You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

yanzu domin basussukan da ake Bina sun kusan miliyan guda to amma acan cikin zuciyata ni nasan auren fadila ba daidai bane na farko dai ba dole bane tace tana sona in kuma ma ta amince Dani ba itace irin uwar daya kyautatu na samarwa 'ya' yana ba domin ayanda ubanta ya bani labarin halin ta ko na aure ta zaiyi wuya in zata daina bin maza.
A dacan kuma wani bangare na zuciyata nasan duk kwane kwanen da nake na abu daya ne hakika na kamu da son lauriyya tabbas in har zan auri wata mace a duniya toh lauriyya ya kamata na aura nace da kaina.......
.
NIMA YARIMA NACE KA HAKURA DA FADILA KA AURO LAURIYYA TALAUCI YACI GABA DA SUBURBUDAR KA.
.
NI KAM INA JAM'IYYAR FADILA DA BABANTA
[13:28, 1/27/2018] ‪+234 806 858 0203‬: ALAKAKAI-21
.
(m) Nazir Adam Salih
.
(c) Yarima Gangariya
.
Idan har zan auri mace a duniyar nan toh lauriyya ce nace da kaina.
.
To sai dai fa ga fadila ga miliyan biyar. Wani zazzafan gumi yafara sartu akan goshina acan wani bangare na ofishin agogon bango ya fara buga kararrawa karfe biyar da rabi na yamma.
Zuciyata tagama shiga rudani abubuwa uku agabana.
Lauriyya
Miliyan biyar da fadila
Biyu nafi son na mallaka daga ciki to Saidai kuma daya daga cikinsu yashiga tsakanina da guda daya tabbas in har Inason lauriyya to sai dai in hakura da miliyan biyar.
In kuwa kudin nake so dole ne saina hada da Fadila. Allah kiyaye nace cikin zuciyata. A can wani bangare kuma wata zuciya sai cewa takeyi dani kai shashashan banza saikace ba wayayye ba ka manta kawai da lauriyya ka auri fadila ko ka rabu da talauci da wulakancin Abokan harkar ka na shirin fim yanzu in banda shirmen ka har akwai wani abun kunya da aibu da miliyan biyar bazata iya lullubewa ba?
Hilal..... Naji muryar lauriyya ta daki dodon kunnena na dago kaina firgigit ina shafar fuskata da hannu.
Tunanin me kake yi? Ta tambaya lokaci guda kuma ta matsa kusa dani ta zauna akan teburin dake gaban kujerar danake zaune kadan ya rage gwiwarta ta gogi tawa.
Akwai alamun damuwa karara a fuskar ta.
Uhm.. Bawani tunani nake ba gajiya kawai nayi lauriyya ta zuba min idanu na tsawon lokaci na lura karyar dana shirya bata samu matsugunni ba.
Mintunan ka ashirin fa kenan kana zaune cikin ofishin nan kai kadai kuma kace ba tunani kake ba? Sai fa dana kira sunan ka har sau hudu kafin kaji ni... Ban amsa mata ba dan banida abin cewa Gaskiyar ta tabbas tunani nake.
Lauriyya ta ci gaba da wasa da Biron dake hannun ta tana kida dashi a tausashe akan teburin.
Da wata shawara nazo da ita Hilal... Kokuma ince neman alfarma. Nan da nan na juya na kalle ta cikin mamaki sai a lokacin ne na lura ashe akwai jaka rataye a kafadarta.
Ina zaki tafi ne naga kin dauko jaka? Lauriyya ta girgiza kai.
Babu inda zani muka sake yin shiru.
Ni Nafara magana. Wacce shawara ce.... Kokuma ince wacce alfarma kike nema? Na tambaye ta zuciyata na harbawa abin na da rudarwa. Yan sa'o'i kadan fa kenan da attajirin ya nemi alfarmar na Auri 'yarsa to ko itama alfarmar na aure ta zata nema?
.
Hilal nasan ana binka basusuka dayawa wadanda na tabbata bazaka iya biya ba a kwana kusa.
Lauriyya ta dago kanta ta dube ni sainaga kwalla ta taru cikin idanun ta.
SHI Yasa nazo neman alfarma. Alfarmar itace zanyi Maka kyauta ta musamman da wani abu wanda zai taimaka maka ka rage mafi yawan bashi da ake binka.
Idan na baka so nake ka karɓa kada ka juya hannun kyauta baya shine kawai alfarmar..... Wani abu mai kamar gare gare yafara zaryar cikin kwakwalwata.
Me kike son ki bani? Na tambaye ta a iya tunanina lauriyya bata da wani abu da zai iya biyan koda rabin bashin da ake Bina.
Jikinta na rawa ta sauke yar madaidaiciyar jakar dake makale a kafadarta ta dorata akan bencin dake gabana sannan saita daga jakar sama ta zazzage abubuwan dake ciki akan teburin. Alokacin sa al'amarin ke faruwa duhu ya gauraye dakin domin tuni har an fara kiran Sallar magariba kuma bamu kunna kwan lantarkin dake cikin ofishin ba. Amma duk da hakanan sai kyalkyalin abubuwan ya haskake dakin sarkokine yan kunnaye da sauran tarkacen kayan karau na kwalliyar mata duk dayake bansan darajar su ba amma nasan sunada tsadar gaske bakina na rawa na girgiza kai.
Lauriyya.... Baza ta yiwu ba bazan iya raba ki da kayanki ba... Kuma ina kika same su ban taba ganinsu ajikin ki ba dan abin da kike samu kuwa a kamfanin nan bai isa ko iya tarawa kike balle har ya sayi wannan ba. Lauriyya ta matso gareni ta dafa kafadata tace.
Kayiwa Allah Hilal kayiwa Annabi ka karɓa tunda nake ban taba neman alfarma agurinka ba sai wannan idan kaki karɓa ka gama bata min rai ka konan zuciya.
Toh amma dai lauriyya bai kyautu ba ace in har ni ban yi miki ba ke ki..... Ta katse ni ta hanyar daga hannayen ta.
Kada ma kafara wannan zancen Hilal tunda nazo garin nan wake wahala dani in ba kai ba Kaine uwata Kaine ubana Kaine abin kaunata ka kadai ne ka iya sani dariya har cikin zuciyata. Ta danyi shiru tana kokarin share hawaye.
Farin cikin ka shine farin ciki na tunda nazo garin nan baka taba sanin tarihina ba baka kuma takura min saina fada maka sirrina ba amma kake taimaka min iya karfin ka yau juyi nane na taimake ka don Allah kwashe su Hilal ko a kasuwar barayi ka sayar dasu akalla zasu kai dubu dari shida. Ta dafa hannuna ta kankame.
Kaji Hilal don Allah kwashe su Narasa abin da zance da ita. Wata zuciyar nacewa dani kada ka yarda ta rudeka dubu dari shida basu kai miliyan biyar ba.
Karkari dai su biya ma bashin amma zata kare babu komai a hannun ka
Nayi fatali da kururuwar zuciyar. Hakika abunda lauriyya tayi min bazan taba mantawa da ita ba har iya rayuwata nasan cewa a yadda take da Matsalar ta sa komai tabani kadarar ta cancak ta makudan kudi zata iya bani naira miliyan dari inda ita tana da shi.
Hilal... Hilal kayi magana mana ka zura min idanu in kuma banida matsayin da zan nemi alfarma kayi min saika fada na kwashe kayana na tafi.
Kada kice haka lauriyya ki kuma daina cewa alfarma kike nema ai nine kika yiwa alfarmar bakisan wani abu ba lauriyya nace da ita ina duban ta ido da ido.
DUK duniya a yanzu banida wadda tafiki in babu ke lauriyya bansan inda zan sa kaina ba kece garkuwa ta mai tallafa min na yarda zan karɓa amma ki ajiye min su agurin ki daga nan zuwa sati guda kawai.
Lauriyya ta dada kankame hannuna saita fashe da wani tattausan KUKA.
Ban taba farin ciki irin na yau ba Hilal kuma.....
Kwankwasa kofar da aka yi shine ya katseta nan da nan ta Mike tsaye cikin sauri ta share hawayen dake idanun ta muka dubi kofar lokaci guda aka dada Kwankwasawa.
Bari in je in gano tace dani a tausashe. Na gyada mata kai sannan nayi sauri na boye sauran kudin dubu ashirin da suka rage me yiwuwa wani mai karbar bashin ne nace cikin Raina.
Bata dade da fita ba sai ga lauriyya ta dawo ta tsaya gabana ta rike tsantsa akwai alamun damuwa a fuskarta.
Wata ce wai take son ganin Ka nayi ajiyar zuciya nasan aduk masu Bina bashi babu mace ko daya.
Kice da ita ta shigo nace da ita... Ina Nan zaune sai Naji motsi ina daga kaina sainagan ta tsaye agabana. Nan da nan dakin ya hade da kamshi doguwa ce sanye da doguwar riga ruwan Hoda kanta lullube dan kyalle irin launin rigar. Baba iya ganin fuskar ta Sosai domin haryanzu ban kunna kwan lantarkin dad ofishin ba.
Sannun ki da zuwa malama ga mamakina sainaga ta matso ta zauna a bakin teburina daidai da inda Lauriyya ta zauna.
A'a MALAMA ga kujera nan koma can ki zauna mana ta fashe da dariya cikin wata zazzakar murya.
Hilal Wallahi kabani mamaki daka kasa gane ni.
Ko na kara kyau ne? Naji gabana ya fadi rasss nan da nan sai ta girgiza kanta lullubin dake kanta yafado kan kafadarta siraran gashin ta suka bayyana suna sheki.
Me yiwuwa kafi gane ni ahaka ko haryanzu baka Gane ni ba JARUMIN JARUMAI.
Ta sake fashewa da dariya.
NICE FA FADILA......
.
SHIDA 6 Loading.........
.
ALAKAKAI-22 Loading.......
.
KAI ANYA KUWA NIMA BA JAM'IYAR LAURIYYA ZAN KOMA BA
[13:30, 1/27/2018] ‪+234 806 858 0203‬: ALAKAKAI-22
.
(m)Nazir Adam Salih
.
(c) Yarima Gangariya
.
Me yiwuwa kafi ganeni ahaka ko haryanzu baka ganeni ba JARUNIN JARUMAI.
Ta sake fashewa da dariya.
NICE FA FADILA....
.
SHIDA 6
.
Fadila nakira sunan ta a sanyaye ko shakka babu ta sani bala'in kaduwa domin ban taba tsammanin zan sake ganin ta kwana kusa ba Hilal kenan manyan gari ta tashi daga kan teburin ta nufi kujerar dake fuskantar teburina ta zauna.
Babu wuta a ofishin ne ko kafi son zama acikin duhu ne? Na muskuta akan kujerar na fara farfadowa daga cikin kaduwar danayi.
Akwai..... Wuta ban kunna bane ga makunnar nan a bayan ki Fadila ta Mike tsaye ta lalubi makunnar lantarkin ta kunna dakin ya gauraye da haske numfashina ya dauke yawun bakina ya kafe. Nashiga uku nace cikin Zuciyata ashe kyakkyawace ta gaske kamar ta karanta abin da ke zuciyata saita kashe min idanu tace.
BAKA dauka na kai haka ba ko? Kallon tsoro kayi min jiya ta matso kusa da bakin teburin tana tafiya tana girgiza jikinta da gangan kusan ko ina a jikinta rawa yake ta dafa kan teburin da hamnayen ta na dubi yan yatsunta sirara ne farare sol babu wani alamar tabo ko kwarzane atare dasu kamar jikin maciji.
Tsawon lokaci tana tsaye akaina ta lullube ni da kamshin turare da man dake jikinta bansan sa'ar data dauke hannaye ta daga kan teburin ta Mike tsaye ba.
Hilal yaya naga kayi shiru ko bakaji dadin zuwana bane? Nayi kokarin na tattare hankalina guri guda nace.
Da wacce yau kika zo kuma? Wata sabuwar kyautar kika kawo Min?
Fadila ta bata rai
KA cika rikon magana wannan zancen ya fita daga bakin ka Hilal.
Abinda ya wuce ya riga ya wuce jariri dai tuni an gama binne shi an riga an binne shi tun da safe. Tayi shiru tana tsuke baki muka sake yin shiru.
Amma.... Dai kinsan ai abunda kikayi baki kyauta ba ko? Ko kina ganin daidai ne Abinda kikayi? Fadila ta dauke kai gefe guda.
Da zamu bar zancen nan dai da zaifi.
Don me yasa kika ce haka?
Saboda tone tone bashida dadi. Na Mike tsaye daga kan kujerar na jingina da bang.
Fadila Gaskiya al'amarin ki sun dame ni kin.... Ta katse ni.
Hilal Inason ka sani cewa duk abin da nayi adaren jiya nayi ne saboda mahaifina in baka sani ba kasani duk da cewa kuwa mahaifiyata tafi kaunata da shagwaba ni duk duniya babu wanda nake kauna kamar sa.
A zuciyata nace duk yadda akayi yarinyar nan tanada tabin hankali babu mamaki Hakan ne yasa ake kokarin bani auren ta.
Nasan Abinda kake tunani banida hankali ko? Ta dubeni. Na girgiza kai.
Kada ka boye min jarumi Hilal naga alamu a idanunka amma yana da kyau ka yi tambaya kafin ka yanke hukunci.
Toh..... Amma saiki kashe jariri kice wai saboda kaunar mahaifin ki kikayi? Ta kada min idanu tace.
....... Nan da wata bakwai mahaifina zai bayyana aniyarsa ta tsayawa takarar gwamna babu abin da nake buri irin ace yau mahaifina ne Gwamnan garin nan. Tayi shiru tana rangaji agabana kamar bishiya.
Ina Fatan yanzu ka fara fahimtar hoton da nake kokarin zana ma? Kaga Hilal ciki dai nariga nayi Munso mu zubar da cikin nida mahaifiyata tun yana ƙarami mahaifina ya hana lokacin Dana haihu sainaga in har na bari dan ya girma nagama kunyata mahaifina kuma idan zancen yafito Abokan hamayyar siyasar sa na iya yin amfani da damar su bata mahaifina.
Amma kuma bakya ganin yanzun ma bata sauya sani ba tunda dai ai jama'a da dama sun sani kinada cikin shege?
Jama'a kamar su wa? Ta tambaye ni gamida daga girar idanunta sama.
In banda kai dakuma likitan mu da ya auna ni ya tabbatar ina da cikin duk duniya babu wanda yasan inada cikin kai ko wanda yayi min cikin baisan inada shi ba domin tin yana dan wata daya aka hanani fita ko ina aka sa masu gadina har sai dana haife dan.
Kawaye na da Abokan Arziki idan sun zo ne mana sai ace dasu bana Kasar.
.
Nayi shiru ina sauraron shashashan zancen ga mamakina sianaji duk da kyawunta nafara tsanarta ko kadan bata da kunya.
Ina ganin idan babu sauran wani abu da zaki fada ni zan fita nayi sallah kinga har an idar sa sallah a masallaci nafara yar tafiya a cikin ofishin.
Au harma korata kake yi? Ta bata fuska.
Babu zancen kora kora in kina iyawa jirani nayi sallah sai muci gaba da hirar daga nan zuwa asuba.
Muga abunda Allah zaiyi nasaki Murmushi nafara Jin dadin badakalar.
Wai dan Allah da gaske kike yi baki kawo min kyautar komai ba? Ta kawo min duka cikin wasa na kauce.
Ya ishe ka haka kaga bana so.
Ta juya ta fara tafiya akwai alamun farin ciki a fuskar ta.
Muje to ka rakani.
Muka ratsa ta cikin dakin karbar baki.
Ban iya yarda na kalli inda lauriyya ke zaune ba.
Toh amma na lura zaune take ta kifa kanta akan teburin dake gabanta.
Nayi tsammanin zata biyo bayan mu da man Ga al'ada duk bakon da ya zo tare da ita muke raka shi amma Sam Sam bata biyo mu ba tun kafin mu Gama fita na hangi katuwar marsandin tana kyalkyali acikin hasken farin kwan lantarkin daya haskaka kofar ofishin......
.
KAI NIFA NA RIKICE NA RASA WACCE ZAN GOYA WA BAYA
LAURIYYA KO FADILA ????
[21:03, 1/30/2018] ‪+234 806 858 0203‬: ALAKAKAI-23
.
(m) Nazir Adam Salih
Baban Ahmad Da Adam
.
(c) Yarima Gangariya
.
Tana kyalkyali acikin hasken farin kwan lantarkin daya haskake kofar ofishina.
.
Muka karasa gindin motar babu magana muna tafe kafada da kafada da muka isa gindin motar ta fuskanceni
yaushe zaka zo? Tambayar tayi matukar girgizani.
Ina kike nufi? Fadila ta dafe kirji cikin razana ta harareni a fusace.
Au baka san zancen ba?
Wane zance? Fadila ta girgiza kai tace shikenan tunda baka sani ba daman babane yace nazo na sameka amma tunda kace baka san komai ba shikenan. Tana gama fadi saita juya cikin fushi ta shige motar.
Shashashan banza sakarai. Wata zuciya tafara yi min kururuwa idan ka bari ta tafi baka lallasheta ba kamar kayi sallama ne da miliyan biyar. Mafarkinka duk ya zama shirme.
Fadila Fadila na kira sunanta cikin gaggawa ta sauke gilashin tagar motar na sunkuya nace.
Kiyi hakuri dan Allah Fadila... Idan kin kula duk ba'a ahankalina nake ba a rude nake... Fadila ta dubeni ta tabe baki sannan tayi tsaki tace.
Yi sauri ka koma gurinta tana can tana kukan kishi kada ta mutu... Gabana yayi das das.
Wa kenane kike nufi? Na tambaya baki bude.
Kafini saninta... Wancan baiwar taka dake jiranka a ofis. Tasawa motarta giya ta firzgeta aguje tabarni anan tsaye ina hangen kurarta.
SAI WATA RANA MILIYAN BIYAR.
Nace da kaina kamar na fashe da kuka koda na nufi ofishina sainaji wani zazzafan zazzabi yana neman rufeni.
.
*********** ****** **********
.
Har sa'ar dana dawo dakin karbar bakin lauriyya tana nan kamar yadda nabarta kanta kife akan teburina na tsaya akanta.
Lauriyya na kira sunanta akwai alamar rawa a muryata. Ta dago kai ta kalleni da wani fatalwan murmushi. Ba sai an fada ba duk wanda ya kalli idanunta yasan taci uban kuka duk kuwa da matukar kokarin datayi wajen share hawaye.
Har ta tafi? Ta tambayeni hannunta rungume a kirjinta.
Ta.... Tafi na fadi muryata na sarkewa.
Mukayi shiru babu wanda ya sake cewa kala har aka kira sallar isha. Sai lauriyya ta mike ta sakala jakarta akafada.
Hilal zan tafi gida... Na danyi shiru na farko saikuma nace Gida? Haka da wurwuri... Ta danyi tsaki sai gabana yafadi tunda nake da ita bata tabayin tsaki a gabana ba.
Banajin dadi ne... Shiyasa nake son tafiya yau da wuri muka dan sake shiru na tsawon lokaci.
Dan dakata to ina da sauran magana dake.. Ta hade fuska.
Maganar me kuma zakayi min na dauka mun gama komai tun dazu? Ga kayan ai acikin jakata. Ta nuna jakar da hannunta.
Duk lokacin daka shirya saika karba in kuma kana so ma yanzu sainaba ajiye ce agurina.
Akwai sauran magana lauriyya... A ina kika samosu? Naji ta rike numfashi cikin kaduwa.
Hilal me kake nufi da a ina na samo su kana nufin kace ni barauniya ce?
Dan girman Allah kada ki bata zancen nan lauriyya ni bahaka nake nufi ba. Ki tuna fa kyauta zakiyimin da kararki ta makudan kudi a iya sanina kuma ban taba ganinki dasu ba kinga kuwa ashe banida laifi danna tambaya.
Ta sunkuyar dakai cikin takaici. Tambayar ta kona mata rai ta daga kai.
Tunda ka dage saika san inda na samesu bari yo na fada ma MIJINA NE ya saya min su.
Mijinki? Ta gyada kai.
Kwarai kuwa baka san na taba aure ba kafin nazo nan garin ba? Nayi ajiyar zuciya.
Ina fatan yanzu ka gamsu. Lauriyya tace sannan ta matso daf dani kusa dani har takai ina iya jinhucinta akan fuskata.
ITACE TA BATA MAKA RAI ?
Na kalleta a rude.
Wa..wa kenan kike nufi? Lauriyya ta dafa kafadata tace.
Nasan daman kafi karfina Hilal na dade ina kwana ina tashi da fargabar cewa watarana sai anzo har ofishin nan an kwace min kai!
Gabana yafadi nayi sauri na dauke hannunta daga kan kafadata.
Lauriyya nataba fada miki kuwa wata kalma kwaya daya?
Wacce kalma ce wannan? Ga mamakina sai naji ina mai kunyar hada idanu da ita.
Adacan Lauriyya ban dauki amatsayin komai ba fiyeda kawai sakatariya na. Nayi sa'a danaga ta kura min idanu kamar zata hadiyeni.
Yau lauriyya na wayi gari duk fadin duniya babu wata 'ya mace datafiki agurina. Lauriyya ta dada matsowa daf dani.
Na Gode Allah Hilal tun ranar dana dora idanuna akanka nake kaunarka.
Zan baki wani labari lauriyya ki saurareni da kunnen basira lauriyya ta dubeni dakyau. Labarin me kuma? Nakama hannunta muka wuce cikin ofishina. Wannan shine karo na farko dana taaba yi mata haka. Na zaunar da lauriyya akusa dani.
Lauriyya jiya da daddare wasu al'amura masu kama da shirin fim sun faru akaina. Abubuwan na da matukar rikirtarwa to ahaka dai ni gama yanke shawara azcuiayata cewa ni dai KE NA ZABA LAURIYYA.
Dan Amina Muhammadu.
Lauriyya tace tana tafa hannu. Ban fahimce ka ba hilal..... Me kake fadi ne kace ni ka zaba ban gane ba.
Me yiwuwa idan nabaki labarin ki fahimce ni ke dai saurara da kyau.
.
Nafara zubo mata labarin al'amarun kyautar jaririn da akayi min tun daga farko har zuwa kan zuwan fadila ofis.
Karfe tara saura kwata nagama bata labarin.
Lauriyya tayi shiru bata ko motsi kamar ruwa ya cinyeta ga mamakina akaro na farko sainaji da gama fada mata labarin damuwa zuciyata ta ragu.
Lauriyya ta mike tsaye tabar kusa dani sannan tafara safa da marwa....
[06:34, 1/31/2018] ‪+234 806 858 0203‬: ALAKAKAI-24
.
(m)Nazir Adam Salih
.
(c) Yarima Gangariya
.
Lauriyya ta Mike tsaye tabar kusa dani sannan saita fara safa da marwa acikin ofishin akwai wani yanayi dake fuskanta daya hanani na katse mata hanzari don haka sainayi zamana ina jiran naji ta inda zata bullo inada kwarin gwiwar cewa indai har akwai mafita to lauriyya ce zata kawota na yarda da kwakwalwarta akan hakan.
.
Hilal! Nayi firgigit sa'ar danaji ta kira sunana.
Mecece shawarar Ki akai. Lauriyya ta dawo kusa dani ta zauna sannan tace
Zancen gaskiya Hilal indai kabar miliyan biyar ta wuce ka kayi shashanci. Na zabura cikin kaduwa.
Me kike nufi? Lauriyya tayi dariya miliyan biyar tafi karfin wasa Hilal Amatsayina na mai kaunarka bazan so ka rasa naira miliyan biyar saboda ni ba.
Tunanina ya kure na rasa abin da zance da ita.
Ni shawara ta ta Hilal kaje ka aure ta.
Lauriyya meke damunki ne ta girgiza kai.
Lafiya ta Kalau babu abin da ke damuna ni har kullum babu abin da ke faranta min rai irin cigaban ka
Da miliyan biyar kana iya wa duk Abokan hamayyar nisa.
Lauriyya kibar zancen nan tuni nagama fada miki in har akwai wacce zan aura yanzu a duniya to kece. Idan kuwa na Auri fadila bansan da idon zan Kalle ki ba ta daga kai muka hada idanu tace.
Ko?
Kwarai kuwa na Mike tsaye.
Ko sallah banyi ba yakamata naje nayi sallah lauriyya ta biyo ni Abaya.
Kayi tunani Hilal tunda dai sati daya suka baka amma ni ina ganin gara ka aure ta Hilal.
Ban juyo na kalleta ba sa'ar da take maganar domin na lura ita kanta akwai wani sirri datake kokarin boyewa daga gareni. Wata zuciyar ta ci gaba da yi min kururuwa. Duk kabi ka zama wawa Hilal haka kawai kabari matan zamani suna neman su zauta ka.
Daya kasan yadda take dayar kuwa baka ma san koda tarihin taba.
Zan tafi gida Hilal sai goben lauriyya tace.
Mamakin abin da yasa ta firgicewa haka take sauri sauri ta tafi gida.
Toh shikenan sai goben kenan. Ahaka muka rabu da lauriyya ta tsallake bakin titi tana sauri sauri na bita da kallo cikin mamaki meke faruwa ne? Yanzun nan fa take nuna tsananin kishin ta a gareni take nuna cewa duk duniya ni take kauna lokaci guda kuma tana cewa naje na Auri fadila... Tabbas akwai wani abu murdadde acikin al'amarin.. Bi a hankali dan samari kada ka bari matan zamani su haukata ka a banza nace da kaina....
.
*********** *********** *************
.
Karfe tara da rabi agogon mota ta ya nuna nayi kokari tun sa'ar dana baro ofis na fitar da komai daga cikin zuciyata abunda nafi kauna yanzu a duniya shine isashshen barci domin rabona da barci sa'o'i kusan ashirin da hudu kenan.
Nayi fakin da motar a kofar gidana na rufe gilasan sannan na fito zan kulle kofar kenan sai Naji kamar motsi abayana na juya cikin sauri sainaga wata sura ta fito daga cikin duhu ta nufo inda nake.
Tun dazun nake jiran zuwan ka JARUMIN JARUMAI.
.
BAKWAI 7
.
Da wacce kuma kika zo? Na tambayi fadila lokaci guda kuma na jingina ajikin motar barcin dake idanuna ya zama tarihi a halin yanzu domin tuni nagama fahimtar fadila ta zama kamar tauraruwa mai wutsiya ganin ki ba.
Nazo maka ne da wani babban labari domin dazun na fahimci wani gani gani kake yi min ka daukeni kamar wata yar iska fadila tace tana tabe baki.
Fadila abin har Yakai da bakaken maganganu.
Yama wuce da haka Hilal duk abin da nake yi ni ba mahaukaciya bace nasan abunda Nakeyi tayi shiru tana maida numfashi
Babana yayi min bayanin duk abubuwan da kuka tattauna dashi jiya banyi mamaki ba sa'ar da nazo ofishin ka naga kana neman ka wulakanta ni ashe tallata maka ni akayi.
Cool down fadila nace da ita rabi da turanci rabi hausa.
Anki ayi cool down din da asama nake ta ci gaba da huci agabana.
Ka dubi da kyau Hilal tun daga sama har kasa kaga makusa ajikina?
Maganganun ta sun fara bani haushi dan haka sainace.
Azahiri dai kam ko shakka babu baki da makusa amma a badini kuma fa...
Ta yamutse fuska.
Abar kaza cikin gashinta Hilal a kare wanne ne ba bare ba ku yanzu yan fim har kuna da bakin da zaku bude kuce wa wani dan iska? Kai yanzun nan Hilal kana tsammanin kai waliyi ne? Yan mata nawa kuka bata a harkar shirin fim
[06:34, 1/31/2018] ‪+234 806 858 0203‬: ALAKAKAI-25
.
(m) Nazir Adam Salih
.
(c) Yarima Gangariya
.
Yan mata nawa kuka bata a harkar shirin fim?
Kada kice haka fadila ba duka aka taru aka zama daya ba.
Fadila ta zabura cikin fushi kamar zata hau ni da duka
Kasani Hilal na kasance daga cikin dubban yan matan da Allah ya jaraba da son karance karance da kallon Fina finan hausa wannan ne ma tasa duk inda akayi wani gangami na yan shirin fim sainaje gurin ba don komai ba sai kawai don na ganku Abin da baka sani ba shine ba dade da sanin ka abin da yasa ban taba tunkarar ka nayi ma magana ba shine girman kanka musamman ma a lokacin da kake kan ganiyar tashen ka..... Na katse ta.
Fadila duk naji kiyi hakuri don Allah kibar zancen nan mu rabu lafiya Wallahi barci ne a idanuna kamar na fadi nakeji. Tsaho lokaci tana nan tsaye tana ta kokarin dannan bakar zuciyar ta dake ingizota akan dokan danasani.
Dole ne na fada maka tarihina Hilal dole ne na fada maka.
Domin ka daukeni wata tambadaddiyar yar iska bayan kuma dan uwan ku ne dan shirin fim ya batani...... Bazan taba yafe masa ba har abada tafara kuka.
Aure Kam ko zan rasa miji a duniya bazan

Book Chapters
Chapter 1Chapter 2Chapter 3Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6

Please Login or Register in order to submit comment