You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

ne da ita ba, kar a cutar da ita*.

Ammi ta ce "Kana da gaskiya, amma na ga ta su ta zo Waya, in sha Allah babu wani abu da zai faru, tun da ka ji sau?i ma, sai ku tafi amma dan Allah kar ka ce zaka yi faWa, kaga ba ka da cikakkiyar lafiya. Kuma ka sani ko a dalilinta komai ya dai-dai ta tsakaninka da Wan uwanaka?"

Kallon idon ammi yake, tuni har hawaye sun cika mata ido.
"Shikenan ammi, ba zan yi magana ba, ki yi ha?uri, amma dole in raba shi da iyalina".

***
Da aka tashi daga makaranta, Adam ne ya zo Waukar ta, saboda ya ji sau?i sosai, ciwon bai kuma tashi ba.

Tana ganinsa ta hau dariya "Ka warke ne ka zo da kanka, da adaidaita sahu zan hau na tafi ai".

Fuskar sa babu walwala, yayi mata banza, ya ja motar suka tafi, sai dai ta ga ya nufi gidansu, maimakon na Ammi, ganin ya na ta cika yana batsewa, ya sanya ba ta kula shi ba, ta cigaba da harkokinta.

Ko da suka je gida, su Asiya suka din ga yi musu sannu da zuwa, suna yi wa Adam sannu, dan baba uwani ta gaya musu, maigidan ne babu lafiya.

Ya wuce Wakinsa ta wuce nata, ta yi wanka, ta kwanta baccin da ba ta samu yi jiya ba.

Sai da aka yi la'asar, sannan ta tashi, taje kitchen ta haWa shayi, ta zuba madara fal da milo, ta dafa ?wai ta ci abunta, sannan ta Wau littafinta, ta tafi Wakin Adam.

Yana zaune a kan kujerar Wakin sa, yana dudduba wasu takardu, ta yi sallama ya amsa mata a ciki, ba ta damu ta je gabansa ta tsaya, ta ce "Albishirinka?"

Ya kalleta ya ce "Ya aka yi?".

Ta nuna masa littafinta, na assignment Win da ta yi, ta zana malaminsu, ta ci 10/10.

Ya Wan kalli littafin da mamaki, sannan ya kalleta, alamar yana jiran bayani.

"In gaya maka har malamin ya kirani gaban allo, zai yi disgracing Wina, ya Waga littafin ?an ajin suna dariya, ya tambayeni da turanci wai meye wannan? Ni kuwa na ce ni ban iya ?ir?irar komai ba, amma idan malamai suka yi kyau kamar zanen nan nawa, to za a samu Walibai masu ?o?ari da tsara zane kamar nawa, koma fiye da nawa, Aikuwa aka dinga tafa mini,ya ka ji azancin nawa"

?an murmushi gefen baki ya yi, dan ya fuskanci ita fa dan kana fushi da ita, kai ta shafa.

Ya ce "You try".

"Yauwwa, sai ka saya mini kyauta, teddy bear nake so, da kuma ?ar tsana babba, sai lunch box Wina"

Yayi mata kallon ba zaki girma ba.

"Ya naga kana kallona?"

"Mahmud, Ala?arki da shi bana so, kar ki kai ni bango a kan haka".

"Wai meyasa zaka saka ni a cikin faWa ku? Ni meye nawa yana yi mini kirki, shikenan dan kuna faWa nima sai na din ga jin haushin sa. Jamil, Jabir, Samha ala?ar ka da su bana so, Jamil da Samha, sun wahalarsa da matarka, su meyasa ba ka gaba da su?" Ta yi maganar tana tsare shi da ido.

Rasa bakin magana yayi, duk yadda kake tunanin rumaisa ta wuce nan, a zahiri tana da ?uruciya da wauta, but she have a very sharp brain, ba shi da amsar bata a yanzu dan ta ?ure shi.
Amma saboda kar ta ga ta yi nasara ya ce "Ni ne shugaba, a gaba nake da ke, dan haka duk hukuncin da na yanke dole ki bi".

Ta Wau littafinta ta ce "Babu biyayya ga abokin halitta wurin saSawa mahalicci, duk da?i?ancina a makaranta, na san wannan, kuma Allah ya yanke rahamarsa ga mai yanke zumunta, Annabi ma ba ya tare da mai yanke zumunci, sai ka din ga jin tsoron Allah wurin yanke jiki kai ma" ta fice ta koma falo ta bar masa Wakin.

Mintuna kaWan ya fito ya fice daga gidan gaba Waya, ya dafe kanta ta ce "Na shiga uku wannan wane irin abu ne, anya kuwa zan iya, ni duk na gaji" tayi tsaki, ta tashi ta je ta ciko roba da gugguru, ta Waukko lemo, ta zo ta saka a gaba tana ci, tana kallon cartoon.

Hayaniya ta ji ana hawowa sama, ta tsaya tana jiran taga waye zai shigo?

Samha ce da Fauziyya, da kuma ru?ayya sai zee ?anwar Samha, baba uwani biye da su, hannunta ri?e da foodflask.

Babu ko sallama suka zo suka zazzauna, baba uwani ta ajiye kwanukan, ta ja gefe.

Samha ta kalli rumaisa ta ce "An samu duniyar da babu a gidan tsoho, an yi Wai-Wai a katafaren gida, da duk dangi babu irinsa" rumaisa ta yi mata banza, ya cigaba da kora lemonta.

Ru?ayya ta ce "Allah wadaran naka ya lalace haryanzu ban ga technology a auren wannan busashiyar yarinyar ba, da ko rantsuwa na yi babu kaffara, ragowar masu garkuwa da mutane ce, sun gama lalata ta" Wan shiru ruma ta yi tana tunanin, me take nufi.

Fauziyya ta ce "Ba wani technology, wula?anci ne kawai, dan Allah dubi Samha ki dubeta, ita ta isa ta kira kanta mace ma wallahi wannan ko a mai aikin samha ba ta isa ta zo ba, kalli bakin shegiya yadda take auna madara, saboda samun wuri, ga ?irjinta fayau kamar faifai ba wata mamora, amma wai ita ya aura".

Rumaisa ta yi gyatsa ta ce "Gidan miji daWi, mussman irin gidan papa, auren mai kuWi daWi ba, na samu promotion, gida babu, na samu a gidan miji" tayi maganar tana lashe madarar hannunta.

Fauziyya ta ce "Ke dalla rufewa mutane baki, tashi ki kira mana Wan uwanmu, mun zo duba shi"

Cikin tsawa rumaisa ta ce"Ba zan kirawo shi Win ba tun da ke ba uwata ba ce"

Samha ta ce "Ke, uban wa ki ke yi wa tsawa".

"Uban duk wanda ya tsargu, ba sunana Aisha ba, sunana rumaisa Mahmud, ?anwar maza, ku tambayi yayan naku wace ni, kawai ku zo ku cika mini kunne, wai ko a? ?ar aiki ba zan zo ba, ai Allhan ba naku ne ku kaWai ba, da ban zo a ?ar aikin ba, sai na zo a matar gida, antynku ce ni, tun da matar yayanku ce ni, ke kuma da ki ke cewa ke ce mace, na ji ni namiji ce, ni duk wadda ta yi mini, wallahi sai ta ci ubanta, babu wata barazana da tashin hankali da ban gani ba, dan haka ba zaku Waga mini hankali ba, ke kuma da ki ke cikakkiyar macen, kin san idan ki ka gama cikar, zubewa zaki yi ki fara tsufa, kin ga ni kuma a lokacin da ki ka fara tsufa na cika ko? Banza kawai"

"Ke! Kina ?ar matsiyata ni ki ke gayawa haka? Kina da hankali kuwa, waye ubanki a ?asar nan, har ni ki ke cewa ubana zaki ci?"

"Eh na faWa, sai na ci ubanki, da ke da duk wanda ya ce zai zageni, ?an fashin daji ma, ba su razana ni ba, balle ku shashashai, gwalagwaje, marasa mutunci, idan tunaninku gayya, ku taron mata ne, ni kaWai dai-dai nake da tunanin maza bakwai".

Ayshercool.










Paid book ne, ? 500 via 0009450228, aisha adam jaiz bank, sai shaidar biya ta 08081012243, ga masu bu?atar vip post, suna iya garzayawa arewabooks su yi searching sunan book Win. Kar ku manta da subscribing YouTube channel Winmu na Cool hausa novels, domin samun daWaWan litattafan hausa na sauraro, ciki har da ?anwar maza da yake daf da fara zuwar muku a kan channel Win*

https://www.youtube.com/@CoolhausaNovels

Susbcribe my YouTube channel please =?O?



Ru?ayya ta ri?e haSa ta ce "Kan uban nan, wannan wace irin yarinya ce, mara tarbiyya Binta ta aurawa Wan ta?"

Jin maganar rumaisa ta yi wani iri, yadda ru?ayya ta ambaci sunan Ammi haka kai tsaye kamar sa'arta.

Zee ta ce "Ni wallahi da na san irin wannan abun zamu tarar, da ban zo ba, kawai kun zo kuna zubar mana da mutunci a gaban wannan ?ar yarinyar".

Ruma ta ce "Oho dai, in ma ?ar cikinki ce ku ta shafa, aka gaya mini cuta sai na faWi mutuwa, haka kurum ti?a-ti?a da ku, ku zo kuna ci mini mutunci. Wai wani kun zo wurin Wan uwanku, yo koma menene, duk ?an uwantakar ta ku, tun da dai ni ta ajiye mussaman yake bani abinci, yake kula da ni, yafi so na"

Samha da takaici ya ?ule, ta mi?e a hasale, tana yin?urin ta ?arasa ta tsinke rumaisa da mari. Fauziyya ta ri?e ta, ta ce "Ba girmanki ba ne".

"Ki cikani Fauziyya, in zuba mata da ha?ora na daki banza, dan ubanta"

Rumaisa ta ce "TaS ki dakeni ki ga yadda ake ?aramin ya?i, wallahi sai yayyena sun yi miki bugun sakwara, bar ganin kin fini girma, ni da maza ma dambe nake ba ruwana da girmanki".

Jin hayaniya ya sanya baba uwani hawowa saman, ta zo ta iskae rumaisa tana ta zazzaga musu rashin mutunci.

Baba uwani ta ce "Haba ke kuwa, ba?inki ne fa, ?an uwan mijinki, ya zaki din ga yi musu wula?anci haka, ai ba haka ki ke yi wa ?an uwanki idan sun zo ba, kuma ba sa'anninki bane "

"Baki san meyafaru ba, dan haka ba ruwanki da ni".

Baba uwani ta dafe ?irji ta ce "Ni ki ke gaya wa haka?"

Rumaisa ta dubi dattijantar baba uwani, ta haWiye abun da ta yi niyyar faWa ta ce "Ba ruwanki da abun da na yi, idan ban saka ki a ciki ba, tun da baki san farkon abun ba, kuma kina goyon bayansu"

Ta Wauki kofinta, ta nufi Wakinta, tare da ce musu "Mahukatan banza kawai"

Tun da ta shige Wakinta, ba ta sake fitowa ba, tayi zamanta tana zane-zane, har aka yi sallar magariba, sannan ta tashi ta yi alwala ta yi salla.

Ta idar da salla kenan, ta jiyo takawa yana kwaWa mata kira, yamutsa fuska ta yi, dan ya tsorata ta.

Fita tayi, ta tsaya ta kalli falonta, an ci abinci an Sata falon gaba Waya, har da fasa mata wasu daga cikin farantai.

Kasa magana ta yi, a fusace ya kalleta ya ce "Meye wannan?"

"Oho" ta bashi amsa.

"Which kind of nonsense is this, ina yi miki magana?" Ya yi maganar a zafafe.

Nan da nan ita ma ranta ya Saci, "Amma dai ka san ni ba ?azama ba ce, kuma ba ka taSa ganin nayi irin wannan abun ba, yadda ka gani, nima yanzu nake gani".

"Wai ne ki Waukeni ne? Sa'anki or what, kina da hankali kuwa, kalli falon nan fa?"

Takaici ne ya ?ule rumaisa ta ce "Ni ba mahaukaciya ce ba, ?annenka da wannan Samhar su ne mahaukata, dan su suka yi haka da falon ba ni ba, tun da dai baka taSa gani na yi haka da gidan ba" ta juya ta nufi Wakinta, ya taka da sauri ya janyota ya mayar da ita falon.

"Idan suka yi haka da wurin, ke ba zaki saka a gyara ba, ko ke ki gyara ba? Ba gidanki bane?"

"TaS, ni zan gyara musu, to wallahi ko kai ne ba zaka yi haka in gyara ba, kai da kake ciyar da ni, balle wasu ?artin banza"

"Shut up! ?annen nawa ki ke cewa ?artin banza? Ki kiyayeni, samo abun gyara ki gyara wurin nan, na baki mintuna biyar kawai. Ki gama ki zo ki gaya mini dalilin da ya sanya ki ke yi wa baba uwani rashin kunya"

Wani irin malolon ba?in ciki ya cunkushe mata zuciya, ba ta taSa tunanin Adam yana da kwarjini, da kima a idanunta ba sai yau, da ta ji tamkar an Waure mata harshe, ta kasa bijire masa, wasu hawayen ba?in ciki suka cika mata ido, amma ta danne, ta zo ta fara aikin gyara wurin.

Ya nemi wuri ya zauna, ta gyara ta kammala, ba ta ce masa uffan ba, ta tafi Wakinta.

Bayanta ya bi, ya tarar da ita a gaban mudubi, ta cika ta batse, ba wani abu take a gaban mudubin ba, kawai tana tsaye, tana sauke numfashi.

Tana ganinsa ya shigo, ta share shi ta cigaba da tsayuwa.

"Me baba uwani tayi miki da ki ka yi mata rashin kunya?"

Banza ta yi masa ta?i kula shi.

"Ina sake gargaWinki, duk abun da zasu zo su yi, babu ruwanki da su, sannan idan ki ka kuskura ki ka kuma yi wa baba uwani rashin kunya, sai na Sata miki rai, kawai kin saka tsohuwar mutane kuka, saboda ke baki san abun da ya dace ba?" Yayi maganar yana son ta yi magana, dan ya ji meya haWa su da su Fauziyya, dan ya san idan ya tambaye ta, yadda ta ?ule Win nan, ba zata gaya masa ba.

"Wallahi duk wadda ta kuma zuwa ta zageni, sai na rama, kayi zuciya ka mayar da ni gidanmu, sai ka tattaro su su dawo gidan nan su zauna, gida zan tafi dan ni ba banza ba ce, da za su din ga zagina ina jin su ba, me na yi musu? Nima ?anwar wasu ce, kuma suna sona, dan wallahi ko za su kasheni, suka zageni sai na rama, ita kuma baba uwani ta cigaba da yi mini sharri" ta yi maganar tare da shigewa toilet.

Har dare ta?i ko sake fitowa, dan ko abincin dare ba ta nema ba, ta yi kwanciyarta.

Sai da takawa ya nemi, Asiya da barira ya tambayesu abun da ya faru, amma suka ce ba su sani ba, baba Uwani ta hana su hawa saman, amma sun jiyo su Fauziyya suna zagin rumaisa tana ramawa.

Daga nan gidansu ya wuce, bai ko je sashin Ammi ba, ya nufi sashin Mummy.

Ya tarar da su gaba Wayansu, har da Mahmud da Mummy, da ru?ayya da Fauziyya, sai dai babu Samha.

Mummy na ganinsa ta ce "Ahh, takawa barka da wannan lokaci, ?araso mana, ya jikin naka, tun da na shiga ban sake zuwa ba, ashe ka samu sau?i".

Ya ce "Eh"

"Sabuwa, ?aro plates, a zubawa takawa abinci shi ma".

Ya girgiza kai ya ce "Na gode, Fauziyya"

Ta kalleshi ta ce "Na'am yaya"

"Kun je gidana Wazu?".

"Eh yaya mun je, zamu sake dubaka ne kuma baka nan, matarka ta yi mana rashin mutunci, har da zagin baba uwani".

Adam ya ce "Daga yanzu, idan har ba alkhairi ne zai kai ku gidana ba, kar ku sake zuwa, ina baku wannan sa?on ne har Samha, idan ma baku gaya mata ba, ni zan gaya mata. Kar ku sake zuwar mini gida ku ci mutuncin mata ta, ni na ajiyeta ba ita ta ajiye kanta ba, kuma ban aurota, dan ku je ku ci zarafinta ba, ita Aisha dama taku ce, kuma mai ha?uri ce. Wannan kuma tawa ce, sannan ba zata iya jure abun da Aisha ta jure ba, yarinya ce ba zan lamunci a saka mata tension depression ya kamata da ?uruciyarta ba".

Baki a sake Mummy ta ce "Yanzu matarka ka fifita a kan ?annenka, duk da sun gaya maka ta wula?anta su? Bayan kai suka je dubawa?".

"Mummy ko dabba na ajiye na ce nawa ne, bai kamata a je ci mutuncinsa ba, idan har ina da kima a idon su ba, balle Wan adam na ajiye, idan banda rashin girma, me zai saka su biye mata, tun da ba sa'arsu ba ce ba, na san rigimammiya ce, amma ba ta yi haka kurum, ku kiyaye, aje a ci mata mutunci ace mata ?waila, ko ba mace ba ce, ni a idona mace ce kamar kowa.? Dan haka Please allow her to enjoy her marital home. Ko ba ku yi zumunci da ita ba, ni na isheta, na san yadda nake bi da ita mu zauna lafiya"

Mummy ta yi murmushi ta ce "Hmm, wannan dai kashedin na samha ne, zuwa aka yi a gaya mana ana son ta kenan".

Ya tashi yayi murmushi? ya ce "Ta cancanci hakan Mummy, a rashin Aisha ita ce uwar Wana, idan na bari aka wula?anta ta, ni aka yi wa, dan haka a kiyaye"

Mummy ta yi shiru, tana sa?a wani abu a ranta, lallai akwai ?ura ba ?ar kaWan ba, Samha tana ruwa, dan ba ta tunanin baba uwani na abun aka sakata yadda yakamata.

Mummy ta ce "Gaskiya ne, tayi rawar gani kam, ta cancanci a kula da ita. Duk da ka Soyewa duniya ita, da muhimmancin abun da tayi maka"

"Ni ta yi wa, ba duniya ba, dan haka ni yakamata na girmama abun da tayi mini".

Mahmud kuwa, ya kammala cin abincinsa, danna wayarsa kawai yake yi.
Har Adam ya wuce shi, ya dawo ya zauna a kusa da shi, yayi ?asa da muryarsa yadda shikaWai zai ji me yake cewa ya ce "Am warning you, stay away from my family, da Wana, da kuma matata"

Mahmud ya Wan kalli Adam ya ce "Ban ji zan iya ko Waya ba, ina son Wanka, ina girmama matarka, kasancewar tana girmamani, we are having a deal together, dan haka you should stay away from us"

Wani irin zafi maganganun sa, suka yi wa adam, amma ya shanye ya ce "Shikenan, idan ka ?i ji, ba ka ?i gani ba" ya tashi ya fice.

Mummy kasa zama tayi, ta tashi ta bar falon, Fauziyya kuma suka cigaba da caccakar rumaisa, suna bawa Mahmud labari.

Bayan ya bar sashin Mummy, ya je ya ga Sabir, Ammi ta yi masa ya jiki, tayi masa addu'a kamar yadda ta saba, sannan ya tashi ya tafi.

Kasancewar a cikin garin, gidan Jamil yake, ya sanya ya biya gidan Jamil, sai dai ya tarar baya nan.

Yau ya ji ?warin jikinsa sosai, dan haka ya shirya dan tafiya aiki, ya saba idan da makaranta, shida da rabi, rumaisa za ta zo gyara masa Waki, idak bai tashi ba ma, ta din ga ?wale-?wale kenan sai ya tashi ko baya so.
Amma har ya fito breakfast, ko alamunta bai gani ba.

Kai tsaye ya tafi Wakinta, tana zaune dirshen da kayan bacci, ta cika akwatu da kayanta, tana zugewa.

"Ba zaki shirya tafiya makaranta ba ne?"

"Eh na daina zuwa, gidan matsiyatan iyayena zan koma, in cigaba da zuwa wadda na saba zuwa, sannan in cigaba da cin irin abincin da na saba ci, ba irin wanda nake ci a nan ba ake yi mini gori"

"Dalla tashi ki shirya zan makara"

"Sai kuma ka yi, ni za a din ga yi wa gori, saboda rashin adalci irin naka, da son kai, ka Wora mini laifi, kai ?annenka ba sa laifi, wallahi ko ta katanga sai na haura na koma gida" tayi maganar cikin tsan-tsar takaici.

"Na baki mintuna goma, ki yanke shawara, idan kin zaSi mu rabu, abu ne mai sau?i, amma ki sawa ranki, ba zaki sake ganin Sabir ba, har abada mintuna goma kawai gareki" saroro ta yi, ta bishi da kallo har ya fice.

Ko mintuna bakwai yi ba, sai gata cikin uniform, kamar zata fashe.

A ransa ya ce "Ni zaki yi wa zuciya, bayan na san lagonki?".

Suna tafe a hanya ya saya mata alawar madara, dan ya san tana son harkar madara.

Ta ce bata so, bai kulata ba ya ajiye a kusa da ita, suna zuwa ?ofar makaranta, ta buWe ?ofar motar ta Wau alawarta ta fice.

Yayi murmushi ya ce "Su mimi ba zuciya in dai a kan kwaWayi ne" tana jin sa a ranta ta ce "So ka ke in kulaka, kuma ba zan kula ka ba".

Ana tashinsu ya je ya Waukkota, ya wuce da ita gidan Ammi, ya ajiyeta ya koma wurin aiki, tana jin daWin hakan nan, saboda yana Webe mata kewa sosai, duk da su Iman na makaranta, ta yi ta hira da Ammi, tana wasa da Sabir.

Ammi ta ce "Rumaisa, ashe su Fauziyya ne suka je gidanki jiya?"

Rumaisa ta ce "Eh Ammi, sun je jiya da yamma"

"Ina fatan dai ba wata matsala"

Rumaisa ta ce "Eh Ammi babu komai, sun je duba shi baya nan"

Ammi ta yi murmushi tana dafa kafaWar ruma ta ce "Ashe mutuniyar tawa tana girma, da har take iya Soye abu. Ban san dai meyafaru ba, amma na san ba zasu je su dawo haka ba, sai sun yi miki wani rashin albarkar. Babarsu ta zo Wazu tana ta masifa, wai takawa ya je ya ci musu mutunci a kanki, kamar ba ?an uwansa ba".

Rumaisa ta waro ido ta ce "Papan? Amma ni kuma jiya yayi mini wula?anci, suka Sata Waki wai ni zan gyara".

Ammi ta ce "Ki yi ha?uri, ki cigaba da kula da kanki, ban da surutu a gaban wani"

"To Ammi in sha Allah"

Ammi kuwa daWi ne ya kamata, ganin alamun soyayya a tsakanin rumaisa da takawa, yadda suka din ga turjiya kan ayi auren, ba ta tsammaci haka ba bayan auren.

"Yauwwa, Ammi dan Allah kira mini mama mu gaisa, ke da ita duk kun ?i zuwa gidanmu".

Ammi ta ce "Bari na kirata, to me zamu zo mu yi muku, ku ba gashi kuna zuwar mana ba".

Ammi ta kira mata mama, ta bata wayar sannan ta tashi ta fita.

Mama na yin sallama ta ji muryar ruma, mama ta ce "Ahh babar sabir, ?ar gidan amminta"

Ruma ta ce "Mama na tabattar kin daina so na gaba Waya, baki taSa zuwa gidana ba".

"Ai na san kina lafiya ne, ya Wan naki ya maigidan?"

"?ana lafiya ?alau, maigidan kuma mun yi faWa bama magana"

Mama ta ce "Kun yi faWa ba kwa magana saboda baki da hankali?"

Cikin sangarta ta ce "Mama faWa yake yi mini a kan abun da ba laifina ba"

"Yi mini shiru, dan me ba zai yi miki faWa ba, ya fita ya nemo ya kawo ki ci, ?an uwanki sun ce mini baki nemi komai kin rasa ba, kuma dan yayi miki faWa sai ki daina yi masa magana? Idan ma daina yi miki maganar yayi, ke ba zaki yi masa ba? Kin ga ki kiyayeni".

"To mama kawai sai na bashi ha?uri"

"Kar ki bashi, zan nemo masa wata matar mai Wa'a, tun da ke ba kya ji"

Rumaisa ta ce "Mama ban gane ba, to wallahi ammi ta ce ba zai ?ara aure ba, daga ni shikenan".

"Kar ki canza hali, na fasa zuwa gidan naki ma, sai kin yi hankali"

Kan ta yi magana, mama ta katse wayarta, ruma ta ajiye wayar tana tura baki.
Tayi shiru tana nazarin maganar mama, ba ?arya duk abun da take so yana bata, ko bai amsa mata ba, za taga abun ya bata.

Kuma ga ammi ta ce ya je ya yi wa ?annensa faWa.

"Ai shikenan, zan daina fushin, amma ba zan bashi ha?uri ba"

Har yamma tana gidan Ammi, sai magariba, sannan takawa yayi waya, ya ce Sidi ya mayar da ita gida.

Yawan zuwan nan da take yi, ya sanya ba ta damu lallai, sai an bata sabir ba, saboda tana samun sha?uwa sosai da sosai tsakaninta da Sabir Win, da kuma Ammi, gashi akwai fahimta sosai tsakaninta da iman, sannan a hankali take ?ara sanin kan masarautar, dan wataran idan ammi za ta fita, binta take yi.

Tana tsaye tana ?o?arin shiga motar sidi, sai ga mahmud.

"Daughter, ina ta so mu haWu da ke"

"Ai ban san kana nan ba, da sai na nemeka".

"Kin san bana zuwa ko ina. Jiya mijinki ya zo sashinmu, yayi wa Mamana rashin kunya, saboda su Fauziyya sun je muku gida"

Rumaisa ta ce "Ai gara shi, kishiyar mamansa ya yi wa, wanda yayi wa maman sa fa"

"Ba wannan maganar muke yi ba, idan muna irin wannan maganar, raina zai iya Saci. Yanzu dai ina zaki?".

"Sidi ne zai kai ni gida".

"Duk an yi mini kashedin na fita harkarku, amma ba zan iya ba, Waukko mini Sabir sai na kai ki gidan, na dawo ni da shi"

Rumaisa ta ce "Babu lallai ammi ta bani shi, sai da ka zo mu je tare"

"Ina son yaron nan sosai daughter, mu je"

Tare suka koma Ammi ta din ga kallon Mahmud, Ruma ta gaya mata abun da ya ce, ammi ta ce "Banda abun sa ai shi ma Wan sa ne, Allah ya tsare"

Ruma ta yi ta murna, ta Wauke shi suka fita, Mahmud ya karSe shi, suka shiga motarsa suka tafi.

Nusaiba ta ce "Ammi, kina ganin babu wata, ko takawa ya zo yayi faWa?".

Ammi ta Wan yi shiru sannan ta ce "Yarinyar nan ta zarce duk yadda nake zato, ko da ba ta gaya mini ba, na san ?o?ari take ta sasanta tsakanin Adam da Mahmud, tun da ni na gagara yi, ban sani ba ko ita Allah ya sa ta iya, dan haka ba abun da zan iya, yi mata Addu'a, tare da goyon baya Wari bisa Wari"

Nusaiba ta ce "Ikon Allah, ammi kuma fa haka ne"

"Ku tayani addu'a, a dalilinta sau biyu Mahmud yana zuwa in da nake, in sha Allah ko bai dawo wurina gaba Waya ba, sai an

Please Login or Register in order to submit comment