You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

bai dawo ba zata Biyosa bai hanata ba yace tazo ammh ta sani nan zata zauna itama bai kuma fadamata ga shi dawowa ba ya riga ya gama Shakan takaicin su gabadayansu ba Sakinar ba,Ba sarood din ba dukkansu ba kwanwar lasa bane,A baya sai yake ganin Sarood mai Hakuri ashe itama kyallece haka kawai ya fadamata ya Datse kiran yayi Rantsuwan in har tazo wlh sai dai ta Dauwama a Nageria ita da Madina sai da ziyara ai shima ba kasarsa bane cin arziki yake yi shi yanzu Damuwarsa daya yadda Hajiya ta Dage sai ya nema ma Amina muhallin Zama a Madina Tsakani ga Allah zai Takura baisan ta ina ma zai Fara ba kuma yadda Hajiya ta kafe din nan ko mallam bazai iya Tankwasata ba shima baya so ya fara Saba Umarninta tunda bata taba katsalanta kan sha"aninsa da matansa ba wannan ma Saboda yar gold ce.
Sakina ganin yaki bi ta kanta yasa ta fara jan Hanci tana fadin"Yanzu Habibi haka zaka tafi ka barni sai bayan wata bakwai ka dawo..?
Kana ganin ko ta bangaran addini kayi Daidai kenan..?
Suna Cikin Bedroom dinsa ne yana zaune gefen gadonsa tana sanan Cafet yayi mata kallon sama da kasa kafin ya Dauke kai Sakina ta riga ta tabbatar ma kanta bazai taba Sauya Ra"ayinsa ba.
Shiyasa ta mike tana fadin"Shikenan kasan dai ni macece kuma in da Hakki a kanka..In sha"awata tatashi Watarana har na cutu kai da Allah Umar..!
Ta karishe fada tana jan majinan kuka,har ta fice yana kallonta kafin yaja karamin tsaki bata san shi bane sai yanzu zata san shi ko ajikinsa komawa yayi ya kwanta yana jinsa kamar akan kaya ya kosa ya Bude ido ya gansa a madina matsalan Sarood karamace tsakaninsu ne ya lura in bata ganin Sakina tafi Hankali da natsuwa da kuma Hakuri ammh in dai tana Ganin Sakina akusa da ita tafi korafi da kananun mganganu.

Sakina na fita Dakinta ta koma tana Shesahekan kuka ta daga waya ta Kira Anty wacce ke shashen baba mallam alokacin sun gama cin abinci kenan dukkansu yaransun fita sai su dake falon gabadayansu har da Hajiya Babba suna hira kan yadda Zaman lafiya da rashin Tsaro ya yawaita hirar Tsakanin Mallam ne da Hajiya Babba sai Haj.Uwani Haj.Nasara na gefe tana saka baki jefi jefi,Anty Amarya ne keda Mallam aranar shiyasa tana gefe tana kallonsu bata saka baki daman tana da yawan ware kanta acikinsu
Wayarta na Hannunta sanda kiran Sakina ya shigo sai taki Dauka sai da taga Kiran yaki ya kare ne sannan ta tashi ta fita ba wanda ma ya lura da ita sai Hj.uwani da take ta sakin munafukin Murmishi Domin duk wani Motsin Marliya ai a tafin Hannunta take duk ta gama kokarin nata sai ya tashi a banza..
Sai da ta isa shashenta sannan ta Daga kiran Sakina Dayaki karewa Cikin Fada tace"Miye haka sakina..?
Kina kirana da wannan daran in Kika bada Kofa aka ganemu fa..?
Kuma mijinki na gida in ya fara Zargina fa..?
Ke meyasa baki da Hakuri ne..?
Sakina cikin kuka tace"To Anty yau fa naji yana fada in ya saka kafa ya tafi sai bayan wata takwas fa zai dawo..!
Anty Amarya tayi Tsaki kafin tace"To shi ne me..?
Sakina tayi kasa da Murya kafin tace"Anty kin manta ne..?in yana chan a ina zai ganni har auratayyah ya shiga Tsakaninmu na samu Cikin da muke Fata..?
Sai alokacin Anty Amarya ta Dawo Cikin Hayyacinta cikin Tashin Hankali ta Dafe kanta kafin tace"Kin gane duk nasan da wannan..Na fada miki mallam yace ko ya tafin zai dawo ya tafi dake Sakina ki daina Damuwa..!
Sakina tace"Nidai Anty mu tafi Taren hankalina zai fi kwanciya..!.Anty tace"To sai dai in Tuntuba ta bangaran Mallam,Ammh ta bangaran Umar kina ganin abunda yace min bazai saurareni ba in na matsa ma sai ya fara Zarginmu..!
Ki bari yau ni ke da Turakan mallan in wadanchan matan nasa sun watse zan mai mgana naji..!
Sakina tace"Yauwa Anty nagode don Allah kimai mgana don Allah..!
Anty Amarya tace"Naji zan mai mgana nace..Ki kuma ki daina Damuwa ki kuma rika hakuri kada wannan zalaman naki ya bata mana aiki..!
Da toh sakina ta amsa daganan sukayi sallama Anty Amarya tayi Tsaki afili ta Furta"Sakina tana da matsala wlh..!
Daganan Toilet ta fada domin ta sake Sabon wanka so take ta ruda mallam da nata salon yadda bazai mata gardama ba.

Achan Falon mallam kuwa bayan Fitan Anty Amarya itama Hj.nasara tayi musu sallama ta koma Shashenta ya Rage daga hajiya sai mallam Sai Haj.uwani Dake zaune gefen Hajiya Bisa kujera mai zaman mutum biyu Cikin kissarta data shiga Jikinsu gabadaya domin Hajiya ta yarda da ita Dari Bisa dari hakama mallam.
Sai da ta kalli Hajiya kafin tace"Oh Hajiya wai bawanda zai koma ya Dubomana Amina..?Tunda Suka tafi fa ba wanda yabi bayansu..!
Hajiya batayi yunkurin mgana ba Mallanlm ne ya Murmusa kafin yace"Kamar wasu yara kanana Uwani..?
In ita Amina yarinya ce ai Shi Umaru yana da Hankali na tabbata kuma zai kula da ita..Sannan ai ba ita kadai bace Sakina na tare da ita sannan ko Dazu nan mukayi sallar isha"i dashi kinga kuwa suna nan lafiya..!
Kafin tace wani abu Hajiya ta amshe mganar da cewa"Daman ina da niyyar su hanne su je mata..Na bari ne tayi ko Sati ne ta saba da chan kada su je yanzu ta fara koke koken suma ba Tunani ne dasu ba haka zasu hadu su kara Tada mata hankali..!
Haj.uwani tayi mirmishi kafin tace"Hakane kuma hajiya..ni daman nace ne ko zamu lekata Amina wlh da ita nake kwana araina Tsausayi ta bani Ranar da zasu tafi..!
Mallam yace"Da haka kowa ya saba..kema ai haka kika yi ta kuka ranar da zan taho dake daga Tsafe .!
Har Hajiya gatanan tayi wannan koke kokem ko ba haka ba Hajiya. ?
Hararan wasa hajiya ta sakar mai batayi mgana sukayi Dariya Dukkansu mallam ya cigaba da fadin"Zai koma ma jibin nan..in ya tafi su je su ganta su wunin mata sai taji Dadi..!
Hajiya tace"Eh har kwana ma sai suyi mata..Uwani ai mun girma da zuwa gidan yranmu yanzu sai dai in wani abu ya taso wanda ba"a Fata..!
Haj.uwani ta rausayar dakai kafin tace"Ammh in ya koma nan zai barmana ita ko..?
Hajiya tace"Eh nan zai barta ita da Sakina zasu zauna agidan su..!
Haj.uwani tayi mirmishin jin Dadi kafin tace"to Allah ya zaunar dasu lafiya..!
Gabadaya suka amsa da Ameen basu wani jima ba sukayi mai sallama suka fita,Hj.uwani bata koma Shashenta ba ,shashen Hajiya suka yada Zango suna hira sai hillatan Hajiya take yi tana jin wasu sirrikan saboda ko Mallam bai Fada maata abu ba zata jisa abakin Hajiya harta matakin da Hajiya ta Daukan kan tafiyar Amina madina sai da ta fada mata Hj.uwani tace"Wlh gwara haka hajiya..Yazo ya tafi da matarsa..Ni fa marliya ban yarda da ita ba..so suke su mallake Umar din shi kadai to ta Allah bata su ba..!
Hajiya tace"Ameen da yardan Allah Amina da Danmallam mutu ka raba. !
Aran Haj.uwani sai da tace ba Ameen ba afili kuma ta amsa da Ameen kafin tayi ma Hajiya sallama ta koma Shashenta Cikin Farincikin da sai da ya Bayyana akan Fuskarta
Umaima ta leka ta isketa tayi barci gyara mata Bargo tayi ta fice ta koma Dakinta,Tana shiga tayi wani Shewa lokaci Daya tana Fadin"Cikin ruwan sanyi..Burina zai cika..!
Wayarta ta Dauka Dake saman Mirror ta Kira Batula kanwata tana Dauka ta Sakin mata Shewa tana fadin"Batula albishirinki..!
Dagachan bangaran Batula tace"Goro Uwani Sikari baki farin banza..!
Dariyar Nishadi ta saki kafin tace"Tsarin da muka dora yarinyar nan su Hajiya sun taimaka mana ya tafi Daidai batula..!
Batula tace"kai don Allah..?,Bani na sha..!
Nan uwani ta warware mata komai ta Karishe da fadin"Kinga jibi zai koma kuma sai ya Dau Lokaci kafin ya Dawo..Zuwa kafin ya dawon na riga na Dorata kan Tsarin koda ma zai kulatan watarana kamar Sakinar ce haka ko ta samu zai bi Rariya..!
Batula tace"Dakyau..Hakan yayi kyau sai dai kada ki yi sakaci har adauki wani Lokaci bata hau Tsarin ba kinsan yadda zaki yi ko ta Halin kakane ...Cikin kwanakin nan Namiji fa baka shedarsa..!
Haj.Uwani tace"Naso haka sai dai tunda suka tafi batazo ba..Sannan naso na sakama Hajiya Tunanin muje mu Dubata taki bada Dama..ammh nasan zata zo jibi fa zai tafi Batula wlh ina da Tabbacin Mai mata kamar Sakina da balarabiya bazai kula Amina ba kinganta ne..?
Kwaila ce fa ga kazanta ga rashin Natsuwa ina da tabbacin bazai taba kulata ba..!
Batula tace"Shikenan tunda kina da yakinin haka..Sai dai ina tsoron kada su shammacemu..!
Haj.Uwani tace"Na yarda da aikin Mama..Ba wanda ya isa ya shammaceni Batula sai dai ni na shammacesu kamar yadda na saba..!
Dariya suka saka gabadayanau kafin su cigaba da mganarsu sun manta cewa Allah ne ke zana kaddaran bawa ba Mutum ba,abunda basu sani ba shine Komai da zai faru nan gaba Allah ya riga ya Tsara faruwar hakan Lokacin kawai ake jira.
Tabbas Uwani zata Tsammanci abunda batayi tsammani ba.
Bama ita kadai ba iri irenta ma zasu tsammanci abunda basu taba Tsammani ba..!

Anty Amarya sai da ta chanchara kwalliya,ta fesa turaruka sannan ta koma Shashen mallam cikin gayunta,Mallam bashi a falo yana cikin Bedroom dinsa chan ta Bisa ta iske ya fito wanka kenan ya sauya kaya zuwa saukakkiyar Jallabiya mai ruwan madara furfuran kansa duk yana Waje ne tana shigowa da sallama ya amsa mata yana Binta da kallo Lokaci daya da Mirmishi
Gefen gado ta nemi waje ta zauna tana kallonsa kafin tace"Mallam kayi wanka baka jira ni nazo na tayaka ba..!
Mirmishi yayi mata kafin yace"Na Hutassheki ne marliya..!
Mikewa tayi ta isa garesa ta amshi Man dayake shafawa a Hannunsa ta Lakuto tana tayasa shafawa Lokaci Daya tana fadin"Aikina ne fa..Kada kamin Rowan lada mana mallan..!
Yana kallonta yace"Mun girma marliya wannan aikin duk na Dauke muku yanzu..!
Marairaice masa tayi tana fadin"A"a nidai ban yarda mungirma ba....!
Yana yar dariya yace"Baki yarda mun girma ba..?,To in ke kina da yarintarki ai yunusa kan ya Tsufa..!
Tura bakinta tayi kafin tace"Ni dai wlh Mijina bai Tsufa ba..Yaro ne Danye Sharaf..!
Dukkansu yadda ta fadi mganar yasa sukayi Dariya atare ita ta karishe Shafa mai man suka koma saman gado suka zauna mallam ya mike kafarsa tana shafamai man zafi Saboda sun faramai Tauna kuma aki"da ne duk Dare sai ya shafa yake kwanciya
Tana shafamai suna Hiransu samasama sai da ta gama hillatansa sannan ta kallesa kafin tace"Ni ko mallam yaushe Danmallam zai koma ne..?
Kai tsaye yace mata"Jibi in Allah ya yarda yacemin jiya..!
Kai ta Rausayar kafin tace"Ya sanar dakai nan zai bar Sakina..?
Mallam yayi shuru kafin yace"A"a bai sanar dani ba..!
Anty Amarya ta gyara zama tana fadin"To ni dai baisan me ya faru Tsakaninsu ba..kasan yaran nan su yi ta shirme basa neman shawara ashe sanda zasu taho Bikin su Abida yace ta Zauna achan ta matsa sai tazo Shine fa yace bazai koma da ita ba yanzu..!
Mallam ya yi shuru yana kallonta kafin yace"Haka akayi .?
Anty amarya tace"Eh mallam ita kuma Sakinar ta damu tana ta kirana tan kukan wai na rokesa ya koma da ita bazata iya zama ita kadai ba nidai Fada nayi mata nace Laifinta ne da nace bazan saka Baki bane tace nayi maka mgana don Allah ka Rokesa ya tafi da ita..!
Har ta gama mgama yana Nazarinta Kafin ya sauke ajiyar rai yace"Naji batunki marliya kinsan Allah ni bansan ma duka anyi haka ba..Umaru da na ne ammh bana hirar iyalansa Dashi..Tsakani na dashi Hirar duniya sai kuma ta aiki in ta kama sai kuma ta Rayuwa haka ammh ni bana shiga Sha"anin ya"yana da matansu kinsani marliya..Umaru mijin Sakina ne sannan bansn meya faru Tsakaninsu ba domin ina Mahaifinsa ya gama tsara abunsa sai na kirasa nace masa ya Sauya..kina ganin hakan ba rashin girma bane..? sannan kuma shiga Hurumin da ba nawa bane tunda dai bai Tuntubeni da mganar ba..!
Ya karishe fada yana kallonta itama shi take kallo jikinta yayi sanyi domin taga ba Nasara,girgiza kai tayi cikin sanyin jiki kafin mallam ya cigaba da fadin"To kin gani bai kamata nayi mai mgana ba..Sannan ai ba ita kadai zata Zauna ba ga mamana nan itama nan zai barta sai ya sake dawo wa ki bata Hakuri ta zauna inda mijinta ya ijiyeta..!
Anty Amarya sai ta kasa mgana Shuru kawai tayi,Ganin kamar yanayinta ya Sauya ne yasa Mallam yace"Kiyi hakuri marliya..kema kada ki saka baki wannan ba Hurumin mu bane..!
Da Toh ta amsa mai tana kokarin nuna komai ba komai bane kada mallam ya Fahimci yanayinta..
Washegari ta kira sakina ta lallasheta akan tayi Hakuri da mganar Binsa ta bari in ya koma mallam ya tabbatar mata zai dawo domin ya koma da ita Tunda Sarood bata da wani amfani kamar Hoto take.
Sakina ta yarda ta Hakura ammh tace yana tafiya itama Dutse zata je tayi Sati Daya ta huce daga Bakincikin yadda zata fara zama da Amina agida Daya Matsayin Mijin su daya.

**********

Ana gobe tafiyar Danmallam Da Daddare Sakina ta Fadamai Tana so gobe in ya tafi zata je Dutse ta gaishesu,bai ce mata komai ba alokacin sai da safe domin jirginsu 12pm zai tashi zuwa Jidda,lokacin yayi wanka ya shirya Cikin Shigar jallabiya Fara da bakin wando sai Hula yana Fesa jikinsa da Turaransa na Arab Sakina ta shigo Dakin Cikin Shigarta na kwalliya kamar ko yaushe sai da ta isa kusa dashi ta karbi Turaran Hannunsa ta karishe Fesamai bayan ta gama ta maida Turaran kan Madubun Dake Dakin ta Rumgumesa tana Fadin"Zan yi kewarka Habibi..!
Shima riketa yayi na wani Lokaci kafin ya dago kanta ganin Hawaye ya Cika idanuwanta yasa ya Girgizamata kai yana fadin"Kada kiyi kuka..Ki batamin kwalliya..!
Jin haka yasa ta kara Narkewa tana mai yar shagwaban zai tafi ya barta nan ya lalace wajen ya lallashinta sai da karar wayarsa ta katsesu sannan ya Saketa Wayarsa Dake kan gado ya Dauka ganin Aliyu ne yasa ya Daga yana Fadin"Badai har ka iso ba..?
Dagachan bangaran Aliyu yace"To akace maka ni irinka ne..Gani Falon mallam muna jiranka..!
Umar yace"Ina Jafar ya iso..?
Aliyu yace"To mu da bamu da sabuwar Amarya Swt sixteen ai duk mun Hallara..!tsaki yaja kawai ya Katse kiran yana girgiza kai yana Tunanin Aliyu bai da girma sai na Jikinsa.
Sakina ta kuramai ido tana kallonsa Hannunta ya rike yana fadin"Muje su Aliyu nachan gidan mallam suna jira na..!
Marairaicewa tayi kafin tace"To haka zaka tafi baka karya ba..?
Yana kokaron Daukan jakan kayansa yace"Kinsan bana iya sakama cikina wani abu in zan hau jirgi..Kada ki Damu zan ci wani abu ko achan ne..!
Saman kafadansa ta Dora kanta tana fadin"Zaka tafi bakace min komai ba..!
Kai Tsaye yace"Name fa..?
Ta karkace kai tace"Na tafiyana Dutse mana..su Daada nake son naje na gaishesu tun fa Bikin Sadiya ban koma ba..!
Kai Tsaye yace"Kije ammh ba yau zaki Tafi ba ki bari gobe..!
Da sauri tace"Saboda mene Habibi..?
Har na kirasu nace fa ina tafe yau..!.
Hancinta yaja kafin yace"Saboda Haka nace..Kuma ba Sati zaki yi ba..kwana Uku na baki..!
Baki ta Bude tana kallonsa sai ya Rufe mata bakin da nasa ya bata sumba mai tsawo kafin ya saketa Jakarsa ta amsa ya Riko hannunta suka fito Har Falon,har ga Allah ya manta da Amina sai da ya kalli Dakin sannan ya Tuna da ita Hannun Sakina ya saki kafin yace"Jirani ina zuwa..!
Tana hararansa ya shige dakin Sarood wanda ya zama na Amina yanzu..!
Barcinta take sha sosai domin barcin da batayi bane kwana Biyu take ramasu ga Filet da mug nan har da Sauran Buredi a kasa dataci ta Rage sannan Dakin duk ya Hargitse ga Hijabai nan da kaya saman gadon bata Kwashe ba,Amina sai jiya ta Sake wanka shima kayan jikinta ne suka isheta tayi wanka ta sauya tayi Daidai kan gado tana barci Daga ita sai Zani Tayi Daurin gaba ko Riga bata saka ba.!
Kamar zai tasheta domin zarni da wari ya ishesa yasa kawai yayi Tsaki ya fice Daga Dakin yana Fitowa yaci karo da Sakina inda ya barta tana kallonsa shima ita yake kallo kafin yace"Sakina..!
Ta amsa da Na"am cikin Kaushinsa yace"Zan tafi kada ki shiga shirgin yarinyar nan ki kama girmanki..in kin yi Girki ki bata..Sannan gobe in zaki Tafi ki Fadamata domin ta Rika fitowa tana sama ma kanta wani abu..Ban son Rigima Allah in naji wani abu ke zan bata ma rai saboda ke na bar ma Amanar gidana..!
Sakina ta Tura baki kafin tace"Ni fa bazan dinga mata girki tana kwance ba..Itama ai matarkace sai ta fito ta girka nama na kaima kayi Adalci..!
Kai tsaye yace"Wannan me ta iya banda kazanta..?
Sakina ta Hura hanci kafin tace"Sai tayi kazantarta taci kayanta Daman bani zata mawa ba..!
Kai ya kada kafin yace"Allah ya kyauta sannan Hajiya tace zata koma makaranta nan Idi zai rika zuwa Daukanta..!
Aran sakina tace to ni ina Ruwana batayi mgana ba shima bai ce komai ba ganin zai tafin yasa ta rikesa ta sakamai kuka ganin haka yace ta sako mayafi su tafi gidan mallam tare jiki na rawa ta je ta Dauko hijabi suka Fice shi ya tuka Motar da kansa bayan ya sallami megadi itama Sakinar ya bata katin bankinsa guda daya suna Mota yace mata"Na amfanin yau da kullum in ya taso ke da yarinyar nan kuyi amfani dashi..kayan abinci kuma in ya yi kasa Jafar ko nasir zasu kawo..!
Karba tayi kafin tace'Ni dai ka daina Hadani????? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? 
da kazamar matarka meyasa baka bata nata ba..?
Kai Tsaye yace"Saboda kice babba sannan kuma kin Fita Hankali..kuma Amanar komai da komai a Hannunki na bari..!
Bata kara mgana ba har suka iso ita Cikin gida ta shige shi kuma Falon mallam suka gaisa Aliyu nata kallonsa yana Dariya cikin gida ya shiga yayi ma Duka matan sallama Shashen Hajiya ne na karshe yana Duke gabanta tana fadin"Allah ya sauke ku lafiya..Allah ya Tsare..!
Yana ta ansa mata da Ameen Yana shirin tashi tace"Ina wayar da nace ka siya ma Amina ka ko siya ne..?
Sai alokacin ya tuna kansa na kasa yace"Na manta Hajiya..ammh yanzu zan barma Jafar kudin zai siya mata..tunda su zasu rakani Airport shi da Aliyu..!
Hajiya tace"Ai ya shigo mun gaisa..Sannan ka shiga gidan Sa"idu kuyi sallama da shi da balaraba..!
Da toh ya amsa mata ya tashi ya fice ta Bisa da Fatan nasara.
Bai koma falom mallam ba sai ya wuce gidan Aba ya iskesa ma yana shirin Fitowa haka ya tarbesa ko zama bai yi ba sukayo sallama ya kira Mamanmu suka yi sallama Fadi take Allah ya Tsareka Umar..Allah ya bada sa"a ina Diyata Amina..?
Ina fatan tana lafiya..!
Kansa na kasa yace mata tana lafiya har Haraba ta rakosa tana ta addu"a sai da suka fice da Aba ta saki shewa kafin tace afili"Komai na tafiya daidai..yadda muka Tsara..!
Wajen goma da wani abu suka mika Hanya Jafar da Aliyu zasu rakasa Filin Jirgi,Sakina kuma har suka tafi bai kara ganinta ba.
Ita kuwa tana Shashen Anty Amarya sai da ta tabbatar da sun tafi sannan ta fito ta mata Anty Amarya sallama Domin ta fadamata ne ya barta tatafi Dutse,bata fada mata yace sai gobe zata tafi ba sanin bazata barta tatafi ba in ta fadamata gaskiya.
Gida ta koma ko ta kan Amina bata bi ba,Ta hada kayanta akwati Cike da kaya ta kulle Ko"ina harda Kitchen sai da ta kulle ta saka key din a jaka Dakin da Amina ke ciki ne kadai ta bari sai falo tayi Ficewarta Ta sanar ma da megadi zatayi tafiya ammh akwai wata yarinyar agidan ya bita da Allah ya kiyaye Su Danmallam ko Kano basu kai ba Sakina ta kama Hanyar Dutse ko ajikinta.






*Janafty*
*TFZB2005*

*Ki biya ki karanta cikin Salama kiyi ma girman Allah in baki biya ba kada ki karanta sannan kuma kada ki yad'ashi..Pay N500 via jamila Umar gtb 0552179550 ko katin waya ta wannan Lambar 09069067488*


Sun isa Filin jirgin mallam Aminu dake kano shabiyu saura na rana sai dai sun iske jirgin su Danmallam da zai tashi zuwa Jidda da misalin 12pm na rana an fasa ya koma sai 3pm na rana sakamakon Weather babu kyau an dan samu Tsaiko kadan jin haka yasa Umar yace Aliyu da Jafar su koma kawai basai sun jira ba Tunda an sauya Lokaci.
Basu wani jima ba suka mai sallama suka tafi daman da motar Aliyun suka zo kafin su tafi sai da Umar ya bama Jafar akan ya siyama Amina waya domin in ya sake yatafi bai siya ba Kashin shi ya bushe wajen Hajiya shi kanshi Jafar yayi mamakin jin yace har da layi zai siya mata ya mata Rigister.
Sun koma gida da Labarin Tsaikon da aka samu su maallam suka bisa da Fatan Alheri Aliyu bai tsaya ba Daganan yayi sallama dasu mallam ya Dauki hanyar Dutse..

Amina bata san wainar da ake toyawa ba,sai da ta gaji da barci sannan ta tatashi shima kiran sallar azahar ya tasheta da ake ta kwalawa a wani masallaci dake kusa dasu sannan ta iya tashi gabbanta duk sun gaji Tsami ma kafafunta ke mata sosai,Dakyar ta iya mikewa taja jiki ta shiga Tiolet ta Sha ruwa a famfo sannan tayi alwala tazo tayi sallah sai dai kuma yunwa take ji,Ammh duk da haka bata fita ba ta koma ta kara nadewa a Tunaninta Sakina zata kawo mata kamar yadda ta saba sai har wajen uku saura na Rana bataji motsin kowa ba cikinta har ya fara Curewa waje daya yana mata Rugugi.
Tunawa da tayi sakina ba Imani gareta ba Daga ita har megidan sai su barta ta mutu basu da asara shiyasa ta mike ta taimaki kanta kayan datayi amfani dasu da safe ta Dauka ta fita zuwa Falo tana leken sakina sai dai bata ganta ba ko motsi ma babu agidan.
Bata gama mamaki ba sai da taga Kitchen a rufe sannan Hankalinta ya tashi,Sai alokacin ta Lura duka Dakunan suna kulle ne mamaki ya kara kamata to ina yan gidan suka shiga ne..?
Tabe baki tayi daga baya aranta tace ina Ruwanta dasu sun dade basu tafi ba suma shekara waya damu..!
Nan saman Dining ta watsar da kofin da Filet din,kamar zata koma daki sai wata zuciyar tace mata bafa kowa agidan ki sha iska tuna haka yasa ta koma falo ta samu kujera ta zauna tana kara bin Falon da kallo tana nazarinsa baki ta tabe ko ajikinta.
Sauran buredin data rage da Safe ya Taimaketa shi ta Samuka ya cikamata Ciki,Har barci ya Dauketa nan saman kujera bata sani ba sai bayan La"sar ta tashi tayi mamakin irin barcin Datake yi kwana biyun nan,Tashi tayi ta koma Daki tayi sallah sannan ta kara fitowa Ciki dai ba abinci shiyasa duk ta kasa sukuni Allah ya taimaketa a saman Dinning Sakina ta manta da kayan Tea su Amina ta samu ta sha da Ruwan Sanyi tunda ba na zafi ta kuma Samu katon Buredi a wajen ta hada dashi taci ta koshi tayi Dam ta koma Daki aranta tana fadin kafin su dawo nayi barci Domin ni bana Tare da yunwa..!
Sai dai kuma har akayi mangariba bata ji Duriyar kowa ba sai Hankalin Amina ya fara tashi Har sake fitowa tayi ta Duba ba wanda ya Dawo ta koma ta zauna tayi Tagumi sai kuka tana Tunanin yadda Sakina da Mijinta suka zama marasa imani suka tafi suka barta ita kadai agida wannan Rashin Imani ne Allah ya isanta Bata yafe ba in wani abu ya sameta su da Allah..!
Bata kara Tsorata ba sai Dare yayi Amina tsoro ya cikata gashi nepa sun Dauke wuta Duhu ya cika gidan ita kuma batasan inda ake kunna Solar ba batama san da ita agidan ba,Ga shi Daga waje Hadari ya Hadu Farkon Damuna,sai ta kasa zama itace Dakin ta ko falo ta kasa zama sai ta zauna motsi kadan dataji sai ta mike tana waige waige ta fara Firgita sai kuka Amina Bilhakki da gaskiya take kuka saboda Tana tsoron saukan ruwa barin ma in ana iska ko tsawa,tana wannan kukan aka fara iska mai karfi winduna na kadawa da Labulai sai Amina taji kamar ta yi iska ta ganta agida Bayan mamanmu ko Hamida saboda tsoro Daki ta koma ta Dunkule kan gado tana Kuka Lokaci daya da makyarkyata Idanuwanta a kulle gam bata so ma ta bude ga ko"ina duk Duhu Hankalinta gabadaya ya tashi banda Salati da wayyo wayyo babu abunda take yi.
Adaidai Lokacin aka tsuke da ruwa mai karfi kamar da bakin kwarya,Ga iska ga Rugugin Tsawa Amina ta rasa ina zata sa kanta taji dadi gabadaya ta Tsorace,ta kamkame jikinta waje daya,ta tusa kanta cikin

Please Login or Register in order to submit comment