You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

Tsarkinta tayi tana yi tana kuka Sai da ta gama ta Dauko Zanin gadon nan ta kama inda ya baci ta wanke jinin haka kurum take jin bai kamata ta barsa ba.
Sai da tagama kuma ta rasa tayaya zata fita bata da kaya ko zani babu acikin Tiolet din,Kasanta Zafi yake mata asannu ma take iya tafiya Cikin kwandon kayan wankin ta fara Kokarin Duba abunda zata saka kamar wasa taji shigowarsa Lokaci Daya da fadin"Kin ga...!
Mganarsa ta makale ne sakamkon juyowa da tayi ta kallesa sai kuma ta kalli kanta kafin ta yanka ihu ta koma ta Duka tana kare jikinta cikin kuka take fadin"Don Allah ka fita..Ka fita nace..!
Haka take fada tana wani irin kuka Daman Zani ya Dauko mata Cikin kayanta ya miko mata baya ya juya mata bayan ya ijiye mata Zanin nan saman fanfon tiolet din ya Juya ya Fita yana Dafe kansa sai da ta tabbatar da ya fita sannan ta iya tashi ta dauki Zanin ta saka tana cigaba da Sharan kwallarta.
Lallabawa tayi ta Leko ta jikin kofa sai taga baya Dakin sannan ta iya fitowa? Tana tafiya sannu sannu ko Mai bata Tsaya shafawa ba jikinta na Haduwa waje Daya ta Rarrafa ta koma kan gadon ta kwanta ta Rufe jikinta da Bargo Tana jin gabobinta na ciwo sannan ga Zazzabi na neman Rufeta,Sanyi take ji gashi ta fara rawan sanyi Hakoranta na Haduwa waje Daya.
Shi kuma ihun Datake yi ne baya so sannan ga Halin Dayake ciki yasa ya bara mata Daki ya koma Falo ya Dunkule saman kujera zazzabin bai Damesa bama yadda kansa ke wani Saramai shiyasa ya kasa tashi yaje ya Duba Amina Idanuwansa Biyu aka kira Sallar Farko na asuba yana kwance Cikin matsanancin ciwon kai sannan ga faman kokuwa da Numfashinsa yasa ya kasa tashi ballatana ya Duba Amina sai da yaji an Fara kiran salla na Biyu awasu masallatai ya iya Rarrafawa ya tashi, yana cikin wani Hali Sakina ta Cutar daahi yanzu da Dakinsa na Bude ko panadol sai ya sha sannan yana da mganin mura tunda baya rabo da yin mura Lokaci bayan Lokaci.
Sai alokacin ya koma Dakin Daya baro Amina Halin daya isketa sai yaji nasa ma ba komai bane koda ya yaye bargon Jikinta ya jike da Zafin Zazzabi sannan ta kasa barci sai jan Numfashi take daya taba jikinta sai da hankalinsa ya tashi bai Tsaya ba ya Fada Tiolet ya Dauro alwala ya tafi yana kallon Amina Dake neman shidewa rasa ya zai yi da ita yayi ba Mota a hannunsa gidan Baba mallam ya barta sannan key din na wajen Jafar.
Kuma yanzu ba lalle ya samu abun hawan da zai kai su asibiti ba,Shiyasa ya karisa gareta ya Ciccibota saman jikinsa yana fadin"Amina ki yi hakuri kin ji ko..!
Ba mota a hannuna sannan yanzu asuba ne ba lalle mu samu abun hawa ba balle na kaiki asibiti..!
Amina hannunsa ta kamkame sai kuka Hawaye na bin wasu shima Riketa yayi gam Hannu Daya kuma yana Faman share mata hawaye gabadaya ya shiga wani yanayi tsausayinta ya kamata ganin yadda Take neman shidewa sai ya Tsorata ammh bai bar natsuwarsa ba sai ya shiga Tofe ta da addu"a yana Shafa mata a goshi zuwa kirjinta cikin ikon Allah sai ta Fara Sakin numfashinta asake bai daina mata addu"an samun Sauki ba har barci ya fara Fizgarta aransa yasani ko yunwa sai ya mata Illah Shima yunwar har da ita ta sashi yake jin jiki

Ganin ta samu barci yasa yana ji ana Sallar asuba ya kasa tashi Saboda Duka Amina tana kan jikinsa ne shiyasa bai yi kokarin tashi ba har aka idar da sallar asuba sai wajen karfe shida ta farka da kuka lokacin Har gari ya waye ga Haske nan ta Window din Bedroom din.
Bai Tsaya ma wani Lallashinta ba yace"Amina ki bar kukan nan kaina na kara Daukan zafi wlh..Bari nayi sallah muje asibiti..!
Haka ya koma ya kwantar da ita ya Isa gabas ya tada sallar ko kafin ya Idar Amina ta cika Dakin da kuka Dole yana idarwa ya mike yana neman mata wani Hijabin da kayan da Zata saka.
Doguwar riga ya Daukomata Amina na kuka tana Faman rintse ido wai kar ya tabata ya Daka mata Tsawa yana Fadin"Dillah kima mutane shuru..Taimakom ki fa nake son nayi ko baki ga h????































!
"
#
$
%
&
'
(
)
*
+
,
-
.
/
0
1
2
3
4
5
6
7
8
9
:
;
<
=
>
?
@
A
B
C
D
E
F
G
H
I
J
K
L
M
N
O
P
Q
R
S
T
U
V
W
X
Y
Z
[
\
]
^
_
`
a
b
c
d
e
f
g
h
i
j
k
l
m
n
o
p
q
r
s
t
u
v
w
x
y
z
{
|
}
~

?
alin Da kike ciki bane..?
Jin Muryansa cikin Fada yasa ta koma tayi Gum sai hawaye shi ya saka mata kaya har pant shi ya saka mata saboda ya gansu Cikin kayanta Bra ne bai gani ba kuma bai nema ba Tunda bai ga abunda zata sama bra ba.
Ta daa ita yayi Tsaye ya Zura mata Hijabi yace tayi sallah bari yazo fita yayi zuwa Haraban gidan suka gaisa da Buzu megadi ya fita waje chan bakin Titi ya samu adaidaita suka Dawo Tare sannan ya shiga Cikin gida ya Taho da Amina Walet dinsa kadai ya Dauka wayarsa kuma yasata a chaji Tana kashe.
Sai alokacin Megadi yatuna da Sakina ta fadamai akwai wata agidan sai sannu yake jeramata cikin Hausansa.
Ganin yanayin ta yasa Umar ya Dauketa Cak sai cikin adaidaitan tana faman hawaye ba kukan Fili tunda yayi mata Tsawan nan.
Wani Asibitin kudi ya kaita likitan Dake kula da asibitin abokinsa ne Tare sukayi primary babansa ne ya Budemai asibiti yana kula dashi sun ci sa'a kuwa sun same shi acikin asibitin Lokacin da Nurse ta shiga Office dinsa ta Sanar dashi Umar bazanga? ne yazo wajensa nan da nan ya bada izinin a shigo dasu.
Halin da suka shigo da Amina yasa ko gaisawa ma basu yi da Umar ba yace ya Dorata saman gadon marasa Lafiya Dake office din ya fara Attending dinta shi kuma ya samu kujera ya zauna ya Dafe kansa..!
Daga yanayinta da kukan datake yi ya Fahimci wani abu Nurse ya kira ya Fadamata abunda zata karbo masa a phamarcy cikin Lokaci sai gata ta Dawo.
Amina tunda taga yana Hada allura ta Fara Ihu ganin da gaske ita za"ayi mawa ta fara zumduma musu ihu,Dr Ghali ya Dago yana kallon Danmallam Dake Dafe kansa yace"Bazanga ina ga fa muna bukatarka anan wajen..!
Cikin wani yanayi ya taso kansa ma Saramai yake yi ganinsa a wajensa yasa Amina tayi tsit sai Zaran jajayen ido take cikin wani yanayi yace"Dr yi mata..Bana son hayaniya kainq kamar zai cire..,!
Dr.Ghali Cikin nazarinsa yace"Ai tunda kuka shigo na Fahimci 2 patient ne..!
Shi dai bai ce komai ba kansa ya kara Dafewa Nurse din dake Dakin ta Rike Amina da karfi aka mata allura Fadi take"Wayyo Mamanmu..Wayyo Allah na Aba..,.
Nurse din tana ta lallashinta tana Fadin"Is ok..ai an gama Haba Sister na ki Daina kuka mana an gama baki gani bane..!
Amina kukanta take yi bata Saurara ba Dr Ghali na Dariya yace"yanzu zamu ji shuru barci zata yi..!
Ko minti goma bata kara ba Amina kaji Tsit sai barci Dr.ghali ya samu Damar Nenan jijiyanta ya saka mata Drip guda Daya.
Sannan ya Sallami Nurse din Danmallan ganin hijabin Amina ya Yaye rigarta maa haka har ana ganin Cinyarta yasa ya saka hannu ya gyara mata yana kallonta cikin Lokaci daya ta Rame.
Dr.Ghali ya kallesa yana fadin"Ta samu barci kar ka damu bazanga..!
Juyowa yayi yazo ya zauna inda ya Tashi kafin yace"Bata fa ci abinci ba Tun jiya..!
Dr yace"kada ka damu in tatashi zata ci..bari na Duba ka naga meke damunka dai kafin mu gaisa..!
Umar ya Dafe kansa yana Fadin"Ciwom kai ne da mura ne sai Zazzabi..!
Tasowa yayi da abun awon Bp yazo ya aunasa kafin ya kallesa yana Fadin"Bp dinka ya yi sama kadan Bazanga..!
Sai Murar dakace shiya saka maka ciwon kai..!
Aransa fadi yake ai ihun Amina kadai ya isa bp dinsa yayi sama.
Mgani ya Rubuta a takarda ya saka Telephone ya Kira Nurse din Data fita da sake shigowa yace taje phamarcy ta karbo masa mganin ba Dadewa sai gata ta dawo da mganguna Da yawa a leda da Tambarin asibiti.
Dr.ghali ya Fito dasu yana mai bayanin nasa da na Amina sai da ya gama sannan yace"In ruwan ya kare zata farka sai ku tafi gida..Sannan kai sai ka sha naka saboda kan ya Fadamaka..!
Umar ya girgirza kai kafin yace'No sai na koma gida..,!
Dr ghali ya jinjina kai kafin yace"Bazanga aure ka kara ba labari..?
Aliyu dai mun hadu last yace min ka sake auran wata balarabiya ammh kuma sai naga wannan ba ita bace sannan kuma yarinyace wannan..!
Umar ya rasa me zai ce gashi ya Tsare shi da ido daman tun abaya ghali Haruna akwai son ji kwakwaf bakinsa yaji kawai yace"Matatace..Mallam ya auramin ita..!
Dr Ghali ya Bude ido yana yar Dariya kafin yace"i see..na zata zakamin wasa ne..Kasan na Fahimci komai fa..Gaskiya kai gentel ne Bazanga baka jimata rauni ba duk da tana karamar yarinya kayi abunda ya Dace..Sannan abu Daya ya wahalar da ita tana jin yunwa sanda abun ya Faru shiyasa ta jigata..
Ammh na mata alluran barci sannan ga Drip nan na saka mata zai taimaka wajen Dawo da Karfin jikinta ga mangunanta na pain reliver dana ciwon jiki in kun koma taci abinci mai kyau sai ka bata tasha ta kwanta ta huta..Kaima kana bukatar Hutu..Ango..Ango ya sha kamshi..!
Dariya Umar yayi kawai bai yi mgana ba,shi ya kauda mganar Amina suka shiga hirar duniya yana tambayansa yana madinan har yanzu..?
Sannan suka gangaro Hirar yan ajinsu da sukayi makaranta Tare wasu sun taka matsayin manya manya a gwannati sun Dade suna Hira har Umar yaji ya dan warware kadan awa Uku Amina ta kwashe tana barci sannan ta Farka Lokacin Drip ya kare Allah ya taimaka tatashi ba kuka ita kanta taji karfi ajikinta sai abunda ba"a rasa ba Nurse din nan ya Kira ta Cire mata Canulan ya Sallame su Danmallam ya rike hannun Amina bayan ya taimaka mata ta sanya Hijabinta ayadda ya rike ta Hannunsa Daya rike da ledan mganin sai da suka Burge Dr.ghali matuka yaga sun bala"in dacewa matukar sha"awar auran yarinya mai irin shekarun Amina ya kamasa.
Godiya Umar yayi ma Dr.ghali sukayi Musabaha Dr ghali yace"Allah ya bada zaman lafiya bazanga .!
Aciki ya amsa da Ameen,suna gabda Fita Daga offoce din yace"Kada ka manta ta dinga shiga ruwan zafi..!
Kai ya jinjinamai kafin su fice Har wajen asibiti yana rike da hannunta Adaidaita ya samar musu suka shiga basu koma gida ba sai da ya biya dasu wani Reataurant ya siyan musu abinci Takeway biyu sannan ya siya kaza da Youghourt da Hollandian sannan suka koma gida.
Yadda ya fita da ita haka ya maidota Allah ya taimaketa ta Daina kuka sai dai da gaske tasha yunwa Takeway din Jallop din shinkafa da nama yayi mata shi kuma yayi ma kansa na Tuwon shinkafa miyar agusi.
Amina duka ta cinye shinkafa ko lallashinta bai yi taci ba saboda yunwa tana ci jikinta na rawa.
Bayan ta gama ci ya bata kazan taci Rabi ta Dora da madaran youghourt bata Shanye duka ba sannan taji ta koshi shi ya zauna ya balla mata mganugunanta tasha duka ba gaddama ammh kanta na kasa bata iya Hada ido dashi.
Sai da ya rakata Daki ta kwanta Bisa gado,ya lullba mata bargo sannan ya Dawo Falo yaci nasa abincin ya sha Holladian ya Sha mgani shima ya koma kan kujera ya kwanta ba"a Dauki Lokaci ba wani barci mai nauyi ya kwashesa..!








*Janafty*
*TFZB2007*

*Ki biya ki karanta cikin Salama kiyi ma girman Allah in baki biya ba kada ki karanta sannan kuma kada ki yad'ashi..Pay N500 via jamila Umar gtb 0552179550 ko katin waya ta wannan Lambar 09069067488*

Tunda ya kwanta bai tashi ba sai karfe biyu narana da wani abu Allah ya taimakesa daya tashin ciwon kan ya sauka harda muran ma ta fara sakinsa bai ji dadi ba tun jiya yake rasa salla cikin jam"i abunda baya faruwa dashi sai da wata lalura mai karfi.
Dakin da Amina take ciki ya shiga har Lokacin tana ta barci sanin Halin Datake ciki yasa bai tasheta ba Tiolet ya shiga ya Dauro alwala ya fita Falo yayi sallah jin sa yake yi sakayau kamar ansauke mai wani kaya mai nauyi ajikinsa nan kan kujeran ya cigaba da zama yana Tunanin makomar abunda ya faru Tsakaninsa da karamar yarinya irin Amina inda Allah ya Rufamai asiri natsuwarsa acikin jininsa take bai ce baya rasa natsuwarsa wani Lokacin ba ammh bai cika rasa shi duka ba yanzu da ya zo ma Amina da karfi ya jimata ciwo har ta kai da wata matsalan da asirinsa ya Dade da Tonuwa in kuma Hakan ya faru akwai kunya da kuma zubewar kimarsa ko mallam da Hajiya baya fatan su ji labarin aika aikan daya aikata ita kanta yarinya yana ta mamakin Dauriyanta da jarumtar ta sosai ta bashi mamaki bai taba zaton zata iya Daukansa ba,Duk da abun ba wani Dadewa akayi ba sannan abu ne da yafaru dukkanasu basu da zato ko Tsammani.
Gajiya yayi da zaman shuru yasa ya tashi ya kunna Tv tashar Sunna tv ya saka yana sauraran wa"azin Dr.Jabir mai hula har la"asar tayi ya tashi yayi sallah baya so ya fita ya bar Amina ita kadai ta farka ta fara kukanta na Fama har kuma Lokacin bata tashi ba ya Lura kamar akwai mganin Dake sakata barci aciki shiyasa ya barta ta Huta ba laifi ai taji jiki tana Bukatar Hutu.
Sai wajen Biyar da Rabi na yammah Amina tatashi shima din ya shiga ya Dubata ne ya isketa zaune kan gado tana ganinsa ta dukar dakai bata son suna Hada ido shima dim kunyarta yake ji yasa ya kauda kansa yana fadin'"Ya jikin ki..?
Kanta na kasa ta amsa da cewa da Sauki Tiolet ya shiga ya Hada mata ruwan zafi ya fito yana fadin"Tashi kiyi wanka..Kiyi sallar dake kanki..Azahar da la"asar..!
Batayi gaddama ba ta Sauko daga kan gadon tana jin kuzarinta ya fara Dawowa sannan jikinta ya Daina mata Ciwo kamar dazu sai dai har Lokacin kasanta na mata Zafi Tafiya kadan kadan take yi kamar yar koyo zata wuce ta gabansa ba zato taji hannunsa saman kanta ya taba Lokaci Daya yana fadin"Zazzabin ya sauka..!?
Cikin sigar Tambaya duk da sanda ya Tabatan dukkansu sai da tsigar Jikin su tatashi da sauri ta gyada mai har jikinta na rawa ta shige Tiolet din da Sauri ya Bita da kallo.
Darduma ya shimfida mata ya ijiye mata Hijabi sannan ya koma Falo kada ya Takura mata sai bayan wani Lokaci ya Dawo ya isketa ta gama Sallah bai Tsaya ba ya fita ya Dauko mata Ragowan kazan dazu da youghourt,ya bata daman kamar ya sani Cikinta kamar an yi yasa sai dai bakinta ne ba Dadi ya tasata sai da ta Cinye ta Dora da mdaran sannan ya bata mgungunanta na Rana lum da ido ta dinga yi tana so ta kwanta nan kasa ya Hanata Cikin Sautinsa yace"ki zauna mganin yabi jikinki..Kika kwanta zaki iya yin amai..!
Amina ta ji hawaye ya kawomata cikin Sanyin murya tace"Barci nake ji..!
Mikewa yayi yana Fadin"Ba kyau barcin yammah dazu ma don naga baki tashi bane..!
Ita dai batace komai ba ta maida kanta kasa Filo ta ga ya Dauka ya Fita tana ganin haka ta kwanta saman Cafet ba zato ta ga ya sake dawowa Saboda kada ya ganta yasa ta mike da Saurin da sai da kasanta ya amsa ta Cije baki tana fadin"Wash..!
Kallonta yayi kafin yace"Sannu..Ki taso muje falo ki zauna..yammah tayi kwanciyar bata da amfani..!
Bataisa tayimai gaddama ba ammh da zai gane da ya barta anan ta zauna din bata son hada ido dashi ko zama kusa dashi ammh bai kyaleta kafa kafa ya Satasa suka koma falo kan kujera mai zaman mutum daya ya zaunar da ita bayan ya kara mata Filo shi kuma ya koma mai zaman mutum biyu ya zauna Lokaci daya ya maida kansa wajen kallon abunda ake haskawa a Qur"an tv Saudi domin ya sauya tasha.
Bai kara ma ko kallon barayin Amina ba sai chan ya duba barayinta sai yaga tana barci a zaune mirmishi kawai ya Saki yana da tabbacin mganin akwai mai sa wannan barcin bai tasheta ba sai da aka kira sallah bayan ya Dauro alwala yace taje daki tayi alwala tayi sallah zai tafi masallaci ya dawo Daganan ya fice.
Kamar yadda yace haka tayi sai bayan data idar da sallar shuru shuru bai Dawo ba ta fara jin tsoro ita kadai agida Falo ta koma ta Rakube kan kujera tana Zaran ido abu kadan ke sakata kuka yanzu sai kuka Allah ya Taimaketa akwai wutar nepa.
Shi kuma bai bar masallaci ba sai da ya Tsaya yayi sallar isha"i yaje Atm ya cire kudi saboda na hannunsa sun kare Allah ya taimakesa ba banki Daya garesa ba,Guda uku garesa anan gida sannan yana da Biyu achan Saudiya ba domin haka ba da Abunda Sakina ta aikatamai da kashinsa ya Bushi wato haka take so koda ya tafin yunwa ta kashe yarinyar Mutane tajamai bala'i wlh Nageria tayi kadan shi da Sakina sai ya nuna mata shi ke auranta ba ita ke auransa ba!
Restaurant yaje ya siyo musu abinci da abun sha sannan ya Dawo koda ya Dawo tara ta kusa Amina ya samu nata kuka shi ya zata ma ko ciwon ne ya Dawo ya fara tambayanta ina ne ke mata ciwo..!?
Cikin Hawaye tace"Tsoro nake ji..Ni kadai agida..!
Bai yi mgana ba illah abinci da yace ta Sauko taci ferfesun ganda ya siyo ma kansa ita kuma na kayan ciki sai Fruit salat saboda a yanayin datake ciki yasan zata ji dadinsa sai ruwa da Maltina da yawa,kuma taci sosai saboda barinta yayi ya koma Daki yayi wanka ya Sauya kaya zuwa wata Jallabiya koda ya fito ta cinye duka harda shan romo tana ganinsa ta koma ta nade waje daya kanta na kasa bai nuna ya Fahimceta ba tambayanta yayi ko ya isheta ta Daga kai Fruit salat din ya Turamata gabanta yace ta sha,cikinta ya cika yasa bata sha da yawa ba mganinta ya bata ta sha bayan ta tabbatar mai da tayi sallah yace taje ta kwanta kamar ya sani barci take ji ammh sai ta kasa tafiya Tsoron kwanciya take yi ita kadai ganin haka yasa yace mata ta je in ya gama abunda yake yi zai shigo..!
Dalilin dayasa tatafi taje ta kwanta kenan ba jimawa sai gashi ya shigo shima kadan yaci gandan ya sha mgani nan kasa ya shimfida bargo ya kwanta Alokacin har Amina tayi barci batama sani ba shi ya cire mata Hijabin Jikinta data kwanta dashi Saboda tasha iska ko motsi batayi ba bayan ma mgani ya Lura tana da nauyin barci.
Shima yana kwanciya bai Dade ba sai barci saboda na muran yana saka barci karfe hudu na asuba ya tashi yayi wanka ya fice zuwa masallaci sai 6 ya dawo ganin Amina bata da Niyar tashi ya tasheta yace tayi sallar kamar mashayiya haka tatashi tana Idar da Sallar ta koma ta kwanta tana samun Hutu sosai.
Shi kuma yana falo yana kallon labarai wayarsa tun jiya ta cika ammh Hakanan yaki kunnata baya so ma wani yasan yana nan Tafiyarsa shekaranjiya bata samu ba sai yau,Sai wajen 8am na safe ya leka Amina tana ta barci bai tasheta ba ya shiga Tiolet kayan data tara a Kwandon wanki ya kwashe harda zanin gado yaso ma ya Kira mai musu wanki ne sai kuma ya fasa,Gwara ya wanke su da kansa yasan in ya tafi bai wanke ba akwai matsala Amina bata san ciwon kanta ba Tukunnah ko kuma yace ba"a koyamata ba Daga yanayin yadda bata iya komai sai tace Mamanmu ko Hamida ke mata Daga gani su suka batata ammh ace kamar ta ace batasan gyara ba sai kazanta.
Ta harabn gidan akwai wata Kofa inda suke da famfo da tankinsu na ruwa nan ne sukayi wanki ko shanya in wani abu ya faru na gaggawa,nan ya kwashe kayan ya fita dasu Allah yasa Megadi na Dakinsa bai gansa ba ba Omo kwata kwata agidan sai da ya Fita ya siyo ya Zage ya wanke zanin gadon nan tas da kayan Amina pants dinta kuma Data wanke basu fita ba ya Zubar a Bola domin bazai iya wanke mata ba, ba domin yana kyamarta ba yana da kyamkyami sosai ne sosai bazai iya wankewa ba,Ammah ai karshen kyamkyami kuma ai ya kare tsakaninsa da Amina tunda mai afkuwa ta riga ta afku

Abun da ya kusa bashi Dariya Har da Vests cikin kayanta shi yaushe Rabon da ya ga ana sa Vest aransa yace shi ne madadin Bra dinta shi kadai yana wankin yana Dariya har alokacin in ya Tuna Haduwarsa da Amina sai yaji wani iri acikin Ransa yanayi ne da bazai iya Fasaara shi ba ammh yaji matukar mamakin yanayin daya shiga Lokacin kasancewa da ita ko shi yasa Aliyu ke son auran irin su masu kananun shekaru..? Yadan gano sirrin kadan duk da Abun bai wani Samesa Yadda yake so har yaji ya ishesa ba an Dai Taba kawai an bari shima Tabawan kamar kudirin Allah ne.
Tas ya wanke su ya Daureye ya shanya su saman igiya sannan ya koma Cikin gida ya Zage ya gyara falon ya Share saboda duk yayi kura saboda isar da akayi shekaran jiya..
Dakin da Amina take ciki ya koma har Lokacin tana barci Zagewa yayi ya shiga Tiolet ya wanke shi Tas ya zo kuma ya gyara Dakin ya share duk ya Gaji bayansa har ciwo yake yi bai zauna ba wanka ya shiga yayi ya fito ya Saka Jallabiya baka ya Dauki walet dinsa ya fita yaje ya siyo musu abinci da katan din Faro sai na maltina Saboda Amina da kuma Tafiyarsa.
Sanda ya dawo ta tashi Daga barcin Kuma tayi wanka batare da yace mata ba Sai dai kayan jiya ta maida sai yace ta Cire ta sauya wasu ita daman tayi wankan ne saboda ta Lura yadda yake son wanka kamar kwado koma batayi ba sai yace tayi shiyasa tayi ammh yaushe zata jure wannan aikin kamar wata yar ruwa..!
Atamfa ta saka Riga da Sikat sai Alokacin yake ganin Rashin girman Jikinta tsawo dai gareta ba Kiba,Ammh a shekarunta in da tana da manyan gabbai da Tuni tayi Jiki Tunda Hamida da Hanne sun fita Girma yan kirjinta yake kallo kamar yayi Dariya abun chan manne Lalle kwaila ce Tabbas kwailace ya aura kuma kwailan nan ne ta Daukesa Tsab Allah mai iko domin ya yarda da akace abun ba daga shekaru ne ko Girma ba..!
Chiips ne ya siyo mata shi kuma Ruwan zafi yace su bashi achan yazo dashi ya sha Tea da buredi ita kuma ta Dora da maltina tayi gatsa ta sha mgani da ruwa yace taje ta kwanta Haka ta mike tana Tafiya sannu sannu ya Bita da kallo Hankalinsa ya kwanta ganin har tafiyarta ta Fara Daidaita ya Fara Tunanin in ya tafi yau Amina bazata iya zama agidan nan ita kadai ba ita kuma wanchan baisan yaushe zata Dawo ba..!
Shi kan shi akwai gajiya ajikinsa yasa ya kwanta saman kujera sai barci sai gabda azahar ya farka Sauri Sauri yayi alwala ya tafi msallaci bai Tsaya ba Illah abinci da siyo ma Amina da kayan su Fruit ayaba kankana lemo da Sauransu koda ya dawo ta tashi tayi sallah tana kwance ammh ba barci take yi ba.
Inda yayi wanki ya koma ya kwashe kayan Tunda sun bushe ya kawo su Falo ya zauna ya ninke mata sannan ya Shigar mata dashi har Cikin Wardrope ya saka mata yana Fadin"Mai wanki duk bayan sati daya yake zuwa karba..Ki rika Hada kayanki wadanda suka kamata banda Undies nasan ba hankali kika cika ba sai ki Hadamai da Vest dinki..!
Kunya ta kama Amina taji kamar ta Nitse shikenan ita kuma ya gama ganin komai nata Zanin gadon ya Ciro ya kalleta yana Fadin"Tashi na Shimfida..Kije falo na siyo miki abinci da Fruit..!
Kamar zata fita sai kuma ta fasa ta kallesa yana kakkabe gadon zai shimfida Zanin gadon tace muryanta kasa kasa"Kawo na shimfida..!
Ko kallanta bai yi yace"Ki wuce nace..!.
Da sauri ta wuce har tana Hardewa sai da taji wani iri a kasanta duk da ya fara warkewa sosai ta ke tsarki da Ruwan zafi tana gani a littafan Hausa in haka tafaru kuma tana so ta warke shiyasa batayi wasa ba sannan kuma Ai da sukaje asibiti Dr haka ya fadarmuau hakan.
Tana fita ta jawo ledojin priderice sai kayan Marmari? Ayaba

Please Login or Register in order to submit comment