You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

ta miƙe ta ƙara ƙarfin AC'n

Daga nan suka fita, sashin Affan suka nufa, koda sukaje basu daɗe ba sabida sun samu Mami Bata nan bata dawo gidansu ba.

Ummi kuwa miƙewa tayi tare da cewa.
"Hibba zauna da ita. Bari inje in sanarwar Lamiɗo halin da ake ciki".

To Hibba tace. Har Ummi ta juya zata tafi sai kuma ta tsaya, jin wayarta na rigin.
Amsawa tayi da sauri ganin Umaymah ce.
Bayan sun gaisa ne Umaymah ke ce mata.
"Ya jikin Jazlaan da Aysha.
Jiya Jalal ke gaya min wai duk biyu basu da lfy".
"To Alhamdulillah jiki da sauƙin, shi kam Sheykh naga ya wore sosai.
Amma fa Aysha kam, sai hannun yayi kamar ya lafa sai kuma kiga ta fara haɗa zufa, can kuma sai ya fara tsikarinta hannun yayi zafi jau kamar wuta, sai kiga yanata karkarwa."
Cikin tsoro Umaymah tace.
"Subahanallahi, abin har hakane, to wai hannun ya.
Kumɓura ne ko me yayi".
Da sauri tace.
"Wlh kuwa bai kumburaba ciwo kawai yake mata."

"Subahanallahi, haɗani da ita".
Da sauri tace to. Kana ta miƙawa Aysha wayar.
Ita kuma ta nufi Sashin Lamiɗo.
Nan ta sanar wa Gimbiya Aminatu, a take tayi mata jagora ta gayawa, Lamiɗo abinda ke faruwa da kanta.

Tare suka koma da Gimbiya Aminatu.

Ita kuwa Aysha cikin wahala tace.
"Ina kwana Umaymah".

"Lfy lau Aysha ya jikin naki?".

Cikin sanyi tace.
"Da sauƙi".
Cikin kula tace.
"To Allah ya ƙara mana sauƙi.
Bari zanyiwa Jazlaan mgn ku tafi asibiti".

Cikin rawan murya tace.
"Umaymah ba ciwon asibiti bane bafa".

Cikin tausayawa tace.
"To bari zanyi mgna da Lamiɗo, karki damu in sha Allah zaki samu lfy kinji ko ɗiyata".

To tace tana zubda hawaye.

Tana katse kiran tayi mgna da Lamiɗo, ta gaya mishi yadda sukayi, yace to ba matsala.

Ita kuwa Ummi da Gimbiya Aminatu da Dr Kubra kusan a tare suka shigo.
Zuwa lokacin kuma zogin hannun ya tashi.
Sai jujjuya hannun takeyi tana cewa.
"Wash- wash Allah na wash Ummey na".

Shigowar sune Yasa ta miƙe tsaye gaban Ummi ta tsaya tana jujjuya kai da taune baki tana ɗan bubbuga sawunta a ƙasa.
Da sauri Ummi ta kamo hannun ta mai lfyan ta ajiye ta kan kujera.
Da sauri Dr Kubra ta matso tare da cewa.
"Subahanallahi hannun ne".
Hibba ce ta gyaɗa kai cikin zubda hawaye tace.
"Eh".

Gimbiya Aminatu kuwa gefensu ta zauna, hakane yasa Aysha ta ɗaura mata hannun kan cinyarta tare da zubda zafafan hawaye tanayi tana haɗa zufa.

A hankali Dr Kubra ta kai hannun ta kamo hannun tana mai cewa.
"To kodai kin taɓa karyewa tsohon karaya ne ya tashi".
Wani irin zillo Aysha tayi tare dasa ƙara ta miƙe tsaye gaba ɗaya jikinta karkarwa yakeyi.

Dai-dai lokacin kuma, Sheykh Jabeer ya fito cikin shigar jallabiya da al'kyabbar.

Ido ya zuba mata ganin yadda take karkarwa ga kuma hawaye dake shatata a fuskarta.
Ga zufa da ya jiƙata cakab dan azaban zafi."

Da sauri Dr Kubra ta motso kusa dashi cikin tausaya mata tace.
"Dr ko zamu wuce asibiti da itane".
Da sauri Dr Kubra da sauran duk suka zuba mata ido jin tana mgn murya na rawa take cewa.
"A a ni bazan je asibiti, bazan jeba, bazan jeba".
Kanshi ya girgiza tare da taɓe fuska kana yace.
"To ai shike nan kunji ko".

Gimbiya Aminatu ce, ta miƙe ta kamota
Zaunar da ita tare da cewa.
"Aysha zauna ko".
Kai taketa juyawa, hawaye na zuba.

Shi kuwa Sheykh Jabeer fita yayi.
Dr Kubra kuwa, cikin tausayawa tace.
"To Ummi ciwon kan da zazzaɓin kam da sauƙi ko".
A hankali tace.
"Eh sosai ma kuwa. Yanzu hannun ne kawai ke ciwo".
Numfashin ta fidda tare da cewa.
"Zan turo Dr Imam likitan cancer ne zai zo ya duba hannun."
Cikin sanyi Ummi tace to.

Daga nan Dr Kubra ta fita.
Gimbiya Aminatu kuwa Hibba ta kalla tare da cewa.
"Ke Muhibbatu kira min Umaymah".
To tace kana ta kira mata ita.
Bayan sun gaisa ne tace.
"Khadijah ki kira Jabeer kiji me zaice ayi kan ciwon yarinyar nan, ya fito ya wuce ko kallo bamu isheshiba bafa nason iya hege".
A hankali Umaymah tace.
"Kiyi haƙuri Gimbiya in sha Allah zanyi mgna dashi kuma ma nayi mgna da Lamiɗo yace gobe zai shigo da mai magani. Tunda tace bata son asibitin."
To tace kana ta kashe kiran

A wannan ranar dai haka ta wuni da hannun. in anjima ya lafa anjima kaɗan ya taso.
Haka kuwa da dare ta kwana ita da Ummi ba baccin kirki, domin kuka takeyi sosai sabida azabar da takejin.

Washe gari ma haka ta Wuni Dr Aliyu da kanshi ya shigo ya dubata.

Da yamma Lamiɗo da Galadima da Sarkin bakan masarautar suka shigo.
Bayan sun gaisane Sarkin Bakan ya duba hannun sai yace.
"Laah ba matsala ai wannan abu mai sauƙine bari yanzu zan baku mgnin sai dare in zata konta ku shafa mata a hannun.
A kuma bata tasha, da izinin ubangiji zatayi bacci lfy".
Cikin jin daɗi Ummi ta amshi mgnin tare da cewa.
"Mun gode, Allah ya kaimu daren."
Amin Amin sukace.
Kana Lamiɗo ya tashi sannan suma suka tashi suka bi bayanshi.

Shi kam Sheykh baima san anyi hakaba.

Ƙarfe takwas na dare. Ummi na zaune gaban Aysha daketa zubda hawaye tare da karkarɗa hannun.
Maganin da sarkin bakan ya basu ta kwaba da ruwan zafi kamar yadda yace musu.
Kana ta jiƙa ɗayan da ruwan ɗumi, da kuma citta guda uku.

Miƙa mata tayi tare da cewa.
"Sannu Aysha amshi kisha ko, Allah ya baki lfy".
Da sauri tasa hannu ta amshi kofin a karkace ta kafa kofin a baki ta shanye ruwan fes.
Kana ta miƙawa Ummi ƴan ƙwaryar.
Kana ta miƙa mata hannu mai ciwon cikin rauni tace.
"Gashi Ummi shafa min".
Ta karashe tana zubda hawaye.
Cikin tausayawa Hibba tace.
"Sannu Aunty Aysha".
Kai ta iya gyaɗawa.

Ita kuwa Ummi a hankali ta fara shafa mata mgnin.
Saida ta shafe hannun duka, sannan ta ɗago ta kalleta tare da cewa.
"Allah yayi mana mgni".
Amin tace.
Tare da miƙewa tsaye, hannunta mai lafiyar tasa ta tallabe mara lfyan da ta fara jin wani sabon abu na tsikararshi.
A hankali ta rinƙa taku, har taje gaban dreesing mirror.
Kana ta juyo a hankali ta dawo bakin ƙofar ɗakin.
Cikin kula Ummi tace.
"Sannu ko Aysha zoki zauna ki nitsu".
Kai ta kaɗa ba tare da ta bar zirga-zirgan ba.

Hibba kuwa ido kawai ta zuba mata, tana binta da sannu.
Cikin sanyi ta kuma juyowa hawaye na kwaranya daga cikin manyan fararen idanunta da suka juye zuwa ja.

A hankali ta fara salati tare da kiran sunan Allah.

Jikin gini ta jingina kanta tare da sakin shessheƙan kuka mai cike da azaba murya na rawa take cewa.
"Innalillahi wa innailaihi rajiun.
Hasbunallahuwani'imal wakil, la haulawala ƙauta illabillah.
Wayyo Ummey na, Wayyo Bappa na, zan mutu baku sani ba."
Wasu zafafan hawaye masu ɗumine suka zubowa Ummi saboda tsananin abin tausayi da ta gani a tare da yarinyar.

Hibba kuwa cikin kuka ta kira Umaymah tana kuka tace.
"Umaymah Aunty Aysha tanata kuka tana cewa, zata mutu Ummeyn ta bata samiba, tunda aka shafa mata mgnin da sarkim baka ya bayar bata sake zamaba sai zirga-zirga takeyi".
Cikin kiɗima Umaymah tace.
"Innalillahi. Ina Ummin ku? bata waya".
Cikin kuka tace.
"Ummi ma kuka takeyi".
A hargitse Umaymah tace.
Ki bata waya nace dan ubanki".
Da sauri ta miƙawa Ummi wayar.
Cikin raunin murya Ummi tace.
"Khadijah Aysha ba lfy, azaba yayi mata yawa fa. Ta ƙasa zaune ta kasa tsaye".
Cikin sauri Umaymah tace.
"Ina Jazlaan!?."
Cikin sanyi tace ban san inda yajeba, amman tunda magriba bai dawoba."
Da sauri Umaymah ta katse kiran
Number Sheykh tayi ta kira.
Sai dai duk layukanshi suna shiga baya ɗagawa.

Cikin tashin hankali ta kuma kiran.
Lamiɗo tayi mishi bayani.
Anan take Lamiɗo ya kira sarkin baka yace mishi, ga halin da ake ciki.

Sai ya bawa Lamiɗo tabbacin.
Eh dama zaiyi iya zafin da anjima zai lafa.

To nan Lamiɗo ya kira Umaymah ya gaya mata.
Ita kuma ta kira Ummi ta gaya mata yadda Lamiɗo ya gaya mata,
ta ɗora da cewa.
"In sha Allah gobe zan biyo jirgi inzo.
Kuma ko ban samu jirgiba Haroon zai kawoni a mota, zanzo Ummin Jabeer hankalina yayi matuƙar tashi kan matsalar nan".
Cikin kukan tausayi Aysha daketa ɗan bubbuga sawunta tana cewa.
"Wahyyy wahhyy".
Tace.
"Eh gsky kam kizo, Umaymah ɗazu ko Hajia Mama da tazo saida tayi ta kukan tausayin Aysha".
Katse kiran Umaymah tayi.
Tare da wucewa turakan Abban Haroon nan ta gaya mishi abinda ke faruwa.
Nan take ya bata izinin zuwa.

Sheykh Jabeer, kuwa sai ƙarfe sha ɗaya saura ya shigo gidan.
Lokacin kuma Ummi ta rufe ƙofar ɗakin Aysha sabida hanyar fita take kamawa.
To hakane yasa sam baiji motsin komaiba ya wuce Side ɗinsa.
Wonka yayi kana yayi nafilfilinshi sannan ya kwanta baccin.

Ummi kuwa da Aysha kwanan tsaye sukayi.
Aysha tana kuka tana zirgani.
Sai can gabanin asuba irin iskar sanyin asuba ɗin nan ta fara kaɗawane wani sassanyan baccin azaba da wahala ya saceta.
Hibba ma sai lokacin tayi bacci.
Nanne Ummi ta samu ta koma ɗakinta tayi al'wala.
Jin ana salla a masallacin ne yasa tace sai tayi salla taje ta tashesu kafin nan ta ɗanyi bacci kaɗan.

Bayan an idar da sallane.
Ta miƙe a hankali cikin magagin baccin da batayi ba, ta nufi ɗakin Aysha.
A hankali ta wuce bathroom.
Abun buƙatar yin wonka duka ta motso matashi kusa,
Hatta makilin saida ta matsa matashi bisa Brosh.
Sannan ta fito, a ta sunkuyo kan Hibba tare da cewa.
"Hibba! Hibba!! Muhibbat!!!".
A hankali ta buɗe idonta.
Cikin sanyi tace.
"Je kiyi al'wala kizo kiyi salla sai ki maida baccin".
Miƙa tayi a hankali tare da cewa.
"Ummi nayi salla".
Jin hakane Ummi ta gane kenan tana fashin salla.

Kai ta gyaɗa kana ta isa inda Aysha take.
A hankali ta sunkuyo kanta tafin hannunta ta kife kan goshinta.
pit-pit haka jijiyoyin kanta ke harbawa.
A hankali tace.
"Aysha! Aysha!! Cikin sanyi tayi ajiyan zuciya mai tsawo tare da buɗe kumburarrun idanunta a hankali.
Cikin sanyi Ummi tace.
"Ya jikin".
A hankali tace.
"Alhamdulillah".
Cike da jin daɗi Ummi tace.
"Masha Allah. Allah ya ƙara mana lfy, yanzu tashi kiyi wonka al'wala kiyi salla sai kizo kiyi baccin ko".
A hankali tace.
"To". Kana ta yunƙura zata tashi da sauri ta zaro idonta waje cikin tsoro take kallon hannun nata.
Ummi ma cike da tsoro take kallon hannun.
Ya kumbura yayi jazir.
Cikin tsoro da jin raɗaɗi cikin fata da naman hannun tace.
"Ummi kalli".
Cikin danne fargabanta, dan kada ta razanata tace.
"Yauwa ba komai kinga abin cikin ya fito ko.
Tashi kije kiyi wanka kizo kiyi salla.
Kisha tea kafin nan ki konta zuwa sha ɗaya dai sarkin baka zaizo shida Lamiɗo.

Cikin sanyi ta miƙe tana mai kallon hannun ta nufi Bathroom ɗin.
Da ido Ummi ta rakata.
Ganin ta maida ƙofar ta rufe ne yasa.
Ummi juyawa durowarta ta buɗe wata doguwar riga ta ɗauko mata mai taushi hannunta guntu kuma tanada ɗan fadi da ɗan kwalinta.
Wondon irin mai tsayuwa iya guiwa nar ta fito mata dashi sai bra turare ta fesa musu kana ta ajiye mata su kan gadon.
Sannan ta fita ta nufi kitchen.

Ita kuwa Aysha, a hankali ta tsaɓule kayan jikinta, kana ta goge bakinta, fes sannan tayi wonka.
Saidai duk abinda takeyi hannun na gefe sabida tana jin yana ɗan zuƙa da tauna.
Wurin yin al'wala ne tayi ta zubda hawaye tana tausayawa masu hannu ɗaya.

Koda ta fito a bakin gado ta zauna.
Wondon ta saka, sannan ta zura doguwar rigar dake mai faɗice.
A hankali ta sa hannunta ta ɗaura ɗan kwalin a kanta a kaikaice.
Bra ɗin kuma, medashi tayi cikin wodurob.

Da kyar tayi salla, tana idarwa.
Ummi na shigowa da kofin tea a hannunta.
Amsa tayi tasha.
Ajiye kofin tayi tare da yin gyatsa a hankali tace.
"Alhamdulillah".
Sannu Ummi tace tare da kallon agogon dake jikin ginin ƙarfe Shida da minti arba'in.
"To yanzu konta ni, bari in shiga kitchen inyi mana breakfast".
Kai ta gyaɗa kana ta miƙe ta dawo, kan gadon ta kwanta.

Ita kuwa Ummi juyawa tayi ta nufi kitchen.
Nan ta samu Saratu tazo fara aikin sukayi.

Ita kuwa Aysha, a hankali ta buɗe idonta data lumshe, sabida jiyo zafin da ta kwana dashi daren jiya, yana tasowa a hankali take jinshi.
Ɗis-ɗas sai kuma ya ɗanyi shiru.

A hankali hasken rana ya bayyana a sararin samani.
Wanda haka yayi dai-dai da bayyanan ciwon da taji jiya, ya mamaye hannunta da jikinta da zuciyarta.
Wani irin yunƙuri tayi tare da tashi zaune.
Cikin zafi tace.
"Sheehhhhhhh Wayyo! wayyo!! wayyo!!! Ummi hannuna yana dawowa."
Wani irin tsalle ta daka tare da miƙewa tsaye.
Cikin tsananin zafin da taji ya mamaye illahirin jikinta ne yasata, sakin wani irin kuka mai baiyana azabar da takeji.

Kife kanta tayi a jikin wodurob, tana bubbugashi tare da cewa.
"Innalillahi wa innailaihi rajiun."

Da sauri Ummi ta fito daga kitchen ta nufi falon Aysha, jin Hibba na rabka mata kira.
Da sauri ta iso tare da cewa.
"Suhanallali!. Aysha hannun ne kuma".
Da sauri ta ɗago hannun ta nunama Ummi shi, gaba ɗaya hannun rawa yakeyi kar-kar tamkar mazari.

Wani irin juyi tayi da ƙarfi tare da kife kanta jikin gini.
Tare da sakin shessheƙan kuka mai sauti, tana cewa.
"Wayyo Allah na, Wayyo Ummey na. Wayyo Bappa na, zan mutu".
Sai kuma ta kuma muƙewa cikin azabar rawan jiki da alamun a gigice take, cikin rawan murya tace.
"Wayyo Allah na, Ummi ku kaini wurin Bappa na ku maidani gidanmu ku kaini wurin Ummey na".
Ta ƙarishe mgnar tana wani irin tsastsafo zufa mai zafi.
Safa da marwa ta farayi tare da cewa.
Wayyoooooooo hannuna zai tsinƙe".
Sai kuma ta juya a gigice cikin kiɗima da fitar hayyaci.
Ta nufi falo, sabida yadda rana ke ƙara zafi, haka ciwon ke ƙara tunzura da ruruwa.
Da gudu Ummi tabi bayanta tana cewa.
"Shatu! Shatu!! Tsaya mana".
Amman ina kafin ta fito falon tama ita kuma ta isa babban falon.
Ganin hakane yasa Ummi da Hibba biyota a guje.
Da sauri Ummi tasa hannu ta kamo hannun ta, mai lafiyar tana cewa.
"Shatu ki nitsu ki tsaya ina zakije".
Wani irin kuka ta saka mai cike da rauni hannunta ta fizge a hannun Ummi kana ta ɗaurashi tsakiyar kanta.

Dai-dai lokacin Sheykh ya turo ƙofar falon ya shigo.
Jamil da Jalal na binshi a baya,
Cikin al'ajabi ya zuba musu ido.
Jalal da Jamil kuwa da sauri suka nufi inda suke.
Shi kuwa shigowa cikin falon yayi ya ɗan tsaya gefen hanyar fita.

Ita kuwa Aysha aza hannunta tayi tsakiyar kanta, tare da kife kanta jikin gini tana bubbugawa tare da buga sawunta tana cewa.
"Wayyoooooooo Allah na wayyoooooooo hannuna. Ummey zan mutu".
Ta ƙarashe mgnar cikin rauni, abin gwanin ban tausayi.
Hibba kam da Ummi tuni kuka sukeyi.
Hakama sara.
Ummi kuka takeyi tana cewa.
"Sheykh zata fasa kantafa zata yiwa kanta illa".
Wani irin zabura tayi ta juyo a firgice sabida wani irin masifeffen ciwo da suka da raɗaɗin da taji yana ratsa jiki da jinin da zuciyarta.
Hannu tasa ta ture ɗan kwalin kanta, tare da yamutsa gashin kanta, fit ta fice cikin haiyacinta, wani irin juyawa da sassarfa tayi ta nufi hanyar fita tare da buɗe bakinta da ƙarfi zata kurma wani irin gigitaccen ihu.

Cikin wani irin zafin nama.
Da tamkar gilmawar walƙiya Sheykh yasa hannunshi ya kamo hannunta na hagu.
Tare da fizgo ta ya tsaida ita gabanshi.
Da sauri yasa tafin hannunshi ya rufe bakinta data buɗe da niyar kurma ihun.
Wani irin fizge-fizgen azaba ta farayi tana ƙoƙarin ƙwace kanta.
Tuni su Ummi sun cika falon da kuka ganin tamkar ta zauce.
Jalal da Jamil ma tuni idonsu ya cika da hawaye tab.

Ganin yadda take fizge-fizge ne.
Yasashi janta ya nufi Side ɗinshi da ita, amman ina abin ya wuce zaton mai zato.
Ganin yadda takeyine, yasa suna shiga cikin corridor'n.
Ya ɗan juyo ya kalleta jin yadda taketa fizge hannunta.
Idonshi ya tsura cikin nata,
da sauri tayi ƙasa da kanta, tare da ƙara sakin kuka.
Ganin haka ne ya cicciɓeta ya nufi bedroom ɗin shi kai tsaye.
Yana shiga ya sauƙeta tare da maida ƙofar ya rufe ya jingina da ƙofar yana kallonta.
Ita kuwa cikin kuka da fita haiyacinta.
Ta nufi bakin ƙofar gefen ƙofar ta fara buga kanta.
A hankali yasa hannunshin ya jawota gabanshi.
Ido ya zuba mata yana kallon fuskarta data kumbura tayi ja dan yawan kuka, ga zufa daketa tsastsafo mata ga jikinta daketa karkarwa.
Taune lip ɗin shi na ƙasa yayi tare dasa hannunshi kan ƙugunta ya zagayo ƙugunta da hannun nashi kana ya jata ya mannata da jikinshi tare da ruggumet....!




🤣🤣🤣🤣 Hahaha ko ya wannan salon jinyar zata kaya?

Ko meye Ba'ana zaiyi kan jinyar Shatu?.

To ina hayaƙin daya fita ya shiga a part's ɗin masarautar Joɗa?

Anya kuwa Sarkin bakan masarautar Joɗa ba Magauta yakewa aikiba?

Shin Ɗalha mai gyaran tayis ma zuwa yakewa aiki?

Wacce nasara ce kan shiga tsakanin Sheykh da Shatu a zaman jinyar?

To wai ina lbrin Boleru ne?

Shin waye ne ya jinyaci su Junaidu wanne asibiti aka medasu?

Jalal da Jamil kam menene sana'ar su ko aikinsu?

Meyasa Shatu ke zargin Hajia Mama da Aunty Juwairiyya?

Shin menene gsky abinda Lamiɗo da Galadima ke son ƙullawa?

Menene manufar Arɗo Bani nayin kalaman da suka tunzura Lamiɗo har akayi gasar Shaɗi kuma har akayi aure?
Me suke son cimwa a masarautar Joɗa?

Su waye baiyannun da boyayyun magautan Sheykh da ahlinsa?

Me yasa Yah Jafar ke ji da Shatu?

Shin Jazrah da Batool zasu haƙura da burin ransu na son Sheykh?

Wai waye Sheykh ya gani a harami lokacin yin ɗawafin ban kwana?
Waye ya kuma gani a Airport?

To wai ina lbrin su Yah Giɗi, Seyo, Gaini? Yayun Shatu? Ina suke suna raye ko sun mutu!

Waye Boleru?

By
*GARKUWAR FULANI*


Hannunshi bisa suman kanta dake zube a kafaɗunta.
Yana karatu cikin daddaɗan sautin shi mai ratsa jiki da zuciya.
Yana mata tofi a hannun.
Ita kuma tasa hannun hagun ta.
Ta saƙalo wuyanshi ta cusa yatsunta cikin tattausan sumar dake kwance a ƙeyarshi tana maida numfashi a hankali.

Wasu irin abubuwa yakeji sunayi mishin yawo a jiki yana zaga jinin jikinshi gaba ɗaya.
Yar-yar haka yakejin tsikar jikinshi na zubawa.

Hancinsa ya ɗan cutsa kan suman kanta, ƙamshin ya ɗan shaƙa tare da lumshe idonsa yana nazari maijin wani irin sassanyan abu a zuciyarshi.

A haka bacci ya ɗauke su gaba ɗayansu.

Ummi da Saratu ne suka shiga kitchen sukayi girki
Umaymah kuma ta share mata ɗakinta fes.
Kana ta kira Jadda ta sanar mishi duk abinda ke faruwa.

Yace zai turo mai magani.

Tana gama waya da Jadda ta kira ƙanwarta Aunty Hafsat itama ta gaya mata.

Nan dai ta ɗan kwanta itama tayi bacci.

Bappa kuwa ya kamo hanyar zuwa masarautar Joɗa.
Hakama Barun ɗan aiken Ba'ana.

Sai sha biyu saura suka farka, a tare.
A hankali ya buɗe kyawawan idanunshi, miƙa ya ɗanyi a hankali tare da yin addu'a.
"Alhamdullazi ahyana, ba'adama a mautana wa ilaikal nushur".
ajiyan zuciya mai sanyi ya sauƙe tare tsurawa kwanciyar da sukayi ido, cikin sanyi yace.
"Wash tashi na gaji".
Cikin jin kunya ta ƙara lumshe idonta tare da shaƙar ƙamshin jikinshi. dan batasan ya akayi ba kuma ta yayane tazo ɗakinshi har suka kwanta hakaba har sukayi bacci.

A hankali ta mirgina gefe ta kwanta.
Shi kuwa ido ya zubawa hannun tare da ɗan tashi zaune hannunshi ya ɗan sa ya taɓa hannun nata idonshi ya zuba mata cikin nata a hankali yace.
"Ban amince ba, Sarkin baka ya sake baki wani mgnin kisha ko ki shafaba.
Bana so, tunda ya fara baki mgnin ciwon gaba yakeyi ko baya?".
A hankali tace.
"Gaba".
Kanshi ya ɗan jingina da jikin kan gadon acikin lumshe ido yace.
"Saida ya shafa miki hannun ya fara kumɓura, da ya kara ya sake ƙara kumɓura, dan haka bana so kada ki sake bashi jikinki ya shafa miki komai kinji ko?."
Ya ƙarashe mgnar cikin sigar kula

Cikin sanyi tace to.
Tana kallonshi ya sauƙa kan gadon.
Shi kuwa Sheykh Bathroom ɗinsa ya shiga.
Ya rage manyan kayan
Kana ya rage dagashi sai boxes.
cikin mamaki ya sunkuyo ya kalli boxes ɗin, jin damshi da wa kuma harbawa da Sheykh ɗinsa keyi.
Baki ya kuma tsokewa tare da cewa.
"Uhumm tooh abin har ya kai hakane?".
A haka yayi wonka kana ya fito.

Bata ɗakin shiyasa yayi shirinsa yadda ya kamata.

Kana ya fito yayi break
Sannan ya fito.

A falo ya samu Lamiɗo da Galadima da Sarkin bakan.
Cikin tsuke fuskarsa ya nunawa sarkin baka hanyar fita tare da cewa.
"Tashi kaje. Maganin ya isa haka".
Da sauri Umaymah tace.
"Gsky kam a barshi haka tunda anayi ba sauyi sai ci gama yakeyi".
Murmushi Lamiɗo yayi kana yace.
"To shike nan Khadijah."
Sai kuma ya kalli Sarkin bakan yace.
"Kada ka damu jeka kawai".
To yace kana ya fita.
Bayan ya fitane Lamiɗo yace.
"To anyi maka yadda kakeso hankalinka ya kwanta.
Amman munyi mgnar da mahaifinta yace min.
Yana zuwa da wani mai mgnin".

Shi dai gyara al'kyabbar jikinshi yayi, kana ya sallamesu ya tafi.
Daga bisani su Lamiɗo suka tafi, bayan sun tattauna da Umaymah.

Ranar ma dai haka Aysha ta wuni yanzu da sauƙin anjima sai a hankali.

Ƙarfe goma na dare Ummi ta taimaka mata tayi wonka.
Kana tazo tasa wata doguwar ribar baccin.

Hijabi ta zura a kai kamar koda yaushe.
Miƙewa Umaymah tayi tare da cewa.
"Zo mu tafi".
To kawai tace kana ta miƙe tabi bayanta.

Da mamaki take kallonta.
Ganin sun nufi Side ɗinsa.
A falo suka sameshi da jallabiya a jikinshi.
Cikin mamaki yace.
"Lfy kuwa Umaymah?".

Ajiye Aysha tayi bisa kujera kana ta juyo ta kalleshi tare da cewa.
"Lfyar kenan! gata ku kwana ana kaga zahirin yadda take kwana".

Kafin yayi mgna ma ta juya ta fita, taja ƙofar ta baya gim ta rufesu.

A hankali ta jingina da kujera tana mgnar zuci.
"Uhumm ni in Bappana yazoma gwara na bishi mun tafi tare.
Ummey ma zatayi min komai da gatana ba sai anyi ta min hakaba".

Ta gefen ido ya kalleta dan bata san mgnar ta fito fili ba.

A hankali ta miƙe kan kujerar tare da lumshe idonta.

A hankali bacci ya saceta.
Shi kuwa kallon da yakeyi tashar ƙasashen Larabawa, shi yaci gaba dayi.

Sai sha ɗaya da rabi ya miƙe yana kallonta murmushi ya ɗan yi kana ya juya ya shiga Bedroom.

Wonka yaje yayi kana ya dawo.
Ya zura jallabiya kan boxes ɗin shi bnnarshi ya cikashi bam.

A hankali ya fito falon ganin tana baccine, yasa ya koma ɗaki ya kwanta.

Sha biyu nayi ciwo ya tasheta,
Cikin bacci ta miƙe da ƙarfi tare da cewa.
"Innalillahi, wahhhhhhyoohhhhhh Shyyyyyyt".
Sai cikin kunnenshi yaji sautin.
Shiru yayi yana kasa kunne can kuma sai yaji tana.
Kuka tare da alamun tana zirga-zirga.
A hankali ya miƙe kana ya fito.
Ganin yadda ta ɗaura hannun a kaine yasashi.
Jan ɗan gajeren tsaki jawota yayi suka nufi bedroom.
Bisa gado suka zauna.
Hannun shi yasa ya tallaɓe nata.
Kana ya fara mata tofi.

Yanayi tana jin abin na lafawa,
har saida yaga ta daina shishitan.
Sannan yace.
"Kwanta to".
Cikin jin daɗi abin ya lafa ta kwanta.
Shima konciyar yayi ya bata baya.
Mitti biyar tsakani.
Ta miƙa zaune da sauri tare da cewa.
Wayyo Allah na yana dawowa."
Fuskarshi ya kwaɓe kana shima ya tashi zaune.
Hannun ya kuma jawowa.
Ya fara yi mata tofi cikin 15 minutes sai gata tana lumshe idonta alamun bacci zatayi.

A hankali yace.
"Kwanta to". Ba musu ta kwanta.
Kamar da fari bayan 15 minutes ta kuma zabura ta tashi.
Harda kuka wannan karon dan dare ya fara nisa ciwon zai fara tsananta.
Da sauri ya miƙa zaune tare da jawota ta faɗa jikinshi sabida ganin alamun guduwa zatayi.
Cikin sanyi yace.
"Yau naga ta kaina yanzu bazaki barni inyi bacci ba, kiyi addu'a mana".
Jin yadda take shirin ɓare baki zatayi kukane ya sashi.
Fara yi mata tofin still kuwa abu kam ya lafa.

Umaymah kuwa da Ummi sun kasa bacci sai kasa kunne sukayi.

Ita jin shiru-shirun ba motsinsu ba kuka bata kuma dawobane yasa suka ɗan samu nitsuwa suka kwanta bacci.

Sheykh Jabeer kuwa ranar haka suka kwana ba bacci.
Yayi mata tofi har yawun bakinshi ya kafe.

Sai asuba bacci ya saceta.
Shi kuma kawai wonka yayi yazo ya fara nafilfilinshi.
Ana kiran assalatu ya nufi masallaci.
A falo ya samu Umaymah cikin kula ta kalleshi tare da cewa.
"Jazlaan ya jikin nata ka samu kunyi bacci kuwa".
Cikin sanyi yace.
"Ni ai yau kamar jemage na kwana idona biyu bakina bai huta da tofiba.
Yanzu dai tana bacci nayi ta tashin ta ma taƙi.
ki leka ki tasheta."
Yana faɗin haka ya fice.


Sanin bazai dawo da wuri bane yasa da aka idar da sallan.
Umaymah taje ta tasheta.
Suka dawo nan Side ɗinta.
Sosai sukayi mamakin ganin hannin ya ɗan sace kaɗan kumburin ya ragu.

Da kyar aka taima mata tayi wonka tasha tea.

Shi kuwa Sheykh sai bakwai da rabi ya dawo.
Yana dawowa ya konta bacci.
Ita kuwa Aysha tuni rana na tashi ciwon na tashi.
Gashi wani irin masifeffen yunwa takeji tamkar taci babu.
cikin sauri ta miƙe, daga zaune da take da sauri Umaymah ma ta miƙe tare da cewa.
"Bismillah, ya tashi ko?".
Ganin ta nufi hanyar falonne tayi maza ta bita a baya tare da cewa.
"Tsaya Aysha kada ki fita kinji ko?".
Cikin muryar wahala tace.
"Umaymah zanje wurin Yah Sheykh ne yayi min tofi, in yamin tofi yana rage ciwon sosai".
Cikin sauƙe numfashin tace.
"To jeki".

Da sauri taci gaba da tafiya.
Tana yarfa hannunta na hagu.
Kai tsaye bedroom ta wuce.
Cikin borgo ta hangoshi konce.
Da sauri ta iso.
Hannu tasa ta saman borgon da niyar ta tasheshi.
Dai-dai kan bnnarshi dake neman hudo borgon ta sauƙe hannunta tare da kamawa.
Da nufin jan borgon.

Wani irin azabebben abune yajin ya zirta mishi daga tsakiyar ƙoƙon kanshi har zuwa kan babbar yatsar ƙafarshi, lokacin ɗaya yaji wani fitinenne abu ya diro mishi.
Jin yadda ta cabki Sheykh ɗinshi
Ido ya bude cikin magagin

Please Login or Register in order to submit comment