You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

bata bar komai na Madina ba.

Ranar suna yarinya ta ci sunan Fatima Zahrah sunan mahaifiyar Abdulkarim taci. Sannu sannu yarinya ta fara wayo gashi sai ƙara kyau take yi.
A haka suka ci gaba da rayuwa har zuwa lokacin bata san wani idrisu ba ballantana shirin sa.

Kwatsam wata rana mai baƙin tarihi wacce ta kasance katanga tsakani ta da masoyin ta Abdulkarim. A ranar ne aka samu gawar sa a kusa da wani gidan mai an yi mishi kisan wulaƙanci, Madina tayi kuka sosai har sai da aka kwantar da ita a asibiti. Bayan taji sauƙi aka sallamo ta. Kai tsaye gidan ta aka wuce da ita da taimako mamar Bello.

Bayan ta gama takabar ta ne ta yanke shawarar komawa gida saboda wanda ta gudo domin shi ya tafi ya barta. A ranar da ta gama shirye shiryen ta ne aka ce ana sallama da ita a waje.
Bayan ta fita ta tarar da shi cikin wani koɗaɗɗen yadin sa da yaji jiki.
Suka gaida ta tambaye shi ko shi waye yace ai shi ɗan uwa ne ga marigayi idan ba zata damu ba shi yana so ya aure ta ne. Cikin zuciyar ta kuwa wani tsoron mutumin ne ya ɗarsu lokaci ɗaya ta amince da batun sa aka ɗaura musu aure. Cikin gidan ta na da ta tare sai dai tun da ta shiga gidan farin cikin ta ya ƙare.

Farkon auren ya kan kyautata mata, abinci haka baya mata shamaki da shi.
Bayan watanni kaɗan da auren salon shi ya sauya, a kowacce rana sai ya jibgi Madina tamkar dai mahaifin ta haka ya mayar da ita, yarinyar ta Zahrah baya ƙyale ta, akan idon ta yake jibgar ɗiyar ta ta sai dai babu yadda ta iya saboda mugun tsoron shi da take ji.

Shan giya da sauran kayan maye babu abun da ya bari sai ƙaruwa ma da yayi gashi bata da ikon hana shi, a na haka ya fara kafa majalisar matasa irin shi masu zaman kashe wando haka zasu yi ta busa hayaƙi a ƙofar gidan.
Ranar da ta yijarumta ta tunkare shi da maganar majalisa sai da yayi mata dukan Kawo wuƙa, a lokacin Zahrah bata haura shekara biyu a duniya ba haka ita ma tayi ta kuka ganin irin dukan da ake wa mahaifiyar ta. Tun daga wannan rana yarinyar ta sanya tsanar kawun ta a cikin ranta har zuwa girman ta.

Abinci da yake hana su daga gidan mamar Bello ake kawo musu, su ma bayan wani lokaci suka tarkata komatsen su suka koma Birnin Abuja da zama, hakan ba ƙaramin tayar da hankalin Madina yayi ba, takan ji ina ma ta gudu ta koma ga iyayen ta sai dai duk lokacin da tayi yunƙurin hakan sai ta gwammace bata yi ba, rashin lafiya ce zata kamata ga wani abu da zai tsaya mata a ƙirji kamar dutse. Hakan yasa ta fauwala lamurran ta ga Allah ta bar batun guduwa.....

Yanke shawarar sayar da wata sarƙar ta tayi bayan ta siyar ta siyo kayan suya kama daga tanda, bahuna plates na roba da sauran su ta fara soya Masar siyarwa sai dai ba'a kai ko ina ba mutanen unguwar suka daina siya dalilin mijin ta idrisu. Ganin yunwa zata iya yi musu illa ita da ɗiyar ta yasa ta fara soya Masar a kasuwa wanda hakan ya zama maslaha gare ta.

Bayan Zahrah ta kai shekarun shiga makaranta ta sanya ta a makarantar gwamnati, Zahrah ta tashi da rashin haƙuri da kuma masifa ga rashin kallon mutuncin manya, tun tana ƙarama tsanar kawun ta ta ɗarsu a ranta shiyasa ta ƙudurta a ranta duk ranar da tayi ƙarfi sai ta ramawa Mamah dukan ta da yake yi.

Kwanci tashi babu wuya a gurin Allah har Zahrah ta shiga primary school wanda Mamah ke ɗawainiya da komai nata kama daga sutura zuwa karatun ta da kuma cikin ta.
Sam yarinyar ta tsani maza, a tunanin ta duk maza haka suke mugage marasa tausayi shiyasa ta ɗauki aniyar kare kanta daga kowanne irin farmaki namiji zai kawo gare ta, faɗa da maza baya damunta kuma koyaushe takan yi ƙoƙarin ganin tayi nasara kan su.
A kullum burin Zahrah bai wuce ta zama alƙali ba saboda take kulle duk wani mai laifi.

★★★★★


[04/10, 7:45 a.m.] 💎Diamond Bhatool 💎: ️______________★★★_______________
Typing 📲
🏡 *A BABBAN GIDA* 🏡
_(All in a big family🏠)_
★TAKUN FARKO★
_[Labari/Rubutawa]_
*©Fadimatu Adamu Hassan*
*A.K.A DIAMOND BHATOOL*💎

_______________★★★________________



PROLOGUE


*PAGE* 1️⃣5️⃣

*Shafin nan naku ne Ahlul-moonlight 🌙, ubangiji ya ƙara haɗa kanmu ya kuma ƙara ɗaukaka mu*


SHARE AND COMMENT PLEASE!
_______________★★★________________





Zahrah yarinya ce ƙarama sai dai Allah ya bata kaifin basira tamkar wata babba. Kukan da take yi ta tsayar jin kiran Sallah yayin da Mamah ta rungume ta kamar za'a ɗauke mata ita.
“Zahrah ta! Ke ɗin ta musamman ce kuma inada yaƙini akan ki, zaki iya ɗaukar fansar mahaifin ki ta hanyar da ta dace koda kuwa bayan Ni bana nan domin ina ji a jiki na zama na da ke ƙaiyadadde ne.”

Zame jikn ta tayi a hankali sannan ta share hawayen ta yayin da ta mayar da hannayen ta bisa kafaɗar Mamah.
“Na ɗauki wannan alƙawarin Mamah tah! Nayi miki deduk wanda na kama da laifin raba mahaifi na da rayuwar shi bazan ƙyake shi ba, dole doka ta hau kanshi kamar kowa.”
Murmushin yaƙe Mamah tayi ta ƙara rungumo Zahrah jikin ta.
“na yadda dake ɗiya ta, Ni na kasa ɗaukar fansar masoyi na ammah nasan ke zaki ɗau fansar mahaifin ki. Fatan nasara takasance dake a kowanne yanayi.”

Da ƙyar suka tashi suka yi sallah musamman Zahrah da ke fama da gajiya shiyasa ta ce yau ba zata je islamiyya ba, abinci Mamah ta girka bayan sun ci suka kwanta don su huta.
Yinin ranar Zahrah a sukwane tayi shi ga wata fargaba da take ji. Zuciyar ta wani irin bugu take yi innalillahi wa inna ilayhi rajiuun kawai take maimaitawa.

Bayan Badi'a ta kawo abinci kamar kallum Zahrah ta amsa suka ɗan yi taɗin su kafin ta wuce. Serving nasu tayi a plate ɗaya ita da Mamah daga nan suka zauna suna ƴan zantukan su.

Ita dai yau Zahrah cike take da mamakin Mamah, yadda yau take ta ɓarin magana kamar mota maras birki, tun daga taɗin family nata har zuwa kan rayuwar ta gidan Abban Zahrah. Daga ƙarshe da ta ɗauki hakan a matsayin kewa tayi wa Mamah yawa shiyasa take maganar.

Bayan sallar isha'suka yi addu'a kamar kullum suka kwanta bacci.
Bacci mai uban nauyi ne ya kwashe Zahrah.

★★★★★★★

Tafe take cikin wani baƙin daji mai ɗauke da duhun gaske, babu alamar akwai halitta cikin shi. Ta jima tana tafiya tare da fatan Allah ya haɗa ta da wani wanda zai taimaka mata ta koma gidan kwatsam ta fara jiyo sauti daga can nesa. Yanke shawarar zuwa guriin sautin tayi tare sa fatan Allah yasa mutane ne. The more ta yi tafiya the more sautin ke ƙaruwa.

Tayi doguwar tafiya kafin ta kusanto wurin sautin sai dai alamu sun nuna cewa sautin ba na mutane bane....gurnanin da take ji ne tare da wata mahaukaciyar dariya mai ɗan karen sauti da amo maras daɗi yasa ta ɗan ji tsoro daga ƙarshe kuma ta yanke shawarar ƙarasawa.

Bata kai ga ƙarasawar ba taji ƙasa na wata irin girgiza wanda hakan tayi sanadiyar faɗuwar ta ƙasa, da ta tayi ƙoƙarin tashi sai ta koma saboda girgizar ƙara ƙamari take yi. duk ƙoƙarin ta na tashi tsaye ya gagara hakan yasa ta kwanta tare da runtse idanuwan ta tana miƙa wuya

Wasu munanan halittu ta gani masu munin gaske, kayuwan su manya manyan wanda ke ɗauke da ƙaho biyu, na hagu jibgege na dama kuma ɗan ƙarami. Fuskar su ja jawur da ita ga idon su ɗaɗɗaya ne manya manya marasa daɗin kallo. Baƙin su kuwa ya kai faɗin randa Wanda ke ɗauke da wasu gabza gabza haƙora da suke da launin shuɗi.
Gangar jikin su irin ta mutum ce sak ga kyan fata da suke da shi sai dai bakin su da yake a wangale yana zubar da wani kore da jan jini suke ƙara wangalewa.

Ta riga ta saddaƙar cewa tata ta ƙare hakan yasa ta ƙara runtse idanuwan ta tare da karanto wasu addu'oin tsari. A hankali halittun suka matso daf da ita suka ɗaga ta....basu ajiye ta ba sai cikin wani cage Wanda ke ɗauke da wasu mutane kusan biyar.....ana cikin wannan abu sai ga wata mahaukaciya ta bayyana gaban cage ɗin, jikin ta duƙu duƙu ga wasu kayayyakin ta da suka ji jiki. A hankali mahaukaciyar ta jawo ƙofar cafke ɗin tana motsa bakin kamar mai karanta wani abu.


Tana gama buɗe ƙofar ta jawo su ɗaya bayan ɗaya daga ƙarshe ta janyo Zahrah ta faɗo jikin ta. Bata kai ga gane fuskar waye ba taji kiran sallar asuba, ɗauke da addu'ah a bakin ta tayi miƙa.
Mintuna kamar 10 ta kwashe tana nazarin mafarkin da tayi tare da hasaso ko meh yake nufi.
Kan ta ne ya fara juyawa hakan yasa ta buɗe idanuwan ta da suke lumshe.
A hankali ta shashima gefen ta ta gano ta ina Mamah take sai dai babu kowa gurin.

Ƙafar ta ta sanyo ƙasa yayin da ta ware idanuwan ta.
A hankali ta fita don gabatar da alwala tunanin ta Mamah na banɗaki, ganin ƙofar a buɗe yasa zuciyar ta bugawa sai tayi saurin kawar da abun da zuciyar ta ke shirin shirya mata ta hanyar ɗiban ruwa a buta, sai da ta gama ɗiba ta shiga bayi bayan ta fito tayi alwala ta koma ɗaki don yin Sallah.

Tana idarwa bata iya ko yin azkar ba bacci yayi awun gaba da ita. Ba ita ta farka ba sai wajen 8:12am sanadin mummunan mafarki da ta ƙara yi na wannan mahaukaciyar. A sukwane ta miƙe tsaye sai dai ƙara kallon gado da tayi sai taga still babu mamah. Zuciyar ta ne tayi wani irin bugu har sai da ta kusa faɗuwa.

A hankali ta duba wurin da Mamah ke sallar asuba ko yaushe taga wayam kuma babu sallaya shimfiɗe. Mamaki ne ya cika ta yau ko ina Mamah ta tafi?.
Bayan ta fito tayi wanka ta dawo still Babu Mamah babu alamar ta hakan yasa ta tsorata da lamarin.
Kaya kawai ta sanya ta nufi gidan su Badi'a ko can Mamah ta nufa sassafe.

Karo suka ci da Abba ya fito daga part ɗin shi, a natse ta kalle shi tare da sunkuyar da kanta ƙasa.
“ina kwana abba”
“lafiya kau Zahran Mamah ya Maman ki?”

Tsoro tambayar ta bata, wane irin ya Mamah bayan kuma nan ta zo. Kawar da abun da zuciyar ta ke saƙawa tayi tare da faɗin
“lafiyar ta ƙalau”
“toh madallah” daga haka ya wuce ita ma Zahrah ta shiga part ɗin Ammi.
Breakfast ta tarar Badi'a da Ammi nayi wanda hakan yasa zuciyar ta yin wani mummunan bugu, a daidai lokacin ta faɗi ƙasa a yashe.

Cike da ruɗewa Ammi da Badi'a suka yi kan Zahrah.
Tunani meh za'a fara yi mata Ammi tayi cikin ruɗu tace
“badi'ah kawo ruwa masu sanyi”
Da gudu Badi'a ta nufi fridge ta ɗauko ruwa.
Har Ammi ta gama yayyafawa Zahrah wannan ruwan babu alamun numfashi a tattare da ita. Kuka Ammi take yi kamar ranta zai fita haka Badi'a, gashi ƙwaƙwalwar ta duk ta toshe ta ma rasa MEH zata yi.

A cikin wannan yanayin Abba ya shigo ganin suna kuka yasa shi ƙarasowa yadda suke da sauri.
“Lafiya kuke kuka haka” kasa magana suka yi hakan yasa ya kai kallon sa ga wurin da idanuwan su ke. Ganin Zahrah da suka gaisa tare cikin mintuna marasa yawa yasa ya matso
“meh ya samu zahrah?" Badi'a da ta shiɗe tace
“Abbah Zahrah ta mutu, shikenan ta mutu kuma babu abun da aka yi mata”
A hankali Abba ya kai hannun shi ya riƙo hannun ta, jin akwai pulse yasa ya ɗago Zahrah da sauri.
“ku biyo baya na”

Cikin hanzari ya fita da Zahrah direct parking. Space ya nufa ya kwantar da ita, Ammi da Badi'a suka shiga.
Kai tsaye Northern Specialist hospital ya nufa da ita. Ba a ɓata lokaci ba aka karɓe ta saboda yanayin da aka zo da ita.

Cikin aƙalla 30minutes aka taro numfashin Zahrah da taimakon doctors da kuma Nurses. Daga nan aka saka mata line na N/A sannan aka yi mata antidepressants injection tuni bacci yayi awun gaba da ita.

Ganin doctors na fitowa yasa Ammi saurin nufar su
“ehm Please ta tashi ko? Zahrah bata mutu ba ko yauwah ku faɗa min meh ke damun zahrah”
Ganin yadda ta bi ta ruɗe yasa doctor murmusawa have
“she's Alright now, ammah tana buƙatar hutu, so zuwa jimawa za'a ɗauke ta daga nan a mayar da ita paediatric medical ward sai ku duba ta”
Jijjiga kai ammi tayi ba tare da ta fahimci dogon bayanin shi ba tunda yace she's alright.

Reception suka koma suka zauna suna ta addu'ar fatan sauƙi wa Zahrah. Sai a lokacin Ammi ta tuna basu bi sun sanar da Mamah ba can tace ba sai an sanar da ita ba kawai saboda kada a ɗaga mata hankali bayan ba cikakkiyar lafiya gare ta ba.

Har wajen azahar shiru hakan yasa Ammi komawa A&E wadda ɗin, karo suka ci da doctor ɗin da yayi mata bayani.
“ehm doctor Bata tashi ba har yanzu?”
“eh yanzu dai a je a nemo mata abun da zata ci zuwa jimawa zata iya farkawa anytime”
“ok” daga nan Ammi suka koma suka yi girki suka dawo.

Har yamma Zahrah bata tashi ba, hankalin su ba ƙaramin tashi yayi ba shine Mamah ta yanke hukuncin sanar da Mamah kada ta ji Zahrah shiru.
Abba na gida kawai ta ƙira shi tace ya aika yaro ya sanar da Mamah Zahrah na asibiti ammah ba sai ta zo ba da an sallamo ta zasu dawo.

Cikin sauri Mamah ta yi picking call ɗin da ke shigowa wayar ta.
“Eh ina ji”
Ta ɗaya ɓangaren kuma ban ji MEH aka ce ba. A zabure ta miƙe tsaye
“ban gane ba.....tooooh ko zaka sa a tambayi amaryar gidan ko tana kwance ba lafiya ne ita ma?.....ohk ina jira”

Daga haka ta dawo ta zauna.
Wasa wasa maghrib tayi kuma Zahrah dai bata farka ba, kuma Abba bai ƙira Ammi ba.
Yanke shawarar barin Badi'a tayi in yaso in Zahrah ta tashi kafin su dawo ma ita tana nan.

Tana isa bayan tayi girki ta nufi gidan Mamah, ɗakin Mamah ta nufa kai tsaye tare da sallama a bakin ta. Jin shiru babu amsa wa tasa ta shiga da sauri tunanin ta ko Mamah na bayan gida ne.
Shiga tayi ta ɗan zauna saboda ta jira ta. Jira shiru shiru Mamah bata fito ba gashi Ammi na son wucewa asibiti. Kai tsaye ta nufi hanyar banɗakin.
“da mutum ne a ciki?”
Sai da Ammi ta maimaita sau biyar ammah shiru ita ma nan da nan zuciyar ta buga wani irin tsoro ya kama ta.

Ganin jiran ba shi da amfani yasa Ammi ta shawarar tambayar baba amarya ko ta ga fitar ta.
Wani kallon banza Baba amarya ta wulla wa Ammi tare da jan tsaki ta koma ɗaki bayan jin ƙudirin Ammi.

Cikin ruɗu Ammi ta fice zuwa gida, ta sanar da abba kafin yace ta wuce babu damuwa wata ƙila Mamah gidan wasu ƴan uwan su ta tafi.

Har lokacin da Ammi ta koma ba'a sauyawa Zahrah waje ba saboda har lokacin bata farka ba.
Allah Sarki ƙauna Badi'a kam kasa cin komai tayi sai kuka ta ke yi

“kiyi haƙuri kiyi wa Zahrah addu'a idan kina kukan babu abun da zai miki sai dai kema ki fara ciwon kai.”
Kai ta gyaɗa tace
“toh mamah”
“oyah zo ki ci abinci” babu musu ta ƙarasa Mamah tayi serving nata, ta ɗauki spoon kenan zata kai loma tace
“Ammi baki bi kin yi wa Mamah magana ba ne?”
“eh tana kan hanya” haka kawai ta faɗa saboda kada ta tayar mata hankali.

Bayan Badi'a ta ci abinci ta ƙara barin reception ta nufi wurin A&E ta tsaya.
Tana cikin tsayuwar Dr. Ya fito. Ganin ɗazu ya ganta tare da Ammi yasa ya nufe ta.
“Baby ina mamar taku?”
“tana can reception” kallon ta yayi yace ta ƙura Maman su.
Da sauri ammi ta biyo bayan Badi'a suka taho.
Ganin irin tashin hankalin da Maman nasu ta shiga yasa Dr. Yin murmushi.

“Yauwah Hajiya ke ce kika kawo wannan yarinyar ko?”
“e...eeeh nice ta farka ne?”
“eh ta farka ammah bata cikin hayyacin ta, so yanzu za'a sauya mata ɗaki sai a bata abinci taci”
“tooh shikenan”

Bayan an sauya wa Zahrah ɗaki zuwa medical ward Ammi da Badi'a suka wuce. So da yake amenity suka kai ta ya sa duk su biyun suka shiga.

Lumshe idanuwan ta suke yayin da fuskar ta tayi pale, sai kamannin ta da Mamah ya ƙara bayyana.

Ƙarasawa wajen ta suka yi suna ambaton sunan ta.


MU HAƊU GOBE DON JIN YADDA ZATA KAYA HAƊU GOBE DON JIN YADDA ZATA KAYA

[05/10, 7:26 a.m.] 💎Diamond Bhatool 💎: ______________★★★_______________
Typing 📲
🏡 *A BABBAN GIDA* 🏡
_(All in a big family🏠)_
★TAKUN FARKO★
_[Labari/Rubutawa]_
*©Fadimatu Adamu Hassan*
*A.K.A DIAMOND BHATOOL*💎

_______________★★★________________️






PROLOGUE


*PAGE* 1️⃣6️⃣

Dedicated to Aunty fateemah (oum sa'eem)

*Masu son labarin daga farko kuyi following channel ɗin nan:* https://whatsapp.com/channel/0029VanUFkw5kg7G2ci16o2X

SHARE AND COMMENT PLEASE
_______________★★★_________

A hankali Zahrah ke buɗe idanuwan ta yayin da suka buɗe ras sun sauƙa kan Ammi da Badi'a.
Juya idon tayi don gane a wani wuri take, ganin I.V line maƙale hannun ta ga kuma ruwan da ke zuba a hankali yasa ta fahimci a asibiti take. Ammah me ya kawo ta?
A hankali ta fara tuna last scene nata ta shiga duba Mamah gidan Ammi kuma bata ganta ba daga nan ta manta yadda take.

Katse mata tunani Ammi tayi ta hanyar zuba cips and fried egg da ta soyo mata a plate. Kujera ta na ta zauna yayin da ta miƙawa Badi'a plate ɗin wacce fuskar ta ke ɗauke da murmushi.
A hankali Ammi ta ɗago Zahrah bayan ta zaunar da ita da kyau ta amso plate ɗin hannun Badi'a ta fara feeding Zahrah, bata Musa ba ta buɗe baki ta naɗi child ɗin tas.

Bayan ta kammala ci Ammi ta dama mata tea Mai kauri ta Sha, daga nan nurse da ke duty ta shigo, ganin IV fluid ɗin ya ƙare yasa ta zare mata shi kada jini ya zuba. Daga nan ta turo doctor.
Dr. Yayi farin ciki sosai ganin ta ji sauƙi har ya jata da zance. Tuni ta ware kamar babu abun da ke damun ta.
Da zai fita ya kira Ammi zuwa office ɗin shi, a nan ta sanar da ita abun da ke damun Zahrah
“ba komai ke damun ta ba sai anxiety Wanda yayi sanadiyar faɗawar ta shock ammah abun bai yi nisa ba Alhamdulillah, sai dai yarinyar taki na buƙatar kulawa ta musamman in ba haka ba akwai matsala. So yanzu na rubuta drugs sai ku bi pharmacy ku amsa. Don Allah Hajiya a kula da ita kuma a nuna mata soyayya”

Daga nan Ammi tayi mishi godia ta koma ward ɗin cike da fargaban ina Maman Zahrah ta je yau kuma, sannan menene dalilin faɗuwar Zahrah.

Basu ɓata wani lokaci ba aka yi discharge nasu, bayan shawarwarin da nurse ɗin da ke duty ta Basu.
A gajiye suka wuce gidan Ammi. Ɗakin Badi'ah Ammi ta raka Zahrah, ta haɗa mata ruwa mai zafi ta sata tayi wanka. Bayan ta shiga wanka ta turo Badi'a wurin ta sannan ta koma gidan ko mamah ta dawo sai dai shaaaaam kamar yadda taga ɗakin Mamah yanzu haka yake.
A sukwane ta dawo gidan lokacin Zahrah tayi wankan ta ta saka light gown na Badi'a.

Ita dai Zahrah baki ƙimmm bata ce komai ba tunda suka shigo gidan, ganin haka yasa Ammi ta bar ta zuwa safiya suji meh yasa ta faɗi.
“daughter ki kwanta ki huta, sai da safe.”
Kaɗa kai Zahrah tayi daga nan suka kwanta ita da Badi'a.

Ɓangaren Ammi da Abba abun ya ɗaure musu kai. Abba tun bayan Ammi ta sanar da shi mamahn Zahrah fah Bata nan shima ya shiga halin mamaki.
Daga ƙarshe suka yanke shawarar neman ta gobe bayan sun ji damuwar Zahrah ɗin.


★★★★★★★

“gaskiya ƙawata aikin boka Bulebule kamar yankan wuƙa yake”
Tafawa suka yi ita da Asabe kafin Asabe tace
“ke dai ki bari yanzu bani labarin abun da ke faruwa manah, shegiyar ta mutu ne”
Kallon ta baba amarya tayi kafin tace
“ke har kin manta boka Bulebule baya kisa ne?,”
“ooooh haka fah” ta faɗa tana riƙe baki alamun ta tuna
Baba amarya ta Kamo hannun Asabe ta riƙe sannan tace
“ina baki labari, ban san yaushe shegiyar matar ta fita ba ammah dai zancen da nake miki an rasa ta....wataƙila yanzu kam ta riga ta kama bolar zama”
Ta faɗa suna sheƙewa da dariyar shaƙiyyanci.
“baki da dama ƙawa ta, toh ita ƴar tata fah?”
Ɗan zare ido tayi sannan tayi fari
“ohoooh Ni ban sani ba, ammah na sani babu makawa aikin boka ya yi ina jira ta dawo ta sane ni nan”

Girkin da take yi ta ƙarasa ta zuba musu shi duka a tray, suna ci suna magana kamar wasu mahaukata. Bayan sun cinye suka ji gaba da hirarrakin su.
Baba amarya ta dubi Asabe ta ce
“ƙawa ta yaushe ya dace na ɗauko Bibalo ne daga ƙauye don yanzu kam ita ma nan zata dawo NBmu zauna mu mulki ɗiyar shegiyar tare”
Dariya Asabe tayi tace
“ƙwarai ya kamata ki ɗauko mana Bibalo gashi kuma ba zata fi sa'ar ƴar kishiyar taki ba”
Jin kishiya yasa Baba amarya makawa Asabe harara. Da yake duk ƴan duniya ne tuni Asabe ta harbo jirgin ƙawar tata sannan tace
“Kaji uwar kishi, kin zo kin samu mata da ƴa gidan su ammah ke kike kishi ba ma ita ba”
“yo ai dole nayi kishi da ita, da ace irin banzayen nan ne ma tooooh, ammah baki ga matar ba ga kyau ga kamala ni wallahi bata yi min kama da ƴar talakawa daga gani ƴar babban gida ce”
“ai kuwa na lura da hakan, ammah ko ma ƴar jibgegen gida ne ba babban gida ba yanzu kam ai kin wulaƙanta ta ta zama kashi”

Tafawa suka yi suna dariya kafin Baba amarya tace
“yanzu dai gobe ki raka ni ƙauye mu ɗauko Bibalo mudawo nan saboda ina son mu gasawa shegiyar aljanar yarinyar nan aya a hannu, ta yadda zata daina rasar kunyar da ta zama mata jiki”
“Ai Ni ƴar nan tun ranar tariyar ki na ƙullace ta saboda abun da tayi ga kuma shegen kyau har ta so ta fi uwar fa”
Bana amarya ta ce
“hmm ke dai ki bari kawai, zamu ci uban ta ne ai”
Haka suka yi ta hirar su daga ƙarshe Asabe ta koma gidan mata da yake dama can ita a can take da zama.

★★★★★★

Asuba nayi Zahrah ta tashi a hankali tayi alwala tayi sallah bayan tayi ta tayar da Badi'a ma tayi.
Bayan sun yi sallah suka yi wanka saboda yau zasu koma makaranta bayan sun dawo daga Jos.
Basu shirya ba sai around 6:30am suka nufi kitchen don taya Ammi aiki sai dai Ammi ta kora Zahrah kan ta huta ai bata da lafiya ita kam.

Da wuri suka yi breakfast ganin akwai sauran lokaci mai ɗan yawa yasa Ammi tace
“zahrah” a hankali ta ɗago da kanta ta mayar da hankalin ta kan Ammi
“jiya MEH ya same ki

Please Login or Register in order to submit comment