You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

kawai inkunason injidadi Kuma kuga posting Akan lokaci kazuba min
sharhi nafijin dadinsa fiye da godia)



Har yanzu muna Kan shinfida ne, bamu nutsa cikin labarin ba



Mrs Usman ce WAZAN
✍🏻 ZABA?💖



Writing by Amnah El Yaqoub



Bissmillahir-rahmanirraheem



5



Kamar kullum yauma uniform ne ajikinsa saide nayau kalar blue ne, sosai kayan yakarbi jikinsa, wata yar
qaramar bindinga ce asoke ajikin aljihun wandonsa na baya

Shiru yayi yana nazarin kitchen din Kamar wanda yake neman wani Abu daban

Yanzu akansa Har abin yakai Ana Kiran mamynsa awaya Ana fada mata magana? Shikuwa wanne irin
yarone?

Ajiyar zuciya yasauke Mai karfin gaske, Daga bisani yafara magana shi kadai acikin ransa

Insha Allah nasaka araina Cewa Daga yau zansa adubamin yarinyar data dace in aura, basai naganta ba,
inde anganta Kuma halin ta yayi, to zan Aure ta domin mamy



Yana gama maganar yafuto Daga kitchen din cikin fara'ah yayi wajan mamy wadda ta rafka tagumi tana
tunanin halin da Aliyu yasata



Ta Bayan kujerar da take Kai yazagaya, yadora kansa Akan kafadarta, tanajin qamshin turarensa ta share
shi, Murmushi yasaki shi kadai

Cikin Murmushin yace mamy nah kinsan wani Abu?
Batayi masa maganaba kawai de ta girgiza kanta



Wayarsa yadauko Daga aljihun sa, data yabude yashiga Google, Bansan meya bincikaba, naga yazagayo
yazauna kusa da ita

Wayar tashi yamiqa mata, yace "mamy Kinga wannan materials din Kamar zasuyiwa qawayenta kyau
ranar dinner Ko?"



Asheqe ta dubeshi tace "wa Kenan?"



Shima Sarai yagane a kusa take, Yanda tayi kicin kicin da rai ne Daria taso kamashi

Bai Iya boyewaba Saida ya murmusa

Sannan yace "mamy matata mana, wadda nake San aura"



Tanajin Hakan tasaki ranta, harda qara matsowa kusa dashi tana kallan material din, tace "Kai Amma
yayi kyau gaskiya"



Wani irin dadi yaji acikin ransa, ganin mamyn nasa tasaki ranta



Wani less yanuna mata, yace wannan Kuma Kinga zaiyi muku kyau, keda mutananki



Wannan Karon mamy karbe wayar tayi, tace wow, gaskiya baby ka Iya zaben Kaya, Kamar kashiga Raina,
Amma de kungama dedetawa da yarinyar Ko?



Hannunsa yadora akansa yana Sosa qeyarsa yace "a a mamy Wai idan Allah yakawo"



Haidar tashi kafice kabani waje
Mamy yanzu idan akai ordering dinsu tun yanzu ba shikkenan anhutaba idan bikin Yazo



Saboda bacin rai Kasa yi masa magana tayi, kawai hanyar kofar fita Daga falon ta nuna masa



Yana shafa Lallausar sumar kansa ta fulani, yace to mamy, ankirani meeting na gaggawa yanzu, saina
dawo "



Shiru tayi ta qyaleshi



Beyi Shiru ba, yasake Cewa" kinji "



Nanma Bata kulashiba



" kinji mamy na tafi "



Dan tausayi yabata Dan haka tace" naji Haidar Ala kaika lafiya "



Daria yasaka sannan yafice Daga falon cikin takunsa na qasaita



*** *** ***



Shiru dakin nasu Kamar babu kowa aciki, kowa yariqe waya yana abin gabansa, Iman ce tasaki tsaki, yusy
tadubeta



" me akayiwa Besty nane? "

Wlhy wata shegiyace Naga tasa pic din barrister a Instagram, wallahi na tsani yarinyar Nan"
Besty tace "wacce yarinya Kuma?"



Ke babba cefa ba yarinya ce irinmu ba, kullum batada aiki saide takirashi awaya, kiji tawani maqe murya,
hello babban barrister ya gida "



Cewar Billy



Daria ce takama yusy Saida ta Dara sannan tace" Kuma Ke Iman kina gani kika qyaleta? "



Iman tace Toya zanyi yusy, yanzun nasan inda tasamu pic dinsa, bashi yabata ba



Billy tace a a Yaya Iman karkiyiwa Yaya sharri, dagake harshi takanas kuke Zuwa wajan photo ayi muku,
kawai na dorawa a dp ne, Kinga kwa aikonice tunda Naga Ana sakawa dole nadauka, ni wallahi innice
Itama Bayan nasa pic din saina rubuta my fiance to be



Dallah malama kiyiwa mutane Shiru, Kamar antambayeki sai wani zuba kike

Cewar Iman



Yusra ce takatse musu zancen dacewa, Kai Kai Iman Billy kunga wani video danagani yanzu a net

Wallahi wasu sojojine suke karya kafar kidnappers

Suko Imani ma basu dashi ne Besty

Tafadi maganar tana duban Iman



Billy ce tace Kai Kai bani nagani yusy, tasa hannu ta karbe wayar Daga hannun yusy



Cikin Jin Haushi da bacin rai Iman tace yusy, Dan Allah idan zakuyi haukanku kudena sani aciki
Ke waye yafada Miki sojoji mutane ne?



Billy tace to Yaya Iman sudin aljannu ne?



"ni bance Miki aljannu bane, kawai de ni arayuwata Bana qaunar soja, kokadan basa birgeni "



Yusy tace Toda Imran dinki soja ne Yaya zakiyi?



Bana fatan haka Besty, wataran kana zaune acikin gida za'ayi sallama dakai amiqama takarda, kana
budewa zakaga sunan mijinka yafada cikin wadanda suka mutu awajan yaqi"



Yusy tace tab wallahi kuwa hakane



Billy tace ni dama Haroon daba wani kulawa yake bani ba, inda ace soja ne ai nabani



Ai wannan Haroon din naki sai aslow, Cewar yusy



Wallahi ni na matsu ma exam dinnan ta qare nakoma gida kusa da anty na

Wallahi nayi missing dinta, inji Billy



Iman tace eh dole kiyi fada da Haroon, wato shi bakiyi missing dinsa ba,



Billy tace share shi Yaya Iman



"ai Nima sonake mugama aranar nakeso mugudu 9ja, tadubi yusy tace Besty ai Kema zakije Ko?
Yusy tace Anya kuwa zani, one week nefa zamiyi mukoma wata semester kawai zan zauna, basai najeba
"



To Allah yakaimu Cewar Billy



*** *** ***



Dakin taron nasu ya tsaru matuqar tsaruwa, dukanninsu kaki ne ajikinsu , gaban kowa akwai lasifika
wadda aka rubuta NTA ajikinta, da alama duk abinda suka tattauna awajan kai tsaye yana tafiya ne
akafar sadarwa ta nta, daga saman aljihun rigar kowa naga anrubuta sunan kowa ajikin tasa rigar, shine
kawai yake zaune akan babbar kujerar dake nuni dacewa shine shugaba awajan,shima gaban rigar sa
ansa ALIYU SA'AD bayan qaddamar da bayanai dasuka gama , aka miqo masa wata takarda , umarni
yabayar abude takardar akaranta



Wanda yagama karantawa ne yayi bayani akan takardar , takarda ce qasar ghanah taturo musu , suna
gayyatarsu meeting na kwana daya akan dedeto dakuma zaman lafiya tsakanin Nigeria da Ghana



Goshinsa ya dafe da hannunsa

"Yazasu turo mana wannan takardar bayan sunsan bama qasar, yanzu haka muna wajan seminar ne?"



Wanda ya karanta dinne de , yace"Sir ai 1week suka nema muyi da farko, bayan anyi musu bayani ne
suka rage yakoma 1day saboda ansanar musu muna bakin aiki"



"Ok toba damuwa "



na gefensa yaduba sannan yace"jiragenmu sun zama ready ne?"



Eh sir
Toshikkenan, ashirya mana tafiya zuwa next week insha Allah"



Dahaka meeting din nasu yaqare



*** **** ***



Azaune take afalo remote ne ahannunta , Atika ce azaune aqasanta tana matsa mata qafafu

Hankalinta yana kan tv tace "kai Atika nagaji da zaman wannan qasa wallahi"

Dariya atika tasa tace Tab ai mamy nikam bangaji ba wallahi , kofa sati biyu bamuyiba, ai banqi ace muyi
zamanmu anan ba"



Mamy tace lalle atika bakisan dadin gidaba, atika kowa yabar gida ai gida yabarshi"

Banda ma jaraba irinta haidar ai da yabarmu agida



Atika tace a a mamy wallahi gara da mukazo , ai ko yanzu nikam nahau jirgi



Dariya tabawa mamy , danhaka tayi mata murmushi kawai



Lemo ne ahannunsa na gwangwani , rigar jikinsa amless ce sai wando gajere iyakarsa gwiwarsa, sai yau
naganshi cikin qananun kaya, kullum cikin kaki yake



Farar fatarsa saita haska acikin kayan, kamar ba hausa fulani ba, yana zuwa ya ajiye lemon hannunsa
aqasa ya kwanta akan kujerar tareda dora kansa akan cinyar mamy



Atikace ta kalleshi ta qasan idonta

Aranta tace shide wannan kullum kamar qaramin yaro, garama yayi aure ko mamy ta huta da wannan
shagwabar
Shafa kansa tayi tace baby ya akayi, kallanta yayi yana daga kwancen yace mamy tafiya takamamu zuwa
ghana



Murmushi tasaki tace kamar kasan kuwa yanzu nake cewa nagaji da zaman wannan qasar, kaga
shikkenan daga nan saimu wuce nigeria



Murmushi yasaki wanda yasa gefen kumatunsa suka lotsa (dimple)



Yace mamy ai yanzu kuka fara zama kuwa, kwana dayafa zamuyi aghana mudawo , bawani daukan lokaci
zamuyi ba"



Kiyi hakuri mamy banasan abinda zaisa kiyi nesa danine shiyasa



Aikuwa dole kayi nesa dani baby tunda zakayi aure,



Kuma dan zanyi aure mamy shikkenan saina rabu dake

Haba mamy aiko nayi aure ina tare dake



Murmushi tayi tace to Allah yasa baby



Amin mamy nah, amma mamy yunwa nakeji



Tashi kaje kazuba da kanka kaci,



Cikin shagwaba yace haba mamy , haba mamy
To haidar idan kaji haushi kayi aure mana



Baice mata komai ba, yadubi atika fuska babu alamun wasa yace"ke tashi kibamu waje"



Tunma kafin yarufe bakinsa atika tabar wajan, saboda tasan shi da mugunta tsaf zai iya maketa



*** *** ***



Wow teemah gaskiya kinyi kyau ba qarya, rabonda ki tsatso wannan kyan kin dade



Manyan idanuwanta ta juya tace "kekuwa yusy ba gara inyi kwalliyaba, zanje naga MURADINA



Billy tace nikam gaskya katsina zan wuce , bazan shiga kanoba



Iman tace ki gaida anty da baba , amma nikam sainaga Hajiya hankalina zai kwanta



Yusy ce ta yafa mayafinta, tace kutashi mutafi



Sunyi kyau gaba dayansu , billy abaya tasaka tayi rolling da dankwalin abayar



Iman kuwa riga da wando tasaka , kayan sun amshi jikinta, hips dinnan suncika fam acikin wandon jeans
din data saka, sai riga data saka fara me adon Dark blue agaban rigar, dukiyar fulanin masha Allah
gasunan



Sai doguwar riga data dora akai after dress me kalar dark blue itama, zare ne agefen rigar , hannun rigar
kuma baza gareshi , sai stone da aka diga ajikin hannun rigar
Zaren rigar takama tadaureshi acikinta, sai wani shegen takalmi data saka me tsini, batayi kitso ba, kawai
kama dogon gashin kanta tayi tadaure, batayi rollinga kawai dankwalin after dress din ta yafa, jakarta
takama tanaja suka fita daga hostel din nasu



Suna fita mota suka tare direct takaisu Airport



Suna shiga cikin Air port din suka gama abinda zasuyi , suka zauna awasu kujeru agefe sunata firarsu
tareda yusra datace bazata tafi ba saitaga tashinsu



Iman ce tatashi tsaye tace bari inje can insiyo ruwa nadawo



Bata dade da tafiya ba tadawo hannunta dauke da ruwa da chesee



Ruwan tabasu , itakuma tabude chesee din tafaraci tana daga tsayen



Adede wannan lokacin shikuma yashigo cikin Airport din tareda rundinarsa



Yayi masifar kyau cikin kakinsu na sojoji

Yau harda hular yasaka akansa



Already sunada jirginsu , so babu abinda zai jira kawai tafiya zasuyi sukoma Switzerland tunda sungama
meeting din daya kawosu



Wayarsa ce tayi qara, yatsaya yana magana cikeda aji



Juyowar dazaiyi yahangeta atsaye tanacin chesee
Daskarewa yayi atsaye , ga waya ahannunsa yana magana amma yayi shiru



Danqaramin bakinta yake kalla yanda take juyashi



Kamar wani abin arziqi take ci



Yusy ce tace kai teemah kinga wasu sojoji can, inama zani gida kuma ace jirgi daya zamu hau, yasin dasai
munyi selfie indora a Facebook yanzu zakiga anaban girma



Hararar yusy tayi , tace kesuka dama, nikan basa gabana can dayawarsu



Billy ce tadagakai ta hangesu , itama daga kallan farko bata sake yimusu na biyu ba



Sir ga waya ana kira daga nigeria



Sir!

Sir!!



sai alokacin ya kalli musty dayake bashi wata wayar



Dayar wayar datake hannunsa yakatse batare daya gama maganar dayakeba



Qasa qasa yayi da murya yace Musty katse wayar nan in nunama abinda nagani



Kallansa mustapha yayi da mamaki, yace meke faruwa ne?
Da hannunsa yanuna masa iman datake tsaye, yace"kai kaga wata sura"



Masha Allah kawai mustapha yace, sannan yaci gaba dacewa

Gaskya tayi, ba qarya tahadu, kuma abinda zaka duba shine komai yaji, musanman breast dinta, kana
son mace maishi



Cikin kishi ya dakatar da musty da fadin"kuma menene abin maimaitawa, sai wani zancen breast kake,
matar dazan aura cefa insha Allah



Dariyace takama musty , kawai daga ganin yarinya shikkenan harta zama matar dazai aura



Dariyarsa ya gintse, gudun laifi awajan abokin nasa



"Idanunsa yana kanta yace amma kuma musty meyasa zatasa wannan kayan tafuto waje, dubafa dan
Allah mutane sai wani kallanta suke, aida saitasa hijab ko?



shide musty dayake dariya qasa qasa yace inaga ba halinta bane hakan, yanzu ne kawai tasaka



Qasa yasakeyi da muryarsa yace kafadawa daya daga cikin sojojin nigeria dasuke zaune anan ayimin
bincike akan yarinyar nan, akawomin komai nata nanda jibi



Cikin serious mustapha yace angama sir

Ga wayar taka, yabawa Aliyu wayar , shikuma yajuya yana fadawa wani soja dayamusu rakiya zuwa
Airport saqon Aliyu, tareda nuna musu su iman dasuke tsaye



Murmushi yasaki, dayaga me kiran nasa daga nigeria, yana dagawa yace tuba nake bros , inadan wani
uzuri ne shiyasa nayi rejecting call din naka, dakatawa yayi da magana yana sauraron dayan bangaren
Bansan meyace masaba naji haidar yace a a karka damu ai ABIN BROS NA BROS NE



Yana wayar yajuya yasake kallan iman da batasan dashiba, sannan yatafi sojoji suna take masa baya



Suna tafiya, iman tajuya takalli inda yusy tace mata ga sojoji nan hankalinta ne yakai kansu, saide
alokacin sunbasu baya sun riga dasun tafi, sai bayansu tagani



Juyawa tayi taci gaba dacin chesee dinta



(Tofa yanzu chakwakiyar tafara,😱
anya kuwa Haidar bai debo sama da zafi ba😱😱 ????



(Waima wacece iman ne?nasan mai karatu yanaso yaji wacece wannan iman din da ake magana akanta,
to kubiyoni danjin wacece iman)



Mrs Usman ce WAZAN
✍🏻 ZABA?💖



Writing by Amnah El Yaqoub



Bissmillahir-rahmanirraheem



6



Lokaci Nacika sukai sallama da yusy suka tafi



Zuciyar yusra daya tafita tatare taxi saide abinda Bata saniba shine akwai masu bibiyarta Abaya, Saida
sukaga shigarta hostel din sannan suka tsaya wajan masu gadi
*** *** ***

Karfe biyu nadare flight dinsu yasauka, direct Daga Airport Mota ce ta daukesu tamaidasu masauqinsu

Shima gida aka wuce dashi

Yana shiga Shiru gidan kowa yayi bacci, baiyi gigin tashin mamy ba, dakinsa ya wuce yafada Kan gadonsa



Saman dakin yazubawa ido yana kallo, saide azahiri idonsa ne awajan, ruhinsa da tunaninsa Suna gareta



Gaskiya Allah yayi baiwar komai da komai awajan

Ashe a wannan zamanin zaka samu mace haka, wata Zuciyar tace dashi Har fin hakama Ana samu

Tokodan baya shiga sabgar yanmata ne shiyasa Bai hadu da irinta dinba

Kozata Soni? Yake tambayar kansa



Wani bangare na Zuciyar sane yarinjayeshi Akan Cewa ai bashida aibun dazata qishi



Harya matsu lokacin daya Diba su cika domin yaje ya tunkareta gameda abinda yakeji acikin ransa



"To Allah yasa de tasoni"



yafadi Hakan afili cikeda Alhini



Tashi yayi cikin nutsuwa yacire takalmin sa tareda kakin jikinsa yashiga wanka



*** *** ***



Zeey yakamata Musa Yaya yakaimu saloon Ko?
Kanta yana kan cinyar Iman, tace "Eh anty Daga Nanma saiki kaini wajan wasa, ki siyamin Ice Cream, da
sweet"



"a a Zeey, abin Yamin yawa, bazan iyaba, Daga zancen saloon saiki ta jeromin wannan abubuwa haka "



Fizge kanta tayi Daga hannun Iman tayi wajan Hajiya dake zaune tana kallansu

" hajiya Kinga anty Wai bazata saikin sweet ba "



Cikin fada Iman tace yes fadi da ihu yarinya bazan siyaba



Itama cikin hawaye tace dama bakizo ba anty Bilkisu kawai tazo, kekwa ki zauna a school, dog ya cinyeki



Ba Iman kadaiba hatta Hajiya ma Saida tayi Daria, ta janyo zainab jikinta tace Rabu da anty Iman, yanzun
Nan zankira Miki Bilkisu awaya tataho Daga katsina takaiki duk inda kikeso



Washe bakinta tayi, tayi cikin daki dagudu tana murna



Falon yashigo yayi masifar kyau cikin qananun Kaya, agogon dake hannunsa, Yazo dab da ita yazauna
Akan hannun kujerar datake Kai, Kasa yayi da murya yace "muradina zan fita Ko akwai abinda kikeso?"



Hajiya tana kallansu ta gefen idonta, wannan rashin kunya tafara isarta, garama Iman tayi tagama school
dinnan ayi musu Aure Ko sa huta



Itama Ahankali tace masa Saloon suke San Zuwa itada Zeey



Sai a lokacin yadago Daga sunkuyawar dayayi yanayi mata magana
Daga murya yayi yakira Zeey, ai kuwa aguje tataho ta rungumeshi



Yace yanmatana jeki futo muje wajan saloon keda anty Ko?



Saida tayiwa Iman gwalo sannan tajuya ciki da gudu



Tana futowa sukai wa Hajiya sallama data nuna Kamar Bata ganin su



Suna fita tabisu da kallan birgewa, hannu ta Daga tace Allah ka qara hademin Kan yarana Amin



*** *** ***

A dinning suke zaune mamy nacin abinci taga sai juya abincin yake, kallansa tayi da mamaki tace Baby
me yake damunka ne?

Babu tunanin komai yace "mamy akwai aikin Dana bayar ne Bansan asamu matsala aciki"



Spoon din hannunta ta ajiye tace "to menene abin damuwa, kayi hakuri insha Allah babu matsala kaji?"



Cikin sakin fuska yace to mamy



Yauwa baby nah ci abincin ka



Nan take ya ware yana cin abincin, Amma cikin ransa adduah yake Allah yasa angama binciken da za'ayi
Akan yarinyar Nan



Suna gamawa yace mamy zanje nadan motsa jikina, yafice Daga falon
Yana harabar gidan yana motsa jiki Amma tunani yahanashi yin abin kirki



Towel din dake gefen sa yadauka ya share zuffar dake zubomasa



Huci yayi, tare da firzar da iska Mai zafi Daga bakinsa, yajuya yadanna wayarsa Ko zaiga Kiran musty,
nanma Shiru



Haka ya hakura yayi dakinsa tareda shigewa wanka



Har dare yakasa fita Ko Ina yana zaune a daki yana aikin tunani, Wai wannan wacce irin masifa cene?
Dama haka masoya sukeji? To ai Har Gara masoya ma sunsan sun furtawa junansu so, to Amma shifa Ko
yarinyar ma batasan yanayi ba



Kasa hakuri yayi yadau wayar sa yakira Mustapha, bugun farko Mustapha yadauka yace sorry sir gani
Nan a hanyar Zuwa gidan



Batare dayace komai ba yakashe wayar, yafada Kan gadonsa tareda runtse idanunsa



Ba'a dauki lokaci Mai tsawoba musty yashigo gidan, Saida suka gaisa da mamy sannan yayi dakin Aliyu



Yana shiga qamshi hadeda sanyin esi suka bigeshi, qarasawa yayi Kan gadon yazauna yace" Sir gashi
angama komai"



Yanajin haka ya Bude idonsa yace "musty kadameni da wannan sir din wallahi, Dan Allah ya Isa haka,
haba!

Saida yagama mitar tasa sannan yace" bani"
Takarda yamiqa masa yace Nima sai dazu suka turomin ta email Dina, to da zan turoma ta Email din
saina fasa naje aka ciro ta yanzu



Yana gama magana yamiqe Yace "to abokina saina dawo latter naji bayani, Dan yanzu aiki nake nataso"



Batare daya kalleshi ba yace kaide kawai Kace guduwa zakayi babu wani aiki



Da gaske nake, madam tayi kirana, zan dawo Zuwa gobe



Kansa kawai yakada masa Batare daya yarda da maganar ta Mustapha ba, kawai de yasan Cewa yabashi
dama ne yakaranta abinda yakawo masa

Mustapha nafita ya gyara zamansa a Saman gadon yabude takardar tareda karantawa cikin ransa



Wacece Iman?

Sudin cikakkun shuwa Arab ne dasuka Tashi agarin maiduguri, mahaifiyarta da dangin mahaifiyarta
dukkansu maiduguri ne tushan su



Asalin Sunanta shine FATIMA SHU'AIB Amma Ana Kiran ta da (Iman)

Tanada yar'uwa Bilkisu wadda ta kasan ce Shiru Shiru marar magana, komai nasu daya ake musu,
kasancewar su Kamar wasu twince, tare suka fara makaranta tun Suna Yara, Bilkisu nayiwa yar'uwarta
biyaiya,hakane yasanya take Kiran ta da Sunan YAYA IMAN, saide Iman akwai ta da tsiwa, Tanada San
girma, akomai tanaso taga qanwarta Bilkisu tabata girma



mahaifinsu cikakkan bahaushe ne Dan asalin jihar Katsina Garin Funtua



Yanzu Iman tana matakin gama degree dinta na farko ne Aqasar Ghana itada yar'uwarta Bilkisu, saura
Semester daya su kammalla karatun su

Inda suke Karatun bangaren likitanci Ajami'ar KWAME NKRUMAH UNIVERSITY OF SCIENCE AND
TECHNOLOGY
saide abinda ba'a saniba shine Bilkisu tana hannun mahaifinsu ne a katsina, ita Kuma Iman tana hannun
Mahaifiyarsu ne agarin kano



Anyi musu hutun semester ne na one week shine suka shirya tafiya gida hutu



___________

Ajiyar zuciya yasauke daya gama karantawa, idanunsa yakai kasan takardar yaga number wayarta
dakuma sunayen datake amfani dasu ashafukanta na yanar gizo



Baiyi qasa agwiwaba ya adana komai nata acikin wayar ta hanyar saving



Yana saving number ta yaga dashi take whatspp sannan ya tafi shafinta na Facebook da Instagram, anan
yaga ruwan pictures dinta, domin kuwa Iman takanas barrister yake daukanta suje ayi musu pic, da
Hakan take amfani wajan Dora Iya nata ayanar gizo



Afili yace "wannan yarinyar me yake damunta ne take dorawa Dunia pictures dinta?"



Dan qaramin tsaki yasaki yasake Cewa yanzu haka kowa yadauka "



Saving din pictures din nata yayi dayawa, sannan yakashe datar sa



Bama wannan ne damuwar ba, menene yasa sister nata take zaune ahannun babansu?

Dole ne gobe yanemi Mustapha domin qarin haske Akan Hakan



Photunan ta yaci gaba da kalla, dazaran yaga wannan zai koma Kan wani yayita kallah,
Bai Tashi ganin lokaci ba sai gani yayi dare yayi sosai, Dan haka yayi adduah ya kwanta domin yanaso
gobe da sassafe mamy taji daddadan labari



*** *** ***

Next day



Yana Tashi Daga bacci yashiga wanka, Kamar kullum wando yasaka three quarter

Sai rigar jikinsa wadda ta kasance marar hannu



Shi kansa jinsa yake cikin nishadi, Kuma yasan Hakan baya rasa nasaba ne da wannan yarinyar



Wai a hakama Bata fara bashi kulawa ba, to inaga sunyi Aure Kuma, Ko menene zai kasance?



Kiran musty yayi awaya yana dagawa yace "kazo gida ka sameni, akwai sauran abinda ban ganeba game
da yarinyar Nan"



Daga dayan bangaren Mustapha yace eh dama Ina Kan hanya gani Nan Zuwa "



Yana kashe wayar, cikin galary dinsa yashiga, yafara duba pictures dinta, fridge yanufa yadauki lemo
yariqe ahannun sa Batare daya fara shaba yaci gaba da aikin kallan ta



Anya kuwa dayasan yarinyar Nan bazaice ba kalau tabarshi ba? Daga ganin ta yashiga irin wannan
yanayi?



Yana wannan tunanin Mustapha yashigo dakin, yana zama Haidar yabashi labarin komai, yaci gaba da
fadin

Amma abinda bansaniba shine meyasa basa zama waje daya itada yar'uwarta?
Mustapha yace ni aganina kawai ashare wannan maganar Daga baya idan kun dedeta zaka San komai



"eh hakane Musty, Amma gaskiya inasan yarinyar Nan, banajin zan Iya rabuwa da ita, bantaba tunanin
zanso wata yarinya Har hakaba



Murmushi Mustapha yasaki yace ai kaima ba bayaba abokina, nasan insha Allah za'a dace



"to shikkenan Musty, saimun sake waya, zan shiga wajan mamy, Dan Ko break fast banyiba



Hannu musty ya miqa masa suka sake gaisawa sannan ya tafi



Sai wani walwala yake shi kadai, yanata fara'ah, atika ce tafara ganinsa, a ranta tace to yau Kuma me
akayi masa



Kamar qaramin yaro yana Zuwa yazuba ajikin mamy,

Kai Haidar narasa yaushe zaka girma, wannan ai saika karyani



Atika dake gefe tace cikin ranta uhm yaushe zai girma kuwa kullum Ana ce masa baby



Cikin farin ciki yace "mamy albishir"



"goro fari Haidar "



Yaune Karo na farko dayaji nauyin fada mata magana, kodan maganar Tanada alaqa da Zuciyar sane
Qasa yayi da kansa yace" mamy yaude kinsamu in law"



Baby idan wasan daka saba minne, please kadena "



" mamy da gaske nake, inasonta, Kuma so na Aure, gaskiya mamy idan ban sametaba akwai matsala,
meeting din danaje Ghana acan naganta, Amma Har yanzu banyi magana da itaba, sonake sai kinganta
tayi Miki tukunnah "

Wayarsa yadauko yashiga cikin pictures dinta, yabawa mamy wayar yaci gaba da fadin" mamy
Kingantafa "



Tana ganin photon gabanta yafadi, meyasa yarinyar take mata kama da ZAINAB? babu banbanci sak
photo copy din zainab ce



Amma saitayi tunanin may be kama ce kawai



Haidar yanajinta tayi Shiru yace mamy yakika ganta, tayi Ko batayiba, idan Bata Miki ba asake wata



Jijjiga kanta tafara sannan tace Gaskiya Baby wannan maqiyinka ne kawai zaice ma batayiba, but
tanamin kama da wata mata

, ita wannan yarinyar a'ina take?



"mamy akano take wajan mahaifiyarta, "



Jin wannan amsar da Aliyu yabata yasa Zuciyar ta yarda Cewa ba wadda take nufi bace"



Daga murya mamy tayi tace atika zonan
Atika nazuwa mamy ta nuna mata pictures din Iman tace Kinga budurwar baby, yaude gori yaqare "



Atika nagani tace Kai masha Allah, wallahi mamy saikace balarabiya



Dukansu Daria sukayi

Yau Atika saboda anga waje, taganshi yana farin ciki, akace, Kuma ya sunanta?



Kai tsaye yace sunan mamy nah gareta, Fatima, Amma Iman ake cemata



Mamy tace masha Allah, gaskiya yarinyar tayimin, Allah ya tabbatar da alkhairi, kafada mata da Aure
kakesanta bakasan abin yadau lokaci idan tana sanka



Sunkuyar da kansa yayi yace to mamy



Mamy am hungry



Atika ta kallah da sauri tace maza atika kawowa baby abinci nabashi



Shikuwa saboda farin ciki harda Dora kafa daya Kan daya, yau Mamy zata bashi abinci da kanta, yaushe
rabo



Dakanta taciyar dashi, yanaji yaqoshi yayi dakinsa domin Kiran Iman awaya



(waishin wacece wannan zainab din? 😏😏



Anya kuwa Kuna ganin Iman zata amince da Haidar? 🙉🙉🙉🙉
To kubiyoni de fatana ku nishadantu da wannan labari



(Ayau Ina farin cikin sanar da fan's Dina Cewa zaku dinga Jina kullum, Kamar Yanda nasaba yi muku
Abaya, dama nadan samu matsalar waya ne)



Mrs Usman Ce WAZAN
✍🏻 ZABA?💖



Writing by Amnah El Yaqoub



Bissmillahir-rahmanirraheem



7



Tunda yakoma dakinsa yakasa zaune yakasa tsaye, saiya dauki wayarsa zai kirata saiya fasa, yayi Hakan
yakai sau biyar, to idan yakirata me zai fada mata?



Gyaran murya yayi, yafara gwadawa shi kadai agaban mirror yana kallan kansa



Sunana Aliyu Sa'ad Bilal Ina sonki



Girgiza kansa yayi, "no Hakan baiyi ba"



Salamu alaikum, Am Sunana Aliyu Haidar, dama naganki ne a airport shine nake sanki



Tokuma idan tace nikuma Bana sanka fa, girgiza kansa yayi, Allah ma yakiyaye
Qara gyara tsayuwarsa yayi, harda gyara wuyan Rigarsa, sannan yace "Ni Sunana Haidar, ni soja ne,
nadade Ina neman matar Aure bansamu ba, Saida naganki shine kawai Nima naji Ina sonki



Wata Zuciyar ce tace dashi, wato kace mata kadade bakayi Aure ba, Daga Nan Kuma sai tace dama
kwantai kayi shiyasa ni kazo wajena



Dayawan mata ba'a cika birgesu ba idan kahadu da ita gani na farko ka baiyyana mata sirrin

Please Login or Register in order to submit comment