You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

baby.

Haka suka kamo hanya zuwa bakin ti-ti. Seyan Zuma basma Ta tuna da wanda ya kawo ta nan wato me mashin, Amma ta duba bata ganshi ba, Wanda tun lokacin daya ga Basma taje Gurin su sun fara Biyota kamar zasu daketa shi kuma ya tada mashin d'in sa yabar Gurin. Ganin bata ganshi bane yasa suka tafi.

Har Gurin da Ta bar su Lubna da direban su me mashin d'in ya kai su, Dama kuma ta kira Lubna ta tambaye ta suna Gurin har yanzu ko dau sun tafi?Inda Lubna ta hauta da masifa kafin ta ce mata suna Gurin. Sallama Suka yi da Amar a kan zeje gurin ƴan sandan
Domin jin abin da zai faru motar tashiga tana d'aga masa hannu Shima yana d'aga mata hannun har suka tafi. Tana kallon irin hararar da Lubna take bin tadashi Amma ko kallon ta bata yi ba har suka isa.

Gaskiya Basma abin da ki keyi wallahi Babu 'kyau Yanzu gashi kin samun fasa zuwa gurin da mukayi niya Saboda wani banzan dalilin ki.Lubna ce take wannann masifar ganin Basma ta sa Sun dawo gida, Cikin Sanyin murya basma ta ce .."yanzu haka daddy yana nan yana jiran dawowar mu in yaga mun dad'e kin san zeyi fad'a.Lubna ko magana ba batayi ba ta wuce ciki ta barta.

...............BASMA
turus tayi tana kallon mutanan da bata san suwaye ba tayi tana kallons u a parlon, Cikin mamakin abin da yakawo su gidan nasu ta bisu da gaisuwa amsawa duk sukayi suna kallonta, Kusa da daddy ta je ta zauna Domin jin abin da ya kawo mutanan,amma kash tayi rashin Sa a domin tana zama sukuma mutanan suna cewa.. "Tom Muzamuko ma se in mun dawo,kuma munji dad'in yanda kuka amshi bu'katar mu mungode sosai"cikin fara'a daddy ya ce.."masha Allah bakomai ai yanzu an zama d'aya ya tashi ya raka su izuwa gurin motar su.

Basma babu abin da ta fahimta acikin zancen su, Hakan ne yasa bata bawa maganar wata muhimmanci ba ta cigaba da harkarta .Har cikin d'aki taje ta samu daddy ta ce ..daddy me yakawo Su gidan nan naga kamar nasan su ko daddy? Daddy cikin san yaga ya faran ta mata ya ce.. eh kin sansu amma tun kina yarinya domin tunda kika girma ba suzo ƙasar nan ba sai wannan karan, Kuma yanzum ma sun zone da abin arzi'ki.

"Daddy me suka zo yi?" Basma ta tambaye shi domin ita jikin ta yafara bata ba lafiyaba, "daddy ya ce.. Sunzo ne da batun Suna son abasu auranki ga yaran su, Kuma mun amince domin yaran d'an manyane, Yanzu haka yaran ya daga cikin manyan yan kasuwa da suke cikin 'kasar nan, yajuyo yana kallonta ya ce.. daughter in kin auri yaran nan zaki ji dad'i kuma ni burina kenan Saboda haka na yarda da mutanan kuma nace jibi suzo se ayi maganar domin nasan na isa dake baza kibani 'kunyaba ko my daughter? Ya ƙarasa maganar yana kamo kumatun ta yana ja.

Basma tun da daddy ya fara maganar ta tsaya tana kallon sa cikin mamaki, Aure kuma! Cikin zuciyarta take cewa, to ma wai haka a ke aure bansan mutum ba to bama wannann ba karatuna fa? anya kuwa daddy yasan me yake cewa kuwa! Jin ana ja mata kumatu ne yasa ta dawo daga duniyar tunanin da ta tafi, Ta ce..daddy "aure fa kace? "Daddy ya ce.. "eh aure nake nufi domin mutane sun fara magana a kanki wai nine na hanaki haure Bana jin dad'in abin da dagin suke cewa a kaina da kuma ke. Yay maganar hawaye na zubowa daga fuskar shi, yacigaba da cewa...Suna zagina sosai nikuma ba wai aure ne bana so kiyi ba, inason in samu wanda zai ri'kemin ke da amana ne kuma inason ki auri me arzi'ki domin kihuta, Hakan ne yasa na za'bamiki shi yaran yan kud'i sosai kuma bawai kud'in baban sa bane kudin sa ne zaki ji dadin zama shi kin ji daughter? Yana kamo hannunta.

Basma wannan shine karo nafar ko da taji tausayin daddy, Shine karo na farko da takasa musa abin da ya ke cema ta kuma gashi tasan abin ba me yuwa bane tasan baza ta amince ta auri wani ba in dai ba Amar ba , to amma meyasa ta kasa yin musu? Tambayar da ta keyiwa zuciyar ta kenan. Maganar daddy ne yadawo da ita daga tunanin ya ce... Jibi za suzo tare da yaran se kuyi magana kin ji, in sha Allah zaku fahimci juna dashi , haka tana ji tana kallo daddy ya tashi yatafi amma taka yin musu kuma zuciyar ta takasa amin ta da maganar daddy, haka itama cikin sanyin jiki ta tashi tabar gurin .

...............AMAR
Abba Gani ya na kallon abban nasa cikin son jin me zai cemasa abba ya ce.. "Takardun ka natura izuwa gurin wani professor Dayake *ABUJA,* kuma ya duba yagani ya ce in turaka domin takardun sun yi kyau. "Cikin farin ciki ya ke kallon abban nasa da ya rage masa a duniya wanda ba yason 'bacin ransa ,Wanda akansa yake yin duk wani abu domin gobensa, ya ce... Abba wallhi naji dad'i sosai shima abban dad'i yaji yana ƙara jin 'kaunar d'an nasa a zuciyar.

Numbar Basma yafara kira domin yayi mata albishir da cewa burin sa ya kusa ciki. Kira d'aya ta ɗaga amma kafin yayi magana ta riga shi da cewa.. Amar kana ina ina son mu had'u yan zu? "Yanzu ina gida nima dama a 'kwai abin da zan gaya miki. Basma ta ce.. To yanzu ina zamu had'u, Amar ya ce.. Zaki iya futowa daga gida? Cikin sauri ta ce.."eh zan iya , nan take yace mata ok tom kizo gurin Shagon Sadam ina gurin yanzu haka ok ta ce sanan ta tashi da sauri.

Tunani take yaya zata fita daga gidan nan! Nan take dabara ta fad'o mata da sauri ta fito falor tana zuwa ba kowa sai little, Dasauri ta kamo hannun sa ta nufi d'akin ZAINAB. Tana zuwa ta ce.. Anty little zai rakani gidan su Lubna zan 'kar'bo wayana naman ta da ita a gidan su? "Kasan cewar gidan bawani nisa yasa anty "zainab cewa.. To kuyi sauri domin yanzu Daddy yafita kin ga ba yason yarinka ganin ku a waje kiyi sauri kin ji tana mata hargaɗi da hannu a kan kar su dad'e. ok Basma tace tan kama hannun sa suka bar falon Sai da tabi ta gidan su Lubna Domin taraka kafin suka tafi tare.

Basma da Lubna Sun riga Amar zuwa inda suka samu Sadam agurin. Bayan sun gaisane Suka samu guri suka zauna , Kafin Amar yazo Basma Ta kwashe duk abin da sukayi da Daddy ta gaya mata "cikin mamaki Lubna ta ce... To yanzu me abin yi? Tana tambayar Basma? Basma ta ce ..shine nima ban saniba, Bansan yanda zai dauki maganar b... Kafin tagarasa Sai gashi ya karaso , kai da ka ganshi kasan yana ciki. Farin ciki.

..............AMAR
Yana gan ku cikin wani irin yanayi , To nazo muku da labari kuna sonji, Cikin farin cikin da yakasa 'boyuwa a fuskar sa yake wannan maganar. "Amma jin abin da Basma ta ce ne yasa ya tsaya cak agurin yana kallon ta.

Basma ta ce... Yaka mata muyi Aure Amar , wannan kalmar yaji daga sama tafito daga bakin Basma, Taci gaba dacewa... Saboda kaga jibi masu neman aurena zasu zo gidan mu, kuma Daddy ya amin ce musu, kuma nina ji a jikina daddy na bazai yarda muyi aure da kai ba please dan Allah Amar muje wani guri muyi auran mu Ta karasa tana kuka kamar Ranta zefita .

Amar ya ce..Aure kuma Ban gane ba? Yana tambayar ta

Cikin kuka ta ce.. Amar bana bukatar ina zaka kai ni ko kuma ina zaka ijiye ni ni dai burina dan Allah muje muyi Aure, Bayan soyayyar ka bana bukatar komai a gareka player.

Amar ya ce .. To sai naga ace za ayi aure yanz..."kafin ya karasa ta ce Amar in dai kud'ine matsalar ka zan ji da komai tana kallon shi cikin hawaye.

Amar yace "wai kud'i "kafin yayi maga ta ce .. To menene matsalar ka? Tana bin shi da kallon wanda izuwa yanzu kukan takeyi, ganin yayi shiru ne tace.. "Shin Amar kana sona? Zaka aureni?"

Amar a karo na farko da zai runguume ta ganin irin kukan da takeyi , ya ce ..tabbas zan aureki, kuma zan baki duk wata kulawa da bakiyi tunani ba , tana jikin sa har yanzu kuka takeyi , tanajin damuwar ta tana raguwa, Ta ce ... Ina sonka Amar ina 'kaunar ka ,shima abin da yake fad'a kenan har zawu wani lokaci Sannan ya saketa.

Sannan tace ya a kayi da su Kamal. Yace ban je gurin ba har yanzu amma nasa wani abokina a kan maganar shima police ne. Batace komai ba har ya rako su gunda zasu shiga keke napin sannan suka koma shida Sadam .

Duk wannann abin Da a keyi , lubna da Sadam suna gurin amma babu wanda ya iya cewa komai domin Lamari. Na sune su biyu.

Amar ya ce.. Sadam Wallahi da matsala shin kasan abin da abba yace min? "Sadam ya ce.. Aa, Nan take ya 'kwashe duk yanda sukayi da abban sa ya gaya masa ,

Sadam yace. "To meyasa baka gaya mata ba? "Amar ya ce... To tayaya zan gaya mata acikin wannan halin da take ciki ni yan zu ma wallahi ban san abin yiba

Sadam ya ce ..Amar wallahi Basma tana sonka kuma son da ta kemaka ne yasa tace kuyi aure please dan Allah kar ka bata kunya pls

Amar yace ...sadam bari zan yi tunani a kai ..daga haka babu wan da ya kara magana har suka bar gurin ....✍️📝






*YAU A KE YIN TA ANYA KUWA HANYAR DA BASMA TABI ZATA 'BULLE KUWA ,. Shin Amar Ze yarda ya bar aikin da baban sa ya sama Masa , ya auri Basma ,. Shin waye Wanda DADDY YAZA BAWA BASMA,. KU KASANCE DA... S REZA*



HAQIKA ALQALAMI YAFI TAKOBI ✍️📝


the end of Part 5️⃣
To be continue..✍️


*ALQALAMI S REZA✍️*


*PLEASE COMMENT AND SHARE DAN ALLAH 🙏🥰*

~BY SALIS M REZA~
[12/23, 6:01 PM] +234 810 078 5178: CAKWAKIYAR SOYAYYA❤❤
NA

S REZA ✍
©🎆
*Al'umma Writers Asso...✍🏻*
_{Al'umma Writers Ƙungiya 'Daya Tamkar Da dubu Farin Cikinmu, Mu Faɗakar Da Al'umma Domin Su Farfaɗo Su Gane Gaskiya Al'umma. Sai Don Al'umma Allah Ya Ba Mu Ikon Fadakar Da Al'umma}._
https://www.facebook.com/102282991949826
بسم الله الرحمن الرحيم...
**DAGA, S REZA*
*Wannan littafin yana da sar'ka'kiya yana da hargitsi 'kunshir ya, fahimta mu cigaba domin kuwa, Sai kun bi ni a hankali cakwakwakiyar soyayya. Ba a *ma fara komai ba fa ku kasance da S REZA** 🙏
________________________________
HAPPY MAULUD 🕌
❤CAKWAKIYAR SOYAYYA❤. PAGE ⚓️ 3⃣

...Sun riga shi 'karasawa gurin, Amar yake ce mata "Abin da nake so da ke, Shi ne. In ya zo kar ki ji tsoran shi, ki zare masa idanu, ki gaya masa magana babu abin da zai iya. Ya cigaba da ce mata, kin ga can ya nuna mata. Ɓarin hannunsu na dama, ta bi hannun da kallo, ta ce "Na gan su me za su mini? Ya ce Ba za su bari ya yi miki komai ba."
Basma ta ce"Ni gaskiya tsoro nake ji ba zan iya ba don Allah abar shi kawai. Cikin san ya ga ya taimake ta ya ce:
"Kar ki saka tsoro a zuciyarki, ba abin da zai iya."
Suna cikin haka ne, suka hango motarsa tana zuwa gurin. Amar ya ce:
" Ki dage ina kusa da ke, kar ki ji tsoro."
Yana gama fad'in haka ya bar gurin, cikin sauri, domin kar ya gan shi. Basma tana ganin ya tafi, tsoro ya k'ara kama ta, ga shi kuma mugun yana zuwa.
Kamal tun daga nesa ya hango ta, yana tafiya idon sa yana kanta. Wani irin shu'umin kallo yake bin ta da shi, har sai da ta tsargu. Ta ji gabad'aya ta k'ara tsanar shi.
Kamal yana zuwa, ko sallama babu ya ce
" Ga ni na zo me za ki mini?"
Cikin muryar 'yaniska yake magana, me za ki ban? Fad'a min mana. Basma ta kasa magana sai ja baya take yi, shi kuma yana bin ta.Tana kallon gurin da Amar ya nuna mata cewa ba za su bari ya yi mata, komai ba. Kamal ya cigaba da cewa.
"Me kike kallo ne a can ki yi magana mana."
Basma suna had'a ido da Amar ya yi mata nuni, da hannu a kan, ta yi magana. Cikin juriya kuwa ta fara magana.
"To me za ka yi? Na ce me za ka yi? Ko kana tunaninn ina tsoran ka ne,? To bari ka ji in gaya maka, Na kira ka nan ne domin in shaida maka, daga yau. In har ka k'ara shiga harkata, Wallahi sai ka raina kanka, ban za wawa. In ka isa ka taɓa hannuna, tana miƙa masa hannun, tanabin shi. Yana ja baya, kamar yanda ya yi mata d'azu. Ka ta'ba na ce in ka isa. Tana ƙara tura masa hannunta.
Kamal cikin mamaki yake kallon ta. Ya ce
" Ke ko kin sha wani abu ne?"
Yana maganar alamar storo a fuskarsa. Ya ce
"Na ga alama ba kya cikin hankalinki."
Za mu haɗu wani lokaci, ya ja yaransa suka bar gurin da sauri.
Basma lokacin da ta fara ganinn alamar tsoro a fuskarsa, hakanne ya ƙara mata, ƙwarin guiwar cigaba da abin da take yi. Ta yi mamakin ganin bai iya yi mata komai ba.
" Ashe ma mugun matsoraci ne."
Ta fad'a a fili daidai lokacin da Amar ya ƙaraso gurin.
Amar ya ce
"Da ma na gaya miki yanzu ga shi kin gane, ko shi ɗin waye."
Cikin jin dad'i, ta ce
"Amar na gode sosai."
Ta zo da gudu ta rungume shi tana dariya. Amar wani abu ya ji, lokacin da jikinsu ya had'u guri d'aya. Kasa yin magana ya yi, har ta sake shi ta bar gurin. Tana farin ciki ta nufi cikin School.
Amar, tsayawa ya yi a gurin kamar wanda aka kafe, shi yana bin ta da kallo. Har ya daina hango ta, kafin ya ja numfashi, ya bar gurin yana murmushi.
Tun daga ranar ala'karsu me 'karfi ta shiga tsakanin, Amar da Basma. Rawar ma yanzu ba sosai yake koya mata ba.
Ɓangaran Kamal kuwa tuni, yake shirin yadda zai 'bullo mata.
Gobe za ba da hutu school kuma gobe za a rufe, school d'in. Kuma shi Amar wannan shi ne, final year d'insa.
Suna zaune su biyu suna zancen makomarsu, in aka ba da hutu, ya za su yi. Basma Tun lokacin da ya raba ta, da Kamal take jin sa a a zuciyarta. Hakan ne ya sa, take ganin ya dace su samu mafita.
Basma ta ce. Amar, cikin wata irin murya. Bai kar'ba mata ba ya juyo yana kallon ta ta ce.
"Wannan k'warin guiwar da ka ba inda da soyayya a cikin ta, ya za ta kasance? Please ina so ka kasance a rayuwata har abada. Amar na yarda da kai please."
Tana gama fad'in haka ta tashi ta bar gurin, shi kuma ya bi ta da kallo ya kasa magana.
Har ga Allah yarinyar tana burge shi, amma kuma shi halaiyarta ne suke ba shi mamaki. Domin ita ba ta kunyar ta rungume, shi a gaban kowa. Ko kuma ta gaya masa kowacce irin, magana ta zo bakinta. Amma in ba haka ba yarinyar ta yi. Haka dai yake ta tunanin. Abin yi .
Amar ne a gaban mahaifinsa, wato Farfesa Salisu. Shi ma a makarantar yake koyarwa, ya dubi yaron nasa ya ce.
"Gobe za a ba da hutun school, kuma kai gobe za ka gama gabad'aya. Ina son in sanar da kai cewa, har na sama maka, aiki a Abuja. Domin can na ga za su fi biyan albashi mai kauri."
Yana gamawa Amar ya ce.
" Baba ni ba zan iya barin garin nan ba!"
Wace ce yarinyar nan da nake, ganin ku tare a school?"
Ya tambaye shi.
Ya ce. Basma ce.
"Saboda ita ne ba za ka bar garinnan bako? To ni dai na gama magana. Ba ni da darajar da zan sama, maka aiki a cikin garin nan."
Amar ya ce.
" No baba zan samu wata makarantar na dinga koyarwa kafin wani lokaci."
Abbansa ya ce.
"Oho dai in ka ga dama kar ka koyar da kowa, ka tsaya kai ta yawo a gari. Kana koyar da rawa da ba komai kake samu ba."
Ya ce
"Baba kar ka damu na kusa zama wani abu."
Ya fad'a cikin dariya.
______Basma
Cikin tunanin abin da zai ce mata ta dawo gida, tana zuwa gida wanka ta yi. Sannan ta fito Parlon gindan ta zauna, tana tunani. Can ta mi'ke tsaye ta nufi d'akin daddy tana shiga ko sallama babu, ta tura k'ofar d'akin. Ta same shi, shi da Little suna shan kankana. Tana zuwa da gudu ta nufo shi, shi kuma ya ware mata hannu ta fad'a jikinsa. Cikin shagw6a ta ce
"Daddy ni gaskiya wani abu nake so kai mini."
Ya ce
" Gaba 'yar daddy me kike so? Ko mene ne, ki fad'a mini a shirye nake da yi miki."
Bayan ya d'auki kankana, ya saka mata a baki.
Ta ce
"Daddy ka san gobe ne za a ba da hutun school ko?" Daddy ya ce
" E na sani me ya faru? Ta ce.
"Daddy wanda yake koya mini rawa ne, nake so a kawo shi gidan nan. A rik'a biyan shi yana koya min rawa, tun da bai samu aiki ba ka ga sai ait's dinga biyan shi kud'i mai yawa ko daddy?"
Ta k'arasa maganar, ita ma tana saka masa kankana a baki.
Sai da ya shanye kankanan Ya ce.
"Wannan ai ba wata damuwa ba ce, 'yar daddy, kar ki damu ki fad'a masa ya zo ya same ni za mu yi magana da shi kin ji."
Cikin farin ciki ta manna masa kiss 💋 a goshi ta ce "I love you my daddy"
Tana fad'a, ta tashi ta ri'ke hannunn little, suka fita Izuwa d'akinta.
Waya ta d'auka ta kira shi bai d'aga ba. Hakan ya sa ta yi masa text message sannan. Ta kira Lubna ta ce ta zo gida ta same ta za su yi magana.
Amar ne tare da Alhaji Sani wato baban Basma , Bayan ya gaishe shi, Alhaji Sani ya bi shi da kallo daga sama har 'kasa, Sannan ya ce.
"Ya sunanka?"
"Sunana Amar"
ya ba shi amsa.
Daddy ya ce ya yi kyau.
"aikin me kake yi?"
"Na kammala P h d yanzu haka ina jiran aikin yi ne."
( SLHAJI SANI FA BEYI KARATUN BOKOBA KAR KU MAN TA)
Daddy ya ce.
"Wato karanta tsare-tasre ko?"
"Amar ya ce.
A'a ana nufin 'kididdiga Kenan."
Daddy ya ce.
"Kana nufin ka ce mini kana da takardun kammala Karatu ko? To ni ba wannan nake son sani ba. Ina son sanin taya kake samun kud'i wani aiki kake yi yanzu?"
"Ya ce
" ina d'an koyar da rawa Ana biyana."
Daddy ya ce.
" To daga yau ka daina koyar da kowa. Sai yarinyata sannan za ka dawo gidan nan da zama har zuwa lokacin da za ka samu aikin yi."
Cikin mamaki yake bin daddy da kallo. Saboda ya ji ya ce zai dawo nan.
Daddy ya ce.
" Kar ka damu wannan tsarina ne zan dinga biyan ka dubu 50, a kowanne wata. In dai har Basma ta ji dad'in zama da kai."
Jin kud'in da aka ce za a biya shi ne ya sa ya fasa fad'in abun da zai ce sai godiya yake yi cikin jin dad'i, ya tashi ya bar Parlon.
Yana fitowa ya kira ta a waya domin tun da ya shigo bai gan ta ba, tana d'agawa ta ce zan kira ka leter "ok" ya ce.
Haka ya je ya sami Abbansa ya gaya masa, duk abin da ya faru. Amma bai ce masa a gidan zai zauna ba. Don kar ya yi sa a abbansa ya amince.
Washegari haka ya sanar wa da Sadam` shi ma ya yi masa fatan Alkairi.
Bayan ya iso gidan ne Alhaji Sani, ya had'a shida Ali` wanda yake cikin gidan A kan ya nuna masa 'barin da zai zauna.
Suna cikin tafiya ne.
Ali ya ce
" Wannan gidan da ka shigo yana da hatsari sosai` za ka iya yi wa kowa laifi har da Alhaji ya bar ka amma kar ka ta'ba 'yarsa."
Amar ya ce " Ai kuwa ni ma kar ta mini shirme, domin ni ina zane mutane mutuk'ar suka yi ba daidai. A gurin koyar da rawa."
Ali ya ce
"Nan shi ne gurin da za ka zauna ba kowa sai kai ka kad'ai. Can da kake gani sashina ne ni da matana, ba na shekararmu 25 da yin aure amma har yanzu Allah bai ba mu haihuwa ba.
( *ALI IRIN MUTANEN NAN NE MASU SHEGEN SURUTU* )
Amar ya ce
" To Allah Ya ba ku yana zama a kan kujerar da ya gani a cikin d'akin."
Mash Allah! Abubuwa suna tafiya daidai, inda soyayya tsakanin Amar da Basma ta girma kuma Babu wanda ya sani a cikin gidan .
Kafin me afkuwa ta afku yanzu ne za a fara, Cakwakiyar yanzu ne komai zai fara faruwa. Yanzu za a shiga labarin asalin abin da zai faru.. 📝✍️
*TO FA! YANZU ZA A FARA RIKICIN ABUBUWA ZA SU FARA FARUWA , KUDE KU KASANCE DA NI* ~S REZA~
~HAQIQA ALK'ALAMI YA FI TAKOBI ✍️📝~
The end fart 3️⃣
To be continue...✍️
*ALK'ALAMI S REZA..✍️*
PLEASE COMMENT AND SHERE DON ALLAH 🙏🤣
*BY S REZA ON LOVE*
[12/23, 6:01 PM] +234 810 078 5178: *CHAKWAKIYAR SOYAYA*
NA

S REZA



©🎆
*Al'umma Writers Asso...✍🏻*

_{Al'umma writers,Ƙungiya ɗaya Tamkar Da dubu Farin Cikin mu, mu faɗakar da Al'umma domin su Farfaɗo su gane gaskiya Al'umma sai Dan Al'umma ,Allah ya bamu Ikon fadakar da Al'umma}._
https://www.facebook.com/102282991949826

بسم الله الرحمن الرحيم...
*SADAW KARWA GA*

```MAMAN ADNAN🥰 BADAN HALIN KIBA. WANNA NAKINE KEDA ADDNANM`DAKUMA ABBAN ADNAN🙏```

CA'KWAKIYAR SOYAYA
PAGE ⚓️ 4⃣

....... Amar. Zaune Yake akan Mashin d'insa Yana jiranta, Amma shiru yakai 30mt, Agurin yana jiran ta har yafara tinaninn komawa gida, Se jinyayi tace "Sorry Amar Walhi daddy ne yakeson jin ina zanje, Kuma mezan jeyi Shinefa na shirgamasa 'karya Shine yasa kaga nadad'e, Tana magar nar tana 'ko'karin hawa kan mashin din. Amar yace "to yanzu wani 'karya kikamasa Har yabarki. Basma tace "kai nifa ban iya garyaba, Rasa irin 'karyar dazan Masa ne, shine kawai nacemasa, Zamufita Yawon sha'katawa ne nidakai. Cikin wani mahaukacin Tsoro Amar yataka birkin mashin d'in, Yajuyo yana kallonta, Yace.. "Please Dagaske Haha kika cemasa?

Basma cikin dariyar da take 'boyewa Tafito fili tace.. "eh mana Ai nacemaka ban iya 'karyaba Shine kawai nafad'a masa gaskiya, kuma bagashi ya barmuba, Tagarasa tana dariya🥰,

Please Login or Register in order to submit comment