You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

kima baxai barshi ya fito ba, kijira Suleiman idan yaxo akwai sauran kayana sai ku kaimin kinji, ta gyada Kai tana kallonta, ta shiga motar har ta tayarda motar ta juya taga fauxie tana kallonta,


'ki yafemin idan nayi maki wani laifi kinji qanwata,
'anty nima kiyafemin na yafe maki,
Iman tayi murmushi tana ďaga mata hannu itama fauxie ta ďaga mata hannu harta fice, kana ta juya anan taci Karo da baba sai safa da marwa yake a gidan kamar wani xautacce, sai a lokacin ta tuna da Abinda ta ďauko a ďakinsa da gudu tayi ďakinta, under bed ta duba suna nan ynda ta ajiye ta soma dariya xatayi Wasa da kayan tasa hannu ta janyo tukunyar da matsafarsu ce aciki ta ajiye gefe kana ta janyo kwalbar da rayuwar baba ke ciki, suna rungume a hannunta ta fito falo,


Tana saukowa Kan step a hankali gudun wani ya ganta yaje ya gayawa baba aniyarta xata maida masa wadannan sai ta boye tedy ďinsa tana Wasa da ita dan baxata maida ba,


Ta ajiye kayan a qasa taje tana leqa harabar gidan har ynxu yana tsaye bakin falonsa sai waya yake faman Kira ga abokan harkarsa na gurin sima,


Ta dawo da baya da baya ta ďauki tukunyar, kana ta ďauki kwalbar by mistake tukunyar ta faďi a hannunta qasa ta tarwatse jikinta ya ďauki rawa sosai taji tsoro shikenan idan baba ya gani sai ya daketa bata manta Marin da yayi mata ba,


Fashewar tukunyar yayi dai dai da kamawar matsafan su sima da wuta, daga sima har gunkin da suke bautawa da mutanen danaje gunta a Wannan safiyar sai da suka qone qurmus lokaci ďaya wutar ta tashi from no where kafin sima tayi wani yunquri tuni takama jikinsu, tanaji tana gani ta narke a gurin kamar ruwa rayuwarta ta qare,


Baba Kuwa Kamar yaji a jikinsa ynda tsigar jikinsa ke tashi, yana Waya kamar ance ya ďago Kuwa yaga fauxie da wannan kwalbar,


Hankalinsa ya tashi taya ta sami kwalbar?
'ke fauxie... ke tsaya...


Tana jin muryarsa ta tsorata jikinta yafara karkarwa musamman yanda ya tunkarota, ta soma gudu tana kuka a tsorace yana biye da Ita shikuma kamar mahaukaci sai ihu yake Acikin gidan Wanda ya janyo hankalin mutanen gidan garesu,


Sa'eed Kuwa da sauri ya qaraso gidan sai dai a waje yayi parking motarsa shigowarsa gidan tayi dai dai da faduwar fauxie qasa kwalbar dake hannunta ta gangara gefe ďaya ta fashe har wani hayaqi ke fita daga cikinta,


Ihu baba ya Sanya yayi kanta da duka, bugunta yake ta ko ina kamar Wanda aka aiko ga sa'ansa,


Nan take numfashinta na ďauke, bakinta da hancinta sai jini suke fitarwa, da qarfi Sa'eed yayi kansa bai duba girmansa na kasancewa dajjito ba kawai ya ďauke shi da Mari, qoqarin baba na ganin ya illata fauxie duk da bata Numfashi burinsa yaga ya kasheta da hannunsa ta mutu, Sa'eed ya fahimci haka nan take ya ďauketa ya fita da Ita da gudu har lokacin bata numfashi asibiti ya nufa da Ita,


Baba Kuwa tamkar wata Halitta ya dawo yanayinsa ya tsorata mutanen gidan, haqoransa sun xaxxago, akaifun hannunsa dana qafafunsa sun qara tsayi kamar na doki, ga wani gashi daya firfito a jikinsa tamkar wani dabba,


A gaban idon mutane yake cin Naman jikinsa, fisgar jikinsa yake yana ci sosai, wa'iya xubillah, (Allah yasa mucika da imani muyi kyakkyawan qarshe Amin)


Masu hankali da hangen nesa a gurinne suka soma yi masa addua suna tofa masa daga nesa, sai ya xube gurin ragwab, bakinsa da hancinsa sai fitar da jini suke kamar fauxie,


Nan take maxan gidan suka taru akansa aka daukesa aka sanya a mota akayi asibiti dashi,


Deedah Kuwa yana shiga gidan ya sami su oga nas kowane fuskarsa ba walwala, bai damu ba ya sami guri ya xauna,


'ance an ganka station yau mekaje yi Ahmed? Yaji tambayar oga nass daga Sama,


'ba komai naje kan wani case ne Kuma komai ya daidaita,


'bn yarda dakai ba Deedah kwanakinnan ka cnxa mana, lokaci yayi da ya kamata mu rabu dakai kaje ka huta a taka rayuwar mukuma mu cigaba da jin daďin duniyar mu,


Kafin Deedah ya ankara sai jin saukar bullet yayi a qirjinsa, ya dafe gurin yana kallon mai Harbin oga nass ne, kafin yayi yunqurin sake Harbin Deedah shima yaji an harbesa a qirji, police din dake bayan Deedah ne,


Nan take gurin ya kaure da harbe harbe (dama masu irin Wannan sana'a a haka suke qarewa wasu Kuwa suke kashe junansu da kansu, Allah ya shiryamu da zuri'armu gabaki ďaya Amin)


Police ďin sukayi nasara Wannan karon sun kashesu da Dama yayinda suka kama wasu suka sanya masu ankwa, oga nass na cikin mutanen da suka mutu,


Deedah Kuwa baisan inda kansa yake ba, numfashinsa ma da kyar yake fita, jikinsa duk jinine ga bakinsa ma ya soma fitar da jini sai suka garxaya dashi asibiti,


Iman Kuwa tun bayan xuwanta asibitin Dr Merah ya duba ta,


'yace da saura likita, amma kafin lokacin idan kina iyawa kiďan yi exercise ko kaďan ne,


Tayi murmushi dama ba naqudar takeji sosai ba, sai ta fito harabar asibitin anan ta ci Karo da Dr Deen,


Bayan sun gaisa yake tambayarta lfyr jikinta, tana gayamasa maimakon ya shiga asibitin sai ya biye mata suna exercise ďin xagayen asibitin suke a tare suna hira,


Haka xuciyarsa take mai tausayin mata ne musamman masu irin Wannan lalurar, yana tuna matarsa itama yakan sata ta xagaya Acikin gida, kasancewarsa da Iman yau yasa komai ya dawo masa sabo,


Sun xagayo kenan taga motar Sa'eed ta shigo asibitin taja ta tsaya tana kallonsa,


'Wayyo Sa'eed bai sameni gida ba shine ya biyoni har asibiti, Dr Deen ya juya yana kallon inda take kallo tana Mgnr dai dai lokacin da Sa'eed ya fito ďauke da fauxie a hannunsa,


Turus taja ta tsaya, fauxie ce meya sameta, taja ta tsaya idanunta a bude hankalinta a tashe har ya iso,


Yanda taga fuskarta a kumbure Kuma ko ina jini hankalinta yayi matuqar tashi ta fashe da wani irin kuka tana ganin Dr Deen ya karbeta yayi cikin asibiti da Ita, sai suka juya suka bi bayansa da sauri,


Lokaci ďaya aka xo da baba da Deedah asibiti, daukarta atare aka nufi emergency dasu domin suna neman ceton gaggawa,


Dr Fulani taxo ta kirata bata gayamata komai ba sai da suka shiga inda aka kwantar dasu,


Cikinta yayi mata nauyi,
'me nake gani yau ni fatyma, *Babana da mijina*, meke faruwa meya samesu haka, Waye yayi masu wannan aikin har fauxie,


Sai ta ruďe taje ga Deedah numfashinsa sama sama ne, kuka take sosai ta nufi inda mahaifinta,


Halittarsa ta tsoratata badan fuskarsa da muryarsa ba da ta qaryata Abinda idanuwanta ke gano mata,


Surutu yake agaban likitocin dake kansa, duk abinda yayi a rayuwarsa tunda ya fara neman siyasa har kawo ynxu sai da ya faďa,


Believe me Akan ruďewa musamman ma ga mai ciki Iman bata San lokacin da fitsari ke fita a jikinta ba,


'baba ya kashe mata yayyunta da qannenta, ya kashe mata mahaifiya, ya kashe mata ya'yan da take samu, ya sanyata a wani hali Acikin asibitin Wanda mutane suka soma xarginta, she can't believe this ta rufe bakinta da hannayenta duka tana kuka sosai,


Dr Merah kansa jikinsa yayi sanyi sai yaji baxai iya taimakawa baba ba, yayi mummunan abu a rayuwarsa Wanda Allah kaďai xai iya yafe masa tabbas baba baida imani da tausayi tunda har xai iya sanya iyalinsa a Wannan hali, xai iya sadaukar da rayuwar iyalinsa saboda dukiya da duniya to ynxu me gari ya waya, mecece ribar da ya samu a duniyar? Ina dukiyar daya tara yake tinqaho da Ita, ina sima da yake alfahari da Ita yake bauta mata Waye xai cecesa a ynxu?


Dr Merah ya girgixa kansa shida sauran likitocin suka rufawa Deedah baya, na ganin sun cire bullet ďin jikinsa sun ceto rayuwarsa,


Hankalinta baya jikinta, fauxie take gani, ga baba ga Deedah, tana ji tana ganin yanda baba ke fisgar Naman jikinsa ci yake kamar wani dabba yana faďin Duk abinda yayi a rayuwarsa,


Tanaji tana ganin yanda yake shure shuren mutuwa, tana ganin lokacin da numfashinsa na tsaya cak ya mutu, tana ganin ynda fatar jikinsa ke fita daga jikinsa tana yin wata Kala baqiqirin,


Ta fashe da wani irin kuka mai tsananin gaske wannan wace irin rayuwace take fuskanta,


Muryar Deedah takeji yana kiran sunanta sai ta nufesa da sauri lokacin an gama cire masa bullet din jikinsa,


Dr Merah da Bakori baxasu jure ganin halin da Salihar mace take ciki ba a ynxu sai suka fice da sauri suna hawaye cikin tausayamata, itama Fulani kuka take sosai ta fita,


Iman ta faďa jikinsa duk jini,
'ni nasa ka a Wannan halin, kafita kana fushi dani dama kace kome ya sameka nice sanadi, ka yafe min Deedah, Ina sonka, baba ya mutu karka mutu ka barni Deedah, fauxie na can itama xata mutu, idan na rasa ka da fauxie my life will be useful please stay with me Ahmed, (muryarta harta dishe saboda kuka, ga jikinta har lokacin bai daina rawa ba, a rude take Kamar wata xautacciya, sai faman rungumarsa take tana sumbatarsa,


Shima qanqameta yayi sosai a jikinsa yana tayata kuka,


'ki yafemin Iman na kasance mai laifi a gareki, na cutar da rayuwarki haqqinki ne ya kamani, ki yafemin,


Ta ďago tana kallonsa tana share hawayen fuskarsa,


'burina a ynxu ka tashi, Dan Allah karka mutu kabarni, karka mutu Deedah, yaron mu xaixo a yau, karka maidashi MARAYA, ka tausayawa rayuwarta, banda kowa bayan kai da fauxie a ynxu.......tayi shiru sakamakon jin ynda numfashinsa ke fita, tanajin bakinsa na motsi da alama kalmar shahada yake, ta tashi a ruďe ta janyo oxygen xata sanya masa, xaninta har ya kwance a gurin under wear ne kawai a jikinta bata damu ba,


'please Deedah, don't..... karka tafi please,


Ta taba shi baya Numfashi,


'No Deedah will not die, Deedah baxai mutu yabarni ba, Deedah I know suma kayi ka tashi please, ta soma jijjigashi ta dubi gawar mahaifinta kafin ta maida kallonta garesa,


*BABANA DA MIJINA* baxasu mutu su barni ba, *babana da mijina* basuxo duniya a tare ba baxasu je su barni ba, *babana da mijina* suka ďai nake da aduniyarnan they can't die at the same time su barni,


Jin abu nabin qafafuwanta yasa tayi Saurin dubawa, jinine ke xubowa daga qasanta, wani irin ciwon mara na taso mata lokaci ďaya, qafafuwanta suka riqe.......








My wattpad Phertymerh1


*Babana da mijina*




©Fertymerh Xarah 💞




*Dis page goes to masoyan babana da mijina, tnkuuuu ol for your love and care, Pherty loves you more😘*




33






Har lokacin bakinta yaqi rufuwa, Deedah take kira kamar ranta,


Nan ta durqushe qasa riqe da mararta,
Tana haka sai ga likitocin sun shigo,


Ganin yanayinta sukayo kanta ,numfashinta na fita da sauri da sauri kamar xai ďauke,


Dr Fulani da Dr Merah suka riqata ta tashi, suka ďorata akan sick bed ,


Da sauri Dr Deen yaja gadon sukayi waje da ita,


Fauxie a ruďe ta farfado, sai kuka take sosai tana kiran anty, taqi yarda kowa ya tabata daga cikin nurse ďin saboda a firgice take,


Sa'eed ne a waje tsare da Ita baisan abinda ke faruwa game dasu Deedah ba, yana xaune yajiyo kukan fauxie a inda aka kwantar da ita, ya tashi da sauri ya shiga ďakin,


Tana xaune akan gadon asibiti, idanunta a rufe take Kukan tana weaving hannunta sai faďi take,


'don't touch me..... don't touch me,


Ta soma qoqarin saukowa akan gadon ga drip ana sanya mata,


Da sauri yaje ya riqata, tana ganinsa ta qanqame sa yayi Saurin riqa hannun da ake sanya mata drip,


'yaya ka kaini inda anty, baba ya dakeni ka ramamin,


'ki tsaya da kyau karkiji ciwo, kinga ana qara maki ruwa,


Tabi hannunta da kallo kafin ta maida dubanta garesa,


'yaya ka kaini inda anty, ni ka kaini inda anty... ta cigaba da kuka tana son saukowa Saman gadon,


'Bari acire mata drip ďin tunda qanwar Dr fatyma ce itama xata iya Kula da Ita,


Suka cire mata drip ďin, yana rungume da Ita a qirjinsa suka fito, idanunta sunyi jawur ga fuskar ta kumbura, gefen idanunta yayi ja daga ciki baqaramin duka yayi mata ba, sai jikinta yayi xafi rau, yanda ta qanqameshi ma ajikinsa abin tausayi ne,


Suna xuwa office ďin Iman bata nan ko Jakarta babu aciki,


'fauxie anty batanan Kinsan inda take xuwa,


Ta gyada Kai tana kallonsa, ya rufe office ďin suka fito,


Consultant suka nufa nan ma bata nan ba likita ko ďaya,


Tana ganin haka ta boye fuskarta a qirjinsa tana kuka,


'yaya ka kaini inda anty,
'Ina xnga anty ynxu fauxie, ai bata gida kuma, Ina ne take xuwa karban haihuwa kin sani? Ta gyada Kai da sauri tana goge hawayen fuskarta,


Tana nuna masa suka iso labour room anan suka ci Karo da Dr Deen sai safa da marwa yake a bakin qofar ďakin sai kace matarsace ke labour.


Yana ganinsu ya qaraso cikin mamaki,


'meyasa ka fito da Ita, bakaga halin da take ciki bane?


Fauxie naganinsa ta qanqame Sa'eed bataso ya karbeta,


'Dr fatyma muke nema tana kuka sai ta ganta ne,


'batada lafiya haihuwa xatayi,


Gaban Sa'eed ya faďi, yana sauko da fauxie jikinsa taqi sauka, baisan bata lfy ba sam, meyiwuwa wannan dalilin ne ya sanya ta kirashi ya kaita asibiti,


Sam baiji daďi ba, sai ya ciro wayarsa da ďayan hannunsa a aljihunsa yana dialling number Deedah, is switched off, ya maida wayar aljihun cikin jin haushin rashin samun Deedah,


Ya dubi Dr Deen sai yaga duk ya damu sosai ko miye dalilinsa na damuwa da halin da Iman take ciki, nan take yaji wani abu ya taso ya tokare qirjinsa musamman daya qare masa kallo kyakkyawan gaske ne da alama yana da jini da Shuwa Arab, ko sumar kansa baqa ce wulik a kwance,


Dr Deen ya dubesa yana faďin,
'Waye yayiwa fauxie irin Wannan duka?


Sa'eed yaja dogon Numfashi yana faďin mahaifinta ne,


'metayi masa haka?
'shine ban sani ba nima, na sameshi yana dukanta ne,


Dr Deen yaja numfashi wannan mutumin bashida imani, ya tsanesa tun lokacin da yaji yana wannan surutun kan abinda ya aikata a rayuwarsa, Allah wadarai ga mai hali irin nasa,


'amma kai yayan Iman ne?
'no abokin mijinta,
'kasan Baban ya rasu a ynxu, yana emergency aka kawoshi,


Wata irin faďuwar gaba ta riskesa saura qiris fauxie ta faďi hannunsa ai kuwa ta qanqameshi,


'ya mutu fa kace, Inna lillahi wa inna ilaihir raji'un,


Dai dai lokacin da Dr Fulani ta fito ďauke da jinjiri a hannunta sai kuka yake tsalawa, lafiyayyen yaro dashi sak Deedah, kallo ďaya xakayi masa ka gane yaron Deedah ne ba inda ya barshi ta ko ina,


Da sauri Sa'eed ya ajiye fauxie a tare shida Dr Deen suka nufi Fulani sai dai Deen ya rigashi karban yaron,


Kukan da Fulani keyi shike ďaga hankalinsu, suka dubeta kuka take sosai,


'Ina Iman? Sa'eed ya tambaya Idanunsa akan ta,


Iman jikinta yayi tsanani sai suma takeyi tun ďaxu,


Jikinsu na soma karkarwa, fauxie ta qaraso tana kallon jaririn, farin ciki xaka gani bayyane a fuskarta,


'yaya wannan baby anty ne? ya gyada kai yana kallonta,


Tayi cikin ďakin da sauri, alokacin Iman ta sami barci,


Dr Merah yayi ajiyar xuciya cike da tausayamata yana kallonta, haka shima Dr Bakori halin da Iman take ciki ko kuka xaka iya yi mata,


Tana ganin Merah taje ta riqa hannunsa,


'uncle anty ta haifi baby, yana can inda yaya, Merah ya juyo yana kallonta fuskarta da yagani sai da gabansa nayi tsananin bugawa, ya buďe idanu sosai yana kallonta,


'accident ne kome, me yajimiki ciwo haka a fuska? Tayi rau rau da idanu ta qara riqa hannunsa,


'baba ne ya dakeni, xaka ramamin,


'Ya salam lallai ba axxalumi irin Wannan mutumin, dubi fuskarta Bakori wannan yarinya xaiwa irin wannan duka haka,


'kabari kawai Merah amma yarannan sunga rayuwa bama kamar fatyma dubi ynda ta koma fisabilillah, basuyi dacen uba ba kam,


Suka fito a tare,
'Iman fa?
'ta sami barci,


Suka nufi emergency harda Sa'eed da fauxie, Fulani Kuwa ta wuce da jaririn a hannunta sai kuka yaron yake sosai,




Sa'eed yaga gawar baba harda fauxie Kuma bata raxana ba batama gane baba bane tana dai kallonsa ne kawai,


Dr Bakori ya dubi Merah,
'likita xo kagani kamar Ahmed ďin baya Numfashi,


Sukayi kansa da sauri har Dr Deen sai a lokacin Sa'eed ya lura da Wanda ke kwance,


Deedah, meya sami Deedah ya qarasa da sauri, tabbas shine jikinsa duk jini,


Iya ruďewa Sa'eed ya rude musamman da yaga Merah yaja farin kyalle ya rufe Deedah da shi,


'Deedah is dead Allah ya jiqansa ya gafartamasa shine abinda Merah ke faďi yana sharar kwallah a fakaice, ya tsorata da mutuwar Deedah yana tuna xamansa dashi sanadiyar Iman yasan irin alaqar dake tsakaninsa da Iman, yasan irin son da suke ma juna tabbas Iman tayi babban rashi, ba uba ba miji a irin Wannan lokacin da suke tsananin buqatar taimako tunda basu da uwa,


Inaji tun da Merah ke asibitin bai taba kuka ba sai wannan lokacin, duk dauriyarsa a yau ya kasa yaja da baya yana sharar kwalla baxai iyaba jikinsa har rawa yake tunanin halin da Iman xata kasance yakeyi,


Sa'eed ma baisan sanda kuka ya xo masa ba, abokinsa koma ince amininsa.....


Kukan fauxie da Merah sun tayarda hankalin fauxie ganin manyan maxa irin su na kuka ba qaramin abu bane, duk da take qarama tana jin wani feeling a jikinta ba daďi, jikinta yayi sanyi ta matsa kusa da Bakori tana kallonsa dan taji suna ambatar Deedah tasan shine kwance a wurin taga sun rufeshi da xani, tasan haka akewa duk wanda ya mutu kamar yanda malam ya sanarda ita,


Xuciyarta na soma bugawa fal fal numfashinta har wani sama yake,


'yaya ya mutu? ya gyada kai yana kallonta,


Shikenan ya tafi ya barsu, shikenan baxai dawo ba, shikenan baxai qara siyamata tedy, biscuits da chocolate ba, shikenan baxai qara Wasa da ita suje yawo ba, shikenan baxasu qara cin abinci tare ba, baxata qara ganinsa ba itada anty, ta juya tana kallonsu duk sunyi shiru, ta gigice ta fita daga ďakin haďe da fashewa da irin Kukan nan Mai qara irin na yara, da ka ganta kasan a gigice take batasan inda xataje ba,


A tsorace ta farfado daga barcin da take, xuciyarta na tsananta bugawa ta tuna Deedah da yanda ta barshi, ta sauko daga Saman gadon da sauri haďe da fisge drip ďin da ake sanyamata a hannu,


Mararta a qule take har lokacin tafiya take a hankali ba takalmi ba mayafi sai kallabi akanta, kallon xararra ake mata a asibitin ga Waďanda basu Santa ba duk inda tabi sai an kalleta, kai da kaganta kasan haihuwa tayi saboda xaninta duk jinine,


Nurses ďin da suka Santa suka biyo bayanta da sauri suna kiran sunanta, tanaji ta kyalesu sai ta qara Saurin qafafunta musamman ynxu da take jiyo Kukan fauxie sai ta qara ruďewa,


Tun daga nesa ta tsinkayo fauxie na kuka a jikin Dr Deen, tana qarasowa ana fitowa da gawar baba,


Ta tsaya cak tana maida Numfashi da kyar kamar wata zakanya jikinta sai karkarwa yake, juyowar da xatayi taga anfito da Deedah, Sa'eed na bayansu yana sharar kwalla Idanunsa sunyi matuqar ja,


Fauxie na ganin an fito dashi ta qara fasa ihu a gigice tana neman kwacewa jikin Deen, iman Kuwa qarasawa tayi ta riqe gawar,


'meyasa kuka rufesa ai bai mutu ba, ku duba suma ne yayi, Deedah baxai mutu ya barni ba, wannan lokacin Kukan da take harda majina ta xama wata xautacciya,


Duk qarfin hali irin na mutum idan yaga halin da Iman take ciki a Wannan lokacin sai ya xubar da kwalla,


'Deedah ka tashi sugani su San cewa Baka mutu ba, Deedah ka tashi kaga yaron da muka haifa, meyasa xakaje ka barmu a lokacin da muke tsananin buqatar ka,


Taje ta riqe Merah,
'kace su dawo dashi acigaba da kula dashi anan, Deedah bai mutu sai idan kune xaku kashe shi,


Fulani ta qaraso da jaririn a hannunta har lokacin kuka yake kamar yasan abinda ke faruwa, tunda ya faďo duniya yake kuka,


Kukan yaron har cikin kanta take jinsa, ga Kukan fauxie dake qara rikita kwakwalwarta, tana ganin lokacin da suka sanyasu a mota ta tabbata lallai gida xa'a je dasu ayi masu wanka da sallah akaisu makwancinsu, shikenan Deedah yaje yabarta.....




Cak numfashinta na ďauke, sai ta xube gurin a sume....








My wattpad Phertymerh1


*Babana da mijina*




©Fertymerh Xarah 💞




34




*Masu turo ta'aziyar Deedah, iman na godiya sosai, saqonku ya iso*.




Tana xubewa gurin su Dr Umayma sukayi kanta, fauxie na ganin lokacin da ta faďi ta soma neman saukowa jikin Deen tana kuka amma ya riqe ta tamau sosai a jikinsa,


Aka sanya gawarsu a motar Sa'eed, shi yaja motar su Merah na bi bayansa da nasu motocin,


Iman Kuwa motar Dr Deen aka sanyata tare da sauran likitocin fauxie na kusa da ita fuskarta ta qara kumbura tayi jawur ga ciwo ga kuka, kanta har nauyi yake mata ga wani Xaxxabi da take ji wannan karon baxata sami kulawar Iman ba cos ita kanta bata cikin hayyacinta, mutuwar mahaifi da miji a lokaci ďaya (it's the greatest loss of all losses),


A Wannan ranar xo kaga jama'a, mutane kamar me, nan da nan gari na ďauka mutuwar Alhaji Abdallah abinka da ďan siyasa sananne a gari,


Mutuwar taxowa mutane a baxata daga shi har Deedah ba Wanda aka yiwa tsammanin mutuwa a ynxu,


Abokan Deedah suna cikin ruďani da tsoron Allah, duk Wanda yace shine yau ba shi bane gobe, mutuwar sa ta girgixa shi idan suka tuna jiyama suna tare dashi a office, ya sami kyakkyawar Shaida daga garesu,


Ma'aikatan gidan maza da mata tamkar sune akayiwa mutuwar, kuka suke sosai sun san qarshen barin su gidan yaxo, ba uban gidansu to Waye xai riqa biyansu Waye xai riqa ciyar dasu, wasu ma da gidan suka dogara,


Sa'eed da kansa yaje part din baba ya rufe ďakunan sa na dukiya, mutanen ynxu basu da amana wani baxaiji tsoron ana cikin wannan tashin hankali ba suje yiwa marayu sata wannan ne dalilin dayasa ya rufe,


Anje yiwa gawarwakinsu wanka, a Wannan lokacin fauxie na rakube a bed side kanta a langabe, barci take daga xaune tana gyangyaďawa kamar xata faďi,


Iman Kuwa tana xaune da jinjirin a hannunta tana bashi mamma, ance kuka ma rahama ne Wannan Karon kam Kukan yaqi ya xo xuciyarta a bushe take, kallon jaririn take,


Yaxo a MARAYA, yaxo duniya babanshi yabar duniya, kakanshi ma yabar duniyar, duk da haka yaronta baxai taso cikin maraici da rashin gata ba, xata bashi tarbiya ta kula dashi shida fauxie tamkar Iyayen su na raye, bata da sauran buri a rayuwarta ynxu na ganin ta Kula da marayun biyu, ta sauke nauyin dake kanta akansu, aure baxata sanyoshi gaba ba aynxu a tsorace take da kowane namiji da halayyarsa, xata cigaba da rayuwarta a hakan, Wanda take so ya tafi yabarta tana roqon Allah ya sa shine mijinta ko a lahira,


Sai a lokacin hawaye na samu xubowa daga idanuwanta ta rumtse idanuwanta suka xubo akan fuskar jaririn Wanda ke barci tuntuni,


Fulani ta karbi yaron ta goya, sai Iman ta maida kanta jikin cinyoyinta tana kuka sosai,


Sanda aka gama masu wanka aka Kira Iman tayi masu addua, kuma tayi cikin jarumta da dakewa irin tata, ba Wanda batayiwa addua ba acikinsu, tana gani aka ďauki gawarsu,


Sai ta bisu da ido idanunta taf da hawaye fuskarta ďauke da murmushi,


'I know Deedah must come back to me, ni nasan bai mutu ba, nasan Deedah baxai je yabarni ba, bayan yace xamuyi rayuwa tare mu raini jaririn mu tare,


Xuciyarta ta cigaba da bugawa lokacin da aka fita dasu, taga yawan jama'ar da suka cika gidan sai taja jikinta ta koma ta xauna, tana bin mutanen dake falon da ido tana kallonsu suna kuka,

Please Login or Register in order to submit comment