You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

rasu, sai aka rinƙa mata dariya ana cewa saura *Joɗa* shima ya *Dilli.*
Wato wai saura Joɗa shima ya *tafi.*
Cikin ikon Allah kuwa ya raya Joɗa ya girma.
Ya zama shine ƙarami cikin ƴaƴan sarki Sule kenan.

Bayan wasu shekaru, sai Sarki Sule yace to shi zaiyi murabus, a cikin yayanshi yace zai naɗa babban ɗanshi Madu.
Ɗan Gimbiya Falmata.
Sai ko sauran ƴan uba duk suka tashi akece to sai ayi zaɓen manyan.

To akwai ɗan Madu wanda yake mai ilimin addini dana zamani sunanshi Bala, sai ya shiga cikin masu neman mulkin ya kafa hujja da cewa.
"Babanshi Madu jahiline dan haka a bashi shine ya dace da mulkar garin.
Haka kuwa akayi aka ba Bala mulkin masarautar Fulɓe.
Dole babanshi Madu wanda shine Magajin gari ya ƙaura ya bar garin.
Tunda kinga bazai yiwuba ace yana mahaifinshi ya rinƙa serving ɗan shiba da baƙinsa ba.

Haka dai Bala yayi mulki tsawon shekaru arba'in inda Joɗa kuma yake matsayin Galadima tunda ɗan tsohon sarki ne.
To shi kuma Sarki Bala sai Allah ya azirtashi da tarin ya'ya mata ɗan shi na miji daya ne,
Sadik.
Ya bawa Sadik sarautan Sardaun.
Bayan wani lokacin sai tsoro ke rufe Sarki Bala kada fa abinda ya samu babanshi ya sameshi.
Wato kar ɗanshi bai gaji mulkiba kamar yadda sarautar ta tsallake babanshi ta dawo kanshi.
To shinefa ya tura ɗan shi Sadik wuraren sauran sarakunan ƙasar, cewa zaiyi murabus zai bawa Sadik mulkin.
To dama bisa ƙaida dole sai sarakunan sun yarda.
Cikin Sa'a kuwa duk sarakunan suka yarda sukasa hatimin amincewa a takardun.
To a kan hanyar dawowanshi ne kuma Allah yayi mishi rasuwa.
Wannan abu yayi masifar tada hankalin Sarki Bala.
Da mahaifiyarsa Gimbiya Salame, da kakarsa Gimbiya Falmata.
Saboda wannan pain ɗin mutuwar ɗan nasa, shene ya tattara yaranshi mata kab ya Aurar dasu.
Harda ƴar shekara takwas duk ya kwashesu ya aurar.
Sabida wai baya son ya mutu baiga aurensu ba.
Ya musu aure ya kuma basu sarauta.
Suka zama hakimai."

Cikin sanyi Shatu tace.
"Tirƙashi duk wannan don son mulki ne?".

Kai Ummi ta jinjina tare da cewa.
"Uhum ai akan sarauta babu abinda ba'ayi sabida matsalar sai kowa yace shi ɗan sarkine zai gada.
Sabida in basu gadaba sarautar tabar hannunsu, Shatu Sarauta masiface a zuciyar masoyansa da zasu iya komai a kanta."
Kai Shatu ta gyaɗa tare da cewa.
"To Ummi ina jinki".
Gyara zama tayi tare daci gaba da cewa.
"To in takai ce miki a ƙarshe dai Joɗa shiya zama sarki wanda shine ɗan ƙaramin a ahlin Sule.

A lokacin ne kuma sunan jihar nan ya dawo Ɓadawaya sabida.
Nunawa duniya ba haka bane duniya Allah zai iya baka zai iya hanaka.
Masarautar Fulɓe kuma ta zama masarautar *JOƊA.*
Sabida sunan sarkin kenan.
Kuna ya zama adalin sarki mai son baƙi duk inda baƙo yazo zai wuce.
Sai Sarki Joɗa ya bashi wurin zama yace mushi Joɗa wato zauna ga wurin zama kayi kasuwanci kayi kiwo ki ciya ka ciyar kasha ka shayar."
Shiyasa Jihar Ɓadamaya tayi zarra da tarin ƙabilu sabida son baƙi da basu muhallin zama a wancan lokacin kawai fili za'a yanka a baka ka zauna in Kai baƙone

To babban ɗan Joɗa shine Bubayero wato kakan Lamiɗo.
Bayan Joɗa ya rasune Bubayero ya hau kan karagar mulki masarautar Joɗa.
Ahlin Gimbiya Falmata kuma suna yaɗuwa suma buri da kwaɗayin sarauta na jiƙa a ransu duk burinsu suga yadda sarauta zata dawo ɗakinsu.
To koda Bubayero zaiyi murabus ya bawa ɗansa Nuruddeen mulki sai ya aurawa ɗansa yar bappan shi jikar Madu ɗanshi.
Sukayi aure aka naɗa Sarki Nuruddeen da matarsa yakura.
Bayan anyi aurene da shekara biyu.
Ya auro wata ƴar masarautar su Gimbiya Sumaye.
To itace tazo ta haifi Lamiɗo.
Ita waccar bata taɓa haihuwa ba.
To shima Lamiɗo sai ya auro yar masarautarsun Gimbiya Sumaye, wato Gimbiya Aminatu a matsayin matarsa ta biyu.
To Galadima da kike gani yanzu bappan Lamiɗo ne ɗan autan su marigayi sarki Nuruddeen.

To shi kuma Lamiɗo da aka bashi mulki sai aka aura mishi yar zuriyar Gimbiya Falmata itace uwar gida.
Ta haifi Baba Basiru da Baba Nasiru da kuma Baba Kamal da kuma babban yayansu Marigayi Auwalu. Sai Dr Aliyu shi kuwa mamanshi daban itama ta rasu su biyu ta haifa da Gimbiya Surayyah.

To Mamansu Baba Nasiru.
Yanzu haka tana raye amman ta haukace babu mai shiga Side ɗinta, sai Lamiɗo da yaranta. Duk wanda yaje sai tace zatayi duka, ita da bakinta take bayanin Abbansu Sheykh da Gimbiya Aminatu da Gimbiya Aisha tayiwa asiri ya dawo kanta.

Galadima da yaga ya tsufane kuma baida ɗa namiji da zai gajeshi shine.
Yacewa Lamiɗo ya naɗan babban ɗan shi Auwalu mijin Gimbiya Saudatu a matsayin Galadima.

To bayan ya naɗa shi da shekara biyu ne, ya rasu.
To sai ya naɗa Ya Jafar ɗin nan da kike gani a matsayin Galadiman Masarautar Joɗa.
Lokacin lafiyarsa lau yadda kikaga Sheykh haka yake da ibada addini ilimi nitsuwa tausayi.

Kwananshi goma a kan mulkin washe gari za'a naɗa shi ne, ya dawo haka babu mgna sabida wani babban ibtila'i da tashin hankalin ɗaya samemu.
Kuma a lokacin an kusa amishi aure sabida sarautar da za'a bashi.
To wannan shine babban mafarin hargitsi da kitimurmurar dake masarautar Joɗa a yanzu.
Dan ranar da Jafar ya zama haka akwai babbar masifar data fi wannan muni daya faru a masarautar Joɗa.
Shine abunda yayi masifar girgiza mutane.

Lokacin Sheykh yana saudia yana karatu a jami'atul Madina.
Hankalin Hajia Mama yayi masifar tashi tayi ta suma tana sakewa Umaymah kuwa da Sitti mutuwace kawai da basuyi ba, dan baƙin ciki da tashin hankalin ɗaya samemu.

To kuma tun daga nan sai duk magautan suka dena kiyayyarsu kansu Jafar da ƙannensa.
Koda Jabeer yayi karatunshi a can yayi digirinsa na biyu da PHD dinsa duk a can.
Wani sabon tashin hankalin da Jabeer ya dawo Lamiɗo yabashi mulkin GARKUWAn FULANI, nanfa Magauta sukace zasu mutu.
Dan ma mulkin na gefen yaya mata aka bashi shine abin ya ɗanyi sanyi.
To kuma ingiza gabar sunga ɗawisun masarautar Joɗa tayiwa Jabeer abinda sai sarki takeyiwa.

To kinji lbrin a taƙaice sai a hankali zaki gane komai in kina bin komai a hankali."
Numfashi mai sanyi Shatu ta sauƙe tare da cewa.
"Ummi wacece Gimbiya Aisha?".
Da sauri Ummi tace.
"Baki santaba".
Da sauri Shatu tace.
"Toh ina take?".
"Bata nan". Ummi ta bata amsa a gajarce.
Da sauri Shatu tace.
"Ta rasu ne?".
Cikin zubda hawaye Ummi tace.
"Bamu san halin da take cikiba shine babban burin Sheykh a duniya, sanin inda take".
Cikin sanyi Shatu ta kauda waccar tambayar dan ko Ummi bata amsa mataba ita ta gane matsayin Gimbiya Aisha. Haka yasa a hankali tace.
"Allah ya baiyana ta. Ya cika mishi burinsa."
Amin Amin Ummi tace tana sharce hawaye.
Cikin nitsuwa Shatu tace.
"To Ummi mene kuma banbancin mulkin gefen yaya mata dana maza".

Cikin jin bacci tace.
"Da safe ki tambayi Hibba ko Jamil zasu gaya miki, yanzu jeki shiga dare yayi bacci nakeji".
Da haka tatashi taje ta shiga ta fahimci a duddunƙule Ummi ta bata lbrin Sarkin yanzu da matsalar dake faruwa.

Washe gari da safe, bayan sunci abinci.
Ummi ta miƙe dan taje tayi walaha, Hibba kuma ta tafi sashin Juwairiyya da tun jiya da safe bata sake shigowa ba.
Jamil ne ya shigo neman Jalal da sauri tace.
"Uhum yauwa Jamil zo mana".
To yace kana ya dawo ya zauna.
Cikin nitsuwa tace.
"Dan Allah in ɗan tambayeka mana".
Jingina yayi da jikin kujera tare da cewa.
"To ba matsala Allah yasa na sani".
Wayarta ta ajiye kana tace.
"In sha Allah ka sanima.
Wai menene banbanci sarautar gefen ƴaƴan ƴaƴa mata, dana gefen ƴaƴan ƴaƴa maza".

Dariya yayi mai sauti tare da cewa.
"Uhumm kema kin shiga Masarautar Joɗa cikin kitimurmuran yanayi ko kin ratso cikin ahlin da ba'a sonmu, kin fara fuskantar ƙalubale ko".

Tashi yayi yaje ya sha ruwa kana ya dawo ya zauna ya fuskanceta da kyau a hankali yace.
"Banbancin tsakanin sarautar gefen ƴaƴan ƴaƴa maza da gefen ƴaƴan ƴaƴa mata.
Shine kamar haka.
1 Galadima (must be a prince )
2 Chiroma (crown prince)first born to the king
3 Tafida ( most be a prince )
4 Santuraki (must be a prince )
5 Sarkin dawaki ( prince)
6 Ɗan buram
7 Ɗan isa
8 Ɗan lawan
9 Durbi
10 Wambai
11 Turaki
12 Ɗan maje
13 Yarima
14 Ɗan iya
15 Majidadi.
Dan ɗagowa yayi ya kalleta tare da saƙe yatsunshi da yake naɗewa yana irga mata yace.
"Wannan duk royal family ne mostly biological sons din sarki ne wasu kuma jikokin sarki kuma kunne biyu sukeyi a rawunansu sabida su ƴaƴan sarki ne ko kuma iyayensu ƴaƴan sarki ne.
Kanta ta jinjina mishi alamun ta gamsu tana kuma ganewa.
Shi kuwa a nitse yaci ga da ce mata.
"Anan ake samin chief of staff da kuma senior councillor kamar galadima mostly shine senior councillor shine elders in royal bloodline ana samun galadima yapi sarki a shekaru kuma shi ake bama riqon gari in sarki bayanan.

Sannan duka anan sunayen dana irga miki da fari kowa zai iya yin sarki tunda daga ɗan sarki sai jikokinsa na gegen ƴaƴa maza, shiyasa su kunne biyu sukeyi a rawanunsu.

A hankali ya kalli Ummi data fito da Hijabi a jikinta ta zauna kusa da Shatu.
Tare da cewa.
"To kinji bayanin ƴaƴan ƴaƴa maza na sarki."
Kai ta gyaɗa tare da cewa.
"Na gane kuwa Ummi, yanzu gaya min na ƴaƴan yaran sarki mata kuma inji".

Gyara zama Jamil yayi tare da cewa.
"To sukuma sarautar gefen yaya mata sune.

1 Madawaki
2 Garkuwa
3 Makama
4 Majidadi
4 Waziri
5 Matawalle
6 Sarkin yaki
7 Magayaki
8 Jarma
9 Talba
10 Shatima
11 Ubandoma
12 Ɗan kadai
13 Magajin gari
14 Ɗan masani
15 Barma.
Ɗan sauƙe numfashi yayi tare da ci gaba da cewa.
All of these hakimai ne wanda sukeyin kunne daya a rawunansu.
Kuma wasu a cikinsu jikokin sarki ne ta bangaren mamansu, mum dinsu ce yar sarki kamar dai mu a Masarautar su Sitti ko za'a bamu mulki iya waɗannan za'a bamu kinga baza suyi kunne biyu ba shiyasa suke kunne daya amma suma hakimai ne manya kuma yan majalissar sarki also akwai kin makers a cikinsu.
Sai dai su cikin jerinsu babu wanda zai gaji sarautar sarki kamar dai mu yanzu bazamu gaji Jadda ba da masarautar gargajiyace sai dai da yake nasu na musulcine, in Kuma a masarautar Joɗa ne sunayen da na ƙirga miki na forko cikinsu za'a iya bamu, domin yanzu GARKUWA da aka bawa Hamma Jabeer matsayinsa yafi ƙarfin hakan shiyasa Magauta basu damuba."

Ya ƙarishe mgnar da cewa kin gane ko Aunty Shatu,
Kinga shiyasa da aka bawa Ya Jafar Galadima cikin kwana goma aka sabauta manashi.
Ana tsoron kada tarihin Sarki Bala da mahaifinshi Madu ɗan Sarki Sule ya maimaita kanshi a kan ƴaƴan ɗakinmu.
Shiyasa da aka bawa Hamma Jabeer Garkuwa mu bamu soba.
To sauƙin abin ma ɗaya ne da suga sarautar gefen ƴaƴan ƴaƴa mata aka bashi duk da shi jikan ɗan ɗan ɗansa namiji ne".

Ajiyan numfashin tayi kana a hankali tasa hannunta ta tallaɓe habarta, cikin alamun nisan zango na tunani da nazari.

A hankali Ummi ta matso kusa da ita cikin sanyi da kuma yin ƙasa da murya tace.
"Shatu ni kuma in tambayeki wani abu mana".
Kanta ta jujjuya a hankali ta buɗe baki tace.
"Na sani! Ummi nasan abinda zaki tambayeni! Zakimin tambaya ne kan menene yasa da na shiga ɗakin Yah Sheykh na suma na fita haiyacina, ko?".
Ta ƙarishe mgnar wasu hawaye masu ɗumi suna kwaranyo mata a fuskarta.
Cikin sanyin jiki ganin Ummi ta gyaɗa mata kai alamar eh.
Jamil ma jiki a mace ya zuba mata ido.
Tafin hannunta tasa ta sharce hawayenta murya na rawa alamun tana son danne kukanta tace.
"Ummi ɗakin Yan Sheykh ɗakine mai cike da hatsara a rayuwarshi.
Tabbas dan Allah yayi shi mutun ne mai ibada da imani da kekyawar zuciya, da yawan ambaton sunan Allah da zama da al'wala wlh da badan wannan nagartar da Addu'o'in da suka zame mishi abokan rayuwa suka zame mishi GARKUWA ba, kamar yadda Manzon Allah yace.
"Addu'a'u saiful muminin da tuni sun kasheshi sun sabauta rayuwarshi.
Ummi ban san komai ba kan masarautar Joɗa.
Amman dan al'farma Annabi da darajar Umaymah.
Zan taimaki Yah Sheykh iyakar iyawata.
Zan taimake shi akan abinda Allah ya bani ikon gani".
A hankali Jamil ya zamo ya zauna a ƙasa.
Yana mai jin tsikar jikinshi na tashi.
Itama Ummi zamowa tayi ta zauna ƙasa.
Hakama Shatu a hankali ta zauna gaban Ummi hannunta tasa.
Ta kamo hannun Ummi cikin muryar kuka tace.
"Ummi ku yarda dani, ku bani haɗin kai, zan tone duk abun cutarwa dake ɗakin Yah Sheykh. Bazan cutar dashi ba, zan taimake shi kamar yadda Bappa na yake bani umarni duk sanda mukayi mgn dashi.
Ummi keda Jamil ina buƙatar taimakon ku.
Amman kafin nan ki gayawa Umaymah in ta amince,
sai inyi aikin amman kada a gayawa Yah Sheykh dan bazai yarda ba."
Cikin tsoro ido cike da hawaye Ummi tace.
"To Shatu me zancewa Umaymah, me kika gani a ɗakin har ya firgitaki yasaki suma?".
Cikin kuka tace.
"Ummi kada ku tsaya bincike a kaina.
Ni dai ku yarda dani bazan cutar da kowaba na cikin Masarautar Joɗa sai wanda ya cutar da kanshi Ummi bamu da sauran lokaci mai tsawo fa, komai zai iya faruwa da Yah Sheykh".
Cikin tsoro da firgici Jamil yace.
"Ba matsala mun yarda dake, ni yanzu taimakon me zan miki?".
Cikin sauri ta share hawayenta tare da juyowa ta kalli shi kana tace.
"Yauwa Jamilu zaka samo mana mai saka tayis, yazo da katon ɗaya na tayis ɗin irin na bedroom ɗin Yah Sheykh sak da sak.

Sai kuma kayi ƙoƙarin mu samu ya Sheykh in ya fita ya wuni sai dare zai dawo".
Cikin sauri yace.
"Tayis da mai sawa ba matsala, batun in ya fita sai dare ya dawo kuma inaga.
Sai zuwa jibi ranar ne zaije asibitin gwamnatin Genaral Hospital.
To in yaje can wuni yakeyi wani lokacin sai dare zai dawo".
Cikin gamsuwa da hakan tace.
"To ba matsala.
Ummi ke kuma ki kira mana Umaymah ki sanar mata, muyi abun da saninta."

To Ummi tace kana a wurin ta kira Umaymah tayi mata bayani.
Ba wani neman ba'asi tace.
"A barta Ummin Jabeer na amince, tayi duk abinda ya dace a kan mijinta da yayanshi da ƙannenshi dama duk wani abu nashi".

Cikin jin daɗi ta jinjina kai lokacin da take jin mgnar Umaymah.

Wani irin dogon numfashi taja mai ƙarfi sai gata ta tafi luuuh kan...!



Wasa farin girki? Shatu kadafa allura ta tono garma.


By
*GARKUWAR FULANI*


Ta konta, kamar maiyin bacci kamar wacce ta suma.
Cikin mamaki suka bita da ido kana suka juya suka kalli juna,
Cikin mamaki Jamil yace.
"Ummi suma ta kumayi ne?".
Kai ta jijjiga mishi alamar a a.
Kana tasa hannun damanta ta gyarawa Shatu'n.
Kwanciyarta.
Tare da cewa.
"Bacci ne tayi".
Kai ya kuma gyaɗawa cike da mamaki yace.
"Wannan baiwar Allah'n, itama da akwai abin al'ajabi tare da ita.
Da akwai abinda yake a duhu wanda bamu sanshi ba a kanta."

Cikin gamsuwa da bayan shi Ummi ta gyaɗa kai tare da cewa.
"Na daɗe da dasa ayar tambaya a kanta, sai dai bani da mai bani amsar dole sai zaman yauda kullum zai ƙara fahimtar dani ko wacece ita.
Yanzu dai Jamil wannan mgnar ta zama sirri tsakaninmu.
Da Allah kada kowa yaji!".
Cikin nitsuwa yace.
"In Sha Allah Ummi babu wanda zaiji".

To da haka dai sukaci gaba da hira a wurin.
Cikin Sa'a baccin nata baiyi nisaba ta farka.

Lokacin sallan azahar nayi suka watse.

Bayan sunyi salla da jimawa ne, ta miƙe a hankali ta nufi ɗakinshi.
A falo ta tsaya, tana nazarin to in ta shiga ta sameshi idonshi biyu fa?
Akwai abinda take son idonta ya ƙara gani dan ta tabbatar.

Shi kuwa Sheykh yana ciki, a kwance kamar mafi akasarin lokuta, waya yakeyi da Aunty Hafsat.
Tana ce mishi ya haɗata da amryar zasuyi mgna.
Cikin sanyi yace.
"Bacci, Aunty Hafsat Bacci fa zanyi, afwan ki bari sai anjima mana".
Cikin sanyinta tace.
"Oho Jazlaan, nace ka haɗani da ita shine wannan magiyar yanzu Yezeed yazo ya nuna min hotunanta wai Hibba ce ta turo mishi.
Tamin kyau sosai, ina son yarinyar.
Zakiya ma tana amshi number ta, wurin Hibba tana kira kuma bata ɗagawa.
Jazlaan haɗani da ita nace ko!".
A hankali ya yunƙura ya tashi zaune.
Cikin sanyin baccin daya fara yi yace.
"To ɗan katse kiran in naje zan kiraki."
A hankali ya miƙe tsaye. Al'kyabbar sa ya ɗauka, tare da nufar bakin ƙofar.
Yana mai sa hannunshi cikin rigar al'kyabbar.
Har yazo bakin ƙofar bai gama sa hannun rigar ba ya buɗata da faɗi.

Ita kuma Shatu a hankali ta tura ƙofar.
Ta sako kai ciki dai-dai lokacin kuma shima ya sako kai waje.
Ba zato ba tsammani sukaji sunyi kiciɓis da juna ta faɗa cikin faffaɗan ƙirjinshi.
Cikin sauri ya sauƙo da hannayeshi dake buɗe kuma al'kyabbar na buɗe da faɗinta sanadin sauƙo da hannun da yayine sai ya zama ya sauƙe hannunshi kanta, yayi mata ƙawanya da faffaɗan al'kyabbar jikinshi ya haɗasu wuri ɗaya ya rufesu.

Wani irin harbawa zuƙatansu suka farayi da ƙarfi-ƙarfi, suna jam junansu i ziwa jikin juna tamkar mayen ƙarfe.

A hankali Shatu taji jikinta na macewa.
Kanta ta manna a ƙirjinta kunnenta na dai-dai kan ƙahon zuciyarshi.
Lumshe idonta tayi tanajin wani irin masifeffen ƙamshi turare mai daɗin shaƙa dasa baccin daɗi cikin ƙanƙanin lokaci, koda yake baccin nata baya rasa nasaba da abinda ke wujijjigata.

Shi kuwa Sheykh Jabeer, shiru yayi yanajin yadda tasa hannunta, ta zagayo ƙugunshi ta riƙe gam-gam da iya ƙarfin ta.
Sai kuma ya ɗan sunkuyo cike da mamaki yakkali fuskarta, tuni tayi bacci cikin ƴan second nin nan.

Cike da mamaki ya zubawa fuskarta kallon tuhuma.
A hankali yasa yatsunshi ya fara ɓanɓaro hannunta,
yanayi yana ja da baya-baya yana komawa cikin ɗakin.

Ita kuwa binshi take amman ba bi irin na takuba,
Cike da mamaki ya ƙara leƙa fuskarta.
Tabbas bacci tayi.
Janyeta yayi daga jikinshi kana ya saketa a hankali ta tafi zata faɗi, bai tareta ba, sai dai yasa ƙafarshi ya tare dai-dai inda yaga kanta zai bugu.
Cikin Sa'a kanta ya sauƙa kan rumfar ƙafarshi.
A hankali ya ajiye ƙafar tashi a ƙasa.
Kana ya janye ƙafarsa, kanta ya konta a ƙasa.

Cike da mamaki, ya juya ya koma can inda yake konciyar.
Bai cire al'kyabbar ba ya konta yana mgnar zuciya.
"Mutun kamar mayya, wannan baccin kuma na meye to".

A haka shima yayi baccin da yasan in bai yishiba, zaiji ciwon kai.

Kiran sallane ya tadashi.
Tanan konce har yanzu.
Al'wala yaje yayi kana ya fito ya kimtsa ya fesa turare.
A hankali yazo kusa da ita.
Ɗan sauran ruwan dake tafin hannunshi ya yarfa mata a fuska.

A hankali ta buɗe idonta, kana ta kuma lumshesu haka tayi kusan sau uku ganin hakane a hankali yace.
"Ke kasa uwar bacci tashi kiyi salla".
Miƙa tayi a hankali tare da cewa.
"To". Shiru yayi yana nazarin muryarta, ba haka muryarta yakeba.
Wannan shine abinda su Ummi basu ganeba, shi gashi ya gane a take,
Su kuwa basu gane cewa muryarna ba tata bace.

Kanshi ya ɗan juya tare da cewa.
"Uhummmm". Daga nan ya fita, ita kuma Shatu da ido ta bishi.
Yana fita ta miƙe kalle-kalle tayi a ɗakin nashi sosai har ƙarƙashin gado ta leƙe.

Tana gamawa ta shiga Bathroom nashi.

Wani irin murmushi tayi tare da cewa.
"Komai nashi mai kyau da tsabta".

Al'wala tayi kana ta fito, a falo ta samu Ummi da Hibba da alamun a nan sukayi salla.

Sosai Ummi tayi mamakin kenan, tana ɗakin Sheykh ne, murmushin jin daɗi tayi a ranta tace.
"Ikon Allah kenan".

Ita kuwa Shatu hijabin Hibba ta amsa tayi salla.
Suna zaune a nan ya shigo.
Wayarshi na kunne cikin nitsuwa yace.
"To Aunty Hafsat gata nan ɗazu bacci takeyi".
Cikin murmushin tace.
"To bata".
A hankali ya iso tsakiyar falon wayar ya miƙo mata tare da cewa.
"Aunty Hafsat ce ƙanwar Umaymah saura kiyi mata rashin ta ido".
Ya ƙarishe mgnar a hankali yadda ita Aunty Hafsat bazata jishiba.

Ita kuwa amsa tayi tare da karawa a kunne cikin nitsuwa tace.
"Assalamu alaikum".
Fuska a sake tace wa alaikissalam ɗiyata, ya gida ya sanyi".
Muryar matar sak irin ta Umaymah shiyasa cikin jin daɗi tace.
"Lfy lau Alhamdulillah Aunty ya gida da aiyuka".

"Alhamdulillah". Tace kana ta ɗora da cewa.
"Sunana Hafsat Jalaluddin Muhammad Sultan".
Cikin jin daɗi tace.
"Eh Aunty na sanki ai Umaymah ta gaya min sunanki ta nuna min hotonki da Aunty Rahma da Zakiya da Yezeed dama duk sauran".
Cikin jin daɗi tace.
"Masha Allah, to ki amshi number ta data Rahma da Zakiya a wurin Hibba, ɗazuma Zakiya taita kiranki ashe kina bacci ne".
Cikin nitsuwa tace.
"To Aunty yanzu kuwa, ngd matuƙa".
Cikin jin daɗi Aunty Hafsat tace.
"Allah ya muku al'barka ya baku zaman lafiya.
In Sha Allah zamuzo auren Haroon zaki gammu mu ganki".

"Amin Amin. Aunty Allah ya kaimu lokacin ya kawoku lfy".
Tace kana sukayi sallama.

Daga nan suka shiga kitchen.
Jamil kuwa tuni yaje yayiwa wani mai musu aikin gidansu.
Yasa ya nemi irin wannan tayis ɗin. Yace gobe da safe misalin sha ɗaya zaizo ya ɗauke shi.

Washe gari da safe.
Misalin karfe tara, Sheykh ya fito cikin shiga ta al'farma, yau ba al'kyabba a jikinshi riga da wondone sai malum-malum gariya mai kyau.
Getzner ce mai masifar kyau Brownish red color mai ɗan karen kyau da sheƙi, gariyar tasha aiki mai ɗan karen kyau da zaren surfani mai sheƙin piash color.
Hular kanshi da red and piash color, takalmin shi kuwa fatar ta kifa kalar red ɗin.
Yayi kyau sosai ya kafa hular nan cas a kanshi. Kekyawan suman kanshi ya konto gefe da gefe da ƙeyarshi sai sheƙi da ƙelli yakeyi.
Sajenshi ya kwanta lib, gashin girarsa dana gemunshi ɗan cas dashi misalin kamu ɗaya, sai sheƙi suke zubawa.
Ɗan madai-daicin bakinshi mai jajayen laɓɓa sai sheƙi sukeyi.
Yar ƙaramar jakar na'urar System ya riƙe a hannunshi, sai wani ƙamshi mai daɗin ji yake fiddawa, ɗan farin siririn Glass irin na manyan Doctors ya manna a fuskarshi kana ya fito.

A falonshi ya sameta, tana jera mishi breakfast.
Ganin zai wucene ta ɗan biyoshi a hankali ya zama suna tafe a jere.
Cikin kallon suman ƙeyarshi tace.
"You are breakfast is ready".
Bai kulata ba yaci gaba da tafiya.
Ita kuma ƙeyanshi ta mannawa harara.
A haka suka fito.
Ya sallami Ummi da Jamil da tunda suka karya bai tafiba.
Da sauri Jamil yabi bayanshi yana cewa.
"Uhum Dakta sai yaushe zaka dawo ne?".
Juyowa yayi ya kalli Jamil sai kuma yace.
"Kanada matsala ne?".
Da sauri ya jujjuya kanshi tare da cewa.
"No. I'm very fine".
yayi mgnar yana jijjiga jikinsa.
Kai ya kaɗa ya juya zai fita,
Da sauri Jamil ya kuma tambayarsa.
"Dakta yaushe zai dawone".
Cikin tsuke fuskarsa yace.
"Ban sani ba".
Daga nan ya fita, shi kuwa Jamil tsalle yayi tare da cewa.
"Yesss, Dakta Allah ya kiyaye hanya, a wuni lfy a asibiti".

Murmushi Ummi tayi tare da cewa.
"Yi maza to ka ɗauki shi".
To yace kana ya miƙe ya fita.
Sanin cewa yanzu Sheykh yana sashin Hajia Mama ne.

Haka yasa ya rigashi fita.

Ummi kuwa miƙewa tayi taje ta rufe ƙofar sabida bata son wani yazo ya shigo.
Kiran Jamil tayi a waya tace in sun isoma ya kirata a wayane zata buɗe mishi.

Tana katse kiran ta juyo ta kalli Shatu dake zaune gefenta tana ce mata.
"Yauwa to Ummi muje mu fara aikin kafin ya iso mun kusa cimma aikin."

Cikin mamaki tace.
"A a keda kikace sai an matsar da gadonshi sannan aikin tono ai bazamu iyaba. Dole sai mazan".
Cikin muryar da har yau Ummi ta kasa banbance shi da asalin muryarta tace.
"A a ba matsala Ummi muje zamu iya".
Ta ƙarishe mgnar tana yin gaba, ganin hakane yasa Ummi Binta a baya.
A hankali suka shiga falon.
Tana mai cewa Ummi.
"A nan ma an mishi wani aikin amman shi bai shiga jikinsa ba, sabida yanada Garkuwar addu'o'in da yakeyi yau da kullum.
Shiyasa duk sabbin sihirurruka basa shigarsa.
Sai dai waɗanda akayi mishi tun bai gama girma ba."
To kawai Ummi ke ce mata sabida jin kamar muryarta na canza mata.

A haka ta kuma nuna mata wani wurin.

Tare da cewa.
"Uhumm Ya Jafar suke nema, su maida majanunin kan bola sai kuma sharrinsu ya zame mishi al'khairi,
Tsawon shekaru baya mgn sai ambaton Allah. Bashi ba zunibi sai tarin lada da yake samu na karatun al'ƙur'ani da ya zame mishi abokin hira.

To ita kuma me take nema a duniya da zata cutar da baiwar Allah da ahlinta duka haka.
In banda lalaci da son duniya na miji ya lalace da bin matsafa yana sawa ana sabauta ɗan uwanshi da yayanshi."
Ita dai Ummi binta takeyi da ido da ƙafa har suka isa bedroom ɗin shi.

Ɗan lungun da ɗaya Bedside drower'n take ta shiga.
Kana ta kalli Ummi fuska a juye tace.
"Naɗe min carpet ɗin nan.
To Ummi tace da sauri ta fara naɗe carpet ɗin.
Bayan ta janyeshi da kyar ne, ita kuma Shatu.
A hankali tasa hannun damanta bisa jikin gadon ba tare da ta ɓallashi ba ko, ta cire wani abu a jikinshi ba, ta yunƙura ta tura gadon tare da cewa.
"Bismillahirahamanirahim".
Da sauri Ummi taja da baya cike da mamaki da tsoron ganin yadda take tura tamfatsetsen gadon mai ɗirkekiyar katifa da ko tura katifar kawai aikine.

Guuuuuuh haka sautin tura gadon

Please Login or Register in order to submit comment