You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

wasu albarkatu cike da tausayin ta a ranta. Ta ƙara yi wa auren
kyakkyawar addu'ar da ko a cikin zuciyar Minal ba ta ji za ta iya amsa ko ɗaya ba.
Tana ƙoƙarin barin wurin Minal ta yi hanzarin riƙo hannunta, sannan ta durƙushe ƙasa gwiwa biyu tana
ƙoƙarin danne kukan da ke son kufce mata. A haka ta yi ƙarfin halin yin magana a cikin sanyin murya ta ce,

"Don Allah idan kin san dalilin da ya sa Nur ta bar mini aurenta ki sanar da n... saboda ba zan taɓa yafe
wa kaina ba matuƙar na shiga tsakiyarta da angonta. Idan kuma har da gaske ta gudu ta bar mini
masoyinta a irin wannan rana da ta jima tana dakon zuwanta; zan ci gaba da tuhumar kaina daga yau har
ranar da na bar duniya. Ki sanar da ni gaskiya don Allah Hajiya, saboda zuciyata ba za ta taɓa nutsuwa ba
matuƙar ban san dalilin da ya sa Nur ta bar mini Jamal ba."

"Hmmmmm!"

Ajiyar zuciyar da Hajiyar ta sauke kenan tare da miƙar da ita tsaye, sannan ta shiga bubbuga bayanta cikin
sigar rarrashi. Saboda a lokacin hawaye sun ba ta haɗin kai ta hanyar zubowa ziii suna layi a kumatunta.

"Ko ma me ya sa ta bar miki shi; ki bar shi a matsayin ya wuce daga yau. Don haka ki karɓi mijinki kuma ki
kwantar masa da hankali ta hanyar da za ku daidaita kanku ba tare da kowa ya sani ba. Saboda Jamal yana
da zafi amma yana da sauƙin kai idan aka biyar da shi ta hanyoyin da yake so."
Jim Hajiyar ta yi tana kallon gefe, yayin da kan Minal yake ƙasa tana shesshekar kuka. Cike da son kawar
da zancen Hajiyar ta sake cewa,

"Dare yana ƙara yi Amina, ki yi haƙuri na manta da abinci a mota Amna za ta kawo miki kafin mu wuce.
Kuma ki saki jiki ki ci kada ki yi wa kanki horon yunwa. In sha Allahu komai zai wuce kuma za ki ji daɗin
zama da shi idan kuka daidaita."

Waɗannan maganganun nata suka sa ta gama sarewa a kan za ta samu amsar tambayar da ta yi mata.
Idonta a kan bayansu suka fice daga ɗakin tare da takun saukarsu a ƙasan benen har zuwa lokacin da ta
daina jin motsinsu. Ta jima a tsaye inda n'take ba ta motsa ba, kafin ta ja ƙafafuwanta n'ta ɗosana
ɗuwawunta a bakin gado. Amna ta dawo da foodflaks a hannunta ta ajiye gabanta cikin sauri ta fice, ba
tare da ta ce da ita komai ba.

Shiru ya ratsa falon sai sautin agogon bango da ke ta aikinsa yana harbawa ƙit-ƙit. Hakan ya sa ta cira kai
tana ƙare masa kallo cike da mamakin ganin adadin lokacin da agogon ya nuna mata. Karfe ɗaya da minti
goma na dare 1:10am, amma ba ta gasgata ba har sai da ta duba ƙaramar wayarta da ke cikin jakar
hannunta, a nan n'ta ga zahirin abin da agogon ya sanar da ita babu ƙarya.
Nan take wani sabon tsoro ya shige ta, saboda ba ta da masaniyar ita kaɗai ce a cikin gidan ko akwai
wasu mutanen. Saboda ko kaɗan ba ta yi zaton ƙiyayyar da Jamal ya nuna mata ta bar shi kwana a cikin
gidan ba. Sai dai tuno akwai maigadin da ke kula da shiga da ficen gidan ta ɗan rage jin tsoron. Amma
tabbas ba ta tunanin zuciyarta za ta samu nutsuwa matuƙar ba ta yi ido biyu da Nur ta amsa mini
tambayoyin da ke zuciyarta ba.
Hakan ya sa ta shiga ƙwala wa lambobinta kira ɗaya bayan ɗaya amma babu wadda n'ta samu. Ajiyar
zuciya ta sauke mai ƙarfi tare da furzar da wani iska mai zafi daga bakina.
Gadon ta sauko ta rafka tagumi hannu biyu, don ta gaji da zaman har ƙafafuwanta sun fara kumbura.
Saboda ba ta san ta yi zurfi a tunanin da ta lula ba sai da ta sake duba agogon wayarta ta ga 2:30am ƙarfe
biyun dare daidai. Kenan ta kwashe awa ɗaya har da wasu ɗorin mintuna a zaunen ba tare da ta sani ba.
Guntun tsaki ta ja tare da Allah wadai a kan abin da ya faru, musamman da ta tuno maganganun Nur a
lokacin da aka ce ga motocin ɗaurkar amarya sun zo. Da irin diriricewar da ta yi ta faɗa bayin da ke cikin
ɗakinsu har ƙawayensu suna tsokanarta.
Jimawar da ta yi a bayin ya sa Minal bin ta tana faɗin, "Malama ki fito ke fa ake jira!"
Nur ta buɗe bayin tana dariyar yaƙe, domin alamunta duka ya nuna kuka ta yi a cikin bayin, cikin wata
kalar murya sassanya ta ce,
"Ba sai kin kore ni ba, na sani yau za ki yi kwanan farinciki."
"Ke fa wata irin mutum ce wallahi, yanzu rabuwa da ke shi zai sa na yi kwanan farincikin?"

Minal ta jefa mata tambayar tana hararar ta cike da jin haushin abin da ta faɗa. "Kwantas Hajiyata, in sha
Allah daga yau sai kin jima ba ki saka ni cikin idanuwanki ba."

"Ke dai kika sani, kuma komai za ki faɗa ki faɗa, daga yau dai mun sauke nauyinki a kanmu."
Zancen Minal kenan wanda ya saka Nur juyawa tana yi mata wani kallo mai ɗauke da ma'anoni da yawa.
Kamar ta ce wani abu amma ta yi hanzarin tsuke bakinta gum, fuskarta a cure ta bar wurin tana ƙoƙarin
saita kanta a lokacin da mata suka cika ɗakin da guɗa.

Wannan nazarin ya ƙara ɗaukar lokaci kafin Minal ta gano kwanan zaune ta yi. Saboda bacci bai ɗauke ta
ba sai da asuba ta kawo jiki. Kasancewar ana yanayin zafi hakan ya sa ta ƙara bajewa ƙasan tayis tana
nannauyan baccin mai ɗauke da mafarkai kala-kala.
Ba ta tashi farkawa ba sai da ƙarfe 9:11am na safiya. ko shi kiran waya ne ya tayar da ita, a firgice ta
farka tana dube-duben da ya tabbatar mata ba gidansu ba ne, kuma da gaske abin da ya faru ba almara ne.
Cike da ƙuncin zuciya ta nufi bayi, saboda kiran ya katse kuma lokaci ya ƙure mata ba tare da ta yi sallar
asuba ba. A gurguje ta nemo hijabi a cikin wardrobe ɗin kayan Nur, ta miƙa raka'a biyu ta tofa addu'ar da
ba ta san me ta roƙa ba. Allah Ya taimake ta tun kafin a fito da amarya ta yi sallar Isha. Da ba ta yi sallar ba
wataƙila tashin hankalin da ya kunno mata kai ba zai bar ta nutsuwar yin sallar a cikin daren ba.
Ta jima saman sallayar da tagumi kafin wani kiran ya sake shigowa cikin ƙaramar wayarta. Muryar Hajiya
ta jiyo ta yi hanzarin gaishe ta ba tare da ta amsa ina kwanan da take yi mata ba. Saboda ganin ita ce ya
dace ta gaishe ta a matsayinta na babba.

"Ki ƙara haƙuri kin ji! Na aiko miki da abinci ki sauka ƙasa ki karɓa. Kuma ki ƙara haƙuri da yardar Allah
komai zai daidaita."

"Babu komai."

Iya abin da Minal ta faɗa kenan saboda bakinta ya yi nauyin da ba za ta iya cewa komai ba. Sannan ta
sauke wayar idonta a kan abincin da Amna ta kawo mata cikin dare wanda ko buɗewa ba ta yi ba
ballantana ta san mene ne a ciki. Jiki babu kuzari ta miƙe ta ɗauki foodflaks ɗin ta fice, zuciyarta tana jin
babu wani abinci da zai burge ta a daidai lokacin. Saboda ko yunwar ma ba ta ji kuma ba ta jin sha'awar cin
komai. Amma dole ta isa harabar gidan tana wara ido kafin ta hango maigadin gidan yana nufo ta da wani
madaidaicin kwando.
Cikin ladabi ya gaishe ta ita ma ta amsa babu yabo babu fallasa kafin ta karɓi kwandon ta miƙa masa
foodflaks ɗin ta juya ba tare da ta ce da shi ƙanzil ba. Tana ƙoƙarin shigewa cikin gidan ta ji sautin maigadin
yana cewa,

"Me za a yi da wannan Hajiya?"

"Abinci ne, ka je ka ci."

Amsar da ta bayar kenan ba tare da ta juya ba. Ranta yana tafarfasa ta koma saman ta zauna a kan bedside
tare da rungume hannuwanta a ƙirji tana cizon leɓenta. Hawaye ta shiga gogewa a kan fuskarta saboda
kanta ya yi ƙullewar da ba ta san ta ina za ta fara ba. Saboda tunanin a wane hali saurayinta yake wanda
bai zo a ranta ba sai da safiya ta waye ta tabbatar abin da ya faru babu wasa a ciki. Saɓanin kallon da take
yi wa abin kamar shirin da zai ƙare Nur ta dawo ɗakinta ita ta koma gida.

Zumbur ta miƙe, ta shiga watso kayan Nur da ke cikin wardrobe ɗin ɗakin ta shiga birgima a cikin su.
Saboda tuno lokacin da take jera mata kayan da hannunta cike da farincikin burin aminiyarta ya cika ta auri
wanda take so. Kayan ta shiga runguma tana shinshina ƙamshin turaren Nur da ta feshe mata kayan da shi
yayin jera su.
Wani sabon kuka ya zo mata, wanda ta kwashe lokaci tana juya zantuka a ranta babu mai rarrashin ta.
Kafin ta ji takun tafiyar mutane yana nufo ɗakin da sautin maganganu sama-sama. Amma ko kaɗan hakan
bai saka ta motsawa ba, har aka fara ƙwanƙwasa mata ɗaki ba ta yi magana ba ballantana ta tashi ta buɗe.

Muryar Innarmu ce a gaba kafin ta jiyo muryar gwaggonta Salame, waton ƙanwar Babanta. Da ido kawai
ta bi su, ganin salatin da suke yi a kan hango halin da suka iske ta cikin sa.

"Ahir ɗin ki Amina! Wallahi ki kiyaye ni tun muna shaida jun..."

"Dakata Binta, abin fa sai da rarrashi. Kuma abin da kike so ta bi ba zai biyu ta daɗin rai ba. Don haka ki
bar mini komai ni zan shawo kan matsalar."

Zancen gwaggonta Salame kenan cikin tausasa murya. Sannan ta nufi inda Minal take kwance cikin kayan
Nur, ta kama hannunta ta miƙar da ita tsaye tana faɗin,

"Kwantar da hankalinki Amina, ai ita rayuwar duniya mai sauƙi ce idan aka bi ta a hankali. Yaushe za ki
hana kanki zama lafiya a kan abin da ke ma kina da ikon taimakon kanki da kanki? Don Allah yi shiru share
hawayenki lamarin duniya ba a yi masa gaggawa. A sannu ake bin komai har cim ma nasara cikin iyawar
Allah."

Da waɗannan kalaman Gwaggo Salame ta yi nasarar hana Minal wani kuka, sannan cikin dabara ta zuba
mata abinci ta shiga tsakura duk da shesshekan kukan da take yi jefi-jefi. Amma ko kaɗan ba ta son haɗa
ido da Innarmu, saboda hararar da take wurga mata kamar ta rufe ta da mugun duka. Bayan ta ɗan ci
abincin ta kai ta bayi da kanta ta haɗa mata ruwan wanka ta baro ta, tare da ba ta lokacin da za ta
kammala ta fito tana jiran ta.
Minal ba ta ɓata lokaci a bayin ba, ta yi wankan a gaggauce ta fito. Gwaggo Salame ta miƙa mata ɗaya
daga cikin kayan Nur da ta gama gyara ta mayar wardrobe kamar yadda suke tun farko. Minal kayan ta
kalla sannan ta kawar da kai ƙirjinta yana bugawa ta ce,

"Ba kayana ba ne."

Gwaggon ta matsa kusa da ita cikin ƙarafafa gwiwa ta ce, "Duk abin da kika gani a cikin gidan nan naki
kuma haƙƙinki ne. Don A'isha da ta bar miki mijin har da komai nata ta bar miki, tun daga kan kayan
ɗakinta har zuwa suturarta."

"Gwaggo kayan Nur..."

"Kada ki ce komai saka kayan kawai."

Ta yi hanzarin katse ta saboda ganin tana so ta kawo mata wasa. Minal ta buɗe doguwar rigar lesin ta saka,
wadda ta sha adon aiki mai ɗauke da ɗinki stone work. Sannan gwaggo Salame ta ɗaura mata ɗankwali
tana faɗin,

"Ko ke fa! Kin ga yadda kika yi kyawu kuwa? Ma sha Allah ki tsaya a haka kada na sake ganin kuka a
idonki."

Nur ta yi marau-marau da ido ƙwalla ta cika idonta ta saka gefen hannunta ta share. Sannan ta zuƙe
majinar kukan tana cewa,

"Don Allah Gwaggo ku tausaya mini, wallahi ba zan iya zama a gidan nan ba. Saboda mutane za su zarge
ni a kan na ci amanar Nur. Sannan shi kansa angon nata ba zai taɓa karɓa ta a matsayin matarsa b..."
Ohh Allah 😔




D. Auta ce🙋
[2/20, 22:02] Hadiza D. Auta: *FANSAR ƘAUNA!*

*HADIZA D. AUTA*

*Masu neman littafaina ga su kamar haka; ABOKIN AIKINA, BAƘON YANAYI, JIKI DA JINI (A'ISHA), AMFANIN
FITILA, MAKANTAR SO, DIJE ƘARANGIYA, RUWA DA ƘANƘARA, GIDAN AURE. BAKAN GIZO, ZUBAR
HAWAYENA, DAKAN ƊAKA.., MUSAYAR ZUCIYA, TARTSATSI, SHAGALALLIYA da sauran su. Ga mai buƙata ya
tuntuɓe ni ta wannan lambar; 08022014771.*

*LAMBA TA UKU.*

"A hir ɗin ki amina! Wallahi ki fita idona na rufe. Yaushe arziƙi yana kiran ki tsiya tana korar ki da gudu! To
ban son shashancin banza, don ke Allah ya bai wa mijin ba A'isha ba, kuma ita da kanta ta bar miki shi ba
matsa mata aka yi dole sai ta aikata ba, yo ɓata lokacinki na me za ki dinga yi a kan abin da kina zaune allah
ya ba ki ba tare da kin roƙa ba?"

Fusatattun kalmomin Innarmu kenan waɗanda tsabar haushin da Minal ta ba ta ya sa ta miƙe tsaye tana
neman hanyar kai mata duka. Ƙur Minal ta kafe ta da ido cike da zargi ta sake cewa,

"Yanzu ya zan yi da Aminu? Wanda kowa ya san yadda yake faɗi-tashi a kaina?"

"Yi mini shiru sakarya! Shi Aminun idan kika aure shi zai ajiye ki irin gidan nan ne? Ki faɗa mini a kaf cikin
danginmu waye ya samu arziƙin zama irin wannan gidan? To ba ki isa ki yi mana baƙinciki ba, dole ne ki
zauna ko kina so ko ba kya so! An riga an ɗaura aurenki da shi, kuma babu uban da ya isa ya kunce auren
nan! Ke ko mutuwa za ki yi sai dai a fitar da gawarki ehe!"

Innarmu ta ƙare maganar tana kumfar baki da zaro wa Minal ido, alamun ƙiris ya rage ta jibge ta don ta
gama kaiwa bango a kan lamuranta. Minal ma tsaye take kanta a duƙe tana kallon yatsunta fuskarta a
kumbure bayan bakin da ta turo tana gunguni. Tafasar da zuciyarta ke yi ya sa ta yi maganar da take jin
dole sai ta amayar da ita ko za a kashe ta. Domin idanuwan da Innarmu ta kafe ta da su ba su hana ta
furzar da abin da ke cikin bakinta ba.

"Ni fa wallahi ko kaɗan kuɗinsa ba sa gabanta..."

"Mu su ne a gabanmu! Na ce miki mu su ne a gabanmu ki je ki faɗa wa duk uban da za ki faɗawa. Kuma
za mu ci sai inda karfimu ya ƙare, matuƙar muka samu damar cin sai mun ci...ke Amina wallahi na kusa
nakasa ki! Ni za ki gwada wa ƙarfin imani da taƙawa? To idan kin so ki ce da mu kwaɗayayyiya ai ba a
kanmu aka fara son abin duniya ba. Wawuyar banza ana nuna miki hanyar arziƙi kina runtse ido. Kuma
Aminu da kike zancensa a yanzu babu ke babu shi har abada! Saura kuma na ji labarin kin neme shi ko shi
ya neme ki ki ga irin matakin da zan ɗauka a kanku. Sakaryar banza sai na shayar da ke gubar mamaki
matuƙar ba ki shiga taitayinki a kan auren nan ba....Salame ni na tafi idan kin gama ki same ni waje ina jiran
ki..."
Martanin Innarmu ya ƙara lalata nutsuwar Minal, ta kasa shanye zafin maganganun a ranta tun kafin ta
dire zantukan, waɗanda ta ji mugun ɗacinsu a zuciya har cikin bakinta. Bayan ta gama kumbura ta fashe
da wani kalar kuka cikin ɗaga murya tamkar wadda ake tsula wa bulala. Innarmu tana gama faɗar
batutuwanta ta fice daga ɗakin a fusace tana ci gaba da faɗar duk abin da ya zo bakinta cikin faɗan da
sautinta yake tashi.
Ajiyar zuciya Gwaggo Salame ta saki mai ƙarfi kafin ta riƙo Minal ta zaunar da ita a kan gado. Jarumtar
rarrashin ta ta shiga yi har ta samu ta rage sautin kukan da take yi. Sannan ta yi jim na tsawon mintuna
kafin ta yi ƙarfin halin faɗin,

"Kowace rayuwa da kalar tata jarabawa, ke taki jarabawar ita ce wannan. Don haka ki bar wa Allah
lamuranki kada ki yi jayayya da ƙaddararki, saboda ba a sani ba ko ita ce alherinki kina ƙoƙarin turewa."

Shiru Minal ta yi ba tare da ta ce uffan ba, saboda maganganun Gwaggo Salame sun shiga jikinta, ta
share hawayenta ta koma ajiyar zuciya wata bayan wata. Duk da a ranta ba ta jin ta karɓi cushen da aka yi
mata a matsayin ingantaccen auren da ake yi wa kowace mace. Amma kuma ta fi jin daɗin maganganunta
a kan na Innarmu masu kama da ana yaƙi.

"Abu biyu zuwa uku nake so ki riƙe gam kafin mu ga kamun ludayin tafiyar." Maganar Gwaggo Salame ta
farauto hankalinta wuri ɗaya, ta nutsu tana sauraron ta ba tare da ta yi motsin kirki ba

"Na farko ki yi haƙuri a kan ba a nemi amincewarki ba, amma ki kalli hakan a matsayin gata ne da wasu
iyaye suke yi wa 'ya'yansu. Na biyu ki riƙe Ya Wadadu ɗari huɗu bayan kowace sallar asuba, tana ƙara
danƙon soyayya da kwarjini bayan farinjini na yankan shakku. Na uku kuma ki lizimci raya dare da nafilolin
biyan buƙatu a wurin Ubangiji. Na san kin sani akwai su kala-kala, amma kafin mu je ɓangaren abin da za ki
yi ki jawo hankalin mijinki; zan sanar da ke nafilar da nake yawan yi, wadda ni ma na gwada kuma nake
ganin amfaninta, saboda ina so ke ma ki amfana."

Shiru ya ziyarci ɗakin tsawon sakonni kafin Gwaggo Salame ta sauke nannauyar ajiyar zuciya ta ce. "Ki
tashi misalin ƙarfe ɗaya na dare zuwa biyun daren, ki yi nafila raka'a biyu kacal kuma kowace ki karanta
fatiha da Suratul Ahad, waton surar ƙulhuwallahu Ahad. idan kika sallame sai ki yi wata sujuda kada ki
ɗago kanki sai kin karanta La'ilaha Illa antassubhanaka inni kuntu minazzalumina sau arba'in. Kada ki bar
sujudar har sai kin faɗa wa Allah buƙatunki. Ina mai tabbatar miki za ki ga aikin addu'ar tamkar yankan
wuƙa da yardar Allah...."

Kiran wayar da aka yi wa Gwaggon ya sa ta yi hanzarin fito da ita daga aljihunta, ganin Innarmu ce mai
kiran; hakan ya sa ta tuno ashe ita take jira a waje. Ta miƙe tana gyara zaman lulluɓinta ta ce,

"Mu za mu tafi, zuwa anjima za a aiko miki wasu daga cikin kayanki, sauran kuma za a raba wa ƙannenki
da wanda Allah ya ciyar. Amma don Allah ki tsayar da hankalinki wuri ɗaya ki nemi zaɓin Allah. Ubangiji Ya
ba ku zaman lafiya, kuma ki riƙe sirrin mijink..."

Kiran da Innarmu ta sake bugo mata ya sa ta fice da sassarfa ta bar Minal a daskare bakin gadon, don ta
kasa motsa laɓɓanta ta yi mata sai anjima ballantana ta raka ta. Bayan idon da ta bi ƙofa da kallo tsawon
mintuna da fitarta ba tare da ta ɗauke kanta ba.

***
Jamal kuwa, tun da ya fice daga ɗakin bayan ya gama jaddada wa Hajiya ba ya son Minal. Cikin ƙunar rai ya
buga motarsa jikinsa yana rawa ya nufi gidansu. Sai dai kuma Allah ne ya kai shi gida lafiya, saboda
mahaukacin gudun da yake yi tamkar an koro shi ko kaɗan ba ya cikin nutsuwarsa. Uban horn ɗin da ya
dinga bugawa babu ƙaƙƙautawa; ya sa Baba maigadin gidansu ruɗewa jikinsa yana rawa ya buɗe gidan
bayan ya tabbatar shi ne ba gizo ya yi masa ba. Amma zuciyarsa cike da mamakin dawowarsa cikin gidan a
daidai lokacin, wanda ya dace a ce yana tare da amaryarsa a matsayinsa na sabon ango mai zumuɗi da
daren farkonsa.
Da ido Baban ya bi shi baki buɗe har Jamal ya shige sashen da ɗaƙinsa yake ba tare da ya bi ta kan
motar da ya bari a kunne ba, ballantana ya rufe murfi bayan fitarsa. Saboda idanuwansa ko gani ba sa yi
daidai ya faɗa ɗakinsa ya datse ƙofa, a sukwane ya isa bayi ya dinga zuba wa kansa ruwan shawa ba tare da
ya cire komai na jikinsa ba. Ya ɗauki tsawon minti talatin idanuwansa rufe ba tare da ya yi dogon motsi ba.
Zuciyarsa danƙare da ƙuncin da yake haddasa mata bugawa da ƙarfi tamkar ta ɓalle daga mazauninta ta
fito ƙirjinsa.
Wata nannauyar ajiyar zuciya ya saki mai ƙarfi, kafin ya fara atishawa wata bayan wata kuma har
lokacin ruwan yana sauka kansa zuwa jikinsa. Da lalube ya rufe shawar amma ya kasa ɗagawa daga wurin
tsawon mintuna. Saboda zuciyarsa ta ci gaba da hasko masa fuskar Nur tana feshin tsadadden
murmushinta har dimple ɗin ta biyu suna lotsawa. Hoton zuciyarsa ya hasko masa ita ne a wani lokacin da
suka je yawon shaƙatawa, inda ya ba ta cake a baki tana tauna tana yi masa wani kalar kallon da ya saukar
masa da kasala.

"Ya Allah!"

Furucinsa kenan a lokacin da kansa ya ƙara sarawa tamkar an kwaɗa masa guduma. Dafe da kan ya fito
yana layi saboda jirin da ke kwasar sa har ya zube kan gado riƙe da kansa yana faɗar kalmar Innalillahi fili
da zuciyarsa. Nan take ya fara rawar sanyi jikinsa ya hau fisga babu ƙaƙƙautawa, cikin mintuna kaɗan
numfashinsa ya fara sarƙewa, kafin ya yi luf bayan ya gama tari sama-sama yana dafe da zuciyarsa, saboda
idauwansa sun gama kafewa numfashinsa ya tsaya cak.

Ya kwashe tsawon lokaci a halin da yake ciki kafin dawowar Hajiya, bayan ta gama neman sa a waya ba
ta samu ba. Kuma maigadin gidansa ya tabbatar mata da lalle ya fita. Cikin tashin hankali ta kira
maigadinsu sannan ta samu nutsuwar faɗawa mota direban da ya kawo ta ya juya da su zuwa gida. Saboda
jin Jamal yana gidan ya rage mata kaso bakwai a cikin goman tashin hankalin da ta afka. Don zuciyarta ta
gama tsinkewa cike da tsoron faruwar abubuwa biyu, na farko kada ɓacin rai ya saka shi barin garin ba tare
da ta sani ba. Na biyu tsoron kada ya yi tsautsayi ya ja shi ya yi haɗari, don a halin da yake ciki bai dace ya
yi tuƙi ba.
Makullin motarsa da maigadinsu ya ba ta tare da yi mata bayanin yanayin da ya shigo gidan; jikinta ya yi
sanyi ƙalau, amma hakan bai hana ta isa ƙofar ɗakinsa da sassarfa ba. Amna biye da ita a cikin firgicin suka
shiga bugun ƙofarsa tare da kiran sunansa a lokaci ɗaya. Ganin babu motsinsa ballantana alamun zai buɗe
ƙofar, ga tagoginsa duka a rufe. Hakan ya sa Hajiya ta sa Baba maigadi ya ɓalle ƙofar iya ƙarfinsa.

Hajiya Mummy da Amna ihu mai ƙarfi suka fasa yayin da suka yi ido biyu da Jamal a kan gado. Baba
maigadi ya hau salati saboda alamunsa ya nuna babu numfashi a tattare da shi. Hajiya Mummy ta faɗi ƙasa
tana kuka bakinta ɗauke da kalolin salati saboda idanuwanta sun gama tabbatar mata da Jamal ya jima da
barin duniya. Amna kuma jikinsa ta haye tana ihu tare da faman jijjigarsa a kan ya tashi cikin ƙaraji da
zaucewa, bayan kururuwar da take yi a kan don Allah a kawo musu agaji.




Hmmm!😪




D. AUTA CE✍️
[2/20, 22:02] Hadiza D. Auta: *FANSAR ƘAUNA!*

*HADIZA D. AUTA*
*Masu neman littafaina akwai free akwai na kuɗi sai wanda kuke so.*
*ABOKIN AIKINA, BAƘON YANAYI.*
*JIKI DA JINI (A'ISHA), AMFANIN FITILA.* *MAKANTAR SO, DIJE ƘARANGIYA.*
*RUWA DA ƘANƘARA, GIDAN AURE.* *BAKAN GIZO, ZUBAR HAWAYENA.*
*DAKAN ƊAKA.., MUSAYAR ZUCIYA.* *TARTSATSI, SHAGALALLIYA da sauran su.'Yan kasuwa masu neman a
tallata musu hajarsu ƙofa a buɗe take. Ga mai buƙata ya tuntuɓe ni ta wannan lambar; 08022014771.*


*LAMBA TA HUƊU.*

"Ba..ba..bai mutu ba!"

Zancen direban Hajiya kenan a lokacin da ya taɓa gefen idon Jamal, waton tsakanin ƙwayar idonsa da
kunnensa, inda ya danne wurin ya ji jijiyarsa tana harbawa ɓal-ɓal. Hakan ya sa gumin tashin hankali karyo
masa ya yi maganar a rikice bakinsa yana rawa. Shi ma Baba maigadin yana taɓa wurin ya yi gaggawar
nanata zancen cike da jaddadawa ya ce,

"Da sauran numfashinsa Hajiya! A gaggauta kai shi asibit..."

Kallon da Hajiyar ke yi wa Jamal ya ƙara tabbatar mata da gaske ne. Saboda kallon da take yi musu ya nuna
zuciyarta ta gama sarewa a kan sun yi rashin Jamal, rashi na har abada. Amma maganar Baban

Please Login or Register in order to submit comment