You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register




Bataga dalilinsu na kuka ba, Wanda suke wa kuka xai dawo tasan xai dawo, xai dawo..... xai dawo haka kwakwalwarta ke bata


Sai ta fashe da dariya, duk gurin aka juyo ana kallonta, ko miye abin dariya ga Wanda akayiwa mutuwa?


'lafiyar ki kuwa? Cewar salima tana kallonta cikin tsananin mamaki,


'tor miye amfanin Kukan da kuke, baba ne kawai ya mutu banda mijina, nasan Deedah yana raye, ynxu xaku ganshi ya dawo xaiyi wanka yayi shirin xuwa masallaci bara naje na fidda mashi kayan da xai sanya a yau, ta tashi tayi ďakin sa,


Mutanen falon suka kalli juna cikin tsananin mamaki, Fulani tabi bayanta da sauri,


Ta juyo da kafadunta suna fuskantar juna,
'Kinsan me kikeyi fatyma, me kike son nunawa mutane, baki yarda da qaddara bane keba musulma bace?


'my husband is alive Dr Fulani, Kune keson kashe sa, jiya fa muna tare, yau ma munyi mgn dashi, ya roqeni gafara Kuma na yafe masa, shine fa ya suma kuke kiran ya mutu,


'Wanda ya mutu baya dawowa Iman, kada ki ruďar da kanki, ki nutsu dan Allah kada wani abu ya sami kwakwalwarki, dan Allah fatyma kixo muje falo kicigaba da yi masu addua, kinga ga yan uwanku ma suna ta xuwa.


Iman tayi shiru Kamar mai naxari sai Kuma ta dubeta,


'tell me Fulani idan Marhoom ne ya mutu me xakiji?


Sai da xuciyarta na buga ta gyara goyonta tana kallonta,


'me ya kawo wannan mgnr Kuma? Idan ma mutuwa yayi haquri xanyi nayi tawakkali ga Allah, nasan yafini sonsa Kuma nasan yafiye masa duniya daďi,


Iman ta girgixa kanta,
'you are not saying the truth Dr fulani, baxaki iya jurewa ba, bakisan xafin dana keji a xuciyata ba, bakisan ciwon da Mace take ji idan ta rasa abokin rayuwarta ba, ballantana irin nawa rashi na *babana da mijina* a lokaci ďaya, ta soma hawaye sosai,


ta juya tana ciro kayan Deedah,
'ni nasan bai mutu ba xaki ganshi sun dawo dashi,


Fulani tayi shiru tana kallonta cikin tausayawa, itama ta tsinci kanta cikin kuka sosai ta fice daga ďakin da sauri.


Haka Iman ta fito da kayansa, juyowar da xatayi tayi arba da tangamemen hotonsu dake manne a ďakin, yana rungume da Ita suna yiwa juna murmushi, sai ta saki murmushi tana faďin,


'Haba taya ma xasu ce Deedah na ya mutu, nasan xaka dawo kaxo kabasu mamaki su san cewa kana raye......




An kaisu makwancinsu an rufesu daga su sai halayyarsu sai abinda suka shuka a duniya, in hairan hairan in shairan shairan, wani abin tsakaninka ne da mahaliccinka, idan ka kasance mai tuba agaresa,


Duniya kenan....


Babu dukiya aciki, babu gida mai tsada, babu mota mai tsada, babu abinci mai tsada, babu lallausar katifa mai taushi da tsada, babu Mulkin da ake taqama dashi,


An kaika inda xaka xamo abinci ga tsutsoci, qasar da kake taki da takalmi yau kaine acikinta timbir, babu mai ceton ka aciki sai Allah, sai aikin da ka aikata a duniya, ya Allah ka tsare mu da azabar kabari, kasa muyi kyakkyawan qarshe mucika da imani Amin.


Sa'eed kuka yake sosai Idanunsa sunyi jawur, shikenan Deedah yaje ya barsu, baxasu qara ganin Deedah ba, yayi rashin aboki, Allah ka gafartawa Deedah ka Kai haske a kabarinsa kamar yanda goshinsa yayi haske lokacin da suke masa wanka,




Suna dawowa jana'iza suka nufi gidan, tun daga waje suka fara gaisuwa ga mutane birjik an shimfida Manya Manya tabarma saboda masu gaisuwa, yan uwan su Iman ne a waje da suka xo,




Kai tsaye su Dr Merah suka nufi falon Iman domin yi mata ta'aziya, tana ganinsu ta tashi da sauri ta nufesu, sai leqen bayansu take burinta taga Deedah a bayansu amma wayam,


Ta dubi Dr Merah, Dr Deen, Dr Bakori, Sa'eed, sai taga suna hawaye kowane na jin nauyin haďa ido da ita a yau, bakinsu yayi nauyi ga duk kalmar da xata fito bakinsu,


'Banga Deedah ba likita, ina kuka barshi?


Merah yayi qarfin halin mgn, Idanunsa akan nata,


'Dama Wanda ya mutu yana dawowa ne Iman? Deedah is dead, Deedah has gone and he will never come back, ya tafi ya barmu dole haquri xamuyi da wannan rashin Allah ya fimu sonsa mutuwa na kan kowa,


'wace mgn kakeyi likita, Kada kace min da gaske Deedah na ya mutu, ya tafi ya barni nida qanwata, ya tafi yabar jinjirinsa, dan Allah kace masa ya dawo, yaxo ga kayanshi ya Sanya yaje jumma'a, ta juya tana neman inda ta ajiye kayan,


Kai da kaganta kasan bata hayyacinta a ruďe take, inbashi ba, mace kamar Iman Mai kunya da kawaici, Mai haquri da tawakkali, Mai hankali da nutsuwa, yasan da hankalinta baxata tsaya gabansa tana wannan mgn ba ynda take matuqar girmamashi,




Gabaki ďaya falon suka ďauki kuka, Dr Deen ya fita da sauri shida Sa'eed baxasu jure ganinta a Wannan halin ba,


'ki nutsu fatyma, Merah ke gabanki, baxan maki qarya dan na cutar dake ba kinsani, Deedah ya tafi inda baxai dawo ba Kinsan miye mutuwa please pray for your father yana buqatar addua sosai akan Deedah, Deedah ya tafi cikin kyakkyawan qarshe fuskarsa kaďai xata Shaida hakan da ynda jikinsa yayi kyau, ki roqa masu gafara ki masu addua, please fatyma ki nutsu,


Nan da nan jikinta na soma rawa sai karkarwa take sai ga hawaye sharrrrr,


Shikenan da gaske Deedah ya tafi,


Bakinta na rawa ta nemi gurin xama da kyar tana faďin,


'Allah ya jiqansu, Allah ya gafarta masu, Allah ya haskaka kabarinsu,


Duk falon aka ďauki Amin, wasu Kuwa suka fashe da kuka......




*Babana da mijina*




©Fertymerh Xarah 💞




36




_Congratulations for the completion of ur book Rabi'atu Sk Mashi, MATATA CE, ko ina xanga Rabi'atul Adawiya? Nagode da qaunarki,_




_mistake page 35 in babana da mijina, ban sani ba ko tsananin ruďewa ce tasanya Iman sallah bayan ta haihu, it's a mistake pls._








Da kyar yaja qafafunsa yabar gidan, duk jikinsa a sanyaye yake har ya iso gidansa,


Sai da yaje ya duba mahaifinsa har lokacin barci yake kafin ya koma side ďin sa, kwanciya tayi haďe da lumshe idanuwansa, fuskarta yake gani, murmushinta wani abu ne mai girma a xuciyarsa, da alama tana matuqar son yaron ya gani a kwayar idonta don haka yayi alqawarin Kula da Ita da yaron kamar shi ya haifesa, da Wannan tunanin barci ya ďauke sa,




Sa'eed Kuwa yana xuwa gida ya sameta xaune a falonsa tana jiransa, cikin wasu irin shu'uman kayan barci, rabonta da sanyasu yana ji tun farkon aurensu, ya ďauke kansa cikin basarwa kamar bai ganta ba yayi hanyar ďakinsa ta biyosa tana faďin,


'ina kaje da wannan daren Abban Adnan,


Yau kuma har wani Abban Adnan ya samu ya raya hakan a xuciyarsa shi da ake kira da xallar sunansa Sa'eed,


Bai dubeta ba bai Kuma tankata ba ya hau gadonsa yayi kwanciyarsa fuskarsa ba walwala hakan yasa take tsoron tunkararsa Kada ya sauke fushin akanta, sai ta soma mgn a hankali,


'Dan Allah ina kaje, Allah yasa ba gurin wata kaje ba dan bansan yanda xnyi da xuciyataba,


A fakaice ya ďan dubeta cikin mamaki bai bari sun haďa ido ba ya ďauke kansa, tana sonsa ne bata iya Kula da shi,


Ganin baxai tankata ba ta kwanta a qirjinsa, da sauri ya juya mata baya haďe da Jan dogon tsaki, Hakan da yayi hankalinta yayi matuqar tashi tasan idan Sa'eed yayi mata haka to yana fushi da itane,


'kayi haquri ďaxu wasa nake ma xnyima tausa ďin,


'karki kuskura ki tabamin jiki, inba haka ba ranki xai baci... duk wannan mgnr da yake fuskarsa ba walwala,


Nan da nan ta soma hawaye tayi xaune xuruu tana kallonsa, tana gani ya tashi ya kashe wutar ďakin Kafin ya dawo ya kwanta batare da ya kalleta ba, hankalinta ya tashi sosai ta tashi tabar ďakin ta nufi nata, ranar barci a idonta sai dai barawo....


Sa'eed Kuwa barcinsa duk na Iman ne, yana tare da Iman, ya tashi yana adduar Allah ya bashi Iman su kasance tare cikin farinciki da kula da junansu.




Iman Kuwa tana shiga ďaki ta shimfide yaron, ta gyarawa fauxie kwanciyarta anan taji jikinta xafi rau, ta manta da taci abinci batasha magani ba, gefen fuskarta ma ya fara ďebe kumburi, tausayin yarinyar ya kamata,


Taya akayi fauxie ta fita wayo da dabara, Ashe surutunta bana banxa bane, sai komai yake dawo mata sabo, lallai fauxie ba qaramin namijin qoqari tayi ba dan da baba bai gayamasu komai kafin ya mutu ba da baxatasan komai ba,


Ashe da gskyr Deedah da yace fauxie ce ajalin baba, sanda yayi furucin taso ta tambayesa dalili amma ta manta, Ashe Deedah yasan baba matsafine amma bai taba gayamata ba sai Faďan da sukayi na qarshe dashi inda yake cewa, *gwanda xama da barawo akan xama da matsafi..*,


Inama Deedah ta xai dawo, xata xauna dashi a matsayinsa na barawo, tana son mijinta fiye da tunanin mai karatu,


*Babana da mijina* sune jigon rayuwata, yau babu su daga ita sai qanwarta da ďanta... ta soma waige waige a ďakin kamar xataga Deedah, dama a irin wannan lokacin yake dawowa gida, ta tashi da sauri tana kallo ta window gani take xataga motar mahaifinta ya dawo, xuciyarta ta kasa amincewa da mutuwarsu, meyiwuwa xasu dawo Gobe a tunaninta sunyi tafiya ne tadawo cikin ďakin har lokacin hawaye take,


Magani ta ďauko da ruwa taxo ta tayar da fauxie,


Kuka ta fara, tayi saurin toshe mata baki da hannu gudun kada ta tayarda jaririn,


'yi shiru karki tayarda baby, magani xaki sha sai ki koma barcin,


'anty baxan sha ba.... ta qara kwanciya idanunta a lumshe, Iman ta riqo hannunta haďe da sunkuyawa dai dai fuskarta,


'please babyn yaya, idan kinsha magani yaya will be happy, kuma xakiji sauqi kafin ki koma Skul fuskarki xata dawo dai dai, your friends will not laugh at you,


Ta buďe idanunta a hankali tana kallon Iman itama kallonta take, sai ta tashi xaune, Iman ta bata maganin tasha tana yatsina fuska kamar xatayi kuka bata barta ta kwanta ba sai da ta tabbatar ya kwanta mata, fauxie taje kusa da yaron ta riqo hannunsa ta riqa da nata,


'Anty shi hannunshi yana da laushi, yaushe xaiyi girma kamar ni muyi wasa,


'kiyi barci ba surutu na tayarda ke kiyiba, fauxie tayi shiru haďe da rufe idanuwanta bata saki hannun yaron ba, Iman ta kwanta a kusa dasu tana kallonsu, barcinta a ranar sama sama ne sai ta fara ta tashi a firgice.


*


Washe garin ranar Dr Deen tare da mahaifinsa baffa, nan yake bashi lbrn Iman, sosai ya tausayamasu sai yaji inama Xahradeen xai aureta ya kula da yaronta da qanwarta sai ya tuntubesa da Mgnr,


Dr Deen yayi shiru kafin ya dubi baffa,

'xamuyi Mgnr wani lokaci baffa, ya tashi ya fice cikin shirinsa na xuwa asibiti,


Sa'eed ma yana shirin xuwa bank salima ta shigo, ta gaidashi ya amsa fuskarsa ba walwala,


'breakfast ďin fa,
'na qoshi,
'Dan Allah kayi haquri ka yafemin,


Ya ďauki jakarsa yasa kai ya fice batare daya dubeta ba, tabisa da kallo ranta a bace tabbas idan har wata mace kesa yana mata Wulaqanci a ynxu wallahi ko Wacece sai taga bayanta.....




Tunda sassafe Iman ta shiga wankan ruwan xafi, yaran basu tashi ba harta gama ta fito, sai taji daďin jikinta sosai, tana shirinta take jiyo hayaniyar mutane tasan baxai wuce yan uwansu bane da suka xo, ita batason xaman makokin nan da duk yawanci Munapurci ake, sai ayita qananan maganganu kan mamaci, sun maida gidan kamar gidan biki ba mutuwa ba, sai fita ake da abinci da juice, jiya kaďai tana lura da yanda yanayin gidan ke tafiya, almubazzarancin yayi yawa.


Wata dattijuwace tayi Sallama ta shigo ďakin,


Iman ta amsa sallamar tana kallonta bayan sun gaisa,


'Tace Inna ai bai tashi daga barci ba,


'banda abinki fatyma shi jariri ai baya tashi barci karkiyi mamaki ma ynxu har ayi wankan a gama bai tashi daga barci ba, bani shi nan ki gani, Iman ta ďauki yaron tana kallonsa kafin ta miqa mata shi,


Tana xaune tana shan kunun kanwa fauxie ta tashi barci lokacin har angama yiwa yaron wanka ana gasa masa cibiya,


'anty nima ayimin wanka cikin robar baby,


'a'a kije dijeh tayi maki a toilet ke bakisan kin girma ba kinaso Inna taga jikinkine,


Ta make kafada kamar xatayi kuka,


'ni banaso anan nake so,
'yi haquri aje toilet ayi maki kinji, keda akewa a Jacuzzi 🛀 Ina ruwanki da robar wankan jariri,


Ta soma cire kayanta Iman bata ankaraba sai ganinta tayi cikin robar, Inna ta soma dariya, iman bata ce komai ba har dijeh taxo ta ďauketa da robar tayi toilet da ita sai daďi takeji,


Angama wankan tafito komai sai na jariri xa'a shafa mata,


Lokaci ďaya Sa'eed da Dr Deen suka xo, ta fita suka gaisa dasu kafin su wuce gurin aikinsu,


Dr Merah ma na qoqari akansu har akayi adduar qarshe, ranar komai ya dawowa Iman sabo da kyar Merah ya kwantar da hankalinta harta yi shiru,




Ranar suna yaron yaci sunan mahaifin sa Ahmed, Dr Deen, Sa'eed da Dr Merah sosai sunyi namijin qoqari gurin sunan yaron tamkar Deedah na raye, ba abinda suke nema suka rasa daga ita har jaririn da qanwarta, ba abinda xata cewa waďannan maza uku sai godiya da fatan alkhairi a rayuwarsu,


Haka rayuwa ke cigaba da tafiya, Dr Deen da Sa'eed na iya qoqarinsu na ganin sun kula da Ita tare da nuna mata soyayya,


Ba wannan ne a gabanta ba a ynxu, ba wanda takeji a xuciyarta, ba wanda take ita ba lokacinta a cikinsu bayan qanwarta da ďanta,


Sai addua Sa'eed da Deen keyi a xukatansu na ganin ta amince da soyayyarsu a shirye suke da su bata farin cikin da ta rasa a baya,


Xuwa wannan lokacin iman tasan ta rasa Deedah ďinta, ta rasa wanda takeso, farincikinta, a ynxu da ta jima bata ganshi ba bataji ďumin jikinsaba ta yarda ya mutu ya barta har abada, xuciyar musulunci ce kawai ke riqe da Ita a yanxu,


Hankici tasa tana ďauke hawayen fuskarta cikin tausayin kanta,


Tunda ta iya ta karbi rashin Deedah, na wanene baxata iya karba ba a ynxu? But it's still painful.... Yeah so painful!




Bata burin mai kuďi ko wane irin mutum ne shi, tafison talaka xama da Wanda bashi da meyiwuwa hakan xaisa xuciyarta ta xamo so contacted, kuďi basu amfana ta da komai ba illah baqin ciki a rayuwa,


Wannan dalilin ne ma yasa ba abinda ke burgeta a duniya balle ya sanyata nishaďi, haka take xaune ba doguwar magana, babu hope, no future, babu xabi acikin rayuwarta, duk yanda Allah yayi da rayuwarta dai dai ne.


A yau ta tuno da Deedah kan abubuwa da yawa, baxai barta cikin damuwa ba, hawayenta kaďai xai gani gigicewa xaiyi da tarairaya concern da emotional pity amma ynxu babu shi,


Ba Wanda xai rarrasheta, ba wanda xai sanyata a jikinsa ya nuna damuwarsa akanta, babu wannan Deedah dake son farin cikinta Wanda xai iya barin komai na rayuwarsa dan yaga ya faranta tata rayuwar,


Wasu irin hawaye masu ďumi suka barko daga idanunta, a hankali bakinta ya soma motsi,




_"This life has changed... and we go our separate ways Deedah... but you'll still be in my heart till my dying days... my world has never meet a person like you..... I love you Deedah."_






My wattpad Phertymerh1
*Babana da Mijina*




©Fertymerh Xarah 💞




38




_dis page is for you Faxyfashion_






Ta ďauke kanta daga kallonsa ta maida hankalinta kacokan Kan abincin da take ci,




Fauxie taxo da gudu ta rungumesa tana dariya,


'Mrng yaya...
'Mrng little angel, bakije Skul ba,
'ina jiran driver bai xo ba,


Ya ďauki little yana yi masa wasa, yaron sai dariya yake daka ganshi kaga Deedah photocopy sak....


Adama ta shigo da kayan kai tsaye ďakin Iman ta nufa dasu duk da batasan ko menene acikiba amma bata ďebe tsammani ga kayan Iman ne,


Driver yaxo fauxie ta fice tana yi masu bye bye,


Iman ma Acikin shirin fita aiki take tana gama kalaci ta taso ta karbi little yaqi xuwa ya liqewa Deen,


Ta rataya Jakarta tana faďin,
'xan barka anan kuwa inda adama tunda yau ni kakewa quya,


Dr Deen ya juya dashi tabi bayansa, motarta ta shiga shima ya shiga tasa tare da little,


Itace ta fara fita da motarta yana bayanta, tafiya suke akan titi hankalinta na gunsu, yanda ya biyota abaya ya tuna mata da Deedah, Allah ya jiqan Deedah ta faďa a hankali.


Tana isowa kai tsaye office ďinta ta nufa shima bai kulataba yayi nasa office da little....


Haka rayuwarsu ta cigabada tafiya tsawon shekara ďaya kenan Iman ta kasa tsaida xuciyarta akansu, Dr Merah yayi iya qoqarinsa akanta taqi sai ya xuba mata ido yana kallonta yasan komai daren daďewa dole xata xabi ďaya acikinsu Sa'eed ko Deen ta aura.




Shaquwa ta musamman ta shiga tsakanin little, fauxie da baffa, akoda yaushe suna can sun maidashi kakansu shi kansa yana jin daďin kasancewa tare dasu badan komai ba dan shima ba yara ba jikoki daga shi sai masu yi masa aiki sai Deen Idan yana gidan bai fita aiki ba.


A yanda ta lura yaran a ynxu sunfi son xama da baffa akan ta, bata yaye little ba yana shekara ďaya da wata biyar idan ka ganshi xakayi tsammanin ya tasamma shekara biyu saboda girmansa da wayonsa ko ina xuwa yake gashi da rigima sosai, sau tari ba'a gidan suke kwana ba sai inda baffa, yanda suke sonsa yasanyata qaunar tsohon itama akai akai take xuwa gaidashi ta daukeshi da girma haka take ganinsa Kamar mahaifinta kamar yanda ya ďauketa ya',


Idan tayi ba dai dai ba yakan xaunar da Ita yayi mata faďa Kamar yanda xaiyiwa Deen, haka duk wani abu daya shige mata duhu na rayuwa shike warware mata, sai ta daukesa tabashi wani matsayi a xuciyarta na UBA, a Yanxu tana samun kulawar da bata samu a baya, ga yaranta suna jin daďin kasancewa dashi ba abinda xata cewa wannan tsohon bayan yi masa addua a tsawon rayuwarta.




A nata ganin Sa'eed yafi dacewa da aurenta, yafi kowa sanin halinta da mijinta sannan tasan halinsa fiye da halin Deen, miskilancin Deen kesa take qinsa komai yana yinsa cikin nuna isa da gadara, ta tambayi Dr Merah xabi acikinsu ya xaba mata Dr Deen Wanda Sam bata amince da wannan xabin ba, sai taje ga baffa tana tsammanin xaice ta auri yaronsa Deen ga mamakinta sai ji tayi yace,


'fatyma ki auri Wanda xuciyarki tafi amince maki dashi, Wanda kike gani yafi kusanci gareki inda hankalinki xaifi kwanciya kiyi xaman aure, ki kuma kula da yarannan guda biyu da suke amana agareki,


Sai taji kunyarsa da nauyinsa, akwai kawaici a gareta baxata iya fitowa ta gayamasa Sa'eed xuciyarta tafi aminta da ta aura ba, sai ta kawar da mgnr ta ďauko wani xancen suka cigaba da hira kamar ya' da uba....


Akwai wani lokaci da lauyoyin babanta dana Deedah suka xo gareta domin dukiyar mamanta dake hannunsu suna so su rabu da Ita,


Tayi mamakin dukiyar da Deedah ya bari, bar mgnr Waďanda ke cikin account ďinsa, bata taba sanin yanada irin waďanna kuďin ba, sai ta boye mamakinta lokacin da taga dukiyar baba, kusan tsoro da ruďewa tayi a inda take xaune,


Files files dake xube a gabanta na kamfani, gidajensa, filaye da shagunansa bata san iya Karsu ba, ga makullayen motocin da aka xube mata a qalla xasu kai ashirin inma basu haura hakan ba, anan gida ma tanajin makullan motarsa dake hannunta sun kai bakwai, na Deedah biyar ne Kuma tasan suka ďai ne motocinsa a duniya Gashi kuma taga xahiri sai ta qara yarda da mijinta akan babanta,


Ta dubi Sa'eed kafin ta maida dubanta ga Deen domin sune shaidarta sai lauyoyin, idanunta sukayi rau bakinta har rawa yake kamar xatayi kuka data tuna Deedah,



'Dukiyar Deedah na yafewa ďan mu Ahmed, ku shaidane ko bayan mutuwata idan ya girma xaku iya bashi, in kuma ina raye Alhamdulillah,


'sai dukiyar baba a raba biyu dani da qanwata, a ajiye mata nata daban, Acikin nawa xan sallami yan uwanmu da duka ma'aikatan gidan nan, sauran kuďin xn kaisu gidan marayu da asibiti saboda masu buqata, xan gina masa makarantar islamiya shida Deedah domin lada ta kai garesu Allah ya gafarta masu,


'banajin xn iyacin dukiyar baba koda kwandalace a ynxu danasan da jinin mahaifiyata da yayyuna da qannena aka tara wannan dukiyar, kuka take sosai


'Allah ya gafartawa baba, Allah ka yafewa baba, Allah ka yafe kuskurensa daya aikata,


Suka amsa da Amin suna kallonta cikin tausayawa....ta tsurawa dukiyar ido, xuciyarta ta taushe ta dacewa,


'duniya ba komai bace tamkar matafiyi ne akan tafarki, baba kaďai ya isheta misali, Waye baisan baba a Nigeria ba shahararren ďan siyasa mai ji da dukiya, a yau yana ina? ya tafi yabar kuďin a inda ya samesu, ya tafi inda abinda ka shuka shine jarinka, bai tafi da gidajen ba bai tafi da motocin ba, bai tafi qasashen da yake xuwa ba, qarqashin qasa ya tafi cikin yadin likkafani dai dai dana kowa, babu AC babu katifa mai taushi, sauran al'amarin tsakaninsa da ubangijinsa ne, to haka kowa fa xai mutu yabar wannan dukiyar dayake taqama da Ita, dukiyar nan da ake tarawa ana hana talakawa da masu buqata, dukiyar da ake kashe bayin Allah saboda ita, dukiyarda xaka ga yan uwa suna faďa suna gaba saboda ita, duk xa'a mutu abarta Allah ya gafartamana Amin.


2 months later ~~~




Tana xaune a falo cikin Atampha mai qarshen tsada, kanta babu kallabi ta matse gashinta a tsakiyar kanta, farin glass dake idanunta ya qara ma fuskarta ilhami da kwarjini tana naxarin wani littafin ilimin halin ďan adam Wanda a fakaice ba komai bane aciki ba sai applied Christianity, malaman kimiyar halin ďan adam ke amfani dashi jami'oi matsayin hanyoyin gyara mu'amalar xamantakewar ďan adam tana tsintar na tsinta tana xubar dana xubarwa, sunan littafin 'The power of positive thinking'.


Da Sallama ya shiga falon ya bayyana cikin kyakkyawar suit (Japanese) da baqin gilashin Prada a idanunshi, falon ya gauraye da qamshin Dior addict daka ganshi kaga gogaggen ďan boko.


Kallo ďaya tayi masa taji xuciyarta ta buga a yau, kamar yau tafara ganinsa, bawai yau ta fara ganinsa ba sai dai bata fiye yiwa mutum kyakyawan kallo ba, yau ta ganshine sosai a gabanta yayi mata kyau, shima gabansane ya faďi sakamakon ganin Iman yau a ainihinta ba cikin mayafi da labcoat ba kamar kullum,


Ta lalubi ďan kwalinta ta ďaura ta xare gilashin idanunta tayi mishi barka da xuwa,


Shiru ya ratsa na wani daqiqai wani chemistry mai ban mamaki na aiki a zuciyoyinsu da kwayoyin idanunsu yana shiga cikin xukatansu dai dai lokacin fauxie ta shigo da gudu da ball a hannunta little na biye da Ita yana kuka akan tabashi taqi sai dariya take masa,


Suna ganin Dr Deen duk sukayi kansa suka rungumesa suna dariya,


'ďanki kike hanawa ball fauxie, bakiji kunya ba yana kuka yana biye dake,


Ta soma dariya tana kallonsa kafin ta bawa little ball ďin,


'amma shine ya jefomin ita a goshi ina assignment,


'Kiyi haquri kidaina sashi kuka kinji,


Little ya dubesa yana gauranci da alama ya kawo qarar fauxie ne, daga shi har Iman suka kwashe da dariya yanda yake Mgnr komai baxaka fahimta aciki ba amma yanayin fuskarsa xaka gane da faďa yake Mgnr, Deen ya rarrashesa haďe da bashi ball ďin ya fice da gudu,


'yaya yau xakaje damu inda baffa,


'kujirani a waje gani fitowa ynxu sai muje, ta fita da gudu itama,


Deen ya dubeta wannan karon ba walwala a fuskarsa,


'inason nasan matsayina a gunki fatyma,


'Sa'eed na xaba, shi nake ganin yafi kowa sanina da halin dana fuskanta a baya, nasanshi ya sanni,


Ya dubeta da tsananin mamaki,


'kina tunanin har akwai wani abu daya shafi rayuwarki a baya wanda ban sani ba, fiye da shekara muna tare kina nufin bakisan hali na bakisan ko waye niba, ban taba roqon mace ta soni ba sai akan ki Iman, kinsan yawan matan dake bibiyata domin

Please Login or Register in order to submit comment