You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

dake ranka,
wasu matan sunfi son saikun fahinci Juna tukunna kafin ka baiyyana musu sonka atare dasu



Ajiyar zuciya yasauke, yanemi waje yazauna



Afili yace gaba dayama bazan fadi Ko dayaba, kawai zanbi shawarar mamy, datace nafada mata Cewa da
Aure nake Santa

May be Tunda Nabi shawarar mahaifiya saina dace



Da wannan shawarar yayi amfani wajan dauko wayarsa yabude data, Kai tsaye whatspp yahau



Yaduba number dinta, yatura mata da "hi"



Kuma sai akai dace adede lokacin tana chatting ne da yusy



Ganin sabuwar number taturo mata da hi, Kuma gashi batasan number dinba, hakanne yaja hankalinta
wajan Bude saqon



Yana ganin alamun an Bude saqon yazuba tagumi yace to Allah gamu gareka
Kai tsaye tatura masa tambaya "waye?"



"Sunana Aliyu Sa'ad "



Afili ta furta Aliyu Sa'ad Kuma?

Waye Hakan?



Tambayarsa tayi Cewa" waye?

Kuma wakake nema?



Yace "ke nake nema"



"kasan dawa kake magana kuwa? "



Shima anasa bangaren yatura mata Cewa" da Yaya Iman "



Mamaki ne yakamata, to wannan duk Yanda akai may be yasanta sosai, Tunda Har yasan ta da wannan
sunan



" me yake faruwa?

Abinda tatura masa Kenan



Shima yace "inasan nakiraki idan kin bani damar Hakan"



"no, kafadamin menene, Bana buqatar Kira "
Afili yafurta" tofa"



Achat din saiya tura mata Cewa, "Sunana Ali Sa'ad Bilal, Kamar Yanda nafada Miki, Ina aiki ne tareda
Rundunar sojan Sama ta Nigeria, naganki ne aghana, inason na Aure ki"



Daria maganar ta Bata, Saida Tasha dariyarta, Afili tace wannan wanne irin mutum ne? Kuma ma Wai
soja, Anya kuwa yasan Yanda ta tsani sojoji, kwata Kwata basa birgeta



Amma acht saita ce masa 'thank you "



Shikuma yarasa me zai fada mata, Kenan Bata sanshi ne kokuma tana sanshi, me wannan thank you take
nufi



Tambayarta yayi, Zaki Iya Aure na?



Itama tatura masa Cewa bansankaba, bantaba ganinkaba, kawai Daga haduwa a cht sai in amince inyima
alqawarin Aure?



Kansa yashafa, zuciyarsa tafara daukar zafi, gabansa na faduwa yace mata, ga pic Dina Nan a dp, ki duba



Abangaren Iman kuwa mamaki ne yake sake kasheta a zaune, wannan wanne irin mutum ne? Kana
neman Abu a wajena Amma aji za'ace kokuma girman Kai yahanaka yin biyaiya



Wato pic dinma bazai Iya turo mataba, saide ita tabude, inta matsu



Shikuma anasa bangaren Bai fadi Hakan dawata manufa ba, shide na farko Bai saba hulda da yanmata
ba, bare yasan abinda suke so Ko abinda basa so, sannan shi aganinsa atsaya Ana wani kece farin cikina,
kace kaza Dina, duk ba abin birgewa bane, shi yafi San idan kana San Abu, toka nuna abaiyane Kuma
agaban kowa
Abinda yasani shine Allah yadasa masa soyaiyarta acikin Zuciyar sa Yanda baya zato



Iman batayi qasa agwiwaba tabude pic din Naka



Photo ne dayayi shi acikin jirgi, yana gefen window, da farin kaki ajikinsa na sojan Sama



Saving pic din tayi a wayarta, sannan tace masa Amma Kai fulani ne Ko?



Sai a sannan yayi dariya harda gyara zama ganin tafara kulashi, yace no, babu wani fulani, ni bahaushene
dan'uwanki



Itama tatura masa Cewa ai ni ba bahaushiya bace



Yace sorry namanta, ashe fa ke Shuwah ce



Afili tace Wai wannan mutumin ya akai yasan abubuwana dayawa ne?



Bata bashi amsaba yace nabaki dama kiyi bincike akaina, Kuma kiyi tunani idan Zaki Iya Aure nah, Ki
gaida Bilkisu Bye



Yana gama tura mata yasauka online



Gaba dayama tarasa tunanin mezatayi, wakuma zata fara tunkara da wannan magana? Billy batanan
tana katsina, Amma ga yusra Nan ai Suna chatting Bari tabata labari
Ta chat din takira yusy tace Besty akwai labari, yusy tace Kai Teemah saboda tsabar gulma Akan ki
turomin saikin kirani

Iman tace inaa ai babban labari ne yafi karfin chat

Yusy tace to qawata bani Nasha

Iman ta kwashe komai tafada mata, harda pic dinsa ma duk tatura mata

Yusy tace 'Besty Anya kuwa ba qarya yake Miki ba? Ba irin samarin unguwa bane Yan renin sense?



"Nima abinda nayi tunani dafarko Kenan Besty, but abinda zai baki mamaki shine harfa Bilkisu yasani,
Wai harda Cewa Yaya Iman, sannan Wai ni Shuwah ce



Yusy tace to yanzu yaza'ayi?



Nikam yusra ai ban Isa in saurari waniba, Bayan ga Yaya Imran, Kinga wannan pic din nasama Ina turo
Miki nagogeshi a wayata, gudun matsala, Wai harda Cewa aghana yaganni, inba qaryar mazaba aghana
a'ina? Muda ba yawo mukeba



Yusy tace a a karkice komai, Tunda yafadi Hakan nasan ba zaiyi qaryaba, Tunda naganshi babba ne,
yanzu abinda za'ayi shine Tunda yace kiyi bincike akansa, kiyi din mugani waye shi



Nifa ba zanyi wani bincikeba yusy, kawai zan bashi hakuri in fada masa inada wanda zan aura



Yusy tace karkiyi haka Iman, bahaushene fa yace so Mai sonka, ke zakiji dadi idan Allah yadora Miki son
wani daban, ki tunkareshi kifada masa Amma aqarshe irin wannan amsar tabiyo baya?



Ki lallabashi ku Rabu lafiya, ni aganina hakanne mafita, Kinga kun Rabu lafiya, Shima beji haushinki yaje
ya dirka Miki wani asirin ba



Tanajin zancen asiri tace na shiga ukuna
Yusy tace a a bafa Cewa nayi zaiyi Miki asiri ba, kawai de nafada Miki abubuwan dasuke faruwa ne
gameda wasu samarin idan kace Baka kaunarsu



Cikin sanyin jiki Iman tace to yanzu Yaya zanyi?



Yusy tace menene sunansa?

Kai tsaye Iman tace yacemin sunansa Aliyu Sa'ad, Kuma shidin sojan samane na Nigeria



Yauwa Kinga saimu bincike mugani inma qarya yake ai zamu gani, inji yusy



Iman tace to tayaya zamu bincika?



Yusy tace kadaa ki kashe wayar Bari naduba sunayen sojojin Sama a Google nagani, inma babushi ai
zamu gani



Iman tace toyi sauri Ina jiranki



Yusy batafi minti biyar ba tasaki ihu ta cikin wayar



Iman tace Besty karki kashen kunne, yusy tace Iman wallahi Ina searching sunansa naganshi, shine
shugaban sojojin Sama na Nigeria baki daya



Sunansa kawai nasaka, Amma anturomin harda pic dinsa, Kuma shine de wannan wanda kika turomin
ajikin pic din



Shikkenan Besty keda bakyason soja, gashinan kin kwaso shugaban su
Ajiyar zuciya Iman tayi, sannan tace zan fada masa gaskiya Besty, bazan boye masa komai ba, karma
yaga narabu dashi yayi zatan na yaudareshi



(Yaya kuke ganin Aliyu zaiji idan Iman tafada masa gaskiya?)



Duk wanda yaga banturo masa WAZAN ZABA a group dinsaba, to banga sharhi bane

Idan anjini Shiru, tokada anemeni, Nima najika Shiru ne



Mrs Usman ce WAZAN
✍🏻 ZABA? 💖



Writing by Amnah El Yaqoub



Bissmillahir-rahmanirraheem




8



Da wannan shawarar ta yusy Iman tayi amfani, wajan kawar da maganar Aliyu Daga cikin ranta, tama
manta dashi taci gaba da sabgogin gabanta



*** *** ***

Tunda sukai wannan mgnr da Iman acht ya tsinci kansa cikin farin ciki, shida kansa yasan yasauya, komai
yanayinsa cikin walwala, hatta da abokan aikinsa sun fahinci Hakan, saide musty ne kawai yasan sirrin

Mamy kanta tana lura da yanayinsa, saide tayi Murmushi taqara godewa Allah, daya karkato mata da
hankalin danta izuwa abinda takeso
Kamar Koda yaushe yauma break sukeyi shida mamy, atika tana goge kayan falon, Bayan tagama
mopping

Ruwan tea yakesha Amma wayarsa tana hannunsa yana danne danne, wanda azahiri pic din Iman yake
kalla, mamy data kula hankalin sa baya Kan abincin

Tayi Murmushi tace" baby mekake kalla ne bakasan cin abinci? "



Kamar wani marar gaskiya haka yadauko wayarsa yanuna mata screen din wayar,

Pic din Iman tagani, tace to yanzu Haidar aida kabari kagama saikaje kayi ta kallanta Ko"



Babu kunya Aliyu yace "mamy ai idan Ina ganin photon zanfi cin abincin?"



Girgiza kanta mamy tayi, tace um duniya Ina Zaki damu?

Wai yau Kaine me kallana kace in kana ganin girl friend dinka zakafi cin abinci



Sai a lokacin ya lura da katobarar dayayi, ashefa mamy ce

Dan haka kawai saiyayi Shiru yana sosa kansa, wayar ya ajiye asaman dining din sannan yamaida
hankalin sa Kan tea din dayakesha



Mamy data zuba masa ido tana kallansa cikin ranta tace damafa hakane, duk wanda zakaga baya kule
kulen yanmata, Ko Kuma yanmatan Suna sonsa baya saurarensu qarshe sai kaga soyaiyar wata daban
tana wahalar dasu



Farfesun datasa atika tayi, tadauko flet tazuba masa, spoon tasa tadiba ta nufi bakinsa dashi, tace "dauki
wayarka kayi kallanka, saina baka abincin,

Shima baiyi musuba yadauki wayar, yana kallan pictures din Iman mamy Kuma na bashi abinci



Saida ta tabbatar ya qoshi sannan ta qyaleshi
Tissue yadauka yana goge bakinsa, yace" mamy ai dole ne inkira Bros awaya in bashi labarin yarinyar
Nan, "



To ai daka Bari idan muka koma gida saika fada masa, Nima sainayiwa Yaya magana, kaga sai manya su
shiga cikin maganar



" to shikkenan mamy nah yanzu Bari inji muryarsa kawai, ni kada ma yayi fishi, kullum saide yakirani
bancika nemansa ba



Ringing biyu wayar tayi, akayi picking Daga dayan bangaren

"Bros ya akayi?

Aliyu yace "normal ya gida ya harkoki, dafatan mutanan gida kowa lafiya



Lafiyarmu kalau Bros, kasan akwai wasu zafafan motoci Ahmad muhd marzuq yakawosu Daga Cairo,
inaso saika dawo Nigeria saimuje mu siyosu, but yaushe zaka dawo ne,? Saina tura masa da kudin da
wuri



Murmushi Aliyu yayi, yace no, wannan Karon bakaine zaka siya manaba, nine zan siya mana



Shima yace no Bros



Aliyu ma yace karka damu, ai ABIN BROS NA BROS NE



Daria sukasa gaba dayansu, sannan sukai sallama



Mamy tace wato Aliyu bazaku Dena wannan sarar taku bako?
Yana Daria yace mamy ai wasa ne kawai



*** *** ***



Tundaga wannan lokacin Iman Bata sake magana da Aliyu ba, Har tsawon kwana biyar, adede wannan
lokacin Har hutunsu yaqare sunkoma school, sai yau yayanke shawarar kiranta awaya, domin yasan
Cewa Zuwa wannan lokacin ai ta Riga data gama yanke shawara



Tana zaune adakinsu ita kadai, su Billy sun fita itada yusy, taji wayarta na ringing

Zuciyar ta daya tadauka, cikin Isa da taqama irin tasa yayi Mata sallama



Bata Gane wayeba, kawai de abinda tasani shine taga number wata qasar tana kiranta, amsawa tayi
tareda Cewa waye



Agajarce yace Ali Sa'ad



Lokaci guda ta ganeshi, tace OK yakake



Kai tsaye yace Alhmdlh,



Dama nakirane inji Yaya kike, sannan Kuma me kika yanke game da maganar da mukayi



Handout din dake hannunta ta ajiye tace kasan abinda ake nufi da Trailer irin babbar motar Nan?



Da mamaki yace nasani mana,



To Kamar haka samari na suke, inada samari dayawa, akwai wanda nakeso, da Kuma wanda banaso
Cikin yarda da Kai da Kuma ji dakai irin nasa yace "zanso shiga daya Daga cikin wannan motocin, harma
nazama nine nake Jan motar watarana



Taqamarsa ce tasata Daria, tace bazaka iyaba, domin sudin ba qananun qwari bane Kamar Yanda kake
tunani



" kidena hadani da irin wannan samarin, nasan kaina, ni ba irin su bane, Zaki Gane hakanne idan kika
bani dama guda daya tak, damar kuwa itace ki amince da soyaiya ta, zakiga Yanda zanyi fatali da
gwamnatin kowa, tawa gwamnatin ce kawai zata mulki birnin Zuciyar Ki



Aranta tace waishi irin jiji da kannan zai nuna min, nikuwa zan nuna masa yayi kadan, zanga karshan
qaryar tasa



Domin ta qureshi tace shikkenan nabaka dama



Wani sanyi yaji acikin ransa, Murmushin Nan take ya wanzu a fuskarsa yace godia nake MATAR ALIYU



yakashe wayarsa



*** *** ***



Wayar ta riqe a hannunta cike da mamaki, afili tace waishi ji yake irin babban qwaron nanne a soyaiya



Karatun ta taci gaba dayi, tana cikin karatun su yusy suka dawo



Suna zama ta dubi yusy tace Besty wannan gayen fa yakirani yanzu, Nan tabata labarin komai
Yusra tace ai kuwa zamu qureshi, muga karshan cika bakin nasa



Bilkisu tana jinsu tatabe baki tayi Shiru, to basu sata acikiba, yanzu tana magana Yaya Iman zata hauta da
bala'i



*** *** ***

Tundaga wannan lokaci Aliyu yafara shigar da kansa awajan Iman, Kiran safe daban, na Rana daban na
dare wannan daban ne



Wataran tayi picking wataran Kuma ta share shi



Duk lokacin da taqi dagawa yusra ce maiyi mata fada Akan ta saurareshi ai Suna so su qureshi ne



Ahankali take kulashi, harya kasan ce kullum sai sunyi chatting



Kamar kullum yauma Suna chatting taje tasaka pictures dinta a status masu zafi

Bata dauki lokaci dasakawa ba, kiransa yashigo cikin wayarta



Tana dagawa, yace "kije kicire pictures din dakika saka yanzu,



" meyasa zan cire? "

Damafa Ina sakawa



Zuciyar sa na quna yace nasani, nikwa nasan kina sakawa, Amma abinda nakeso kisani shine, Ina sonki,

Qasa yayi da muryarsa cikin Shagwaba yace" Ina kishinki Iman, bazan Iya ganin pictures dinki wasu
mazan Suna kallah ba
"batasan meyasaba haka kawai ta tsinci kanta da Cewa to shikkenan Bari nacire



Tana cire pictures din, tarufe datar Tama gaba daya

Duniyar tunani tafada, shi wannan yana sonta, yana kishinta bayasan wasu mazan suga pictures dinta

Haqiqa kowacce mace tanaso asota, Kuma nuna kishi shine alamun soyaiya, Aliyu halinsa daya yar'uwar
ta Bilkisu, inama ita yanema da farko, da halaiyarsu ta dace da Juna, Bilkisu tana saka Kaya na kirki na
mutunci, Bata da rigima, Kuma Bata da magana, Haka Kuma saka pictures dinta a yanar gizo Bai
dametaba




Shikuma wannan

yasonta, yana Bata kowacce irin kulawa, Amma Kuma shine yake kaita wajan photo da kansa tadauka,
harma tasa a Internet Amma Bai taba hanataba



It means yana sonta, bayasan ganin laifinta, yana Bata dama tayi duk abinda takeso



Runtse Idanunta tayi, kanta fa yafara daukar zafi



Jaruman maza guda biyu, ma banbanta awajan Halaiya



Yusra na bacci, Sai Billy dake zaune a gefe duk tana kallan duk wani motsi na yar'uwar Tata



Duban ta tayi tare da Cewa Yaya Iman ya akayi ne? Meyake damunki?



Wayarta ta ajiye a gefe daya, sannan takamo hannun yar'uwar Tata,
Bilkisu cike da mamakin yayar Tata tace Yaya Iman, keda waye kike waya yanzu?



Bata amsa mata tambayar tataba tace "Bilkisu idan mutum yana kishinka me Hakan yake nufi?



Manyan idanuwanta ta juya tace Yaya Iman Hakan yana nufin yana sonki ne mana



Jijjiga kanta tayi, sannan tasake jefo mata wata tambayar

" Tokuma yanzu misali kece mutum biyu suke sonki, daya yana kishinki, daya Kuma yana nuna Miki
soyaiya Amma Bai cika nuna Miki kishi ba, kullum zakici kwalliya ki fita babu ruwansa da wanda zai ganki
da wanda bazai ganki ba

Abu daya kawai yasani shine kece Muradinsa



Shin wazaki zaba acikinsu?



Murmushi Bilkisu tayi Kamar ba yar'uwarta ce take cikin damuwa ba

Tace "Yaya Iman, idan na fahinceki kina magana ne Akan Yaya Imran da Kuma wannan sabon boyfriend
din naki dakika yi, Yaya Iman ki godewa Allah, Yaya Imran yana sonki, yana qaunarki,, kowa dayake
familynmu ya shaida Hakan, bance Miki wannan sabon saurayin naki baya sonki ba, a a

Amma abinda Zaki duba shine, Yaya Imran dashi muka tashi, yasanki, kinsan shi, yana sonki, kina sonshi

To meyasa ma Zaki tantama a kansa?



Ki godewa Allah da baba yabaki dama kika saurari Imran, kinsan halin mahaifin mu Yaya Iman



Kina gani de, Ina zaune yakawo Haroon yace shine mijina, shine wanda zan aura, baya sona, Bana sonsa,
Amma ahaka nayi hakuri nayi masa biyaiya



Yaya Iman ni kadai ma na isheki ishara, dazatasa kici gaba dason Yaya Imran
Ni yanzu na Isa na saurari wani namiji Bayan Haroon? Ban isaba, Tunda umarnin babane Hakan



Maganar dakikemin ta innice wazan zaba Kuma, shine idan nice adduah zanyi, Allah yaciremin son sabon
saurayin araina

Shikkenan an zauna lafiya



Iman tace "nagode da shawarar Ki Bilkisu, insha Allah zanyi Yanda kika ce



Itama Billy cikin Murmushi tace yauwa Yaya Iman



Rungume Juna sukayi cike da kaunar juna



*** *** ***

Agajiye yadawo Daga wajan aiki

Hajiya dake sake gwadawa Zeey auta home work, ta dubeshi tace sannu Imran

Kaine bakasan zama, kullum cikin yawo kake



Cike da Shagwaba yace to hajiya ai hujjoji nake nema, Kuma yanzu ai shari'ar ma taqare, nine nayi
winning



Murmushi tasaki tace to Dana, Allah yaqara temakawa

Duban zainab tayi tace auta riqe littafinki nabaka Yaya abinci Ko?



Kyabe fuska yarinyar tayi alamun kuka

Imran na ganin haka yace Hajiya zauna, Naga alama Yan gidannan gaba dayansu kishi suke Dani
Ai Gara Zeey Akan Farhan ma

Kusha Zaman ku Bari inje inyi Sarving din kaina



Yana gama fadar haka yatashi yayi dinning



Bayan yagama yadawo wajan hajiya, lokacin zainab tatashi, kansa yashafa yana kallanta



Murmushi tayi tace Imran Dina, Kamar akwai abinda yake damunka Ko?

Sosa kansa yayi sannan yace Hajiya dama inaso ne kifadawa Alhaji idan su Iman sun qare semester dinsu
sun dawo, Dan Allah dasun dawo atsaida ranar bikinmu



Yana gama fadar Hakan, yatashi yayi part dinsa kansa aqasa



Ha'ba hajiya takama, oh yaran yanzu zai Ahankali, Imran Ko kunya babu? To dama Yanda ake wannan
rashin kunyar agabanta shida Iman, ai yaran nata Suna gamawa za'a tsaida lokacin biki ayi kowama
yahuta



*** *** ***

Kuka take sosai, Idanunta sunyi jajir, yusy ce me rarrashinta

Best ki fadamin mana me yake damunki ne Wai? Ko akwai abinda yake faruwa a gida?



Girgiza kanta tayi alamun a a

Yusy tace nashiga uku, Kinga Bari nakira Barrister nafada masa



Dasauri tariqe hannunta, cikin kuka tace yusy.... Pls.. Karki kirashi, nashiga ukuna Besty Yaya zanyi?



Nifa Iman kin dauremin Kai, Dan Allah ki sanar Dani me yake faruwa
Kasancewarta fara yasa kukan datasha yasa Kan hancinta yayi jajir

Cikin kukan tadago da kanta ta kalli Yusra tace

"Besty nashiga ukuna wallahi Ina sonsa"



Adede wannan lokacin Billy tashigo cikin dakin, wannan maganar ce tasauka akunnanta



Iman taci gaba da Cewa

"Bansan yaushe Hakan tafaru ba, bilkisu tabani shawara, Kuma nayi Amfani da ita, duk addu'oin
danakeyi abinma qaruwa naji yanayi

Halayensa, kulawarsa agareni, ajinsa da komai Nasa sunja hankalina, wallahi idan ban sameshi ba
ayanda nakeji cikin zuciya ta Besty akwai matsala

Nashiga ukuna, shikkenan nazama butulu ni Iman "



Cikin zafin rai Billy dake gefe aqame, tace" Butulu kuwa ta gaske Yaya Iman "

Dukansu Juyawa sukai suka kalleta, domin kuwa ba Susan da zuwanta ba



Cikin hawaye Iman tace Dr.



Daga mata hannu Billy tayi tace, babu wani Dr. Ayau Yaya Iman, wallahi kin bani mamaki, Har yaushe
Zaki Bari Zuciyar Ki takamu dason wani bare, bakisanshi ba, besankiba, haduwar network, Har yaushe
Zaki soshi Akan Yaya Imran?



Ina shawarar Dana baki Yaya Iman? Tsautsayin dayasa kika amince dashi shi zaisa kije kirabu dashi



Wani lokacin kina bani mamaki Yaya Iman, Wai kokin manta da wacece Hajiya awajanmu ne?

Halaccin Hajiya agaremu Dani, dake, da baba, kadai ya Isa yasa kiso Yaya Imran
Yusy dake gefe ta dafe kanta da hannunta duka biyu, tace ni duk kun dauremin Kai wallahi



Please ku fadamin wacece HAJIYA? Kuma Yaya kuke da BARRISTER IMRAN?



(tonima de inaso naji wacece hajiya,🤔)



(Anya kuwa Hatsaniyar da Iman ta debo me bullewace 😱😱?



Ba anan Hatsaniyar ta qare ba, fatana kuci gaba da hakurin bibiyata



Share

Comments

Sharhi



Mrs Usman ce WAZAN
✍🏻 ZABA?💖



Writing by Amnah El Yaqoub



Bissmillahir-rahmanirraheem



9



Alhaji Abubakar, shine cikakken sunan Mai gidan, gogaggen Dan kasuwa ne, daya Shahara aharkar Saida
yari
Yanada shaguna dayawa akano duk na Saida yari ne, mugun me kudi ne dayasan mutane dayawa
manyan Yan kasuwa dakuma manyan Yan gwamnati

Matarsa daya Hajiya Maryam, wadda ake Kira da Hajiya, tana business dinta a gida, tana Saida kayan
mata irin su less da shadda da atamfofi, idan mutum yatashi Aure kawai waya za'a yi mata tahada kayan
lefe saidai kawai katura mata da kudin ta account



Yawan sanyin halin ta da haba haba datake da jama'ah yasa mutane dayawa suka Santa

Kowa kataba Hajiya Maryam hajiya Maryam

Sai Maryam din tabuya, kowa yake kiranta da Hajiya



Hatta da yaran gidan Hajiya suke kiranta, Alhaji Abubakar da kansa Shima Hajiya yake Cewa



Ita Ana kiranta da Hajiya, shikuma suke kiransa da Alhaji, wani lokacin suce Alhaji wataran Kuma suce
Abba, Amma alhajin yafi yawa



Yanada zafi, musanman Akan iyalansa, shi mutum ne Mai magana daya, idan yayita tota zauna agidansa,
zaiyi wahala yayi Maka magana biyu



Kowa na gidan shakkarsa yake, more especially yayansa



Lokaci dadama saide yaran suyiwa Hajiya magana Akan su tunkareshi da magana, saide suce Hajiya
kifadawa Alhaji Abu kaza



Taurin Kai Gare shi Kamar mutanan farko

Mutum ne Mai aqida daya



Dansa na farko shine Imran, cikakken saura yi Mai aji dakuma qwalisa

Baida Yawan magana sosai, idan kaga yana zuba surutu tofa saide da Yan gidansu ne
Yana 33 years yanzu,yayi karatunsa na bangaren lauya degree da masters yanzu yana aiki A hight court
dake Garin kano



Sai Farhan dayake 23 year's

Yagama degree na farko ajami'ar ghanah



Saikuma yar auta wato zainab



Hajiya Maryam tanada yar'uwa guda daya, wadda suka tashi tare Kamar wasu Yan biyu sunanta ZAINAB



hawaye bilkisu dake bada labari ta share, sannan taci gaba dacewa,wannan ZAINAB din itace
mahaifiyarmu Nida Yaya Iman, agarin katsina aka haifemu, Bayan mun girma munyi wayo, Allah yahada
mahaifiyarmu da cutar asma, Bata dauki tsawon lokaci ba, tana Fama da wannan jinyar Allah yayi Mata
rasuwa



Awajan mahaifinmu mukaci gaba da zama, dagamu saishi a gida, yau muci me dadi gobe muci akasin
haka, kasancewarsa talaka



Ganin dagamu saishi a gida ne yasa mutane suka fara surutu Akan ya ajiye mu a gida shibai nemi mace
ya aura ba,da wannan damar Hajiya tayi amfani wajan nunawa baba tanason riqonmu yadawo hannunta



Bamusan dalili ba haka baba yaqi yarda, agabanmu Hajiya take zarya tsakanin kano da katsina, Akan
baba yabata mu Amma yaqi, daqyar ya yarda yabata Yaya Iman, nikuma na zauna ahannunsa, Kuma Har
gobe Bamusan dalilin dayasa baba baya Shiri da yan'gidan Hajiya ba, kwata Kwata bayaso yaga mun rabi
Hajiya, gashi Kuma itace kadai muka sani wadda zamu Kallah amatsayin mahaifiyarmu



Zamana da baba mu biyu a gida ne yasa baba ya auri wata yarinya Mai hankali nuriyya, muna kiranta da
anty
Yanzu haka yaranta biyu tareda baba, mace da namiji



Riqon Yaya Iman yana dawowa hannun Hajiya komai yasauya

Sai abinda Iman takeso akeyi agidan, ke Hatta abinci sai wanda Yaya Iman takeso akeyi agidan

Tasamu kulawa sosai, Baga Alhaji ba, Baga Hajiya ba

Saikuma Barrister daya dauki son Dunia yadora mata

Tunda tazo gidan, ya wayar mata dakai, kasancewarsa mutum wayaiye, duk wani abin gayu na qawata
mace budurwa Imran yayiwa Yaya Iman shi



Shine yakoya mata Yanda zata soshi tun Bamusan kanmu ba, Haka Hajiya Bata taba nuna mana wani
banbanci ba tsakaninmu da yaranta



Idan ta nuna ma to mu taso Akan yaranta

Kuma Har gobe idan kikaje gidan Hajiya idan ba fada Miki akayiba, bazakice ba itace ta haifemu ba



Umma kawai haifarmu tayi da renonmu nadan wani lokaci, Amma Hajiya itace komai namu



Duk zafin Alhaji, shi da kansa yana son Yaya Iman, domin kuwa da kansa yasai mata Mota, wadda muke
yawanmu aciki, muje duk inda ranmu keso



Yusy ta duba sannan tace Kuma ahakan idan ban Kira Yaya Iman da butulu ba, da wannne Suna kikeso na
kirata saboda tana nema taqi jinin Hajiya?



Sake duban Iman tayi sannan tace da kinqi da kinso Yaya Imran jinin Hajiya ne Kuma shi muka sani
bawani bare ba, Dan haka shi Zaki aura



Cikin fada tace wallahi bilkisu idan bakimin Shiru ba zan sabar Miki anan wajan
Itama cikin Haushi tace a a to Yaya Iman saboda me bazan fadi gaskyaba



Dakeda yusy Yanda kukaje kuka qullah haka zakuje ku warware



Baqin ciki ne yakama Iman, cikin kuka tace to Wai Dan Allah Nina dorawa kaina sonsa ne?

Nimafa haka naji, shikkenan Zaki zauna kinamin rashin kunya, Wai harda Cewa haduwar network



Shiru bilkisu tayi tana kallan yar'uwar Tata da karfin Hali

Tace ikon Allah, to Yaya Iman ba haduwar network din bane? Qarya nayi?



Itama cikin kuka tace Ko haduwar iska ne ahakan Yamin, Kuma inasonsa, bazan Dena sonsa ba, inyaso
Haushi yakashe ki



Abin natama saiya Bawa Billy Daria, Dan haka batace mata komai ba, tayi Daria kawai ta kwanta, tareda
juya musu baya



Sai asannan yusra tasaki nannauyar Ajiyar zuciya, tace Gaskiya Teemah al'amarin Nan ba Dan qarami
bane, ni inda nasan tun farko haka kuke da barrister gaskiya da bazan baki damar kallan namiji Bama
bare ince ki saurareshi



Kanta ta Jijjiga cikeda gamsuwa sannan taci gaba da Cewa Barrister mutum ne Teemah

Dole ki Rabu da Ali Sa'ad



Cikeda masifa ta Daga Kai ta kalli yusra tace dallah malama Niki kyaleni, duk ba kece kika sani kulashiba,
Kuma yanzu zakice narabu dashi, anqi arabu dashi din, banzaye kawai
Tatashi fuuuuuu tayi waje



Billy najinsu tana ta Daria qasa qasa, ita kadai



*** *** ***



Kinsan me?



Teddyn dake gefen gadon ta taja ta rungume sannan tace "um um saika fada"



Inaso ne kibani dama nazo Ghana naganki, but da sharadin saina gama da wannan seminar din



Cikin shauqi da Jin dadi tace kabari saina koma Nigeria saikazo, saboda yanzu semester dinmu yayi Nisa



Shima cikin wani irin shauqi yace kin amince Bayan kin koma Nigeria nataho Nida mamy nah duka muzo
gidanku?



Batare da tantamaba tace why not



(nikwa nace jama'ah a wanne gidan 🤔🤔)??



Zara zaran gashin idanunsa ya Lumshe cikin Jin dadin Yanda yasamu karbuwa awajan ta, yasan Cewa
Zuwa wannan lokacin idan baiyi fatali da kowanne namiji acikin ranta ba Toya kusa

Domin tabbatar da Hakan saiyace Ina samari?



Zuwa wannan lokacin babu kowanne irin tsoro acikin Zuciyar Iman, Yanda take jinsa acikin ranta gani
take bazata Iya boye masa komai daya shafeta ba
Dan haka tace, samari Suna Nan kalau



Cikin taqaicaccan Murmushi yace, wato ban koresu ba Kenan duk Suna Nan Kamar da



Wannan karfin halin nasa yana birgeta, yanada iko Kamar wata Matarsa

Tace, kayi nasarar korar kowa but banda mutum daya



Cikin mamaki yace waye Hakan?

Kai tsaye tace MURADINA



mamaki ne yakamashi yace shikuma hakane sunansa?

Idanunta alumshe tace bahaka sunansa ba, kawai de munhana Juna fadar sunanmu ne, saide wannan
sunan



Cikin dakiya yace Zanso kituromin pic din wannan muradin naki naganshi



Kai tsaye tace OK, tareda kashe wayar



Zuwa tayi tatura masa ta whatspp, already yana online Dan haka Nan take ta tura masa pic din

Please Login or Register in order to submit comment