isa suyi abinda ubangiji baiyi ba.
Cikin sanyin jiki tace hakane.
Toh kikwantar da hankalinki kinga daga nan ma wajen DPO nakeson wucewa dan yasanar da ni asibitin da aka kwantar da matar Alhaji Mu'azu dan haka koma mekenan zan sanar da ke kikwantar da hankalinki komai zai zo cikin sauk'i.
'Daga kai kawai tayi alamun toh.

Nan yayi mata sallama yatashi yatafi.



Yana isa station number d'in DPO yakira yasanar da shi zuwanshi nan yabada izini da ashigo da shi office d'inshi.

Faruk yana shiga yasameshi yana waya dan haka yaja kujera yazauna har saida yagama sannan yamik'a mashi hannu suka gaisa.
Bayan sun gaisa ne DPO yace ina saurarenka me ke tafe da kai?
Murmushi yayi sannan yace ba komai bane yake tafe da ni sai akan dai case d'in jawahir kamar yadda a binciken da nakeyi nagano cewa matar Alhaji Mu'azu tana nan a raye ana jinyarta a wani asibiti shine nakeso asanar da ni asibitin dan inason ganawa da it.

Da mamaki DPO yake kallonshi dan ya san in ba shi da su Alhaji Mansur ba babu wanda yasan tana asibiti, Faruk kamar ya san abinda yake tunani yace baidace ace kun 'boye ma kotu tana raye ba domin duk a cikin k'undin case d'in jawahir da naduba banga inda aka fad'i matarshi tana raye ko ta mutu ba.
Jikin DPO sanyi yayi yace tabbas tana raye kuma wannan ba laifina bane polices d'in da suka bada sheda ne basu rubuta ba ammah shikenan zan sanar da kai asibitin saidai ko ka je babu abinda zaka samu daga wajenta dan har yanzu batasan inda kanta yake ba.
Jinjina kai Barr Faruk yayi yace babu damuwa.
Nan DPO yasanar da shi.
Sallama yayi mashi yatafi shi kanshi cikin ranshi ya yi mamakin yadda yau DPO bai mashi rainin wayo ba haka yashiga motarshi yawuce private hospital d'in, yana isa baisha wahalar gane room d'in da takeba dan haka yawuce, yana shiga yasameta a kwance tsaye yayi yana kallonta tana kwance bata ko motsi, wata dattijuwa ce tajuyo takalleshi tace sannu da zuwa.
Murmushi yayi sannan yayi sallama tare da ida shiga d'akin.
Bayan ta amsa gaisawa sukayi yatambayeta ya me jiki?
Cikin sanyin jiki tace toh Alhamdulillah za'a ce.
Kallonshi yamaida ga Ummah da akasa ma drip idanuwanta a rufe kamar me bacci yace bacci ma takeyi ko?

Uhm wane bacci yaro ko ma idanonta biyu ba'a ganewa dan har yanzu kusan shekara d'aya kenan babu uhm bare uhm uhm saidai kallon mutane kawai da take.

Mamaki ne yakama Barr Faruk yace Allah yasauk'e Allah yabata lafiya ko zan iya sanin Doctor d'in da yake dubata.
Goge hawayen da suka zubo mata tayi tace Eh Dr Aminu ne.
Ohk Allah yabada lafiya.




___________

Washe gari da marece yanufi gidan su Nasiba yana isa megadi yasanar da shi bata nan murmushi yayi sannan yace toh babu damuwa Alhaji fa?
Eh toh Alhaji yana ciki.
Toh ko zan iya ganinshi?

Wani yaron gidan ne megadi yatura yace yaje yace ana sallama da Alhaji, sannan yabud'e ma Barr Faruk gate yashiga da motarshi yana yin parking yafito yajingina a jikin motar sai ga yaron ya fito ya ce ance wai wa ke nemanshi?
Kace mashi Faruk ne.
Toh yace nan yakoma yashaida mashi.

Barr Faruk ya yi kusan mintuna goma a wajen tsaye kafin Alhaji Sufyan yafito.
Fuska a murtuk'e yanufo wajen da Faruk yake tun kan ya ida isowa yace lafiya me yakawo ka gidana? Ko ka zone kashaida min ka janye daga case d'in.
'Dan rissinawa Faruk yayi yagaisheshi a maimakon ya amsa sai ma k'ara jefo mashi tambaya yayi yace ina fata ba'a kan aurenku da d'iyata kazoba ko, dan bazan ta'ba amincewa ba har sai ka janye k'udurinka.
'Dagowa Faruk yayi yakalleshi sannan yace ko d'aya Alhaji ba wannan ne dalilin zuwana ba.
Toh menene dalilin zuwan naka?
Shuru Faruk yayi.
Nan Alhaji Sufyan ya ida harzuk'a yace ba tambayarka nake ba!.....








_Sis Nerja'art✍🏻_
[7/24, 11:14 PM] Sis Nerja'art 2: *......FANSAR RAI......*



*INTELLIGENT WRITER'S ASSO....®*
[On Ward Together]

_Follow me on Wattpad: *Sis-nerja*_


_Wannan Littafin na kud'i ne domin karantawa cikin aminci da yarda ga duk me buk'ata zai turo katin Mtn na d'ari biyu N200 kacal ta wannan number d'in 09035938246, ko ta account number 5330055604, Idan katura ka aiko da screen shot na transaction a wannan number d'in 09035938246_


_Akwai gara'basar *RESHE YA JUYE DA MUJIYA* na shahararriyar marubuciyar nan *AMEENA ABBA UMAR* tare da novel d'in *FANSAR RAI* akan farashin N300 kacal, ko da kud'in ka sai da rabonka_




*PAGE 14*

Ganin yadda yaharzuk'a yasa Faruk yayi murmushi yace kakwantar da hankalinka ba wai dalilin d'iyarka yasa nazoba na zone akan aikina.
Cikin nuna rashin fahimtar inda zancen yadosa yace ban fahimceka ba wane irin aikin kenan?

Juyawa yayi yakalli gefe d'aya sannan yace a matsayina na barrister ko ma ince akan case d'in jawahir na zone dan ind'an maka wasu tambayoyi wad'anda suka shige min duhu.

Wani irin kallo Alhaji Sufyan yayi mashi mai wuyar fassarawa koda Barr Faruk bai san ya yi ba saboda ba shi yake kallo ba, ida harzuk'a Alhaji Sufyan yayi yanuna kanshi yace ni ni zakazo kayi ma tambaboyin banza akan wacchan yarinyar? Miye had'ina da ita da har zakazo kace zaka tambayeni, inma kana yi ne saboda na hakana ka auren d'iyata toh bari kaji kayi duk abinda kaga dama ammah Nasiba ta fi k'arfinka dan haka kabar gidan nan yanzu tun kan insa'ba maka,,, yana fad'in haka yajuya a harzuk'e zai koma gida.
Sai a lokacin Faruk yajuyo yakalleshi yace shin me zaka iya cewa akan kisan da akayi ma Alhaji Muhammad Mai kud'i?
Chak Alhaji Sufyan yaja yatsaya batare da ya juyoba ganin haka yasa Faruk yacigaba da cewa sannan dukiyar yarinyar chan da take hannunku shin kun ajiye mata ne da sunan idan ta fito zaku mallaka mata ita? Sannan dukiyarta da kuka amsa hannun Alhaji Mu'azu da sunan zakuyi business shin ya maganar business d'in?

Jikin Alhaji Sufyan sanyi yayi yai saurin juyowa yakalleshi cikin 'bacin rai yace ban fahimceka ba kana nufin dukiyarta tana wajenmu ko kuma kana nufin muna da hannu a cikin mutuwar shi? Faruk kana da hankali kuwa?

Murmushi yayi cikin nuna rashin damuwa yace ba wai haka ba Alhaji kowa ya san kusancinku da Alhaji Muhammad sannan bayan mutuwarshi kuka koma abota da d'an uwanshi wanda yake da gurin ganin ya mallake dukiyarshi sannan sanin kanku ne Alhaji Muhammad ya bar duniya yana binku bashi kuma kun ci guri sosai akan wasu abubuwa nashi hatta.......katseshi yayi yace ya isa haka Faruk wannan tatsinniyoyin naka duk kasan wanda zakayi masu ba wai niba kowa ya san cewa Alhaji Muhammad abokin alk'alla ta ne ba wai abokina bane akan wane dalili zan so mallakar wani abu nashi bayan dukiya nima ina da ita tun daga tsarin gidana da matsayina ya kamata kafahimci hakan.

'Daga kai Faruk yayi yana kallon gidan sannan cikin nuna rashin damuwa yace ammah toh idan yakasance wannan gidan mallakinshi ne fa mezaka iya cewa?

Kai!!! Banason shashancin banza me kake nufi da maganarka gidan nawa ne mallakin wani? Inji wane mak'aryacin yafad'i haka? Fad'amin!

Girgiza kai Faruk yayi yace babu wani mak'aryaci da yafad'i hakan saidai ka sayi gidan a hannun Alhaji Mu'azu a kan farashi me sauk'i bayan kuma kun san gidan ba mallakinshi bane.

Tsawa yadaka mashi yace Faruk na gaji da jin wad'annan k'aryayyakin naka na banza wanda me hankali bazai ta'ba d'aukarsu ba tun muna mu biyu kafita kabar min gida!

Har Faruk ya bud'e baki zaiyi magana yayi saurin tarar numfashinshi cikin d'aga murya yace na ce kafita kabar min gida ko bakaji abinda nace ba!?

Ganin yadda yad'au zafi sosai yasa Faruk yace shikenan na ji zan tafi ammah.....
Kar kasaki kafad'i wani abu a wajen nan katafi nace!!!

Gyad'a kai yayi yajuya yabud'e motarshi yashiga yana jin Alhaji Sufyan yana ta fad'a haka yatada motar, yana fitar da motarshi daga gate d'in gidan Nasiba tana 'bullowa da tata motar wani irin dad'i taji a ranta dan ta d'auka wajenta yazo saidai abinda yabata mamaki ya ganta ammah yashare yayi tafiyarshi, duk sai taji babu dad'i cikin ranta tace ko lafiyarshi shi kuma? Girgiza kai tayi tashigar da motarta cikin gidan hango Daddynta tayi yana ta kaiwa da kawowa a wajen ranshi duk a 'bace, mamakine yacikata tayi saurin yin parking d'in motar tafito tanufi wajen mahaifin nata tana cewa Daddy lafiya? Me yafaru?

Juyowa yayi yai mata wani irin kallo cikin 'bacin rai sannan yajuya yashige gida.

Mutuwar tsaye Nasiba tayi tace ikon Allah me yafaru? Ko dai dan Faruk ya zo gidan ne yasa ranshi ya'baci kuma fa na ga shima Faruk ya tafi ranshi a 'bace toh me yafaru? Ajiyar zuciya tasafke sannan itama tabi bayan Daddynta tashiga cikin gidan a parlor tasameshi tsaye Hajiya Maijidda tana tambayarshi abinda yafaru.
Hucci kawai yake dan ranshi ba k'aramin 'baci yayi ba chan yajuyo yakalli Nasiba sannan yamaida kallonshi ga matarshi cikin d'aga murya yace wai ni ni Faruk zai zo yaci ma mutunci har cikin gidana.

Kusan a tare sukace cin mutun kuma?
Cize le'be yayi sannan yace eh man duka nawa yaron nan yake da har zai kalli tsabar idona yatuhumeni akan mutuwar Alhaji Muhammad har yana ik'irarin cewa wai muncinye ma d'iyar shi dukiya, gidan nan ma da nake ciki cewa yayi na yarinyar ne.
Nasiba a kid'ime tace Daddy, nan tasa hannu tatoshe bakinta tare da fashewa da kuka ahankali tace Faruk meyasa kayi haka.

Hajiya Maijidda cike da mamaki tace Faruk d'in yace haka Alhaji?
Toh in ba shiba wanene? murmushi yayi mai ciwo sannan yace duka yaron nan nawa yake wallahi da ace bani mutunci da mahaifinshi da yau yau d'innan sai na sa an d'aureshi a garin nan!

Baya baya Nasiba tafara ja sannan taruga dagudu tanufi d'akinta tare da fashewa da wani irin kuka me shiga rai tana shiga saman gadonta tafad'a tana me cigaba da kukan, wani irin haushin Faruk ne taji cikin ranta tace wai shine yaci mutuncin mahaifina daman ya san abinda zai aikata saisa yace insamo mashi number d'in Alhaji Mansur,, , kuka tacigaba da yi sosai.


Hajiya Maijidda kallon mijin nata tayi da ranshi yayi matuk'ar 'baci tace Alhaji baidace ka'bata ranka saboda wannan yaron ba ina tunanin ya yi hakane kawai dan ka hanashi auren d'iyarka ammah ko indai dan hakane baida mutunci.

K'wafa yayi yace kibarni Hajiya baisan wanene ni ba wallahi idan baibi a sannuba sai na sa and'aureshi a garin nan inga ubanda yatsaya mashi babu ruwana da mutuncin da muke da mahaifinshi tunda shi haka yake, ba barister ba ko alk'aline babu ruwana.
A'a Alhaji kayi hak'uri abi komai a sannu kawai dai kaje kayi ma mahaifinshi magana dan yagargad'i d'anshi yafita daga harkar ka idan har bai daina ba toh shine kake da damar yi mashi kowane irin hukunci.
Jinjina kai Alhaji Sufyan yayi yace kibarni da shi kawai Hajiya zai san da ni yake, je kid'auko min key d'in motata.
Amsawa tayi da toh, taje tad'auko mashi har tadawo yana nan tsaye inda yake mik'a mashi tayi ya amsa yawuce yafita cemashi tayi Allah yakiyaye ammah bai amsataba saboda yanayin da yake na 'bacin rai.

Rik'e baki tayi tace oh ni Maijidda wannan yaro ammah dai baida mutunci da ace mahaifinshi shima ba mai kud'i bane da nace bak'in ciki yake da dukiyarmu,,, tunowa tayi da Nasiba dan haka cikin sauri tanufi part d'inta tana isa tasameta a bedroom kwance sai faman rusar kuka take daga gefen gadon tazauna tare da kiran sunanta nan Nasiba tayi shuru.
Ganin haka yasa tace kindai ji abinda Faruk yayi ma mahaifinki yaron nan ashe baida mutunci bai gaji arzik'iba.
Tashi tayi zaune tare da tsaida kukanta tace wallahi Mummy da ace banga fitar Faruk daga gidan nan ba da bazan ta'ba yarda da cewa shine ya aikata ba yanzu dan rashin mutunci yakalli tsabar idanun mahaifina yafad'a mashi haka? Kenan soyayyar da yakeyi min duk ta k'aryace.
Ta'be baki tayi tace toh ai yanzu gashinan dai kin gani da idanunki.
Fashewa tayi da wani sabon kukan tace wallahi indai har Faruk ya yi min haka dan yatozarta mu toh yaje ya yi ma kanshi ni kuma zanyi k'ok'ari wajen ganin na cireshi a raina dan iyayena sun fiye min komai ba'ayi wanda zai zo yaci musu fuska har ransu ya'baci ba.

Jin kalaman da tayi yasa Mummynta tajawota jikinta kamar jira take tafad'a tare da rungume mahaifiyartata tana cigaba da rusa kuka.
Lallashinta Hajiya Maijidda tashiga yi dak'yar tasamu tashawo kanta har tahak'ura tadaina kukan.


________


A chan wani k'urmin daji dake wajen garin katsina tsakanin wasu k'auyuka biyu, dajin yana da duhu da yawan itatuwa sosai, iska kawai yake kad'awa a cikinshi baka jin motsin komai sai kukan tsuntsaye kawai babu mahalukin da yake shigarshi saboda ansan had'arin da ke cikinshi dan a tsakiyar dajin wasu 'yan fashi su biyar da suke rayuwa a cikinshi a duk lokacin da sukaso suna fita suyi fashi a gari

Please Login or Register in order to submit comment